Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 32 By Hafsat Bature

💋KURKUKUN ƘADDARA💋

takun farko🌹

Dedicated to aunty kubra❤

E32

daga alkalamin Boss bature writer of Abban sojoji✍️

Tun daga ƙasa har sama su Angel ke binsu da kallo, Yayin da giants suka Wuce Cikin ɗakin zuwa Inda Dining carpet ɗinsu Yake, Bayan sun ajiye masu dinner ɗinsu, Batare da 6ata lokaci ba, Suka fuce daga Cikin ɗakin,

Atare Suka kalli juna ita da danish fuskokin su da alamaun mamaki, ga dukkan alamu basu gane su wanene ba, duk sunyi tsammanin Ko sabbin ɗauka ne aka kawo musu acikin kurkukun,

“Danish su wanene ko ka gane su”? Girgixa mata kai Yayi alamar a’a, Jan hannunshi Tayi”muje mu gani,” Tayi gaba Yabi Bayanta, Suna ƙarasowa bakin benan Inda suke atsaye, Ta haska fuskokinsu da fitilar Hannunta, Ras taji gabanta ya faɗi, da ƙarfi ta ambaci sunayensu”PARVEEN! RUBINA! DEEJA” sai da ta kira sunayen su Tukunna danish Ya gane cewa sune, Sunyi matuƙar girgiza da yanayin da suka Yi tozali da ƴan uwan nasu, Sam sun kasa Yi masu magana, Fatar Jikinsu Tayi haske sosai, Fuskarsu tayi jawur abunka ga farar fata, Idanuwansu duk sun kumbra suntum ga dukkan alamu ba ƙaramin kuka su kayi ba, Kayan jikinsu sun yi uban squeezing Kamar waɗanda aka kwato daga Bakin kura, Sumar Kansu Kuwa Ta hargitse ta fita hayyacinta, kai kace sabbin mahaukata ne, Kwata kwata babu natsuwa atare dasu, Yatsun hannayensu dana ƙafafuwansu sae kerma suke Yi, kamar waɗanda sanyi yayi ma mugun kamu, Tsabar ruɗu Ya hana Angel da danish su furta wani abu, Duk irin Zumuɗin da suke Yi nasan adawo musu Da ƴan uwansu Jikinsu Yayi laƙwas, domin kuwa ba haka suka tsammaci ganinsu ba, wani tashin hankalin ma La66ansu dake a bushe sun faffashe, hada busasshen jini ajikinsu,

Muryar angel cikin damuwa ta ambaci “Innalallahi wa’inna ilaihirraji”un! Parveen! Deeja! Rubina! Meya faru daku? Meyasa kuka canza har haka? Dan Allah kuyi mini magana, Me akayi maku? Duk kun canza kun rame kun fita hayyacin ku,” Idanuwanta acike tab da kwalla ta yi maganar, hawaye ne masu ɗumi suka soma gangarowa akan fuskokinsu, Lokaci ɗaya suka fashe da matsanancin kuka mai tsuma Zuciya, hankalinsu danish Yayi matuƙar tashi, Koke koken Da suke Yi ne Ya yi silar farkawar su Batool, har cikin kunnuwansu sautin kukansu parveen ke kai musu, Aikuwa Jiki na rawa suka Yaye bargunan da suka lullu6a dashi, Da gudun gaske Suka nufi wurin su ɗaya bayan ɗaya suka ƙaraso bakin stairs ɗin banda mutun ɗaya, Azeeza dake fama da lalurar makarantar dare, Ta farka daga bacci amma bazata Iya kawo kanta inda suke ba,

Koda su Batool Suka ɗaura idanuwansu akan fuskokinsu Parveen, wani irin farin Ciki ne Ya bayyana akan fuskokinsu, Sam basu Lura da yanayin da suke Ciki ba, Saboda tsabar murna Batool ta cakumo deeja da niyar ta rungumeta aikuwa Ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara, wadda tayi matuƙar girgizasu, da sauri Danish ya sanya hannayenshi Saman Ears ɗinshi Ya toshe su gudun kada lalurar shi ta motsa, aruɗe suka haɗa baki suna tambayar lafiya meya faru dasu? Meyasa su ke Kuka? maimakon suga farin Ciki akan fuskokinsu,

Muryar batool a sanyaye tace”deeja meyasa kika saki ƙara saboda ina ƙoƙarin Rungumarki ajikina? Ba ku yi farin Ciki da dawowa Cikin Mu bane”? shiru babu wanda ya amsa mata acikinsu sai kuka suke Yi, Yasmin tace”Na lura gaba ɗaya ma basa acikin hayyacinsu zaiyi wuya ace sun gane mu” javed yace”pls Stop shedding ur tears kuna ƙara tayar mana da hankali, meyasa duk kuka canza? Tsohuwa ta faɗa mana cewa kuna acikin ƙoshin lafiya, Har ma tace mana kuna kewarmu, amma sai gashi Yadda muka ganku a yanzu ba haka mukayi tsammani ba, why pls”? Zuciyarshi a hautsine ya ƙarasa maganar,

