Hausa novels

Cuta Ta Dau Cuta Chapter 2 By Billyn Abdull Complete Novel

Billyn Abdull Novel

*_Typing📲_*

   *_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_

_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_

_Shafi na biyu_

……..“Ai babu gurin zuwa, saboda da hannunka ka rufe duka ƙofofin guduwar Mr JJ ango mijin amarya Alimah”. Muryar da baya jin zai manta a rayuwarsa ta ratsa kunnuwansa. Dauriyarsa ta ƙare, hakama ƙarfin halinsa ya kai ƙarshe. A take jikinsa ya fara rawa kar-kar. Gashi an riƙesa irin riƙon da ko numfashin kirki ya gagara yi. Jin saukar numfashin mutum a fuskarsa ta saka shi buɗe idanunsa da sauri. A matuƙar razane ya fasa gigitacciyar ƙarar data ɗauke numfashinsa gaba ɗaya sai gashi ƙasa wanwar a sume…..

       A firgice ta buɗe idanunta itama tamkar wadda aka farkar da ga nannauyan barci. Waige-waige ta fara ƙirjinta na wani irin luguden daka. To ita yaushe ma barci ya ɗauketa ne, ba yanzu babu jimawa suka shigo ɗakin nan tare da angonta JJ ba. Dan fitarsa babu daɗewa rakkiyar abokansa ko cikakken minti biyu baiyi ba ya dawo, batama jin yabar jikin ƙofar falon. Cike da zumuɗi da aka san duk wani ango da shi ya koma ya zauna inda ya tashi a kusa da ita. Batare da yayi magana ba kawai ya jawota jikinsa ya rungume yana shinshinar wuyanta. Kunya ta sakata shiga wani yanayi, a take jikinta ya fara mazari ta shiga noƙewa. Dariya ya sakar mata cikin kunne da faɗin, “Ai yau dai kunya ta ƙare Love, miya rage kin zama matar JJ, JJ ya zama mijinki. Please ki ajiye wannan kunyar da safe ƙya maidata dan kin san yau ɗin ta musamman ce fa”.
Bata iya tace da shi komai ba, dan a matsanancin tsorace take ga kuma kunya. Sai dai hakan baisa ta hanashi yin yanda yaso da ita ba. Bayan ya gama shinshinar ta ne da rungumeta ya ɗakkota cak zuwa wannan ɗakin yana faɗin, “Yanzu dai muje muyi sallah kafin komai ko. Dan nasan matar tawa ustaziya ce”.
A karo na farko ta sakar masa murmushi, tare da tura kanta a jikinsa dan kunya takeji matuƙa kamar me. Dan tunda take a rayuwarta bata jin wani ya taɓa riƙe mata hannu, sai a jiya wajen dinner da JJ ya aikata hakan gareta. To ita dai tasan sun shigo ɗaki, daga haka kuma bata san miya faruba sai ƙarar ihun nan da bata san daga ina ya fito ba da ya farkar da ita, a yanda kuma taga kanta alamu sun nuna barci tayi. Gadon ta sakko da sauri, sai kuma tai tsamm ta dakata saboda jin motsin ruwa a toilet ɗin ɗakin, hakan na nufin JJ na ciki kenan. Numfashi ta ɗan sauke a hankali, tare da komawa ta zauna tana gyara mayafinta, zuciyarta na tabbatar mata wanka ya shiga kenan, ita kuma barci ya ɗauke ta, ihun da taji kuma maybe a maƙwafta ne. To amma abin mamakin anan taya tayi barcin? Haka cikin ƙanƙanin lokaci? Rashin amsa ya sakata ɗan sauke numfashi kawai.. dai-dai nan JJ ya fito a toilet ɗin babu alamar wanka yayi sai dai ko alwala. Kanta ta duƙar ganin ita yake kallo, shi kuma ya saki murmushin da har ta iya jiyo sautinsa da ga inda take tare da faɗin, “Naga a takure kike, jeki falo ki jirani”.
Kamar mai jiran jin hakan ta mike zumbur, har harɗewa take wajen fita tana mai sauke ajiyar zuciya, sai dai mamaki fal kanta dan sai take jin kamar wani banbarakwai hakan nan….

