Novel Document

Taswirar Kaddara Complete Novel Document

Description/Story:

Taswirar Kaddara Complete Novel Document Written By Mrs A.M

 

Description Of Taswirar Kaddara Complete Novel Document

Ina zaune a matsakai cin tsakar gidan mu ina duba littafina kasancewar Jamb din da zan rubuta wannan shekarar gashi lokaci yana ta kurewa saura sati biyu mu zama jamb din.

Hankali na ya kasu kashi biyu, daya yana kan English din dana ke rubutawa daya kuma yana ga tunanin inda *MIMI* ta shiga, tun da akai la’asar ta fita ban kara ganin taba, kwafa nai ina tunanin yadda zan hukunta ta tunda tasan cewa bana son tana fita da yamma haka ita kadai.

Wata yarinya mai kimanin shekaru 4 fara kar kamar balarabiya sbd tsabar kyaun da Allah yai mata ta shigo gidan tana sanye da riga yar kanti har kasa duk da rigar tadan kode amma kal take a wanke sai alamun kasa kasa daka kasan rigar da alama yarinyar tayi wasa a kasa ne.

Tunda ta shigo na kafe ta da ido ina tasbihi a raina, kullum na kalli Mimi sai nayi tasbihi ga Ubangiji sbd tsabar kyaun ta, fara ce tass mai dauke da zagayayyiyar fuska tana da manyan idanu sosai tubarkalla sai dogon hanci wanda ya dace da zagayayyiyar fuskar ta sai kuma karamin bakinta jajir dashi, maida kallona kan gashin ta nai dake tufke amma jelar har kusan duwawun ta take sbd tsayin gashin ta.

Lumshe idona nai jin wani hawaye yana kokarin zubo min, muryar ta mai cike da shagwaba naji a kusa dani tana fadin *”MAA* kiyi hakuri baxan sake ba Hidiya ce tace inzo muyi wasa a garden din gidan su.”

Kallon ta nake kawai ina bin kumatun ta da kallo yadda dimple dinta na gefen kumatun ta na dama yake lotsawa sosai, hakan ba karamin kyau yake karama ta ba.

Hade rai nai cikin dan fada fada da saurin maganar da nake da shi nace “ban hana ki fita ba amma wato kin fara raina ni koh Mimi shine har zaki fita BA tare da na sani ba”

Rau rau tai da idonta daya fara tara hawaye ta kama kunnuwan ta da hannayen ta tace “Maa kiyi hakuri bazan sake bafa kar kiyi fushi dani”

Daga bayan mu Umma da ta fito daga daki tayi dariya tace “zo kinji kawata kema kinsan Maa dinki baxa ta iya fushi dake ba”

Makale kafada tai tace “toh Umma ai bata ce ta hakura ba”

Janyo ta jikina nai cikin tsananin kaunar ta nace “na hakura babyta amma kar ki sake fita ba tare da kin fada min ba kinji koh”

Daga kai tai tana kuma kwantar da kanta a jikina sai shagwaba take zuba min ina biye mata, girgiza kai Umma tai kawai tana dauke kwallar dake neman sakko mata a fuska.

Muna zaune a tsakar gidan Umma da Mimi na kan tabarma ni kuma ina daga kitchen Aysha ta shigo cikin uniform din islamiyya.

Fitowa nai hannuna rike da ludayi nace “kinyi saurin dawowa yau Aysha ina su Kamal din”

Zama tai akan tabarma tana ajiye jakar hannun ta cikin gajiya tace “suna hanya Ya *BATUL* ai baxan iya jiran suba wallahi duk ba gaji fah kinji kafa ta”

Dariya nai nace shiyasa nace “sannun ku ai kun kusa sauka ki dinga hutawa kema”

Kallon Mimi tai tace “shine kika ki zuwa islamiyya yau koh ai Malamar ku tace sai ta zane ki gobe”

Murguda karamin bakin ta tai tace “ai bani da lafia kaina yake ciwo shine Maa tace nai zama na gobe sai naje”

Na bude baki zanyi magana knn su Kamal suka shigo, kallonsu nake da dukkan alamu ba lafia ba don yadda Kamal yake ta hura hanci yana goge gumi.

Kallon Khalil nai don nasan yadda kamal yake ko na tambaye sa baxai iya min magana ba, cikin saurin magana ta nace “mai aka masa naga sai huci yake ko fada sukai ne”

Goge goshin sa Khalil yai cikin nutsuwa kasancewar sa komai a nutse yake yace “Ya BATUL Manniru din gidan Kawu Nasiru ne sukai fada dashi, wai kawai don Malamar su Mimi tace bata ganta ba a gaishe mata da ita shine da muka fito ya tare mu yana fadin baiga amfanin saka Mimi a makaranta ba tunda *SHEGIA CE* ita Shi kuma khalid ya mare sa shine suka fara fada da kyar aka rabasu” ya karashe hawaye na zubo masa.

