Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 30 By Hafsat Bature

💋KURKUKUN ƘADDARA💋

Dedicated to Aunty kubra❤

E30

Daga alƙalamin Boss Bature writer of Abban sojoji✍️

*Back to Prison*

After One Day👌

Wani irin narkakken Jini ne mai kauri da ƙarni yake gangarowa ta cikin ƙoramar ruwan dake Gudana, Sassan Jikin mutun ta gani gunduwa gunduwa tsulundum acikin Jinin, Hannu tasa ta dafe kanta tare da fashewa da matsancin kuka na fitar hayyaci,

A firgice ta farka daga baccin da take yi sakamakon bugun ƙafarta da aka yi, wata irin Zabura Ta yi tare da miƙe wa zaune, Tana binsu Da Kallo, ɗaya Bayan ɗaya, Suna a kewaye da gadonta, Batool Hanna hibba, Azeeza, yasmin, eve, javed Sai kiran sunanta suke Yi suna tambayarta lafiya? Me take ma kuka? Abunda ya faru suna a kwance saman gadajensu suka soma Jin shessheƙar kukan angel, Hakan yasa suka yi gaggawar zuwa gaban gadonta don suji dalilin yin kukan nata,

“Angel meya faru ne? Duk kin bi kin ruɗe? ko kinyi mummunan mafarki ne”? batool ce ta jefa mata tambayoyin,

Ƙanƙame Jikinta Ta yi da hannayenta, wata irin zufa Ce ke tsastsafo mata ajikin fatarta, Sai faman zazzare Manyan idanuwanta take Yi, gaba ɗaya bata Acikin hayyacinta, tayi matuƙar tsorata da mafarkin da tayi, muryarta na kerma ta soma Magana”Ina parveen? ina rubina da Deeja an dawo dasu? Ko kuwa har yanzu? Takai ƙarshen maganar tana kallonsu Batool,

Angel Still ba’a dawo dasu ba, Abincin da muka rage musu tun jiya ya riga da ya lalace, da mun sani mun cinye shi,” Hanna ce ta bata amsa, Azeeza tace”Yanzu shikenan baza adawo mana da su Parveenar mu ba? sun tafi kenan”? Muryarta a sanyaye tayi maganar, Hibba tace”Pls Azeeza stop sayin that bana jin daɗi, kuna karya mana zuciya, Tsohuwa fa tace za’a dawo dasu da zarar Sun samu lafiya,” Eve ce ta kalli Hibba da tayi maganar tace”Hib kin manta lokacin baya? Ƴan uwanmu da muke atare dasu? Wasu in an ɗauke su ba’a dawowa dasu sun tafi kenan”? Idon angel akansu tana sauraronsu, kwata kwata bata acikin natsuwarta, tana matuƙar jin tsoron ta yi mummunan mafarki, saboda Xaiyi wuya mafarkinta yaƙi xama gaskiya, kafin zuwanta gidan kurkukun ƙaddara saida tafara mafarkin kasancewa acikin shi kuma sai ga shi ta tabbata, ta tsinci kanta acikin shi,

“Yakamata mu daina wannan maganar, Muna ƙara tayar wa junan mu hankali, Idan muka kwantar da hankalin mu, za’a dawo dasu ne,” acewar Javed, yasmin tace”Yanzu me zamuyi toh? Ni nagaji da zama zugudum, ” fuskarta a yamutse Tayi maganar,

Azeeza tace”Muna da abunyi mana, Angel zata Wanke mana gashin kanmu, ta kuma gyara mana shi, ” tunkan takai karshen maganar, yasmin ta harare ta”Kefa matsalarki kenan, Sai ana magana ta hankali ki wani soko wa mutane Shiririta aciki,” zum6ura baki Azeeza Ta yi tare da murguɗawa mata shi tace”To me kike so Muyi? Wanka ko motsa Jiki? Ko kuma bacci? Ko giants xamu Jira su kawo mana abinci”?
Banza yasmin tayi da ita, Zama batool tayi a gefen gadon angel, ta ruƙo hannun angel acikin nata tace”Sister, na lura sam bakya acikin hayyacin ki, Ki faɗa mini, me kika gani acikin baccin ki wanda ya tsoratar dake”? Idanuwan angel cike tab da ƙwalla ta ɗago ta kalli fuskar batool, bazata Iya faɗa mata ainihin abunda ta gani acikin mafarkin ta ba, Saboda Bata son ta tayar mata da hankali, Kuma faɗin baida amfani, sannan ma babu kyau mutun yayi mummunan mafarki ya faɗi ma wasu,