“Angel Ki yi mana bayani? Yaushe aka dawo dasu? Meyasa kuma basa Iya magana” Cikin shessheƙar kuka Batool Ta jefa mata tambayar, Itama angel ɗin kukan take Yi, daƙyar ta iya tsagaitawa ta bata amsa da cewa”Kamar yarda kuka gansu haka muma muka gansu, Giants ne suka shigo tare dasu, Hada abincin ma suka kawo mana gashi can sun ajiye farantan saman dining carpet, Dukkan mu mun shiga ruɗanin halin da muka riskesu, Ko magana ma sunƙi yi mana”

Matsawa haris yayi tare da kai hannu Ya ruƙo yatsun hannun Rubina, afirgice ta zame hannunta daga nashi, ta runtse idanuwanta tana faɗin”Zafi nake ji ku daina ta6ani bana so, Ku ƙyale ni ku rabu dani, bana son ganinku” lallashinta hannah tayi”Shikenan tunda bakya so ba zamu ƙara ta6aki ba, Kiyi shiru kinji” Tayi maganar tana leƙen fuskarta,

Angel tace”Ni dama nasan za’a rina, Mutanan nan raina mana wayau suke yi, Tsohuwa tayi mana ƙaryar cewa An kaisu treatment room inda za’a duba lafiyarsu, tsawon 2 weeks kenan, Ga shi yau an dawo dasu babu alamun sauƙi ajikin su, ga dukkan alamu ma wani sabon Ciwon aka jaza musu ” rai amatuƙar 6ace angel tayi maganar tana huci, Mubeen yace”pls Mubi komai a hankali, ko dan saboda su Deeja, Ni inaga yakamata aje a sanarma tsohuwa tazo ta duba halin da suke aciki….”tun kafin mubeen yakai karshen maganar shi angel ta wurga mashi uwar harara, kamar zata rufe shi da bugu tace”Amma baka da hankali wlh, wai har yaushe ne zaku fahimci cewa matar nan Muguwace ba sonki take Yi ba, Kuma babbar maƙaryaciya ce! Tayi mana ƙaryar cewa A cikin satin da aka ɗauki su parveen za’a dawo dasu, Sai gashi yau tsawon 2 weeks kenan, Sannan bayan haka ta sanar damu cewa Su parveen sun samu lafiya harma suna tambayarmu, To yau gashi dai an dawo dasu Ba kamar yarda aka ɗauke su ba, kwata kwata babu cikakkiyar lafiya atare da su, ku baku lura da canzawar da su kayi bane? Muryarta a harzuƙe tayi maganar, Jijiyoyin wuyanta duk sun bayyana jikin fatarta saboda tsabar masifa, Kowa yayi shiru yana sauraronta, Cigaba da magana tayi”Kun maida kanku kamar gumaka, Ana cutarku baku ganewa, Yanzu ku kalli fuskokinsu deeja da la66ansu, wlh ko makaho ya shafa jikinsu sai yaji ajikinshi cewa basu da ƙoshin lafiya, Balle ku da kuke Mutane, Su parveen ba Maganin ciwonsu akayi musu ba, Ƙara musu wani ciwon akayi bisa wanda suke dashi”

Wannan bayanin Da angel ta kora musu Yasa sun fara Kokwanton Kalaman tsohuwa, Sun kuma fara yarda da ita,
Muryar hibba asanyaye tace”angel ae mu bamu san komai ba, Rayuwa kawai muke Yi acikin duhu, ba lallai mu iya fahimtarki ba,” Haris Yace”Tun da kike atare damu ban ta6a Yarda dake ba, Saboda ina zargin ke ɗin Kamar babu gaskiya acikin lamurranki, Yau ce rana ta farko Da kika fara sanya mini kokwanton wani abu acikin raina, Sai dai bazan ta6a Yarda dake ba har sai kin bani kwakkwaran Hujja da zata tabbatar mani cewa Cutar da rayuwarmu ake Yi,’ haris na kai karshen maganar shi, Batool tace”Muna goyan bayan haris, Idan har dagaske Ana Cutarmu a gidan kurkukun nan, To kiyi ƙoƙari ki bayyanar mana da kwakkwarar hujjar da zamu aminta dake, Ɗaya bayan ɗaya Angel ke binsu da kallo, wai wace irin hujja ce suke so Ta kawo musu? Bayan ga abu nan zahiri sun gani, acikin zuciyarta tayi tambayar, Tunawa da irin rayuwar da suka taso suna yi yasa ta Yi musu uziri, dole suna da ƙarancin fahimta, kansu Yana acikin duhun Jahilci, idan har bata lalubo hujjar da zasu Gasgata maganarta ba, to kuwa bazasu ta6a yarda da kalamanta ba, taya za’ae ta samo hujja bayan tsohuwa ta gargaɗe ta akan kada ta kuskura Tace zata Zurfafa bincike akan Gidan kurkukun, har ga Allah tana matuƙar fargabar Abunda zai biyo baya idan har tace zata Kawo musu hujja,