Tunda ya ambaci shegia naji kirjina na min wani irin zafi cikin masifar dake taso min na shiga dakin mu, hijab na dauko na fito dashi a hannu na ina kokarin sawa.

Umma da tai shiru kanta a kasa ta dago ta kalle ni tace “meye haka Batul ina zaki je”

Girgiza kai kawai nake don tsabar bala’in dake cina bana Jin ma zan iya magana in da abinda na tsana a duniya shine a dangan ta min Mimi da shegia tabbas nasan gaskia ake fada amma raina baci yake a duk lokacin da aka kirata da haka kuma ko waye ya fada mata sai na gaya masa maganar da nasan zai dade yana jin takaicin ta.

Da kyar na hadiyi wani yawu nace “zanje gidan su ne in jawa uwani kunne akan yaranta wallahi Umma duk lokacin da suka kara shegan tamin yarinya sai nasa an karya musu kafafu don uban babansu.”

“Mai kuma babana yai haka ake zagin sa Batul”.

Juyawa nai ina kallon babanmu daya shigo hannun sa rike da leda wanda wannan dabi’ar sa ce kullum zai dawo daga kasuwa sai ya siyo wani abu komai kankantar sa ya shigo da shi.

Turo karamin bakina nai gaba ciki ciki nace “Manniru neh ya cewa Mimi shegia shine zanje na jawa uwani kunne akan su kar nasa su cilla su karya min kafar su ace ban fada musu ba”

Zaunar dani baba yai akan dakalin kofar dakin mu yace “don sun ce haka sai ki biye musu, kinsan dama abinda suke so knn suyi magana wani ya biye musu su tada fitina ki rabu dasu wata rana ko ance su fadi haka baxa su fada ba Batul”

Nidai Shiru nai kawai ina girgiza kaina tunda Baba yace na rabu da su na kyale su Amma wallahi sai nasa cilla ya zane min yaron nan in da hali na ko yar karamar targade ne ya masa a kafafun.

Ina zaune a wajen Aysha ta shiga kitchen don karasa girkin da ban gama ba, su Khalil kuma sun chanja kaya sun fita, Mai da kallona nai gurin su Baba da yake wa Mimi Wasa sai dariya take tana jan gemun sa. Kafe ta nai da ido ina Jin tsoron zuwan ranar da zata tambaye ni *WAYE MAHAIFIN TA* mai zan ce Mata ban san saba ban taba ganin fuskar sa ba banma san ya yanayin sa yake ba abu daya ne nake da shi mallakin mahaifin ta shi kuma bansan ta yadda zai kaini ga mahaifin nata ba.

 

Lumshe idona nai tsanar ko waye baban ta yana taso min tabbas da zan ido hudu da shi da ina da dama saina caka masa wuka a kirji……

 

*************

 

Zaune suke a lafiyayyan palourn gidan daya kasance mallakin mai gidan ko wanne dare anan iyalan gidan suke taruwa suke zama tare suke cin abincin dare.

Mami ce ta shigo palourn cikin shigar ta da kowa yasan ta da shi wato lifaya mai tsadar gaske red colour wacce ta haska farar fatar ta kana kallon ta zaka san cewa ita din shuwa arab ce, zata kai shekaru 45 Amma jikin ta bai nuna ba sbd tana da jiki nai kyau.

A hankali take tafiya hannun ta rike da kaskon turaren wuta data saka, sai da ta fara ajiye kaskon a kan table din gefen manyan kujerun Palourn sannan ta juya ta kalli Abie da tunda ta shigo ya kafe ta ido yana sakar mata murmushi mai cike da ma’ana, itama mayar masa da martanin murmushin tai tana masa wani kallo na kasan ido kafin ta isa kan kujerar da suke zaune shida Mama ta zauna itama.

Gaisar da Abie tai cikin nutsuwa kafin ta juya taiwa mama sallama, ciki ciki ta amsa ta daga kanta sai hura hanci take, itama bata damu ba ta maida kallon ta kan TV tana kallon news.

*JUNAID* ne ya fara shigowa cikin nutsuwa sanye da jallabiya as usual hannun sa dauke da carbi yana ja a hankali, kara sowa yai kusa da Abie ya tsugunna ya gaishe su, cikin so Abie ya amsa yana shafa kwantaccen sumar sa.

Mami ma murmushi take kafin tace “ina ka baro Samira din yauma baka zo da ita bakoh?”

Sosa goshin sa yai yana sunkuyar da kansa don baya iya hada ido da iyayen sa yace “Mami tana gidan su ne ynxu in zan wuce zan biya na dauke ta”

Gyada kai tai tace “Allah yai muku albarka ya warware muku dukkan matsalolin ku”

Ameen ya amsa yana komawa gefen ya zauna a kasa yana jan charbin sa cikin nutsuwa.

Baiyi minti goma da shigowa ba Yusuf ya shigo bayansa Sagir ne sai auta Mufeeda, Suma sai da suka gaishe da Abie dasu Mami sannan suka koma kusa da Junaid suna masa magana kasa kasa.

