Novel Document

Cutarwa Complete Hausa Novel Document

Cutarwa Complete Novel By Ayshercool

Description/Story:

Cutarwa! Complete Hausa Novel Document Written By Ayshacool

 

Description

Gagarawa Jihar jigawa.

Kasancewar wata ya nausa, domin kuwa watan jumada ula, ya kai kwanaki ashirin da biyar, wanda yake dai-dai da watan Nuwambar shekarar miladiya.

Mislain ƙarfe biyu da rabi, dare ya tsala, duhu ya mamaye ko ina, baka jin sauti ko motsin komai, sai kukan ƙananan ƙwari, da sautin busassun ganyen bishiyu, da iska ke kaɗawa lokaci zuwa lokaci.

A dai-dai wannan lokacin da kusan galibi mutane ke kwasar bacci, ni kuma har a lokacin idon ta tamkar an soya, babu alamar bacci a tare da idanun nata, sakamakon bushewar zuciya da raɗaɗi da take ji.

Sai yau ta tabbatar da  cewa, nutsuwar zuciya, da kwanciyar hankali, da ƙarancin tunani, suke haɗuwa su haifar da daddaɗan bacci, mai cike da annashuwa.

A hankali ta tashi daga kan katifar da take kwance, na nufi tagar ɗakin, ta buɗeta, wani sanyi ya daki fuskarta, ta kalli ƙaton tsakar gidan, da baka iya gane komai a cikin sa, saboda duhu.
Ta ɗaga kanta,  ta kalli taurari, yadda suka yi wa sararin samaniya ado, ƙudura da iko na Ubangiji na riƙe da su a sama.
Tayi ajiyar zuciya, tare da kamanta rayuwarta da wannan baƙin daren, mai cike da duhu, da ban tsoro.

A lokacin da karin maganar bahaushe ya yi amsa amo, a tsakanin ƙabilar ta hausawa, na cewa dauɗar gora ciki ka sha ta, sai dai kash! Zamani ya zo mana da cigaba, ta hanyar nuna mana muhimmancin lafiyarmu.
Duk da cigaban da aka samu, hakan bai hana a tauye ta ba, a shayar da ita dauɗar gorar ta ƙarfin tsiya ba, wanda hakan yake CUTARWA! Domin kuwa ya zame mata tamkar guba, domin ya zama silar sanya mata ciwon da take ta fama da shi, ta rasa maganin sa, wanda tun yana ɓoye, sai da ya fito yayi tsiron da mutane suke yi mata tambari da shi.
Haka zalika, azancin hausawa na ciwon ƴa mace na ƴa mace ne, ya samu gindin zama a da yawa daga bakunan mata, sai dai ita a nata ganin, ciwon ƴa mace, na ta ne ita kaɗai. Wataƙila ko a cikin ta ta rayuwar ne Allah bai sa ta yi katari da waɗanda ciwon ƴa macen yake zama nasu ba.
Duk iya ƙoƙarin da ta yi wurin haɗiye yawun bakinta, ta kasa, saboda bushewar da bakinta yayi, wani irin zafi zuciyarta ke yi mata, wanda ya haddasa numfashina fita cikin huci.

A hankali ta furta “Me ya rage? Tun da duniya cike take da rikici, da tarin ƙalubale, kowa kansa kawai ya sani, kuma kuɗinka shi ne mutuncinka, tabbas! Tura ta kai bango, na ɗaura aniyar fito na fito da duk waɗanda suka cutar da ni. Tun da babu sani babu sabo, dole in fasa ƙwan da warinsa ka iya sanadiyyar tarwatsewar zumunci, idan ya so na gani, ko suma suna iya jure ɗaɗɗake dauɗar gorar a cikin su, kamar yadda suka yi mini, daga nan na ƙara gaba, na basu wuri tare da gwagwarmayar nemawa kaina mafitar rayuwa.

