Uncategorized

Inaya Chapter 2 By Mamuhgee Zafafa2022

INAYAH

        (Riba Biyu)

Mamuhgee

Arewabooks@Mamuhgee

2

Dawowarta gidansu dole dakin Inna ta tare tareda innar tunda babu wani extra daki dazata zauna a gidan bayan  nan.

Karanta>>>> Babu So Chapter 2 By Billyn Abdull

Duka duka dakuna biyu ne gidan sai bandaki dake tsakar gida,

Daki daya na mama daya na innar,

Ko acan dah da mahaifinsu na raye zagayen dakuna yake,

Ita Kuma Idan Yana kwana dakin mama saita kwana a dakin Inna,

Idan a dakin Inna zai kwana saita kwana a dakin mama

Ahaka ta girma harya rasu itama akai mata aure.

Dawowarta gida wata sabuwar rayuwar zullumin kullum tashiga acikinta,

Daga Inna har mama babu Mai wata qwaqwarar sana’a,

Mamace ke Saida lallen hausa

Inna Kuma tana saida su kanwa da borkono

To tundama ta tafi taya hadizan zaman takaba sana’ar ta tafi sbd jarin ba wani Mai yawa bane dakuma hardashi suka hada duk suka cinye a can gurin zaman tunda sun shiga tsanani,

Dan haka sana’ar innace kawai yanzu take Dan taimakawa ta wani bangaren Amma kam suna cikin gararin yanayi sbd Suma dama can salisun ne yake dauke da nauyin nasu tunda nasu yayan basa taimakonsu kansu da matayensu da yayansu kawai suka sani.

Ita Inna Bata taba haihuwaba shiyasa tun take riqon hadiza tun tana yarinya gashi Kuma hadizar ce kawai mace acikin yayan mama dukansu mazane su uku,

Malam Nafi’u Wanda Allah yayi rasuwa watannin baya,

Sai Kabiru da Umar dasu kuma ayanzu kownanensu yakeda mata daddaya da yara kusan Biyar biyar,

Sai ita autarsu Khadija wadda Rashin tsayayyan manemi yasa batai auren wuriba sai data dan girma a gida sosai takai kusan shekara ashirin da takwas  kafin tasamu salisunta dasuke tsananin so da kaunar juna sukai aure ya dauke nauyin tallafawa su Inna daidai gwargwadonsa.

Daga Yaya Umar har Yaya kabiru babu Wanda  ya dauke lalaurar kula dasu mama,

Saidai idan an kwana biyu su samu Kamar dubu daddaya su Basu ko 500 Wanda sukam suke ganin kokarinsu a hakan suyita saka musu albarka duk da innar tasan basa kyautawa suna kallo Salisu ke ciyar dasu bayan Shima ba wani karfin yake dashiba kawai zuciyar alkhairi yafisu.

Yya Kabiru koyarwa yakeyi a secondary school din gwamnati dake kusa da anguwar dayake da iyalinsa 

Kusan shekara goma kenan Yana aikin koyarwar Amma babu wani cigaba kullum Yana Nan a yanda yake.

Yaya Umar kuwa sanaa kowacce yi yakeyi baida tsayayya guda daya Amma dai yafi yin ta dillancin harkar Saida filaye da gidaje Dan Yana samu sosai acikinta shiyasa yafi yya Kabiru rufin asiri,

Qarshema dai fadawa yayi siyasa sbd uban gidansa dayasashi fitowa Dan samun kudin jam’iyyar da zasu fito ta karkashinta tunda sunsan dai ba ci zasuyiba Amma sunsan jam’iyyar zata Basu kudi sosai Dan haka gadan gadan yafada siyasa baji ba gani,

Karanta>>>> Sanadin Labarinah Chapter 2 By Hafsat Rano

Yaya kabiru daya fahimci akwai samu sosai a harkar take ya marawa Umar din Baya Dan Shima ya samma masa Idan ta ‘bulle.

Itakam hadiza ganin zaman baida wata mafita

Ga Abdul ya isa sakawa makaranta tuni

Sbd abbansa koda ya rasu yanada burin sakasa makaranta alokacin,

Yanzu komai ya juye musu Kuma tanada burin bawa Abdul din ilimi Dan ya anfana rayuwarsa,

Gasu Inna da mama kullum cikin dubaru ake

Yau aci kwadon kwaki,

Gobe aci kwadon qanzo,

sai ankwana hudu ko Biyar Daqyar ake hada cinikin da zaai musu tuwon gari da miya.