Don haka tace mata”bakomai batool Just bana Jin daɗin Jikina ne,”

“Ko zakiyi wanka ne? May be kiji daɗin Jikin ki,” cikin sanyin murya tace”eh, xanyi, ” tana rufe baki Azeeza tace”Angel me zamuyi yau”? Murmushi angel ta ƙaƙalo, yayin da take kallonta tace”Little Kome kike so Shi za’ayi, ” ashagwa6e Azeeza ta bubbuga ƙafar tare da cewa”Ni kidaina ce mun little bana so,” gaba ɗaya su kayi dariya, Hanna tace”Ae gaskiya ta faɗi, kallarki fa? Wata ƴar ƙarama dake, Ko kafaɗarmu baki kai ba, banta6a ganin wadda bata cigaba ba acikinmu irin ki, Duk yawan abincin da kike Ci sam baki ƙara auki, ba ƙiba ba tsawo,” dariya suka saki gaba ɗayansu, Rai a6ace Azeeza Ta zuƙunna kasa tana yin kukan ƙarya, Angel tace”pls kudaina janta, Nima na faɗi ne kawai don ayi nishaɗi, amma azeeza ae itace babbarmu,” ta yi maganar tana ƙyaftawa musu ido, atare suka haɗa baki wurin cewa”hakane Azeeza itace babbarmu, muma wasa muke Yi mata, don kawai ayi raha ne” Sunsan azeeza da son girma, jin wannan maganar tasu yasa ta miƙe tana gumtse dariya abaki,

Angel tace mata”Me kike so Muyi yanzu?
“Ki wanke mana gashin kanmu, Kuma ki gyara mana, keda batool kamar yadda ku kayi mana ran nan kin tuna’? Zaro ido angel tayi”Azeeza Baki ga yadda na farka ba yau, sam babu natsuwa atare dani, Taya zamu Iya wanke maku wannan uban gashin kan naku, Kuma mu gyara shi,? Ta6e baki azeeza ta yi, Itafa in taso abu to ayi mata kawai, idan ba haka ba yini zatayi tana faman tur6une musu fuska duk da tana da yawan fara’a kamar Gonar auduga,
“Kada Ki damu sister azeeza, Koda angel bata samu damar tayani ba, Ni xan gyara maku gashin kanku, Mu barta ta huta, tun da bata Jin daɗi, Kuxo muje toilet,” Batool ce ta yi maganar, Ta juya ta nufi toilet suka bi bayanta,

Bayan tafiyarsu Cikin toilet, Angel ta sauke ajiyar zuciya, tare da jingina bayanta Jikin bango, Gefe ta juyar da kanta tana kallon Gadon danish, kamar dai kullum yana a kudundune Cikin bargo, Haris da mubeen da Javed hada naufal duk basu farka daga Bacci ba, sakamon daren da su kayi jiya batare da sun runtsa ba, Suna Xaman Jiran adawo musu ƴan uwansu,

Saƙe saƙe ta shiga Yi acikin zuciyarta, game da wasu tambayoyi da suka cunkushe mata kwakwalwarta, sun hanata sakat, idan ta takura kanta akan tunaninsu Har wani matsanancin ciwon kai take ji, tabbas tana son Yin magana da tsohuwa duk da tasan zaiyi wuya tsohuwa ta amsa mata tambayoyinta, amma zata jaraba tunkararta, Yau ɗin nan,

A6angaren su Batool, sai da tabi kowannan su ɗaya bayan ɗaya ta wanke musu sumar kawunansu, Baƙaramar wahala tasha ba, domin kuwa Dukansu tsayin gashinsu Ya zarce midback ɗinsu, Ga uban yawa dake gare shi, bayan ta kammala wanke musu gashin, Sai da kowannan su Yayi wanka, Kafin suka dawo Cikin ɗakin, Kamar yarda suka bar angel zaune saman gadonta haka suka sameta, ganin sun fito daga wankan Yasa itama ta miƙe domin zuwa yin wankan, Shigarta da ƴan mintuna ta fito, A lokacin Danish dasu Mubeen duk sun farka daga bacci, saukowa su ka yi daga saman gadajen su, Atare suka Nufi Toilet domin suma suyi wankan ko sunji daɗin Jikin su.