      (Bake kaɗai ba amarya, ni kaina fa man kai na ya tsiyaye. Dan na gagara fahimtar komai, shin JJ ɗin ne ba mutum ba ko ke kanki? Masu karatu ko akwai mai amsa min?🥱😆🚴).

    ★★…..

   A ɓangaren JJ ango kam zubur ya miƙa tare da sauke nannauyan numfashi alamar farfaɗowa da ga sumar da ya tafi. Gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi a yanzu, dan tun bayan numfashin da ya kawo cikin zabura sai kuma ya koma laƙwas kwance yana maida idanunsa a hankali ya sake lumshewa. Falaƙi da Naasi ya fara karantawa a zuciyarsa yana ɗan buɗe ido kaɗan, shiru babu motsin komai, sai wata iska mai daɗi dake ƙaɗawa. Kamar wanda aka bama ƙarfi ya miƙe zaune dingangan, waige-waige ya shigayi idanunsa a buɗe sosai mamaki fal kansa na ganinsa a baranda kwance wanwar, tabbas a waje yake, ya kuma kasa iya tuna komai da ya faru. Babu alamar akwai wani abu da zuciyarsa ke ayyana masa kuma, sai ma wata nutsuwa da yake ji ga zuciyarsa na tabbatar masa faɗuwa yay kenan bayan yama abokansa rakkiya, dan abinda ya fara tunawa kenan kafin gittawar da akai masa lokacin da yake ɗaura hannunsa saman handle ɗin ƙofa, sai kuma abinda ya faru na shigarsa falo dama ɗaki, hakan na nufin komai daya faru a mafarki ne ba zahiri ba dai kenan. A take ya gamsu da hakan, dan kamar an masa wanki ƙwaƙwalwa ne ma ya kasa tuna komai a yanda ya kamata balle yayi tunani irin na mutane masu hankali. Sai ma amaryarsa da ta zo masa a zuciya. Miƙewa yay tamkar wanda aka tsikara, ya gyara zaman babbar rigarsa da hula sannan ya ɗaura hannunsa a handle ɗin ƙofar ya murza a hankali yana sakin wani murmushin farin ciki.
A inda ya barta nan ya sameta, tana lulluɓe dai har yanzu cikin mayafinta. Sai ƙamshinta daya gama gauraye falon mai shegen daɗi. Taku ya cigaba dayi cikin shauƙi da bajinta zuwa gareta. Kusa da ita daf ya tsaya batare daya zauna ba ya zuba mata shu’uman idanunsa da suka sake ƙanƙancewa. Tsahon mintuna biyu kafin ya kai durƙushe ƙasa tamkar ɗa a gaban uwarsa. Hannu biyu ya saka ya ɗaga mayafinta ƙyaƙyƙyawar fuskarta mai alamun rashin yawan hayaniya ta bayyana. Ga kwarjini irin wanda aka san amarya da shi tattare da ita. A hankali ya sauke ajiyar zuciya tare da kamo hannayenta da take matsewa cikin juna ya riƙe, sun sha jan lalle da baƙi sai sheƙi suke. Ɗagosu yay zuwa bakinsa ya sumbata tsakkiyarsu ɗaya bayan ɗaya. Sosai ta sake ƙanƙame jikinta da sinne kanta na kunya…
“Babu gaisuwa Love?”.
Ya faɗa cikin wata irin siririyar murya. Kanta ta sake sinnewa cikin tata muryar da ke rawa ta ce, “Kayi haƙuri ina yini”.
“Ai baƙya laifi amarya koda kin kashe JJ ne ma. Dama wannan golden voice ɗin nake son ji ne. Ina miki Barka da zuwa gidanki, fadarki. Alƙawarin ALLAH ya cika yau gani ga Love ɗina a gida ɗaya matsayin ma’aurata. Babu abinda zance da UBANGIJI sai godiya. Kisa a ranki har abada bake ba kishiya, ko’a aljanna ke kaɗai ce”.
