Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 47 By Hafsat Bature

💋KURKUKUN ƘADDARA💋

E47

Daga alƙalamin Boss Bature writer of Abban sojoji❤

Tunkafin ta ƙarasa maganarta, Da ƙarfi Ta buga sandar hannunta, wata irin ƙura ta mamaye idanuwansu, Kafin wani lokaci hayaƙin ya washe, Sai dai koda suka buɗe idanuwansu, ba su yi nasarar samun TSOHUWA TAMIRA ba, Ta riga da ta tafi, ta barsu da kewarta, sun shiga ruɗanin maganganun data faɗa musu, ga fargabar da suke aciki na baƙuncin TSOHUWA ZAFREEN, Lamarin yayi matuƙar gigitasu, yinin ranar da jimamin rashinta suka Yi shi, babu wanda bai matse kwalla ba acikinsu, Sunyi kuka tamkar ransu zai fita, sunyi danasanin duk wani abu da ya shiga atsakaninsu da ita, dama ance sabo turken wawa, hatta angel da tafi kowa tsanar tsohuwa a yau Saman gado ta haye ta rungume pillow tana matsar kwalla, fuskokinsu sunyi jawur gwanin ban tausayi, babu wanda yai kwakkwaran motsi acikinsu, kowa yana tuna irin rayuwar da suka yi da tsohuwa Tamira, Har giants suka kawo musu abinci basu motsa ba, badan Allah yasa parveen tayi tunanin kwashe musu abincin Cikin kwando ta ajiye musu shi ba, da sun yi asarar shi, duk irin zumuɗin da suke yi na sabbin kayan da aka kawo musu babu wanda Ya ta6a su, Kai hatta akwati nan basu ishe su kallo ba.

Sai da yunwa ta fara kai musu karo tukunna suka fara neman abinci, A lokacin dare ya nutsa Haka suka zazzauna saman dining carpet dinsu, parveen ta ɗauko musu abincinsu, Yadda kasan waɗanda akayiwa dole, Suna cin abincin suna matsar kwalla, Musamman parveen idan ta cunkusa Naman abaki, tana tauna Tana ambaton sunan tsohuwa, shikenan ta tafi tabarsu, Yanzu ya zasuyi, Bayan sun kammala cin abincin, babu wanda yai tunanin yin wanka, ga jikinsu sai tsami yake yi, ahaka suka haura saman sabbin gadajen nan kowa ya kwanta, zuciyoyinsu cike fal da jimamin rashin tsohuwa Tamira, da kuma fargabar irin rayuwar da za su yi da tsohuwa Zafreen, ɗaya daga Cikin shuwagabannin kurkukun ƙaddara, suna daga kwance suke Yin fira, Haris yace daga Jin sunanta babu imani atattare da ita, Ni inaga toilet zan koma da kwana, zaifi mini kwanciyar Hankali, ashagwa6e azeeza tace Ni dai Allah ƙarƙashin gado zan dinga 6oyewa duk idan naji takun tafiyarta”

parveen tace nidai in har bazata hanani cin abinci ba, babu ruwana da shiga huruminta, zanyi mata biyayya kodan in tsira da Ciki na,” deeja kuma tace”Allah ya jiƙanmu badan mun mutu ba,” rubina tace”Ai kawai mu ɗauki shawarar tsohuwa mu bita sau da ƙafa, Har Allah ya kawo lokacin da zamu Rabu da ita,” dogon tsoki javed yaja mai sautin gaske kafin yace”Kunga surutun ya isa haka, pls kowa ya lallashi zuciyarshi, Ku rungumi pillows dinku, aja bargo a lullu6e jiki, kowa Yae bacci, zuwan tsohuwa Zafreen ba fashi,” Sai da duk suka gama surutansu, tukunna Angel ta soma magana muryarta adisashe tace”In sha Allah, babu abunda zai faru, koda tazo bazata Iya cutar damu ba, Ni babu bawan da nake jin tsoronshi aduniyar nan, In ba mahalicci na ba, saboda nasan babu wanda ya isa ya cutar dani face da izninsa, Allah shine maganin duk wani mugu mai kafirar zuciya, kafin ayi azzaluman kurkukun kaddara Anyi waɗanda suka fisu, irinsu fir’auna yanzu duk babu su a doron duniyar nan sai dai kajisu a tarihi,’ Tunda angel ta ambaci sunan fir’auna, nan fa suka addabeta akan ta basu tarihinshi suna son Sanin wanene shi, tace musu su yi haƙuri yanzu kanta ke yi mata ciwo, amma ta yi musu alƙawarin idan taji sauƙi zata basu tarihin Annabi musa (AS), bayan haka saida ta kwantar musu da hankulan su, kafin ta samu bacci ya ɗauke su,