A zaune ta samu batool gefen gado ta ruƙe Comb, Zata Gyara musu gashin kansu, hakanan taji tana sha’awar Tayi musu Kitson kalaba Guda Biyu akansu don ta Iyata, Kallon batool tayi tare da cewa”Ki bari In yi musu kitson Kalaba, Nasan ba’ata6a Yi maku ba, Yau zan jaraba mu gani idan zan iya” Cike da Jin daɗi Batool ta mika mata Comb ɗin, Tasa hannu ta kar6a, tare da samun wuri gefen gadon batul ta xauna, Ta ɗago ta kalli su Azeeza dake ta murna za’a gyara musu gashi tace Su zazzauna a ƙasa, zata fara gyarawa azeeza nata idan ta kammala mata zata Kira ta gaba da zata yi mawa,

A ƙasan gadon azeeza ta zauna tsakankanin ƙafafuwan angel, Hannu angel ta sanya tare da Ruƙo sumar kan Azeeza, Launin gashin kanta Dark blonde, mostly Turawa ne suke da irin wannan gashin kan, sharce sumar kan angel tayi, Kafin Ta raba gashin zuwa gida Biyu, a tsanake Ta soma yi mata kalaba, Tunkafin ta kammala su Hanna sai santin kalabar suke yi, duk sun ƙagara a kammala Yima azeeza suma ayi musu, Guda Biyu tayi mata shima daƙyar ta samu Tayi su saboda santsin gashin Ga tsayi da yawa, Tun da aka kammala Yima azeeza kitson, ta miƙe ta koma gefe tana ruƙe wutsiyoyin kalabar da hannayenta, Sai tsalle Take yi Wutsiyoyin kalabar suna yin sama da ƙasa, ita fa yau ta samu abun wasa,

Ɗaya Bayan ɗaya saida angel tayi musu kitson kalaba guda Biyu, Koda akazo kan Batool sai cewa tayi ta gaji bazata Iya ba, bakomai yasa tace haka ba face Fargabar Ta yadda zata Iya kama Gashin batool, Baƙar wahala zata Ci saboda yawan dake gare shi gashi kamar roba kuma Curly irin nata, a dole batool ta haƙura badan taso ba,

Danish Basu Jima da fitowa daga wanka ba, Giants suka zo Kawo musu abinci, Kamar Jiya haka Yau ma suka ɗibarwa Su Parveen Abincin acikin kwandonsu, Da niyar idan Allah yasa Aka dawo dasu Yau sai su basu su ci, gudun kada adawo dasu Da yunwa,

Bayan sun Kammala Cin abincin, Giants suka tattara Farantan suka Fuce daga Cikin ɗakin,

Duk sun damu da rashin ƴan uwansu, hakan yasa suka kasa samun natsuwa especially angel, Zarya ta soma Yi acikin aɗakin, idan takai ƙarshen bango saita dawo ta sake zagayowa, Har saida ƙafafuwanta suka soma Yi mata raɗadi tukunna ta dakata da yin zirga zirgar, Ta nufi gadonta da niyar ta huta, gefen gadon ta zauna Zugudum, Zuciyarta acike fal da tunanin duniya, wuraren marece su ka Jiyo alamun motsin buɗe ƙopar ɗakin tsohuwa, Bayin Allah da gudu suka duro daga saman gadajensu, Jikinsu na 6ari suka ƙarasa ƙopar ɗakin nata suna jira ta fito,

Sandar hannunta ce ta fara leƙowa, Kafin ta zuro kai ta fito waje, Jikinta sanye da jan doguwar rigar nan ta gado,