Sautin kukan Azeeza ne Ya jawo hankulansu, kusan atare suka Waiwaya baya suna kallonta, Har ta sauko daga saman gadonta, Sai faman laluban hanya take Yi tana faɗin” Wai bakowa ne akusa, Ni baza’a nuna mini su parveenar mu ba, dagaske an dawo mana dasu? Ina ta magana tun ɗazu babu mai ji na,”

Kallon Naufal Haris yayi tare da cewa”Kaje ka ruƙo ta kada ta faɗi” Naufal ya amsa mashi da toh, Da hanzari Ya tunkari parveen, Yana ƙarasawa gabanta, Ya ruƙo hannunta acikin nashi, Ya janyota zuwa inda suke abakin benan, “to ina su parveenar suke Ae ban ganinsu” Tsoki Haris Ya ɗan ja”kefa matsalarki kenan abu kaɗan sai kuka, Kamar kinfi kowa baki, Ki barmu muji da abunda Ya ishe mu,” a ƙule yayi maganar, cikin sanyin murya danish yace”haris ka bi ta a hankali, banaso kana yi mata magana irin haka” jinjina kai haris yayi tare da cewa na daina, kawai bana son yawan kukanta ne,”

“Ni dai ku nuna mini Su, kuma kuka bazan daina ba, Yanzu na fara sai dai ka buge ni” rai a6ace azeeza tayi maganar, mutumin dake fama da kanshi, kwata kwata bata iya ganin fuskokinsu, Biji biji take gani,

Matsar da ita naufal Yayi zuwa gabansu deeja da suka ƙame Sai shessheƙar kuka suke yi, ko gajiya basa yi,

“Gasu nan Agabanki Kiyi musu magana” naufal ne yae maganar, Hannayenta ta ɗaura asaman kirjin deeja tana shafata, Harta samu ta ruƙo hannunta ta ɗago shi zuwa saitin hancinta ta shinshina shi, duk suna kallonta, farin Ciki ne ya bayyana akan fuskarta, rungumeta tayi tana faɗin”Deeja Ashe kune dagaske, Nayi farin Ciki da aka dawo mana da ku, yanzu shikenan kunji sauƙi baza’a ƙara raba mu daku ba, Ni dai na roƙe ku kada ku ƙara Yin rashin lafiya, Kodan saboda kada araba mu daku, Saboda bamu jin daɗin rashin ganinku acikinmu” ita kaɗai take ta sambatunta, Javed ya kira sunanta”Azeeza Kiyi hakuri ki ƙyaleta, Basu son ana ta6a su, Har yanzu da sauran Jikin nasu” Cikin shessheƙar kuka tace”meyasa toh basu son ana ta6a su? Basuyi farin Ciki da dawowa Cikin mu bane? Duk irin kewarsu da muka Yi,” babu alamun zata fahimce su, angel ce tace”Javed ka barta, tun da naga yanzu Deeja bata Yi ƙara ba kamar yarda tayi ɗazu da batool ta ruƙota,” Eve tace”Nima na lura da hakan”

“Nidai kuyi mini magana, Wai sai kace baku Ji na, ko fushi kuke Yi damu ne”? matsawa tayi gaban Rubina Ta ruƙo hannayenta takaisu saitin hancinta ta shinshinasu, kafin ta faɗa jikinta ta rungumeta tana faɗin rubina, Kema bazaki Yi mini magana ba? Duk kun shareni,” jin shiru bata amsa mata ba, yasa ta janye jikinta daga na rubuna, da alama Jikinta yayi sanyi, Ruƙo hannun Parveen Tayi, batare data shinshina shi ba tace”parveen, Ke ma ba za kiyi mini magana ba? Meyasa bakwa farin ciki da dawowarku Cikinmu ne? Duk irin kewarku damu kayi, Munji raɗaɗin rashinku acikinmu, Tun ranar da Giants suka zo suka tafi daku, Kusan kullum ne sai Mun ajiye maku abinci, amma abanza yake lalacewa, mun yi maraicinku sosai” takai kai karshen maganar tare da ɗaura kanta saman kirjin parveen, hada ƙoƙarin zagayo da hannayenta zuwa bayan parveen ta ƙanƙameta,

“Yanzu ya zamuyi da su? nifa nagaji da tsayuwa ƙafafuwana har sun fara Yi mini zogi, Yakamata Mu koma Cikin ɗaki Mu xauna, yasmin ce tayi maganar,