Dole hadiza ta tashi ta Saida katifarta da ita kadai ta dawo da ita sai tarkacen kayan kitchen ta kwashesu takai kasuwar Yan kayan hannu ta saida ta tattaro kan kudin taraba biyu ta siyo musu abinci da kayan abincin tadawo gida.

Sana’ar kosan safe dakuma awarar Rana tafara da sauran kudin yafara juyuwa.

Kasancewar ita Inna da sauran karfinta sai tana taya hadizar aikin sana’ar musamman awarar datafi wuyar sha’ani.

Cikin ikon Allah lokaci qanqani saigashi sana’ar ta samu karbuwa sosai duk da farko taci tsananin wuyar wuta da Rashin jamaa masu siya tunda baa saniba,

Babu ranarda Bata konewa shiyasa kusan koina tagama kokkonewa hannuwa da qafafu 

Har fuska ma wani lokacin idan Mai yayi watsi.

Ba laifi yanzu basa neman komai a gurin kowa Wanda dai zasuci saidai Dan abinda baa rasaba.

Inna ma tuni dole suke komai tare sbd aikin yanawa hadizan yawa ga koko dasuke hadawa dashi yanzu da safe,

Da Rana ma yanzu ba awarar kawai sukeba harda dankalin hausa da wainar rogo.

Dole dai yanzu innace take aikin kosai da kokon safe ita Kuma tana awarar da sauransu da Rana sbd dukkaninsu aikin yayi mutsu tsananin wuya musamman tunda aikin wuta ne,

Mama ba cikakkiyar lafiyayyaceba shiyasa Basu taba barin ta shiga sana’ar ba,

Tunda mahaifinsu ya rasu haka take yau lafiya gobe ciwo,

Hawan jini da ciwon sugar ke tsananin damunta Dan haka lallabawa kawai takeyi tana rayuwar.

Ahaka hadiza ta samu ta sanya Abdul a makarantar gwamnati yafara zuwa

Kullum ita ke rakasa da qafa tadawo 

Idan antashi haka take komawa ta dawo dashi sbd akwai Dan nisa sosai.

Hutun farko na makarantar tabi taqarasa hargitsewa sbd yanda kullum saita kaisa ta daukosa ga lattin fara sanaarta datakeyi Idan taje daukosa,

Dole Inna ce take fara yimata kafin ta dawo daukosa ganin mutane sun fara janyewa ansamu wata Yar baqin cikin ta fara sana’ar a makwaftansu.

Ganin Inna ma wahalar duniya tafara sakota gaba sbd ayyukan sun mata yawa ko baccin arziki bata samu sosai dole mama ta ringa karba tanayi sbd Suma su ringa samun sassaauci tunda Allah yasa yanzu da aikin suka dogara kacokam.

Tsawon lokaci rayuwar tana yanda take garesu ba wani dogon sauyi saima ciwo daya kwantar da mama Dan haka suka sake zagewa da Sanaa ga Inna itama karfinta yayi qasa,

Ga Abdul yanzu karatun nasa yafara nisa tunda Yana aji biyu yanzu.

Karanta>>>> Farhatal Qalb Chapter 2 By Nana Hafsat

Ita kanta lafiyarta wani lokacin qaranci take mata sbd ciwon mararta har lokacin Yana taso mata akai akai gashi wani babban ikon Allah dayake kamata shine tunda tayi Bari lokacin rasuwar Salisu har yau Bata taba yin wani al’adar ba,

Tayiwa Inna maganar innar tace mata wasu matan na hakan musamman Idan suntaba samun matsala ta Bari Dan haka ko jinin Al’adar zai koma ya ringa zuwa daidai sai tayi wani auren kilan.

Da Wannan zancen ta tattara maganar Rashin zuwan Al’adar ta watsar tafara neman wata sana’ar sbd wannan din ta daina tafiya sosai sbd kusan anguwar ganin ana samu duk sun fara sana’ar shiyasa yanzu ba mutane sosai.

Ganin wata sana’ar taki samuwane 

Duk Wanda tafara Bata karbuwa gashi jarin nata tafiya gurin hidimar gidan yasa dole tafara zuwa aiki wani gida acan GRA da mama Indo qanwar Inna ta Samar mata.