Murmushi ta saki a karo na farko, sai dai bawai ta amshi kalaman nashi bane da muhimmancin riƙewa, dan duk da ƙananun shekarunta kuma ita bamai yawan hayaniya bace da taron ƙawaye tanada iliminta. Tasha jin yayunsu na faɗin yarda da irin waɗan nan kalaman a bakin namiji yaudarar kaine kawai..
Shiko tuni murmushin nata ya kashesa, dan a tunaninsa kalamansa sunyi irin tasirin da yake buƙata. Tashi yay daga ƙasan da yake ya koma saman kujera kusa da ita, gaba ɗayanta ya jawo ta koma saman cinyarsa ya rungumeta tsam-tsam yana sauke numfashi da sauri-sauri. Dan maganin da MB ya basa ya fara aiki. Itako gaba ɗaya ta gama rikicewa da kunya da tsoro, sai dai batai yunƙurin jaye jikinta ba kamar ɗazun. Tsahon mintuna uku suna a haka kafin ya ɗago fuskarta, kallonta yake tamkar a yau ya fara ganinta, anan ɗin ma dai yaja wasu mintuna biyun cur sannan ya miƙe ɗauke da ita yana faɗin, “Muje muyi sallar godiya ga ALLAH sannan kici abinci da ga nan sai ki…..” ya ƙarasa faɗa mata cikin kunne yana sakin wata siririyar shaƙiyyar dariya. Itako jitai gaba ɗaya ta rikice, gashi yana ɗauke da ita, sai kawai ta sake cusa kanta cikin jikinsa har suka iso ɗakin bata yarda ta ɗago ba. Ba ɗakin da ya kaita bane ɗazun, ta fahimci hakanne lokacin da yake sauketa a kofar toilet ɗin yana faɗin, “Je kiyo alwala bara na rage rigar nan tamun nauyi. Kanta a ƙasa ta amsa da to, ya bita da kallo har sai da ta shige sannan ya juyo yana murmushi da ƙoƙarin cire babbar rigar tasa. Cikin sauri ya ƙarasa janye rigar daga fuskarsa ƙirjinsa na wani irin harbawa. Sai kuma ya waiga da sauri ya kalli ƙofar toilet ɗin, sake waigowa yay ya kuma kalli gadon. Amaryar tasa dai ce data shiga toilet akan idanunsa yanzu zaune a tsakkiyar gado kuma tana murmushi. (Kodai ƙwaya MB ya bani ne) ya faɗa a zuciya jikinsa na rawa, da sauri ya juya baya zuwa ƙofar toilet ɗin. Buɗewa yay ya leƙa. Alimah amarya dake ƙoƙarin fara alwala ta ɗago da sauri.
“Sorry” ya faɗa bakinsa na rawa tare da ja mata ƙofar ya rufe yana juyowa. Yanzun kam gadon wayam babu kowa, yana nan tsaff da shi a gyare tamkar yanda suka shigo suka samesa.. Sautin kuka ne ya fara ratsa ɗakin a hankali har ana shashsheka, da sauri ya buɗe idanunsa daya lumshe na jin relief da farko ya fara waige-waige. Jin zai faɗi ya sashi kaiwa zaune bakin gado, a bisa tsautsayi bai zauna da kyau ba ya zame kasan carpet wanwar. Sai kuma ya miƙe zaune dingangan zuciyarsa na wani irin gudu a cikin ƙirjinsa. Ƙaruwa sautin kukan yake, sai dai babu kowa a ɗakin sai shi kaɗai ɗin dai Alimah bata fito ba. Cikin tsumar jiki ya dafe hannayensa duka biyu ƙasa da nufin jan jikinsa koda da rarrafe ya kai ga toilet yaji ya camɓalasu cikin laima mai kauri da ɗumi, da sauri ya ɗago duka hannayen, yay bala’in waro idanunsa waje tare da maida kallonsa ga ƙasan. Tabbas jini ne malale a duka ɗakin tamkar yanda tiles yake, ga sautin kukan nan na ƙaruwa. A karo na farko JJ ya fashe da kuka kawai idonsa a hanyar toilet komai daya faru ɗazun na dawo masa a zahiri. “Na shiga uku ni Jazool. Mike faruwa dani?…” ya sake ɓarkewa da kuka…..