Kallonsu Deeja Angel ta yi tare da cewa”Ku zo mu shiga Cikin ɗaki, Nasan Kuma kun gaji da tsayuwa” pls ku wuce mu tafi dare yayi sosai” ta karasa maganar tare da nuna musu Hanya, sai lokacin deeja ta iya buɗe baki tace dasu”Ni bazan Iya tafiya ba, ƙafafuwana zafi suke Yi mini,” Kallon Juna su ka yi, Hatta muryarta ta canza, kamar ba deeja da suka sani ba, Muryar parveen na rawa tace”Nima Bazan Iya tafiya ba, raɗaɗi nake Ji,” daƙyar tayi maganar saboda raɗaɗin da bakinta ke Yi mata, wanda shi ya hana su yin magana tun ɗazu amma duk suna jin me suke cewa kuma suna fahimta,

Rubina tace”nima bazan Iya ba,” lamarin yayi matuƙar ɗaure musu kai, Haris yace abunda za’ae yanzu, Zan Goya deeja abayana, danish ka goya rubina ita kuma angel ta goya parveen kai kuma naufal Ka taimaka Ma Azeeza ku shigo ciki, Zuƙunnawa su ka yi agabansu Deeja, Suka haye saman bayansu, Atare suka miƙe suka nufi Cikin ɗakin dasu, Sauran ƴan uwan nasu duk suna abiye dasu, A saman gadajensu suka sauke su, angel ta tambayesu ko suna jin yunwa, suka ce mata a’a, bacci suke so suyi sun gaji,” acikin zuciyarta ta kudiri aniyar idan Suka farka gobe zata Tambaye su game da abunda ya faru dasu, duk da tasan zaiyi wuya su iya tunawa,
Basu kwanta bacci ba har sai da suka Ci abincin da giants suka kawo musu, bayan sun kammala ci suka koma saman gadajensu suka kwanta zuciyar kowannan su acukunshe take Da tunanin halin da suka riski ƴan uwansu,

A daren ranar bayan kowa Ya koma saman gadonshi Ya kwanta, Angel tabi su ɗaya bayan ɗaya Ta tottofe su da addu’a, Ta lullu6e musu jikinsu da bargunansu, Wani abu daya ƙara ɗaure mata kai, A lokacin harta koma saman gadonta ta zauna ta ɗaga hannayenta sama tana Yin addu’o’i kamar yadda ta saba, Kwatsam Taji shessheƙar kukan Deeja, ga dukkan alamu mafarki take Yi, da hanzari angel ta sauko daga saman gadonta taje bakin gadon deeja ta ɗan ranƙwafa tare da kasa kunne tana sauraron me take cewa, Kuka take Yi tana faɗin bana so ku daina kuna cutar dani, zafi nake ji, kashe ni kuke Yi, Ni ku ƙyaleni ku rabu dani” Ciccije la66ata tayi tare da kai hannayenta saman mattress ɗinta tana damkar jikin katifar, Idanuwanta na fitar da ruwan hawaye, Can kuma sai taga deeja ta kai hannu tana sosa gaban wandonta, tana faɗin ƙaiƙayi take ji, zafi yake yi mata, mutuwa zatayi,” Daga bisani ne Deeja tadaina sambatun da take Yi, taci gaba da yin baccinta

Haƙika angel tayi matuƙar girgiza duk da bata Iya gano komai game da sambatun deeja ba, amma Jikinta yayi mugun yin sanyi, tabbas tana hasashen An yi masu wani mugun abunne kuma agabansu a Kayi musu, tun da gashi nan ta gani da idonta deeja na sosa wurin tana faɗin cewa ƙaiƙayi yake Yi mata,

Ikon Allah kenan, An juya musu tunaninsu don kada su Iya tuna komai Da akayi musu, Amma sai gashi Allah Ya haska mata wani abu ta cikin mafarkin da deeja ta yi, yanzu ya rage nata tayi ƙoƙari ta gano me akayi musu,

Kasa kwanciya tayi Domin kuwa baccin ya qauracewa idanuwanta, damuwa ce cunkushe acikin zuciyarta, safa da marwa ta shiga Yi acikin ɗakin yayin da zuciyarta ke tariyo mata abubuwan da suka faru ɗazu, na farko tana so Ta yi bincike akan danish, Taya akai yake Iya shiga cikin wurin dake a kulle, 6acewa yake Yi ne ko kuwa bango yake ratsawa ya shigo? Dole ne ɗaya ya kasance Cikin Biyun nan, Bayan wannan Kuma Ta yi matuƙar girgiza lokacin daya shafa glass Ya ruƙo ƙasan shi Ya 6a66ako shi tun daga tushen shi, to wai shi ɗin Aljani ne Ko mutun? Ko kuwa shigarshi A kayi? Ta rasa gane dawa zata Yarda,

