Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 52 By Hafsat Bature

💋KURKUKUN ƘADDARA💋

E52

Daga alƙalamin Boss Bature❤

Ita ko Unaiza ƴar gidan daddy ta ce musu ba zata ci ba saboda a gidansu saman dining table ake jera mata abinci kala goma sha biyar, sai ta za6a ta darje, hatta abincin ma abaki masu aikin gidansu suke bata tana ci” gaba ɗaya ta rikita su da maganganunta, sun gaza gane inda ta dosa,

Duk yadda suka so su lallasheta akan taci abinci taƙi ci, tace musu dole a kira kukun da suke girƙa abinci a makarantar ta, don ta faɗa musu kalar wanda ake girka mata agidan daddynta, idan har suna son zaman lafiya, idan ba haka ba zata yi magana da shugaban makarantar yayi musu magana, ” Su angel sun sha dariya kamar zautattu jin wani sokiburutsi na Unaiza, Sun maida ta mahaukaciya, ta zamar musu tamkar Comedy, kuma ita har ga Allah dagaske take basu Umarni, Rashin sani yafi dare duhu.

Lokacin da dare Ya tsala, Babu wanda Ya runtsa acikinsu daga su har sabbin prisoners ɗin saboda rigimar Mahaukacin yaron nan MAJNUN! ya addabi rayuwarsu tun da ya farka daga bacci, Ya dinga Tsalle tsalle har saman gadajen su, Ya hanasu sakat, Su azeeza sun sha kuka saboda ƙululun baƙin cikin daya dasa musu, Har bugunshi suka so suyi amma Danish ya hana su, ya basu haƙuri akan kada su ta6a shi yaro ne, ba dan sun so ba suka Haƙura suka ƙyale shi, Taimakon da Allah yayi musu yaron baison duhu, Sun gane hakan ne lokacin da Danish Ya sauko daga saman gadonshi yaje ya kashe floor lamps ɗin ɗakin, Duhu ya gauraye ko’ina, ai kuwa ya birkice musu ya dinga kuka yana fadin su taimaka mashi, dodo zai cinye shi, angel tace munafuki ai kaine dodon daka addabi rayuwarmu ashe kana magana, nayi tunanin kurma ne kai.

Daƙyar Danish Ya ruƙo hannun shi Cikin duhu Ya kai shi saman gadonshi ya haye Yana faman sauke ajiyar zuciya, ganin ya samu natsuwa ne, ya tambaye shi ya sunanshi, Muryarshi adisashe ya ce”CHINONSO” jinjina kai Danish yai kafin ya miƙe ya rufa mishi bargo saman Jikin shi.

A washe garin ranar da aka kawo musu sabbin prisoners, lokacin Da Giants suka zo kawo musu Abinci, Sun ga haukan da basu ta6a gani ba, wato unaiza ce ta tsare giants tana zazzaga musu masifa akan su bi tsarinta, na gidan daddynta, hada ƙoƙarin ɗauko jotter acikin school bag ɗinta tare da biro ta rubuta musu list na abunda take so adinga girka mata tana ci, bayan ta gama ta je gaban su ta miƙa musu paper ɗin data yago cikin jotter din, tace dasu su kar6a, Kamar gumaka babu wanda ya motsa a cikin su,
Su haris suna ta ƙoƙarin fahimtar da ita akan ta matsa daga gabansu basa magana, amma taƙi sauraransu, ba don Allah yasa Naufal Yaje ya janyeta ba, da ranar ta yabawa aya zaƙinta, don wlh mazga zata sha awurin su, don basa ɗaukar raini.

A taƙaice Cikin kwana uku sai da suka fita hayyacinsu, Akan mutun biyun nan Unaiza ƴar gidan daddy da kuma Majnun Chinonso,

Wata sabuwar rigima ta unaiza, ta faɗa musu cewa ita fa Ta saba agidansu masu aiki suna yi mata tausa, don haka suma dole suyi mata, Kuma idan zata kwanta bacci, Da pillow uku take kwana saman gadonta, ta saba duk in zata kwanta, tana ɗaura kanta saman pillow, ɗaya kuma A tsakankanin ƙafafuwanta, Cikon na Ukun A ƙirji take rungume shi, Ba tare da sun yi mata musu ba, Su Parveen su ka yi mata tausa, Lokacin da dare ya yi Danish da Mubeen suka bata pillows ɗin su don ta kwanta kamar yadda ta saba yi agidansu, Idan fa tace su yi mata abu su ka ƙi yi mata, Kamar ƙaramar yarinya haka zata zauna tana raira musu kuka, waya ga shagwa6a66a

Haris yace”Su ƙyaleta Ai wadda tafita iya masifa tazo kuma ta miƙa wuya sun yi rayuwa da daɗi da ba daɗi balle kuma ita, ” Wato yana magana akan angel, sai dai fa akwai banbanci sosai tsakanin Angel da Unaizah.