Fara aikinta sai rayuwa kuwa ta sauya musu Dan yanzu da albashin suke komai.

Bata wani jimaba da fara aikin saigashi hajiyar suka tattara suka bar qasar itada ‘yayanta dole tadawo zaman gida ba wani aikin.

Jin bazata iya zaman ba aikin komaiba yasa takuma zuwa tasamu mama inda dake shirye shiryen tafiya Lagos itama aikin Sanaa tace takuma samar mata wani aikin.

“Babu wani gidan aiki Idan ba Lagos Zaki shirya ki bini ba kya ringa musu aike daga can kokuma abaki Aron kudi ki bar musu Idan munje can kya ringa biyana da kudin aikinki??”

Haka mama indo ta sanar mata Dan haka batada wani sauran zabi bayan amincewarta sbd suna cikin tsananin halin nema gskia.

Ko data sanar dasu Inna farko sunso hanawa Amma ganin yanda mama Indo tai musu bayanin aikine kawai a wani babban restaurant na masu kudi da aka bude Kuma sunada masauki Mai kyau da restaurant din suka tanadarwa ma’aikatansu a tsaftace cikin kwanciyar hankali.

Hakan yasa suka amince tareda bawa mama Indon Amanar kula da hadizar duk da ba yarinya bace.

Kudi sosai hadiza ta karba gurin mama Indo ta siyawa su mama abinci Mai Dan yawa tareda dinkawa Abdul uniforms har kala biyu da sabbin takarman zuwa makaranta da slippers harma da sababbin litattafai.

Sauran kudin taje takuma siyo musu sabulan wanka da omon wanki dasu lalle da kanwar dazasu ringa saidawa daga zaune cikin gida ta damqawa Inna sauran kudaden a hannunta.

Daga Yaya Umar har Yaya kabiru babu Wanda yayi yunqurin hanata tafiya sbd su yanzu siyasar gabansu ta ishesu shi Yaya kabiru harda tattara  aikinsa yayi ya ajiye sbd ganin sun fara samu ba laifi.

_LAGOS_

Da farko tafara Shan wuyar rayuwar garin data aikin dasukeyi sbd wani sabon hotel ne da aka bude aka daukesu aikin Dan haka wainda basajin turanci bangaren restaurant aka ajesu gurin harkar abinci.,

Farko ganin baa bacci kwana akeyi aiki yasa tafarajin zuciyarta tayi sanyi da rayuwar,

Amma ana Bata albashin farko taga irin yawan kudin sai kawai ta tattara kyuya da damuwar komai ta watsar ta zage da aiki gadan gadan.

Kasancewarta mai tsananin kokarin aiki da Amana da ladabi yasa cikin wainda aka daukesu tare watansu biyu aka qara mata matsayi tareda dauketa daga kitchen aka maida bangaren tsafta,

Ma’ana bangaren masu Kai abinci dakunan manyan Idan sunyi odar abinci Dan haka kusan yanzu hutawa takeyi sosai sai anyi odar abinci taje takai.

Gidan dasuke cikin kudinsu na albashi ake Dan tsakura duk wata ana biyan haya Dan haka hankalinta ya kwanta sosai gashi ahakan duk wata take turawa su Inna Yan canji ta hanyar Mai pos din kusada gidan nasu data baro.

Karanta>>>> Gurbin Ido Chapter 2 By Safiyya Huguma

Kwanciyar hankali da hutu da Kuma nutsuwar datake samu yasa tafara sauyawa sosai sbd abinci Mai kyau na hotel din sukeci,

Nama da kayan Dadi kala kala haka suke ci dan haka tafara sauyawa sosai,

Mama indo dai ita a bangaren abinci take har lokacin Kuma babu ranar sauyata daga gurin sbd yanda ta iya wata irin lallausan sakwara da Amala,Eba,semo

duka dai kalolin swallow babu Wanda mama Indo Bata qwareba shiyasa saka barta agurin Kuma itama ahakan ba qananun kudi take samuba sbd yanda suke tsananin son aikinta.