*****
La’asar sakaliya, wata matashiyar mace ce da ba zata gaza shekaru sha takwas a duniya ba, zaune a ƙaton tsakar gida, tana ta ƙoƙarin tsince waken da zata daka, ta zuba a cikin miyar yauƙin da take yi, cinyarta wata yarinya ce ƴar kimanin shekaru uku da rabi a duniya a kwance, ta saka babban ɗan yatsanta a baki ta na sha, hannunta ɗaya kuma tana wasa da cibiyarta.
Idan ka kalli yarinyar sau ɗaya, sai ka sake kallonta, tare da son sanin daga wace ƙabilar wannan yarinyar take?.

Baƙa ce sosai, mai ƙiba, tana da ɗan goshi, sai dai yalwataccen gashin girarta ya rage fitowar goshin nata, tana da manyan idanuwa farare, sai dai ƙwayar idonta brown ce, maimakon baƙa, bakinta ɗan cukul, sai dai laɓɓanta jawur, tamkar an saka mata jambaki. Babban abun da zai baka mamaki, bai wuce yadda take da dogon gashi ba, baƙi wuluk, mai tsayin gaske, ba curkukuɗaɗɗe irin na baƙaƙen fata ba, tamkar gashin larabawa, kalba aka yi mata guda biyu, amma ta saukko har cikinta, hancinta ba shi da wani tsawon kirki, saboda kumatu ya shanye su.

“Wai Mariya ba zaki ajiye wannan gunsumemeiyar yarinyar ki mayar da hankali ki kammala aikin nan ba. Kawai kin ɗauki ƴa kin narka a cinya ƴa ba kaɗan ba ko nauyi ba kya ji? Na ga dai ba nono za ki bata ba”

Mariya a ranta ta ce ‘Ban da abun iya, ta yaya saniya za ta gaza da ƙahonta?’

A zahiri kuwa cewa ta yi “Yanzu zan kammala iya”

“To ki ajiyeta ta shiga cikin yara tayi wasa mana, wannan uwar matan ta zauna a cinya, kema ki haihu ki yi mata ƙani, kin naɗe kin ƙi haihuwa, kiyi ƙoƙari dai ki haifo wani, ko Allah ya sa a samu mai ɗan dama-dama, wannan ƴa muninta yayi yawa, Ko da yake can danginku ta kwaso wannan baƙin da muni, barebari ai haka ku ke baƙi kamar zunubin mutanen farko”

Mariya ta sunkuyar da kai tayi shiru, ta na jin zafin maganganun nan, amma ba yadda ta iya, haka ta ƙaƙalo murmushin dole, ta ce “Hajiya iya kenan, jikar nan taki mamaki zata baki, idan ta tashi kawo miki siriki, mai maiƙo za ta kawo, wanda zai kai ki makka”.

Iya ta furzar da goron bakinta ta ce “Da wannan baƙin da munin? Maza na rububin farar mace, wa zai kwashi kayan muni, ai ko wannan idon nata, ya isa hanata auruwa, ido abun tsoro kamar ragowar maita, sai ido furi-furi kamar bururrun gawayi”

Sake kwanciya yarinyar ta yi a jikin uwarta, tare da kawar da kanta gefe.

Mariya ta shafa kanta ta ce “Ummina, ki tashi in haɗa abinci, kar yayyenki su dawo ban gama girki ba, ki tashi ki je ki yi wasa da su Auwwalu”

Noƙe kafaɗa yarinyar tayi, tana tura ɗan mitsitsin bakinta, ta sake gyara zama ta mayar da hannunta baki.

Sallamar da aka yi ne, ya sanya su haɗa baki wurin amsawa.

Sai dai ba ƙaramar razana ta yi ba, da jin muryar mai sallamar, dan sai da tayi wani zillo ta tashi zaune, wani ɗan matashin saurayi ne, hannunsa riƙe da wata ƴar jaka.

Iya ta ce “Ahh, idris ka dawo?”