Kusan atare suka haɗa baki Wurin gaishe da ita, Ta amsa masu fuskarta asake, Sai faman mamular baki take Yi kamar me cin goro, fuskarnan a jagwale saboda tsabar tsufa ta koma kamar aljana, hurhura ta ko’ina,

“Tsohuwa Ya jikinsu Deeja? Tun jiya muke ta tsammanin jiran dawowarsu amma shiru ba’a dawo mana dasu ba, Munyi kewarsu sosai, Bacci ma daƙyar muka Yi shi, Ko abinci bama Jin daɗin Cin shi saboda rashin ƴan uwanmu” yasmin ce tayi maganar cikin nuna damuwarta,

Mubeen Yace”tun daga Lokacin da aka ɗaukesu har zuwa Yau, kullum Cikin zullumi muke,” Angel dai ta tsareta da ido kamar yarda itama tsohuwar idonta ke akan angel, Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,

“Kinyi shiru baki bamu amsa ba? Yaushe za’a dawo mana da ƴan uwanmu? Idan mensturation ne Yanzu ya isa ace jikinsu Yayi sauƙi,” Fuska aɗaure angel ta yi mata maganar,

Jinjina kai tsohuwa Tayi, Sai da ta mula tasha Iska Tukunna tace”Ƴan uwanku suna acikin koshin Lafiya, Bazan Iya sanar daku lokacin da za’a dawo dasu ba, Saboda bani da masaniya, amma nasan bazasu wuce Cikin week ɗin nan ba,” A ƙagare Azeeza tace”Dagaske Su parveen Sun Ji sauƙi? Kuma Suna tambayar mu? Suma sunyi kewarmu”? Murmushi tsohuwa ta sakar mata tare da cewa”Eh mana, sun damu daku sosai, Kuma suna tambayarku, da zarar Sun ƙarasa Jin sauƙi za’a dawo maku da su” wani irin murmushin farin Ciki ne Ya bayyana akan fuskokinsu, In ka cire mutun Huɗu Batool Angel da javed sam babu walwala akan fuskokinsu, Baka iya tantance awani yanayi suke ciki, da alama suna kokwanton kalaman Tsohuwa, sun dai yi shiru ne kawai,

“Just for today, Ki kaimu inda suke domin muyi musu Ya jiki, Tunda Kince Suma sun Yi kewar mu, hakan zai rage musu damuwa” angel ce tayi maganar

Girgiza kai tsohuwa Tayi tare da cewa”Ba’a bada iznin ɗaya daga Cikin ku, Yaje inda suke ba, Idan Ku ka yi hakuri zasu dawo ne” batare da angel ta yi mata musu ba tace”Shikenan zamu zuba ido mu gani idan za’a dawo mana dasu”

Kallon su Batool angel tayi tare da cewa”Ku koma kuje ku zauna, inaso zanyi magana da tsohuwa” Jin wannan maganar yasa tsohuwa tayi saurin kallon angel fuskarta da alamun mamaki,

Juyawa su batool suka Yi atare suka tafi izuwa saman gadajensu, duk wannan abun dake faruwa danish Yana a kwance saman shimfiɗarshi, ko sarki bazai nuna mashi Jin daɗin gado ba, Ya cancanci da akirashi da MAJI DAƊIN GADO,

“Ƴar nan ina sauraron ki, wata Irin magana ce ki ke son Yi dani kuma? Yau ke da kanki”? tsohuwace tayi maganar, fuskarta akwa6e,

cikin sanyin murya angel tace”Inaso mu shiga daga Cikin ɗakin ki, Muyi magana” zaro ido waje tsohuwa tayi jin abunda angel tace, Can kuma saita yamutsa fuska tace”Ba dole sai mun shiga daga Ciki ba, Kome Ki ke son tattaunawa dani, Kiyi mini magana anan ya wadatar”

“Meyasa baki son in shiga ɗakin ki”? Ko akwai wani abu da bakya son in gani ne? Da tuhuma angel tayi mata maganar, girgiza kai tsohuwa ta yi tare da cewa”Babu abunda nake 6oyewa kawai dai bana bada iznin A shiga ɗakina, idan magana zakiyi dani to mu yi ta anan, babu wanda zai ji mu,”

Ta6e baki angel ta ɗanyi still idanuwanta akan tsohuwa tace”yau tsawon shekarata Biyu agidan kurkukun ƙaddara, Ban ta6a ganin wani ya shiga Cikin ɗakin ki ba, Bansan me kike 6oye mana ba, Amatsayinki na uwa agare su, meyasa baki bari muna leƙawa cikin ɗakin ki? Kuma bakya zama acikin mu domin Yin fira, Ko hakan ya sa6awa dokar prison ne”?