Lokaci ɗaya kuma Ta fara tunanin meyasa Uniform ɗinsu Ya banbanta dana sauran ƴan uwansu? Su Uku ita da danish da batool su kaɗai suke da baƙaƙen Kaya, Yayin da Su Azeeza nasu Uniform ɗin Jajaye ne dukansu, Tabbas akwai dalilin dayasa aka Banbanta masu launin uniform ɗinsu, don me nasu zai kasance launi ɗaya dana GIANTS? Ta sanya alamar tambaya, ranta ne ya bata cewar bazata ta6a Iya gano menene atattare da danish ba, Har sai ta fara gano Dalilin banbance Uniform ɗinsu dana sauran Ƴan uwansu prisoners!!!

Nauyayiyar Azuciyar zuciya ta sauke, saboda yawan tunanin da take Yi da sanya damuwa aranta, Zuciyarta har wani nauyi take Yi mata a ƙirjinta, ita kanta tarasa Ya zatayi wurin rage ɗaura ma kanta damuwa akan hakan Ya faska,

Canza akalar tunanin nata Ta yi zuwa gasu Parveen, a yayin da take Cigaba da yin zirga zirga acikin ɗakin nasu, Tana zargin ana cutar dasu ne sai dai takasa gane wata irin cutarwa ce a ke yi musu, Ɗaukarsu da ake da sunan za’a je a duba lafiyarsu, Ga dukkan alamu Ba Lafiyarsu ake dubawa ba, Wani ciwon ake ƙara Danƙara musu ajikinsu, Shiyasa idan aka ɗaukesu daga Cikinsu Ba’a barinsu Cikin hayyacin su, har sai time da aka dawo da su, Tun akan danish ta lura da hakan, sannan kuma Lokacin da giants suka Shigo cikin ɗakin nasu atare da su parveen, da ƙafafuwansu suka tako, Amma daga baya suka ce baza su Iya tafiya ba, Hakan na nufin adai dai lokacin da suka sauke ƙafafuwansu acikin ɗakin daga nan sihirin da akayi musu ajikinsu Ya warware, Suka dawo hayyacinsu har suka gaza taƙa ƙafafuwansu,’

Jinjina kai angel ta yi a fili tace”Sannu ahankali zan binciko koma menene, babu fashi domin kuwa Alwashi ne na ɗaukarwa kaina Koda Kuwa zan rasa raina saina gano uban me ake aikatawa A Gidan kurkukun ƙaddara,!

Komawa tayi saman gadonta ta kwanta, tare da jan bargo ta lullu6e jikinta, Cikin ƙanƙanin Lokaci Bacci yayi awon gaba da ita,

A washe garin ranar, babu wanda Ya farka daga bacci acikinsu, Saboda daren jiya basu kwanta da wuri ba,

A firgice ta farka sakamakon sautin shessheƙar kukan parveen daya karaɗe kunnuwanta, ware manyan idanuwanta tayi tare da kai hannu ta zame bargon jikinta, Saukowa tayi daga saman gadon ta nufi gadon parveen a zaune ta same ta tsakiyar gadon, fuskarta ta ƙara kumbura sumar kanta duk ta hargitse, Jikinta hada zufa,

Da sauri ta ƙarasa daga gefen gadon ta zaune, tare da kallon fuskar parveen tace”Sister are u ok? Why are u crying? Ko jikin ne”? Daƙyar parveen ta ɗago ta kalli Cikin idanuwan angel, batare da tace komai ba, angel ta kuma cewa”Dan Allah ki faɗa mini meyasa ki kuka? May be Ina da abunda zan iya taimaka maki” cikin nuna damuwa tayi maganar, muryar parveen a disashe tace”bana Jin daɗin Jikina, ƙaiƙayi nake ji, kuma ina so Inyi wanka amma na kasa miƙewa saboda bazan Iya tafiya ba, wahala nake sha” tsananin tausayinta ne ya kama angel, Cikin muryar lallashi tace”shikenan ki daina kuka, kada wannan ya dame ki, Ni zan Iya yi maki komai, Yanzu zan Goya ki in kaiki toilet, idan ma kina so har wankan sai inyi maki”

“Nagode sosai Angel,” saukowa Angel tayi daga saman gadon nata, ta juya tare da zuƙunnawa tace da parveen ta hau bayanta, Matsawo Parveen Tayi ta lalla6a ta haye bayan Angel, hannayenta ta sanya ta ruƙe parveen, Ta daddage ta miƙe ta wuce toilet ɗauke da ita abayanta, Shigarsu toilet keda Wuya acan Cikin ɗakin Deeja da Rubina suka farka da wani irin sautin kuka mai razanarwa, Duk wani mai bacci saida Ya farka sakamakon Kukan nasu daya karaɗe Cikin ɗakin,