Lokacin da dare Ya ratsa, Angel ta sauko daga saman gadonta, zuciyarta duk ba daɗi, ahaka ta lalla6a ta nufi toilet ɗinsu, ba don komai ba, sai don ta duba awani hali furen batool yake aciki, Tana sanya ƙafarta Cikin toilet din ta hango furen batool da alamun lemar ruwa ajikinshi, kamar zufa haka ya tsastsafo ajikin ganyen shi, nan fa hankalinta ya ɗan tashi, da sauri ta ƙarasa inda tukunyar fulawar take, Ta zuƙunna tare dakai hannu tana shafa Jikin ganyen shi, sosai ruwan ke tsastsafowa, Duk saita rasa sukuni, ta shiga damuwa, muryarta na ɗan rawa ta soma faɗin”dan Allah batool ki daina kuka, Ina atare dake, ban manta dake ba, kina araina, kullum ina yi maki addu’a, Duk da nagaza zuwa in taimake ki amma nasan cewa Allah yana atare dake kuma zai kare ki ne,”

cikin shessheƙar kuka angel take lallashin Furen, Batasan cewa Danish Yana tsaye bakin ƙopar toilet ɗin ya la6e yana kallonta, tsananin tausayinta ne ya kama shi, sai dai baijin zai iya zuwa ya lallashe ta, saboda alƙawarin daya ɗaukar mata, abunda baisani ba ita kanta, A halin yanzu a matuƙar ƙagare take da son su shirya da juna don ba ƙaramin azabtuwa take yi ba,

Shiru ta ɗanyi tana ƙarewa furen kallon, ganin Ya daina tsastsafo da ruwa ajikinshi, wani iko na Allah sai taga furen ya kwanta cikin ƙasar tukunyar, alamar mamallakin shi bacci yake yi, murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, aranta ta raya cewa Batool taji lallashin da take yi mata shiyasa tayi shiru ta kwanta tana bacci, A hankali ta mayar da idanuwanta kan furen daddynta, tafi yarda dana batool akan nashi, saboda shi bata da tabbacin yana raye koya mutu, Jikin furen yayi kore shar dashi, kuma iccen yaɗan miƙe ba kamar lokacin farko da ya fito a lanƙwashe ba, Ziraran yatsun hannunta ta ɗaura asaman furen daddynta tare da shafa ganyen shi, a fili ta furta I wish kana araye daddyna, har yanzun kana nan acikin zuciyata, ba abinda ya sauya daga ƙaunar da nake yi maka, I luv u so much, zan cigaba dayi maka addu’a kaida batool ɗina da kuma ƴan uwana prisoners, Alƙawarine na ɗaukarwa kaina,”

murmushi tasaki tana faɗin”Har na tuna lokacin da na ƙala maka sharrin cewa kai ba mahaifina bane, ɗan yankar kaine, aranar kasha bugu wurin ƴan ƙato da gora, kuma duk da abunda nayi maka hakan baisa ka guje ni ba, saima ka ƙara ƙaunata, ashe babu rabon xamu ƙare rayuwarmu atare…..haka na dinga burin in zama house wife, ashe da rabon in zama prison wife, Gidan hutun da nake burin inyi aure, har ina faɗa ma aunty aneelerh zan auri hamshaƙin mai kuɗi saboda masu aiki su dinga yi mini hidima ina daga kwance, sai gashi na ƙare agidan kurkukun ƙaddara, wayyo Allah na, babu daddyna babu aunty aneelerh da uncle uzair, babu mommy adamana da uncle abdallah, babu makaranta, babu house wife, duk waɗannan burinkan sun tashi a tutar babu…..”

daƙyar ta ƙarasa yin maganar saboda kukan da yafi karfinta, ta kifa kanta saman gwiwowinta taci gaba da kuka, tana fadin nayi danasani daddyna ka yafe mini, wlh ina matuƙar ƙaunarka, dama saida ka fada mini cewa bani da tamkarka a duniyar nan yanzu na shida hakan…..’