Bazawarin murmushi tsohuwa tasaki kafin ta Juya Tana dogara sanda tace da angel”Ki shigo daga Ciki,” tsananin mamaki ne Ya kama angel, Jin ta amince mata akan ta shiga Cikin ɗakin nata,

Sai da angel ta fara juyawa ta kalli su batool, ganin hankalinsu gaba ɗaya baya akansu Yasa ta bi bayan tsohuwa, Kafin ta shiga ɗakin tsohuwa Sai da takaranta addu’o’in neman tsari, sannan ta zura ƙafarta Cikin ɗakin, bakinta ɗauke da sallama,

A tsakiyar ɗakin Angel Ta tsaya tana bin Ɗakin tsohuwa da kallo, Abun mamaki abun al’ajabi, Bakomai bane aciki face Shufke sufken fulawowi,Ta ko’ina tamkar ɗan garde, Sai wasu tsoffin Kujeru guda Biyu suna fuskantar Juna, tsakiyarsu table ne mai ɗauke da Tea pot, da ƙananun Kofina guda Biyu, bayansu babu wani abu na furniture, Gado ko katifa,

Bayan ta kammala Kallon Cikin ɗakin na tsohuwa, Ta wurga idanuwanta kan tsohuwa dake yunƙurin zama saman ɗaya daga Cikin kujerun guda biyu dake fuskantar juna,

Muryarta angel ce ta katse mata hanzarinta da cewa”ina kayan ɗakin suke? Naga babu gado ko katifa? A ina kike kwana”?

Wata irin mahaukaciyar dariya tsohuwa tasaki, Mai matuƙar sautin gaske, Angel tuni tasha jinin jikinta, Muryar tsohuwa ashaƙe tace”Ƴar nan Badai Iya tambaya ba, Dama ganin kwakwaf kika zo Yi mini acikin ɗakin nawa? Keda kika ce Magana zamuyi ae kamata Yayi ki zo ki zauna ga kujera har ma da shayinmu na tsoffi in zuba maki musha don muji daɗin tattaunawa” Takai ƙarshen maganar tana nunawa angel kujerar da hannunta,

Jikinta tamkar na wadda aka zarewa Laka haka Taci gaba da tafiya Ta nufi kujerun Ta shiga Ciki ta zauna, tana Bin tsohuwa da kallon Ban yarda dake ba,

Ƙarasa xama saman kujerar tsohuwa Tayi, a yayin da suke fuskantar Juna ita da angel, Ido cikin ido suke Kallon juna,

“Ina sauraronki wata magana ce kikeson tattaunawa dani”? Ta yi tambayar a ƙagare da son ji,

Angel da ƙarfin hali tace”Tambayoyi ne nake son Yi maki, Ina fata zaki amsa mani” Wani irin kallo tsohuwa ta jefa mata, da mitsi mitsin idanuwanta,

Cigaba da magana angel tayi”Badan Hali na ba, Alfarmace nake nema awurinki, duk da nasan zaiyi wuya ki amsa mini tambayoyina, bansani ba ko yin hakan ya sa6awa dokar Prison”

Gajeren murmushi tsohuwa ta saki, kafin tace”A dokar gidan kurkukun ƙaddara, Ba’a ba mu damar Yin magana da prisoner ba dangane da abunda ya shafi Kurkukun, Yin hakan babban laifina wanda hukuncinsa mutuwa ne……….” aruɗe angel ta ɗan zaro ido tana kallonta, Tsohuwa tace”Kinga kuwa babu ta yadda za’ai In iya amsa maki tambayoyinki kodan saboda in tsira da raina”