Jiki na 6ari suka sassauko daga saman gadajensu, Banda Danish Yana kishingiɗe saman gadonshi, Ya farka amma bai buɗe idanuwanshi ba, da alama baccin bai ishe shi ba, ko kuma tsiwar tasu ce ta addabe shi,

Agaban Gadon deeja Haris da Batool, da hibba hada hanna Suka tsaitsaya suna kallonta Fuskokinsu ɗauke da damuwa,

Su javed da sauran ƴan uwan nasu suna a zuƙunne gaban gadon Rubina,

Duk sun ƙanƙame Jikinsu Dake ta kerma, Sun rasa gane masu, gaba ɗaya sun canza, xama batool tayi daga gefen gadon Deeja, muryarta a sanyaye tace”Deeja, Meya ke faru dake ne? Jikin ki Yana yi maki ciwo ne? Ɗaga mata kai ta yi alamar eh, Haris yace”Ni narasa gane wannan ciwon naku, ance Ana baku treatment amma ya akaiba wani sauƙi atattare daku? Kun wani fige kun fita hayyacin ku,” aruɗe yakai karshen maganar, Hanna tace”Deeja zaki Iya faɗa mana inda aka kai ku? Da kuma abunda aka Yi maku? Girgiza kai deeja tayi har lokacin hawaye basu daina zuba kan fuskarta ba,

“Bazan Iya tuna komai ba, tun lokacin da aka ɗauke Ni daga Cikin ku, sai Jiya da aka dawo dani Tukunna Na Iya tuna wacece Ni!” Kaitsaye maganar deeja taje kunnan Angel dake Kokarin Fitowa daga sashen toilet ɗinsu, Bayanta ɗauke da parveen data goyo, ta taimaka mata tayi wanka hada sumar kanta ta wanke mata, Kasa Cigaba da tafiya tayi, ta kasa kunne tana sauraronsu

Hibba tace”Abun da ɗaure kai, Ni fa gani nake kamar an ƙara musu Ciwon ma, To inba haka ba Kallarsu fa ku gani, sati biyu da suka wuce kafin azo a ɗauke su daga Cikin mu, Da ƙibarsu jikinsu da auki amma Yanzu Kamar an ɗibi naman jikinsu,” Kowa fa ya fara Kokwanton wani abu aranshi, Hakan ba ƙaramin daɗi Yayi ma angel ba, saboda sun fara tunani na hankali,

Jin muryoyinsu javed dake a zuƙunne gaban Gadon Rubina. yasa takai idonta kansu, Ta kasa kunne don taji su me suke tattaunawa

“Rubina Acan inda aka kai ku suna baku abinci? Naga duk kun rame kamar akwai Yunwa attatare daku, Sa’an nan Ya akai la66anku suka faffashe wani Ya cije ku ne? Eve ce tayi mata tambayar. idanuwan rubina cike tab da kwalla tace”A’a ni bazan Iya tuna komai ba, ku daina Yi mini tambayoyi dangane da inda aka kaini saboda bansani ba ni kaina” Mamaki ne ya kamasu, Jin tace batasan komai ba, yasmin tace”Nayi matuƙar damuwa da hankalin da kuke Ciki, bamu yi tsammanin Zamu ganku haka ba a wulaƙance, kwata kwata Jikinku babu alamun sauƙi, saima abunda yayi gaba, Gaskiya nidai ban yarda da wannan treatment room ɗin ba, Yakamata mu yi ma tsohuwa magana, idan wani bai da lafiya acikinmu kada a ɗaukar mana shi, abar mana shi acikinmu muyi jinyarshi”

Naufal yace”Wai Ina parveen ne? Naga babu ita asaman gadonta”? A hanzarce suka juya suna kallon Gadon Parveen,

Muryar angel ce ta janyo hankalinsu zura gareta,

“Gata nan abayana, Ta farka tana buƙatar Yin wanka shine na taimaka mata Tayi, Yakamata suma su deejan su yi wanka, Ko sunji daɗin Jikinsu” Ajiyar zuciya kowannan su ya sauke, Wuce wa angel tayi zuwa cikin ɗakin Abakin Gadon parveen Ta ɗan rankwafa tare da kwantar da ita saman mattress ɗin, Da gudu Azeeza ta nufo gadon parveen ta haye gefenta, fuskarta ɗauke da murmushi tace”Ƴar uwa ya Jikin naki? Daƙyar parveen ta ƙaƙalo murmushi tare da cewa”Da sauƙi sister, Nayi missing dinku sosai Ƴan uwana, Ina abincin da nace ku ajiye mini”? Fuskarta aɗaure tayi maganar tana kallonsu,