Duk wannan suratan da take yi akan kunnan Danish, Ya ɗan jingina kanshi jikin ƙopar toilet ɗin, Ya natsu yana sauraronta, Hakanan taji aranta kamar akwai mutun abayan ta, a hankali ta ɗan dago da kanta, tana ƙoƙarin juyawa ta kalli bayanta danish yai saurin fita daga Cikin toilet din ya tsaya daga waje, Yana faman sauke ajiyar zuciya,

Baiyi tsammanin ta biyo shi ba, Sai dai yaji ta ambaci sunan shi,

“Danish”! Kasa juyawa baya yae don ya kalleta, duk yabi ya kama kanshi,

“Shine kana ji inata kuka ko kazo ka lallashe ni” Yayi mamakin jin abunda ta ce, cije lips ɗinsa yae kafin yace”Saboda me zanzo in lallashe ki? Ko kin manta alƙawarin dana ɗaukar miki? Batare daya juyo ya kalleta ba, yayi maganar,

“Meyasa kake bibiyata? Nasan saboda ni kazo bakin ƙopar toilet din nan ka tsaya, Allah kaɗai yasan tun lokacin da kake kallona, kaga kuwa Alƙawarin Ya jima da karyewa,”

girgiza kanshi ya ɗan yi tare da cewa”bana sa6a alƙawari, idan kin manta bari in tuna maki, kin ce kada na kurkura na ƙara hada ido dake kinaso in nisanta kaina agare ki, Tabbas nazo bakin ƙopar toilet din kuma na kalle ki amma ban bari mun hada ido ba. Hope kin fahimta yanzu ban karya miki alƙawarinki ba, Tun da bamu haɗa ido da juna ba kuma banzo kusa dake ba,”

Harara ta shiga jefa ma bayan shi, kamar ƙwayar idanuwan zasu faɗo ƙasa, wani irin kewarshi take ji kamar tae hauka, tayi danasanin sanya shi ya ɗaukar mata alƙawarin nan, ta manta cewa Prisoners basu Iya karya alƙawari ba, ta inda suka banbanta da mutanan dake rayuwa awaje kenan, majority dinsu basa ƙarya kuma basu Iya gulma ba, musamman DANISH!

Takaici ne ya isheta, Can dai tace”Idan nace na fasa alƙawarin fa”? Danish ya bata amsa da cewa”Idan kin fasa Ni bansa fa, bazai ta6a yiyuwa ba” yana faɗin hakan Ya wuce cikin dakinsu yabarta a tsaye tana faman cizon le6enta,

Daga bisani ta gyaɗa kai tare da wuce wa ta nufi cikin dakin, a kwance ta same shi saman gadon shi ya rungume pillow, ta6e baki tayi kafi ta nufi nata gadon ta haye ta zauna daga tsakiyarshi ta ɗaga hannayenta sama tana jera addu’o’i, Cikin harshen larabci,

ta ɗauki tsawon lokaci daga bisani ta shafa hannayenta saman fuskarta, kafin ta gyara kwanciyarta, Sai da ta lumshe idanuwanta, Zuciyarta ta soma tariyo mata maganganun da tsohuwa ta faɗa musu kafin tafiyarta, tabbas akwai wasu kalamai da tayi aciki waɗanda suka ɗaure mata kanta, ta kasa fahimtar inda suka dosa, Duk irin kaifin basirarta, ta gaza gano menene tsohuwa take nufi, da tace musu su dauka cewa su makullaine da zasu Iya buɗewa kansu ƙopar farin ciki, tayaya kenan? daƙyar ta samu bacci ya ɗauketa a daren ranar,!

Ko a washe garin ranar babu wanda ya sanya sabon uniform ɗinshi acikinsu, damuwar rashin tsohuwa ta hanasu sukuni, ga fargabar zuwan tsohuwa Zafreen, da kuma new prisoners, daga Sunji motsin ƙopa a firgice suke kallon ƙopar, don suga wanane, a ƙarshe sai su ga bakowa, Kunnuwansu ne kawai suke Jiyo musu hakan, sakamakon sanya rai da suka yi, wasa wasa yau har tsawon 2 weeks da tafiyar tsohuwa babu wani sabon Labari, ta ko’ina shiru kake ji, su kaɗai suke rayuwarsu, hankalinsu har ya ɗan kwanta don a tunaninsu, An ƙyalesu ne su yi rayuwarsu su kaɗai, Bakomai yafi ɗaga musu hankali ba, face rashin batool don a lissafinsu yau Wata ɗaya kenan babu Ƴar uwarsu acikinsu, Ba’a dawo musu da ita, har sun fara fidda rai da sake ganinta 🥺