Ranar da haƙurinta ya ƙare, ganin anƙi yi mata abunda take so, Tace musu zata kashe kanta, a lokacin sun ɗauka wasa take Yi ashe dagaske take, dama irinsu basu Cika imani ba, basu da tawakkalli, gata dai da sunan musulmai amma babu musuluncin acikin zuciyarta,

Suna zazzaune acikin ɗakinsu kamar masu zaman makoki, ba zato ba tsammani suka soma Jin Ihunta Acikin Toilet, Da gudun gaske suka faɗa Sashen makewayin nasu, sai dai koda suka isa ta datse ƙopa, Suka dinga bugu taƙi buɗe musu, Danish ne ya bugi ƙopar da hannayenshi nan take ta buɗe, Suna Shiga Ciki suka same ta kwance Ƙasa Tana burgima, gefenta ledar detergent ce da tasha duk don ta kashe kanta, Rai a6ace Danish yasa hannu ya damƙo damtse hannunta, ya ɗago da ita, tana ta faman shessheƙar kuka, Da gwiwar hannun shi ya daki bayanta, gaba ɗaya saida ta amayar da abunda tasha kaf ɗinsa, cikinta kamar zai 6alle saboda ɗamewar da yayi, Idanuwanta su kayi luhu luhu, Saboda tsabar kuka hada majina ta hanci ta baki,

Angel ce ta taimaka mata wurin wanke mata fuskarta, ta kuskure bakinta, kafin ta ruƙota ita da hanna suka shigo da ita Cikin ɗakin a saman gadonta suka kwantar da ita, sai nishi take yi, launin idanuwanta sun ciza, daga gani tana acikin mawuyacin hali, zazza6i ya rufe jikinta ta ko’ina, A kewaye da gadon Su angel suka zazzauna tare da Danish, Sauran Ƴan uwan nasu suna atsaye suna kallonta,

“Yanzu idan kika kashe kanki wa kika yi ma asara”? Haris ne yai mata maganar, saboda ƙarfin hali tace mashi”bansani ba, Ni ba ruwana da kowa, Ku ƙyale ni ku bar ni inyi rayuwata, Na tsani ganin ku, bana son Zama acikin ku, i just wanna Go home” Jinjina kai su ka yi, Haris ya kuma cewa”kin ɗauko ta da zafi, Ae duk wanda ya shigo kurkukun ƙaddara, To ya shiga kenan ba hanyar fita, Zaifi ki kwantar da hankalin ki, Ƴar gidan daddy ki yi rayuwarki Cikin salama, kamar yadda kika ga muna yi,”

Wani irin kallon harara ta dinga jefa ma haris da yae maganar, Cikin harshen turanci ta zazzage shi tas hada yi mishi sharrin halittarshi wai baƙi mummuna kamar buri, A fusace Deeja ta ɗaga hannu zata kwashe ta da mari Danish yai saurin ruƙo hannunta, Suka haɗa ido ya girgixa mata kai alamar karta mare ta, zame hannu deeja ta yi yayin da take kallon Ƴar gidan daddy dake kwance saman gadonta, Wani irin kallon tsana take binsu dashi, angel tace”duk wani abu da kike taƙama dashi muma muna dashi, Idan hasken fata ki ke taƙama dashi Muma duk farare ne balle kice xaki nuna mana wariyar launin fata ehe, Sannan kuma idan gashi ne ki kalli kaina da kyau, Nesa ba kusa ba, Nafi ki tsayin gashi da yawa, haka zalika idan launin ƙwayar ido ne, Na ki blue nawa Gray, Idan wayewa ce, yadda kike taƙama da daddynki, Nima haka na taso Gidan daddyna, Yana gatanta ni duk da bamu da ƴan aiki kamar yadda kike faɗin akwai su a gidan ku, Shawarar da zan baki shine idan har kina son xaman lafiya to kija baki kiyi shiru ki rungumi ƙaddararki, Bawai kice xaki ƙi cin abinci ba, ko ki ce zaki kashe kanki, Domin kuwa babu wanda ki kayi ma asara face kanki. hatta shi daddyn naki da kike taƙama dashi Yana can hankalin shi kwance ya sadaukar dake zuwa ga rayuwar ƙunci da takaici, saboda ya samu abunda yake so………” tun da angel ta doma magana, Ƴar daddy ta zazzaro idanuwanta akan fuskar angel, duk da bata fahimci abunda take nufi ba amma ta shiga ruɗani sosai, Muryarta na rawa tace”Naji kince daddy na ya sadaukar dani what does that mean”? Angel na ƙoƙarin yi mata bayani, Danish yae mata gyaran murya nan take ta fahimci me yake nufi, Wato kada ta faɗa mata.