Angel tace”Amma ae babu mai ganin mu, Daga Ni sai ke ne acikin ɗakin nan, Babu wanda zai san anyi” Cikin sigar wayau angel ta yi maganar, hakan ba ƙaramin dariya yaba tsohuwa ba, ganin ƙaramar yarinya na neman raina mata hankali, su da suka ga jiya suka yau

“Mu sha Tea mana, ” tayi maganar tare da kai hannu ta ɗauki tea pot, tana tsirara musu ruwan tea Acikin Cups,

“Ko kin zuba bazan Sha ba,” acewar angel, kallonta tsohuwa tayi”saboda me”?
“Ban yarda da duk wani abu da zai fito daga gare ki ba,”
“Amma meyasa ƴar nan”?

“Saboda Ina kokwanto Akan shayin da da zaki bani, Shekaran Jiya da kika ba su batool apples Sunyi bacci Na tsawon yini guda batare da sun farka ba, Har safiya tayi, ina da tabbacin cewa silar apples ɗin da kika basu ne, Shiyasa nake tsoron in sha tea ɗin nan, wata’ƙil kinsa Poison aciki,”

Fuskar tsohuwa ɗauke da murmushi tace”Da ace naso kashe ki da tuni na aiwatar da hakan, kada ki manta kina acikin ɗakina ke kaɗai, Koda sandar hannu zan Iya cutar dake, ƴan uwanki kuma dana bawa Apples Taimakonsu Nayi saboda bani da ikon da zansa Giants su dawo masu da abinci, Shiyasa na baku Apples ɗinmu na gidan kurkukun ƙaddara, Domin kuyi bacci Har gobe Ta yi saurin zagayowa ko kun samu Ku ci abinci” dariya angel ta ɗanyi Tare da cewa”Hakan Yayi kyau, yanzu dai tun da bakyaso In tambayeki agame da kurkukun ƙaddara, Inaso Nayi maki tambaya biyu bata Cikin kurkukun bace….”tsohuwa tace “ina sauraronki”

“Gidan Kurkukun ƙaddara A Cikin Nigeria Yake? Sa’an nan kince Mutum baya ta6a kasance Acikin kurkukun nan dole sai in na Jininsa ne Ya sadaukar da shi, Abunda da nake so In sani, Na jinin naka daya sadaukar dakai Kamar wa kenan”?

“Kin manta abunda na faɗa maki kenan? kiyi mini ko wace irin tambaya amma kada Ki tambayeni game da gidan kurkukun nan…..” tunkan takai karshen maganar angel ta katse ta da cewa”Amma ae ba’a Cikin kurkukun Nayi maki tambayar ba, Kawai ni inaso insan a wace nahiya Yake, Sannan Na jininka da zai Iya sadaukar dakai Kamar wa kenan”?

Tsohuwa bata amsa mata tambayarta ba, sai da ta fara miƙa hannu ta ɗauki kofin da ta zuba shayi acikin shi, takai bakinta tana kur6arshi kusan sau uku, Angel dai ta zuba mata ido, bayan ta Ajiye kofin saman table ɗin, Tana faman mulmula baki tace”Shayin da daɗi, Ki jaraba sha mana” girgiza kai angel tayi”Na ƙoshi, ni dai kawai ki amsa mini tambayata” dariya tsohuwa tayi”Ban ta6a ganin yarinya mai wayau da kaifin basira ba irin naki, Gaskiya Iyayenki Sun Iya haihuwa gaki Kyakkyawa Kamar ke kika ƙera Kyanki,..” ɗaure fuska angel tayi ganin tsohuwa Na ƙoƙarin Kaucewa Tambayarta, ta hanyar canza wani zancen,

Rai a6ace tace”ba wannan na tambayeki ba, Ki bani amsar tambayarta,”

Jinjina kai tsohuwa Ta yi idonta acikin na angel tace”idan na baki amsar tambayarki, Ni kuma me xaki bani? Kinsan ance gwammanti bata aikin banza” kallon rainin wayau angel tayi mata”Amma ae kinsan bani da abunda zan Iya biyanki da shi ko?, Ni dai kawai ki amsa mini tambayata”

 

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

 

 

( mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, masu yi mun ya jiki ina godiya)

Back to top button