Hade rai Mama tai ta sani kusancin yaran ta da su Junaid tayi yadda zata yi ta raba su Amma abin yaci tura ta zage su ta zuga su amma a banza sudai kome zata yi baza su daina kula Yan uwan suba, kusan kullum ma a part din Mami suke wuni wannan abin yafi komai bata Mata rai.

Kallon su Abie yai kafin ya girgiza kansa yace ina *AZLAN* Junaid ne ya amsa Shi da fadin “Abie yana nan zuwa da zan fito ya shiga wanka neh”

Gyada kai kawai Abie yai yana maida kallon sa TV, ba’a dau lokaci mai tsayi ba suka fara jiyo fito yana doso palourn gaba dayan su suka zubawa kofar shigowa palourn ido duk da kuwa sun san waye zai shigo din.

Cikin takun jarumta ya shigo palourn yana sanye da three quarter brown colour sai armless riga light brown wacce ya bude botir din gaban rigar guda uku hakan ya bayyana kirjin sa, kafar sa sanye da wani takalmi mai kama da silifas, kamar su daya da Junaid don kana ganin su zaka gane Yan biyu neh sai dai Shi yafi Junaid haske kuma ya fisa kyau da kirar jiki mai kyau, cikin takun jarumta ya karaso tsakiyar palourn bayan ya cire takalmin sa.

Binsa da kallo Mami tai tana girgiza kai ganin askin kansa ita ynxu ma data sanin ce masa yaje yai aski take, da kansa sumar ce kawai ya tara sosai duk da sumar tasa a kwance take kamar ta larabawa amma tace yaje ya rage ta gashi ynxu yaje an kwashe gefe data an bar masa gefe daya. Mai da idonta kan damtsen hannun sa na dama tai dake dauke da katon tattoo na zaki a jiki, sai gefen wuyansa na hagu kuma da aka masa tattoo na miciji inda aka biyi da jelar micijin har wajen kirjin sa, girgiza kai tai a ranta tace “Allah ya shirya min kai Azlan”

Daga tsayen da yaje ya dan rankwafo yana tura hannun sa a cikin aljihun sa cikin muryar sa Mai kaushi da kame wa yace “Evening Abie” ba tare daya jira amsar Saba ya juya gun Mami yace “Evening Mami”, Mai da kallon sa kan Mama yai ya zuba mata manyan idon sa da suka sha kwalli yace “Eve Hajia”

Hadiye wani yawu tai a duniya tana tsoron Azlan duk iskancin da zata yi a bayan idon sa take yinsa amma tana matukar tsoron sa, cikin inda inda tace “lafia”

Yamutsa fuska yai yana duba apple watch din dake daure a hannun sa na hagu ganin pass 8 yasa shi kallon Abie yace “zan iya ware wa Abie”

Girgiza masa kai yai takaici kamar zai kashe sa yace “na fada ma wallahi yau baxa ka fita a gate dinnan ba na gaji da halin Ka in Ka fita shashancin Ka baxa ka dawo ba sa tsakar dare”

Girar sa ta hagu ya daga yana shafa gemun sa yace “ta gate nedai Ka haramta min ware koh”

Daga kai Abie yai cikin tabbatar wa, juyawa yai ya kalli su Junaid da suka zuba masa ido gaba dayan su, yana juyowa duk suka juya suka maida kallon su kan TV sai Junaid ne kawai ya tsare sa da ido yana masa magiyar ya saurara yaji abinda Abie zaice.

Tabe bakin sa yai ya kalli Mami yace “kina bina da addua fah Mami kar wata ta danne miki ni tayi min fyade ta raba ni da budurwarcin dana ke ajiye wa”

Sunkuyar da kai su Mufeeda sukai yayinda Abie ya zuba masa ido kawai yana mamakin inda Azlan ya dakko rashin kunya sam bashi da kunya ga kwarjini da Ubangiji yai masa ko shi daya ke mahaifin sa kwarjini yake masa sosai, ita dai Mami addu’ar daya ce tai masa take yi a zuciyar ta tana kuma roka masa shirya.

Juyawa yai yana tafiya cikin jarumta, sai da yakai bakin kofar palourn ya juyo ya kalli Abie yace……

 

Wannan shine somin tabi na littafin Taswirar Kaddara Complete Novel Document wanda Mrs A.M ta rubuta.

Taswirar Kaddara Complete Novel Document txt

File Name   Taswirar Kaddara Complete Novel Document
Title   Taswirar Kaddara Complete
Author    Aisha Aliyu Garkuwa 
Group    Ai  Hausa Novels
Genre    Fiction Story
Published Date    17/07/2024
File Size    700KB
Format Size    TXT
Book Price    Free
Phone No
Download Taswirar Kaddara Complete Novel Document By Mrs A.M

Click the below green button to read the novel online

 READ THE NOVEL TASWIRAR KADDARA COMPLETE NOVEL DOCUMENT


Proceed with your download by clicking the below button

 

 

Be With Us

 

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Back to top button