A tsanake Danish Ya soma yi mata magana

“Yanzu baki da ƙoshin lafiya, ga shi ko abinci kin ƙi ci, why? Ki faɗa mana me kike so muyi maki wanda zaisa ki saki jiki damu” yanayin yadda yake yi mata magana cikin sigar lallashi ba ƙaramin fusata angel yae ba ganin yadda Unaiza ta tsare shi da idanuwanta har wani lumshe su take yi akan fuskarshi, cikin shagwa6a tace mashi”indai zai bata abaki, zata haƙura taci abincin ko ba daɗi” sakin baki angel tai tana kallonta,

Shi ko hada ruƙo hannayenta acikin nashi, saboda jin ta amince indai zai bata abaki, yace mata”ae ba wani abu bane, fiye da haka ma zai iya yi mata, indai zata saki jiki dasu ta xauna batare data ƙara yunkurin kashe kanta ba”

Tun kafin ya rufe baki, Ta miƙe zaune tana faman cizon la66anta, Su haris su ka baza ido suna kallon ikon Allah, duk wannan budurin da suke yi, Majnun yana kwance daman gadonshi yana bacci, Shiyasa suka samu salama.

Hankalin Angel fa ya tashi ganin Unaisa ta kwantar da kanta saman ƙirjin danish, Hada sanya hannu biyu ta ƙankame shi, tana faɗin”In dai ya ɗaukar mata alƙawarin zai yi mata komai take so, to zata daina tunanin kashe kanta, kuma zata xauna dasu lafiya” tana magana tana tura mashi ƙirjinta ana shi, tsabar takaici Ya hana angel buɗe baki tae mgana, Ba ita ba hatta su Hibba sun lura da irin yadda take matse jikinta dana Danish, Lamarin ya ɗaure musu kai matuƙa, sai kace ba ita bace take ƙoƙarin kashe kanta ba, ta zaƙe sai zuba ma Danish shagwa6a take yi, ba lallai su fahimci me take so ba, saboda su awurinsu bawani abu bane don mace ta haɗa jikinta da na Namiji shiyasa basu kawo komai aransu ba, shi kanshi Danish ɗin Bai janye ta daga Jikin shi ba, Duk da atsorace yake da irin mugun kallon da angel take jefa mashi, Ta riga ta gane ainihin wacece yarinyar, tantiriyar ƴar iskace tazo musu da bidi’a……

(Yakamata angel ta koya mata Sunnah🤣)

Har wani ƙara narke mashi take ji ajikin shi, duk hakan bai ishe ta ba, sai da ta zagayo da hannunta ta bayan shi ta ɗaura yatsun saman gaban trouser dinshi, runtse ido angel ta yi don bazata juri kallonsu ba, Su mubeen hada cewa”tun da ta amince zai bata abincin a baki, Aje a ɗauko food basket ɗin,” da sauri parveen tabar bakin gadon unaiza taje ƙarƙashin gadon batool ta ɗauko kwandon abincin da suka rage mata, sai da ci rabon ta kamar yadda ta saba kafin ta miƙe ta koma wurin su ta miƙa ma Danish kwandon Yasa hannu ɗaya ya kar6a Ya ɗaura shi daga gefe saman mattress ɗin.