*PRISONERS💔*

Yau tun da sassafe Angel da hanna suka taimaka ma ƴan uwansu mata wurin gyara sumar kansu, gwanin ban sha’awa kowa saida suka wanke mashi sumar kanshi, suka gyara musu ita, su kansu ba ƙaramin daɗi suka ji ba, ganin yadda sumar kansu tayi kyau ga laushi da kyan gani a ido, ga wani irin ƙamshi da gashin nasu yake fitarwa mai daɗin shaƙa, Bayan Sun kammala gyara ma su azeeza, Hanna da angel suke koma toilet, saboda su wanke nasu gashin kan, sai da angel ta kammala wanke ma hanna, ya rage saura ita, duk yadda hanna taso ta wanke mata gashin kanta, hakan ya faskara, saboda uban yawan dake gare shi, Gashi ya nannaɗe yadda kasan taliyar indomi, Tun tana nish tana ƙoƙarin tattaro gashin kan Angel, kamar hannunta zasu 6alle, a ƙarshe data ga abun yafi ƙarfinta, sai ta fita tabar angel acikin toilet ɗin, sai gasu sun shigo kusan su Shida hada su javed da naufal, wai sun zo wanke mata kai, ashe bayan da hannah ta fita daga cikin toilet ɗin, ɗakinsu ta shiga taje ta kira su, donsu taimaka mata, mamaki Ya kama angel, ganin sun shigo suna nannaɗe hannuwan rigunansu, Kusan dambe akayi acikin toilet din, tana faɗin ita bata so su barshi ta haƙura da wanke gashin, Su kuma suka ce bata isa ba, Yadda aka wanke ma kowa gashi, Itama sai sun wanke mata nata, ko tana ko bata so, A lokacin Danish Yana la6e bakin ƙopar toilet din yana kallonsu, don ba ƙaramin nishaɗi ya samu ba, ganin yadda suke ta yawo acikin toilet din sai zagaye shi suke yi, Ita tana gudu su kuma suna bin bayanta hannayensu ruƙe da shower gel da comb, da sauran abubuwan da zasu yi amfani dasu wurin wanke mata gashin su gyara mata shi, Sai da kowannansu Ya gama galabaita, tukunna suka samu ta basu haɗin kai, Su shida suka wanke mata gashin kanta, tadaici azaba, har wani jiri take gani acikin idanuwanta, saboda yadda suke ja mata gashin, Bayan sun kammala wanke mata shi, waɗanda ke ruƙe da combs, suka soma sharce mata shi, daga bisani suka bi da mayukan gyaran gashi suka shasshafa mata, ‘ Lokacin da suka kammala, Sunyi mamaki Ganin irin yadda gashin kanta ke ta ɗaukar ido, yayi dark brown dashi ya warware tamkar hijabi yayi mata abayanta, ta yi farin Ciki sosai da suka taimaka mata wurin gyara mata gashin kanta, ta ƙara jin ƙaunarsu acikin zuciyarta,

Kafin marece ya doso, ɗaya bayan ɗaya suka soma shiga toilet suna Yin wanka, saboda yau sun shirya canza Uniform dinsu, sai ɗauki suke Yi zasu sanya sabbin kaya, Bayan sun kammala Yin wankan, Ya rage saura Danish Yaƙi zuwa yai wanka, Hatta mazan sun wanke sumar kansu, amma shi duk ya takure kanshi, Ya hana kanshi sukuni acikinsu, duk da ayanzu babu wanda yake nuna mishi wariya, tun ranar da tsohuwa tayi musu faɗa akan su daina ware shi acikinsu, tun daga ranar suka daina gaba da shi, Shi ɗin ne dai kamar baison suna kusanto shi, Kuma bakowa yaja hakan ba face Angel, ita ɗin dai ce da baya son ya karya mata alƙawari.