“Eh, an gama abinci ne?”

“Ina fa, tana nan tana laƙai-laƙai tana fama da wannan jibgegiyar yarinyar, ita ba nono za ta sha ba, sai iskanci da taɓara dan sangarta”.

Ya kalli yarinyar ya ce “Ummi, zo mu je na sai miki biscuits, ki bari anty ta gama mana girki”

Maƙale hannunta tayi, tana zazzaro ƴan idanunta, da tsoro ya bayyana ƙarara a cikin su.

“Ummina, dan Allah ki bi yaya idris, in kammala aikin nan”

Hawaye ya cika mata ido, tana kwantar da kanta a jikin mahaifiyarta.

Ya miƙa hannu zai ɗauke ta, ta fashe da kuka mai kama da na shagwaɓa, amma a zahiri na tsoro ne.

“Kai dalla ƙyale mata ƴar ta, dan ta samu za a ɗauke ta, ji iskancin da take, ita shagwaɓar ma ba kyau take yi mata ba, aba ba kyan gani kamar turotso”.

Ta ƙarfin tsiya ya saka hannu, ya ɗauketa, tana ta kuka, mariya kuwa cikin kara da kawaici, ta tashi tana cewa “rigimammiya sam ba kya girma”.

Ya fita da ita a kafaɗarsa, bai tsaya a ko ina ba, sai wani sashi na gidan, a ƙofar wani ɗaki da ba kowa a sashin, yanayin wurin zai nuna maka wurin ɗakin ƴan maza ne.

Ya buɗe ɗakin ya shiga da ita, yana zuwa ya dungurar da ita a tsakar ɗakin.

“Rufe mini baki, ko na shaƙe ki, ki mutu” cikin sheshsheƙa take ƙoƙarin danne kukan nata, gaba ɗaya ta burkice cikin matsanancin tashin hankali.

Ya bankaɗa gefen wata katifa, ya ɗaukko almakashi, ya durƙusa a gabanta ya ce “Kin gaya wa mamanki ko?” Ta girgiza masa kai, hawaye na zuba daga idonta, ga ƙoƙarin haɗiye kuka da take yi tamkar zata shiɗe.

“Kin faɗa ko baki faɗa ba?” Ta sake girgiza masa kai cikin razani.

“Duk ranar da ki ka faɗa, sai na gutsutstsura namanki da almakashin nan, na zuba a leda na kaiwa karen namadi, ya cinye ki, kuma sai na saka ki a murhun da babarki take girki, ai kin taɓa ƙonewa kin san zafin wuta”

Ba ta iya cewa komai, sai bin sa da ido, hawaye na zuba daga idonta.

Ya ajiye almakashin, ya janyo ta, ya fara ƙoƙarin cire ƴar doguwar rigar jikinta.

Sake fashewa ta yi da kuka, har da ɗan ƙara sauti, aikuwa ya zare mata ido, ya shaƙeta ya ɗaukko almakashin, ya saita tsinin a maƙoshinta, jikinta na rawa ta yi gum da bakinta.

Kamar yadda ya saba ɗaukkota yayi mata, haka yau ma idris yayi mata, sai da ya gama abun da Allah ya nufe shi da yi, sannan ya ƙyale ta, sai dai bai taɓa gangancin ƙetara ta ba.

Ya cigaba da yi mata kashedi, tare da firgita ta, a kan idan ta faɗa, sai ya sakata a murhu ya babbaketa.

 

File Name   Cutarwa… Hausa Novel Doc.
Title    Cutarwa 
Author    Fatima S. Omar
Group    Ai  Hausa Novels
Genre    Fiction Story
Published Date    11/05/2024
File Size    950Kb
Format Size    TXT
Phone No     08081012143
Download Cutarwa Complete Novel Document By Ayshercool

Click the below green button to read the novel online

 READ THE NOVEL


Proceed with your download by clicking the below button

 

 

Be With Us

 

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Back to top button