shi kan shi a takure yake da irin yadda take matse shi da hannunta, hada nishi take saki tana cizon le6enta na ƙasa da teeth ɗinta, zuciyar angel sai tafarfasa take yi sam bata so su haris su fahimci cewa Tana Kishin Danish ne, ko shi Danish ɗin ya gane cewa ta damu dashi, duk da ita har ga Allah babban abunda take gudu shine yarinyar ta gur6ata musu tunaninsu, cos daga gani yarinyar ba ƙaramar tantiriya bace, ga dukkan alamu ta saba bin maza, shiyasa ta gaza jurewa take manne mishi duk don ta samu a bunda take so, hakan kuma ba zai ta6a yiwuwa ba, muddin tana numfashi, yanzu ma tayi shiru ne don taga iya gudun ruwanta…………….” muryar unaiza ce ta sa angel buɗe idanuwanta da suka kaɗa suka canza launi, ashagwa6e take yi mishi magana tana faɗin”ni bana so kana sanya min dayawa, a hankali za ka dinga tura min a baki, ko so kake baki na ya ƙara girma” tana magana tana kallon idanuwanshi cikin shauƙi, babban takaicin angel taƙi cire hannunta daga gaban trouser ɗinshi, har wani murza wurin take yi da hannunta, bawan Allah duk ya rikice ya kasa ɗagowa ya kalli fuskar angel, Su haris kuwa ganin ta fara cin abincin yasa suka bar bakin gadon, Ya rage saura su uku, Unaiza da Danish dake bata abinci abaki sai kuma angel da ta Zabga uban tagumi tana kallon su, abun duniya ya ishe ta.

Kamar jira take Danish Ya kammala ba Unaiza abinci, Ta ruƙo Hannun shi acikin nata, Ya ɗago suka haɗa ido, babu wasa akan fuskarta tace”Tashi muje” kallon harara ƴar gidan daddy tayi mata tare da cewa”Wai ke ina ruwanki dashi ne? Na lura Kin sanya mashi ido, kowa yabar ni dashi sai ke”? Jinjina kai angel ta yi batare da ta tanka mata ba, Saboda gani take ma 6ata baki ne yin magana da ita, muryarta da tsiwa tace da Dashi ba zaka tashi ba”? jiki na rawa ya sauko daga saman gadon, sai da ta fara ɗaukar kwandon abincin, kafin taja hannun shi suka nufi nasu gadajen, A ƙasa ta sauke kwandon kafin ta kalle shi duk ya wani sha jinin jikin shi kamar mara gaskiya

“Ka kwanta ka yi bacci” shaking head ɗinsa yae tare da cewa”bana jin bacci” harara ta jefa mashi”ƙarya ka ke yi, ni naga bacci a cikin idanuwanka, don haka dole ne ka kwanta ka yi bacci,” Lamarin ya ɗaure mishi kai, Jin yadda ta dage akan sai yayi bacci bayan yace shi bai jin bacci, hannayenta biyu ta ɗaura saman fuskarshi, yayin da suke kallon juna, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”Danish ka kwanta kayi bacci nace, bana so na sake maimaita ba” ganin yadda yanayin ta ya canzane yasa shi ce mata toh, zai kwanta amma indai ta amince zata kwanta suyi baccin atare, tace mishi ta amince, ba tare da 6ata lokaci ba, ta hau saman gadonta ta kwanta tana fuskantar shi, yayin da shima ya kwanta saman nashi gadon, suka cigaba da kallon juna, da zarar taga zai gyara kwanciya muryarta har shaƙewa ta ke yi wurin furta mashi kada ka motsa, duk don saboda kada ya ɗaga kan shi su yi tozali da Ƴar gidan daddy.

Kamar tasan kuwa Idonta na akansu, sai faman cizon le6e take yi don ba haka taso ba, taci buri akan Danish, guntun tsoki taja tare da cewa”Ba dai muna a ɗaki ɗaya dashi ba? Zan nuna maki shaiɗanci, zakisan koni wacece, Saina lalata shi ta yadda bazai Iya samun sukuni ba in har baiji ni ajikin shi ba” ta kai ƙarshen zancen zucin nata tare da sakin murmushin shaƙiyanci, ta ɗaura kanta saman pillow, tana shafa tudun ƙirjinta da yatsun hannunta.

“Haris banji daɗin abunda yarinyar can ta furta akan ka ba, Allah naso ace Danish ya ƙyale ni na wanka mata mari data gane bata da wayau, wawiya kawai, Ni bata birgeni ba, ƙyamarta ma nake ji” deeja ce tai maganar yayin da suke zaune saman beds ɗinsu, ta6e baki haris ya ɗanyi tare da cewa”Ni banji komai ba Deeja, Na yi mata uziri ne saboda bata da hankali, kuma ban ji haushin kalaman da ta faɗamin ba saboda kina ƙaunata, kuma baki ta6a kushe ni ba” wani irin ƙayataccen murmushi deeja ta saki jin abunda haris yace mata.