Hutu da nutsuwar da kwanciyar hankalin data samu tareda abinci mai kyau yasa tafara sauyawa jikinta yafara budewa da wata irin kiba,

Hasken fatarta daya jima da dafewa saigashi yafara washewa Yana dawowa,

Da farko tayi mamakin hakan Amma ganin rayuwar nutsuwar datake yasa Bata damuba saima Jin dadin hakan datai sbd tasan inshallah yanzu zata iya samun miji tayi aure tunda tayi kyan gani.

Ba laifi cikin qanqanin lokaci tasan mutane dakuma Yan tsirarrakun areas da streets sbd tana fita Yar siyayyarta

Yanzu har maganin gargajiya take siya daga nan ta aikawa mama da koyaushe take fama da jiki duk da ana cemata taji sauki din saidai yanayin muryar maman yasa ta fahimci suna fadane kawai Dan kwantar mata da hankali.

Hakama Abdul tana Dan yimasa siyayya idan zatai Aiken ta aika musu.

Tana gab da cike shekara a sabuwar rayuwarta ta Lagos ta fahimci wani babban alamari Mai tsananin ban tsoro da firgitarwa a tareda ita.

Bata tabbatarba Dan haka ta saka lokacin zuwa wani qaramin asibiti dake kusada anguwar dasuke,

Ana albashi da kwana biyu ta kwasa ta nufi asibiti a dubata sbd tabbas Idan tanaji Kuma tana fahimtar daidai motsin ciki takeji a cikinta Wanda girman daya fara yasa ta dauka kibar datayi ce Kuma hakan Wainda take taredasu suke fada tayi qiba tayi tumbi.

To me take Shirin ji ne?

Tsakanin kwanaki Biyar zuwa yanzu take Jin motsin sosai da juyi Wanda ta tabbarda cikin haihuwane kawai yake Wannan motsin.

Karanta>>>> Babu So Chapter 2 By Billyn Abdull

GA TSARIN YADDA FARASHIN SU SUKE;

ZAFAFA GUDA BIYAR 1  PAGE 1 NA KOWANNE BOOK A KODA YAUSHE INSHA ALLAH . KAMAR KO WANI YI. FARASHIN NA NAN AKAN NERA DUBU DAYA

ZAFAFA BIYAR

Littafi daya 300

Littafi biyu 400

Littafi uku 500

Littafi hudu 700

Littafi biyar 1k

GURBIN IDO

SAFIYA HUGUMA

SANADIN LABARINA

HAFSAT RANO

INAYAH

MAMUHGEE

FARHATAL QALB

NANA HAFSAT

(Miss Xoxo)

BABU SO

BILLYN ABDUL

ZAFAFA BIYAR VVIP SUITES!! WANNAN SASHI NE NA BANGAREN YAN ZAFAFA NA MUSANMAN DA KE SON KARANTA SHAFUKAN LITTAFAN ZAFAFAN SAMA DA DAYA. TO KU SHA KURUMIN KU. KUDIN VVIIP NA ZAFAFA NERA DUBU BIYAR NE KACAL NA DUKKANIN BOOKS DIN BIYAR. A KALLA A RANA ZAKU DINGA SAMUN SHAFUKA 10 KOWANNE BOOK SHAFUKA 2 KENAN.

PAY 5K FOR ZAFAFA BIYAR VVIP SUITE SECTION. MAXIMUM OF 10 PAGES DAILY, 2-2 PAGES OF EACH BOOK. MAKING 10 PAGES IN WHOLE. LITERALLY

SANNAN AKWAI TSARIN VVIP NA BOOK DAYA GA MASU RAAYIN VVIP NA BOOK DAYA KO BIYU KO UKU KO HUDU GA KUDIN SU KAMAR HAKA;

BOOKS HUDU 4500

BOOKS UKU: 3500

BOOKS BIYU: 2500

BOOK DAYA: 1500

BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK

4 BOOKS  4500

3 BOOKS : 3500

2 BOOKS : 2500

1 BOOK: 1500

MUNA TALLATA HAJOJIN KU CIKIN FARASHI MAI RAHUSA

TALLA SAMAN SHAFI

DAYA NA BOOK DAYA :1000

TSAKIYA 800

KARSHEN SHAFI 500

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

BANK NAME: ZENITH BANK

ACCOUNT NAME: HAFSAT UMAR KABIR

ACCOUNT NUMBER: 2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:

07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA DA SHEDAR A TARE:

09134848107

#MAMUH#

#LOVE#

#ROMANCE#

#ZAFAFABIYAR#

Back to top button