Azeeza tace”Ki tambayi angel kiji, tun ranar da aka ɗauke Ku daga Cikin mu, Kullum sai mun ajiye maku abinci yana lalacewa, Har mun fidda rai da za’a dawo mana da ku ashe da rabon Mu sake sanya ku acikin idanuwanmu,” tana kai karshen maganar ta kifa kanta saman mattress tana kukan karya, murmushi parveen tasaki, tare da miƙa hannunta saman kan azeeza ta ruƙo kalabar da akayi mata,

“Azeeza wa yayi maki wannan”? ɗagowa azeeza tayi tare da kallon kalabarta da parveen ta ruƙe a hannunta tace”Angel ce tayi mini, kema in kina so sai tayi maki idan kika ji sauƙi”

“Batool da Hannah, Ku taimaka masu deeja suyi wanka, ” Angel ce tayi musu magana,

Batare da 6ata Lokaci ba, Batool Da Hanna suka Goya su deeja da rubina asaman bayansu, suka nufi toilet da su,

Ataƙaice Yau dai kusan Sati ɗaya da aka dawo dasu parveen, Jikinsu Yaƙi sauƙi Lafiya ta yi ƙaranci A jikinsu, basu Iya tafiya sai an taimaka musu, ko sunyi yunƙurin miƙewa da niyar su taka ƙafafuwansu Sai kaga ƙafar ta gurɗe, ko daga baya da suka fara Jin sauƙin jikinsu, sai tafiyarsu ta koma irin ta gwami, basu Iyayin tafiya lafiya lou batare da ƙafarsu ta gwame ba, Hankalinsu Batool Yaki kwanciya, Har zuwa bakin kopar ɗakin tsohuwa su kayi domin Su sanar da ita halin da ƴan uwansu suke aciki, Koda suka kwankwasa ƙopar ɗakin tsohuwa ta fito, Suka sanar da ita abunda ke faruwa dasu Parveen Na rashin Iya tafiyarsu, Sai cewa tayi su cigaba da basu kulawa, Zasu dawo dai dai, tana faɗi musu haka Ta juya ta koma ɗakinta tare da jan ƙopa ta rufe, Babu yadda suka Iya haka suka Cigaba da kulawa dasu, Idan zasu Yi wanka Dole sai An taimaka musu, Batool da angel sune ke ɗawainiya dasu, Hatta wankin Uniform ɗinsu sune suke Yi musu, Hakan ba ƙaramin daɗi yake yi musu ba, Hankalinsu Ya kwanta ganin irin soyayyar da ƴan uwansu ke nuna masu,

Da taimakon Allah, jikinsu Yayi sauƙi sosai suka koma yadda suke ada, Tafiyarsu ta dawo dai, Ranar Har wasa su batool suka yi saboda murnar samun sauƙin su deeja, Yanzu babu faɗa a tsakanin Deeja da angel sun daina ƙin junansu, Tun lokacin da aka dawo dasu, angel ta lura da irin canzawar da deeja ta yi, Bata jan kowa faɗa, babu ruwanta da kowa, Sai In ana wasa ne zaka ga ta sanya baki itama ayi da ita, hatta haris Yanzu sun samu jituwa atsakaninshi Da angel, Suna yin rayuwarsu Cikin so da ƙaunar juna, Tsawon kwanaki, Sun samu kwanciyar hankali,

A daren Wata rane ne, Angel Ta kawo masu shawarar su yi wasan Ƴar 6urun 6urun, ta gabatar musu da yarda zasuyi wasan, Gaba ɗayansu suka hallara atsakiyar ɗakinsu, mubeen Ne ya cire rigarshi Ya miƙa ma angel, ta kar6a ta ɗaurewa batool idanuwanta da rigar, Da gudu kowanansu Ya ruga zuwa ma6oyarsa, Wasu suka shige ƙarƙashin gado, wasu suka Nufi Cikin toilet suka 6oye, Hada wanda ya 6oye Ƙarkashin table ɗin da suke ɗaura fitilinsu, Batool taci gaba da bin hanya tana lalubensu tana fadin”6urun 6urun ku 6oye ku 6oye da nisa, Garin gudu ku faɗi ku gurje abanza, Kun 6oye” suka ce a’a, Kusan sau uku Tana tambayarsu sun 6oye sai suce a’a, Ana huɗun ne suka ce mata Eh sun 6oye, nemansu ta dinga Yi acikin dakin, Tarasa ina suka 6oye, ga shi sun ɗaure mata idanuwanta sosai bata Iya gani,