“Nifa awurina, hatta Danish kafi shi kyau Allah,” dariya haris yasaki yana faɗin”Anya kuwa Deeja, Danish fa kika ce? Ɗage mashi gira tae tare da cewa”wallahi dagaske nake, tabbas Danish kyakkyawane sosai, Yafi ka nesa ba kusa ba a idon kowa amma banda nawa, Ni kai kawai nake ganin kyanka, Yadda kasan fure”

Saboda tsabar jin daɗin kalamanta, Haris hada ɗaukar pillow ya rungume a ƙirji yana dariya.

Yayin da su deeja suke Nan suna shan fira ita haris, Su parveen suna acikin toilet su shida kewaye da tukunyar fulawar nan, Duk sun zuƙunna suna kallon furennin, da alama Gulmace ta ciyo su abunda basu ta6a yi ba, abun ne Ya tsaya musu aransu, Ya hana zuciyoyin su sakat, Lamarin ƴar gidan daddy da Majnun Yasha musu kai,

“Wlh an cuce mu, Sai daga baya na dinga regretting kawo mana waɗannan Ciwon kan da zazza6in, mahaukacin yaron nan duk yadda na ƙwallafa rai akan son Cin cake ɗin nan saida ya lalata shi, Har Yau na gaza manta suffar ƙaton cake ɗin acikin idona” Parveen ce tai maganar rai a6ace,

Azeeza tace”Allah ni sai naji dama ba’a tafi da ƴar uwar Namijin nan ba, menene ma sunanta?

Ta kasa faɗan sunan saboda yae mata wahalar furtawa, Hannace ta taimaka mata wurin cewa “Ni kamar Gabriella naji yace, shi kuma Gabriel, Allah yafi sauran hankali da natsuwa, babu ruwanshi da kowa ko surutu baiyi, yanzu haka yana can kwance saman gadon shi, tausayi ma yake bani, hakanan an raba shi da ƴar uwarshi”

Hibba tace”Ae itama Sarah babu ruwanta, matsalarta ɗaya, ƙorafi kullum sai ta ma mutane ƙorafi akan gado yae mata ƙanƙanta ita ala dole ga me tsawo, Ni fa duk wannan Ƙaramar yarinyar tafi burgeni, Menene ma sunanta”? Tae tambayar tana kallon sauran, Rubina tace”Jar miya take da suna ko jimina namanta, nima tana burgeni, babu ruwanta, ita indai zata samu abinci, taci ta ƙoshi gado take hayewa ta naɗe abunta, sai in zatayi wanka, acuɗa mata baya shine kawai damuwarta,”

Ta6e baki yasmin ta yi, tsegumi ya samu wurin zama a prison, ƴar daddy tazo da bidi’a.

“Ni haushina wannan Figaggar yarinyar, wuyanta kamar na cokali mai yatsu, Tun da tazo take ta Turo mana abubuwanta, Allah ji nake kamar insa hannu in matse su, su fashe kowa Ya huta” dariya suka saki gaba ɗayan su jin abunda yasmin tace, Cikin zolaya eve tace”Na lura baƙin Ciki kuke mata don kun gansu tubarkalla ba kamar naku ba, ” harara suka watsa ma Parveen da ta yi maganar, Hanna tace”Allah ya kiyaye me za muyi wa baƙin ciki? da alama kin manta a ina muke ne! Ae ba a tunƙaho da kyawun sura a gidan kurkukun ƙaddara, wlh ba fata nake mata ba, amma duk ranar da ta kuskura giants suka ɗauke ta, bana tunanin zata dawo da ƙirjinta yadda su ke”

Gaba ɗaya Sun shagala suna ta zuba ɗumi, babu wanda ya ji takun tafiyarta, ashe ta shigo Cikin toilet din da alama taji suna gulmarta ne, shiyasa ta faɗo musu, Kamar daga sama suka ji zazzaƙar muryarta ta karaɗe kunnuwansu

“You gossip about me because you’re jealous, wow,”

(Masu so karanta middle Step book 2 whatsapp suyi min magana 08103884440 masu son facebook paid group Ga link ku danna shi za kaiku ga wadda zaku yi ma msgana👇)

 

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

 

 

( mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, masu yi mun ya jiki ina godiya)

Back to top button