Ganin baida niyar tsohuwa ya wanke sumar kanshi Yasa haris zuwa har saman gadonshi, Ya damƙo hannun shi ya janyoshi, Har saida ya sauko daga saman gadonshi suka nufi toilet, Yana fadin Allah idan bakai wanka ba, Ni zanyi maka da kaina, kowa yana nishaɗi sai kai kaɗai duk kabi ka takura rayuwarka sai kace wani bare, Idanma don abunda ya faru ne ae mun yafe maka komai ya wuce mana, tun da ya riga daya faru,” Kamar wani ubanshi haka haris ya dage yana tayi mishi faɗa, har suka shiga cikin toilet din, bawan Allah yai shiru bai tanka mishi ba, haris bai fito daga cikin toilet din ba sai da ya taimaka mashi ya wanke sumar kanshi, Kafin Ya fito yabarshi aciki, don yayi wankan,

Kafin wani lokaci, duk suka hallara acikin ɗakinsu, Angel ta janyo musu akwatin kayansu Ta bude shi, a hankali take zaro uniforms ɗin tana miƙa musu, da yake tasan numbers ɗinsu, shiyasa ba ta sha wahala wurin banbanta na kowa ba, Bayan kowa ya kar6i nashi, nan fa suka soma sanya su ajikinsu, Cikin dabara, Idan suka cire tsohon wandon, sai su zura sabon a jikinsu ta yadda tsiraicinsu bazai fita ba, kafin ma su sanya kayan ajikinsu saida angel ta biya musu addu’ar sanya sabbin tufafi, duk suka yi banda Danish, Ya ruƙe kayan a hannunshi yana zaune gefen gadonshi, babu alamun zai zurasu ajikinshi,

Uniform din sunyi bala’in yi musu kyau, yadda kasan ɗaliban high school na ƙasar Korea, Tabarakallahu ahsanul khalikin, Kyau ne ya haɗu da kyau, abunka ga farare kayan sun fiddo da hasken fatarsu, Sun bi shape din jikinsu sun zauna musu cuf cuf, Especially angel, Wow abun ba’a magana, Yarinyar dama can kalar kyau ce, Ƙarshe ce afagen kyau, Hatta ƴan uwanta su azeeza sai santin kyanta suke Yi, duk da irin kyan da su kayi don itama azeeza ba daga baya ba, jajayen kayanta sun mayar da ita tamkar fure awurin kyau, musamman in tayi dariya fararen hakoran nan suka bayyana ajere kamar gonar auduga, tubarkalla,

Danish fa sai satar kallon angel yake yi da zarar Ta juyo zata fuskanci inda yake sai yae saurin kawar da kanshi gefe, baisan cewa ta lura da irin satar kallon da yake yi mata ba, hakan ba ƙaramin dadi ya yi mata ba,

bakomai Yafi ƙawata kyan uniform ɗinsu ba face Cotton scarves din da suka daura awuyansu, da kuma igiyar wrap coat dinsu da suka daure, Sai takalmansu, da kuma ribbom da matan suka ɗaure Sumar kansu dashi, Banda angel saboda sanin yawan gashinta shiyasa bata yi gigin sanya ribbon ta daure shi ba, don zai iya tsinkewa, hatta giants da suka zo kawo musu abinci, sai da suka yi musu wani abu daya basu mamaki, da hannu suka yi musu thumbs up, wato alamar jinjina, wannan abun dai ya gigitasu, basu ta6a yi musu hakan ba sai yau da suka ga sun ɗauki wanka, angel dai bataji dadi ba, saboda tasan ƙarshe duk wannan gayun da suke Yi, abanza zai tashi, tun da ba fasa daukarsu za’ayi ba, sai daga baya tadinga danasanin Gyaran gashin da su kayi da sabbin uniform ɗin da suka sanya ajikinsu, don ba ƙaramin fiddo da kyawun surar jikinsu kayan su kayi ba, hakan zai ƙara ma ƴan iskan ƙaimi wurin biyan buƙatarsu da su, zasu ji daɗin gur6ata musu rayuwa, in ba haka ba taya akai giants da basu magana Yau kawai don sunga sunyi kyau shine suka yi musu alamar jinjina wato sun burgesu da suka yi gayu, aiko dai akwai matsala babba!!

(Next page gobe in Allah yakaimu da rai da lafiya, wandanda suka shirya yin payment Ga link na wadda zakuyi ma magana, Ku danna zai kai ku ga account ɗinta👇)

https://www.facebook.com/manal.muhd?mibextid=ZbWKwL

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

 

 

( mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, masu yi mun ya jiki ina godiya)

 

Back to top button