Angel da azeeza Suna a rungume da juna ƙarƙashin Gadon Batool ɗin, Sai tiƙar dariya suke Yi, Danish kuma Yana a karkashin gadonshi tare da parveen, Haris da deeja suna a Karkashin gadon angel, Naufal da Mubeen Sun 6oye kasan table, hanna da hibba hada javed suna a la6e Cikin toilet, kamar aljanu ko tsoro basa Ji, Su rubina da yasmin hada Eve, A jikin bango suka la6e, Don sunsan bazata iya gano su ba, tunda an kulle mata idanuwanta, Sai wahala take sha sunƙi bari ta kamasu, na cikin toilet ne Suka Ji motsi aikuwa gaba ɗaya suka watso da gudu waje cikin sa’a ta cafki wuyan rigar Javed, Ta dinga tsalle tana faɗin ta kama ta kama, Jin haka yasa sauran ƴan uwan nasu suka firfito daga ma6oyarsu, angel ta warware mata ɗaurin dake akan fuskarta, ta ɗaure ma Javed idanuwanshi, Da gudu kowa Ya rugo Zuwa wurin 6oyenshi, wannan karan Azeeza ta tona musu asiri, fitsari ya matse ta, tace ma angel ta rakata suje toilet tayi, angel tace mata ta jira akama wani acikinsu sai su fita, Aikuwa ta fashe mata da kuka tana faɗin ta taso su tafi ya matseta kada tayi shi awando , Maganar azeeza tayi matuƙar basu dariya, Javed najin muryoyinsu ya dinga laluban hanya Cikin sa’a Ya kamo rigar azeeza a lokacin ta fito daga karkashin gadon, ta buge mashi hannu tana fadin Ita fitsari take Ji, fitowa daga karkashin gadon angel tayi Tace da danish”Ya jira ta rakata tayo fitsarin, Idan suka dawo ita zata Yi wasan amadadin Azeeza” Yace mata toh , Bayan sunje toilet ɗin sun dawo, Sauran ƴan wasan duk suka fito daga wurin 6oyansu, Batool ta kar6i rigar hannun javed ta ɗaure ma angel idanuwanta sosai, wannan karan basu 6oye ba, Raina mata wayau suka dinga Yi suna zagayeta, daga ta miƙa hannu za ta cafkosu sai suyi sauri suja da baya, baƙaramar wahala tasha ba, Daƙyar ta samu ta ruƙo wandon Hibba, Ta dinga murna tana faɗin ta kama,

Daren Ranar Ba ƙaramin nishaɗi suka yi ba, Sai da dare ya ratsa tukunna suka kwanta domin Yin bacci,

A washe garin da su ka yi wasan ne ta farka fuskarta dauke da murmushi, ta miƙe zaune saman gadonta, Babu wanda ya tashi daga bacci sai ita, Saukowa tayi daga saman gadonta, da sauri ta nufi toilet, da niyar yin wanka, Tana shiga Ciki, taja kopa ta datse, Tsayawa tayi atsaye tana kallon glass din jikin tagar, abunda yasa har yau bata dura ta cikin windown ba, Saboda fargabar maganar da tsohuwa ta faɗa mata na cewa Zata ja musu bala’e, A yanzu bata son duk wani abu da zai tashi hankalinsu, tafi son su kasance Cikin farin Ciki, har zuwa lokacin da Allah Zai Taƙaita zamansu agidan kurkukun idan suna da rabon fita, idan kuma Anan ƙaddarar rayuwasa ta tsaya tana yi musu fatan da cewa,

Hannayenta ta sanya tare da kamo ƙasan rigarta, tana yunƙurin tu6e rigar, Hancinta ya shaƙo mata ƙarnin Jini, Nan take gabanta Yayi wani irin mugun bugu, A matuƙar ruɗe ta saki rigar ta fasa cireta, ta soma bin ko’ina na jikinta tana shinshinawa a ƙoƙarinta nata gano Inda ƙarnin jikin ke fitowa, Hatta wandonta saida ta ɗaga ta leƙe ciki don taga idan itama tafara Period ɗin, amma koda ta bincika bata ga Jinin ba, Sai da ta gama shan wahalar duba Jikinta a karshe idanuwanta suka sauka akan busasshen jinin dake a saman tafin hannunta, waro ido waje tayi tana kallon Jinin, tarasa a ina ta same shi, tun da ta duba ko’ina na jikinta bata ga ciwo ba, a kalla ta kwashe fiye da awa acikin toilet din Cikin yanayi na jin fargaba, Ta shiga ruɗani sosai,

Da gudun gaske ta fito daga Cikin toilet ɗin, bata nufi ko’ina ba sai bakin gadon azeeza, Saboda itace Jiya suka 6oye a karkashin gadon batool atare

(Mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, Tunasarwa, Kamar yadda kuka sani Kurkukun ƙaddara paid book one, Amna nace zan bada takun farko free, Nan badajimawa ba, takun farko zai zo karshe, Wadanda ke son Cigaban story ɗin, Akwai paid group na wanda suka Biya, Whatsapp dana facebook, duk wanda ke so, Yayi mini magana ta account dina)

 

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

 

 

( mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, masu yi mun ya jiki ina godiya)

Back to top button