Dariya ce ta karaɗe ɗakin a maimakon kukan da ake rairawa da farko. Kamar kaɗawar iska a cikin kunnensa aka gwargwaɗa masa, “Oh oh mazan fama kuma da kuka haka. Karka bada maza mana JJ ango” sai kuma aka ƙyalƙyale da dariya mai cika kunnuwa data sake rikita JJ. Kamar ƙyaftawar ido aka kuma ɗaga shi cak aka sauke saman lafiyayyen gadon ɗakin da yasha shimfiɗar alfarma. Yana ƙoƙarin zabura ya miƙe aka rungumeshi..
“Uhhm my D ina kuma zaka? Kasan fa wannan daren na musamman ne a garemu”. Aka faɗa masa a cikin kunne ana kaima wuyarsa sumbata. Bashi da zaɓin da ya wuce wage baki ya ɓarka ihu kawai ko zai samu agajin wannan tashin hankali da ga maƙwafta, sai dai me yana wage bakin caraf aka cafke harshensa cikin wani salo aka hau sumbata tare da sake ƙanƙamesa tamau. Duk yanda JJ yaso yin wani yunƙuri ya kasa hakan, yana ji yana gani aka suleshi zigidir. Kafin a sakar masa baki tare da jirkicesa ya koma ƙasa akai masa rumfa. Fuskar amaryarsa ce ta bayyana a idanunsa, ta sakar masa lallausan murmushi da kashe mar ido ɗaya cike da salon so da ƙauna…
“My D! Ya kake abu kamar wani matsoraci. Karfa ka manta wannan shine dare mafi girma a wajenmu. Daren da kake ta faman zumuɗin zuwansa da lissafinsa.” ta ƙare maganar cikin wata iriyar shagwaɓaɓɓiyar murya tana shafo fuskarsa.
Jujjuya kansa kawai yake hawaye na gangaro masa. Magana yake son yi amma da alama sautinta ya gagara fitowa, sai lips ɗinsa ke wata irin rawa ga hawaye ga majina ga zufa sun masa sharkaf a ƙyaƙyƙyawar fuskarsa ma’abociyar shan gyara iri daban-daban. Sumbata ta sake kaima lips ɗinsa tana dariya, sai kuma ta ɗagashi zaune itama tana zaman harda tamkwashe ƙafa suna fuskantar juna. Ita dai sanye take cikin tufafinta harda mayafi, shiko an masa zigidir sai faman kare jikinsa yake da hannu. Dariya ta sake kwashewa da shi tana kallon yanda yake mammatse jiki. Cikin dariyar take faɗin, “Haba angona minene kuma na ɓoye jiki bayan so nake na kalleka da ƙyau yau ɗin nan. Karfa ka manta ka zama Alimah, Alimah kuma ta zama kai. Jiya aka ɗaura mana aure, yau aka kawoni gidanka. Miya rage kuma garemu banda baje kolin soyayya D?. Koka manta kana tare da Love ɗinka ce, ƴar shilar yarinyar nan mai shekaru goma sha bakwai kacal. Mai tarbiyya da ilimin addini. Kamila ga kunya kullum tana a cikin hijjab. Ƴar malamai da bata san komai ba sai zuwa islamiyya da aikin gida. Haba My JJ”. Ta ƙare faɗa da salon shagwaɓa a yanzun ma har tana turza ƙafafu a gadon. Sake ɓarkewa da kuka JJ yayi lokacin da idanunsa suka sauka akan ƙafafun nata. Dan amaimakon ƙafa shikam kofatai ya gani irin na shanu da dokuna. Ganin ƙafar yake kallo yana kuka itama ta kalli ƙafar, sai ta ɓarke da dariya harda kwanciya kafin ta tashi zaune da ƙyau tana haɗe fuska tamkar ba itace ta gama dariyar ba. Haɓarsa ta kamo tare da matso da fuskarsa gab da tata ta sumbaci lips ɗinsa, sai kuma ta zuro wani irin dogon harshe kamar ana fitowa da abu a rami ta fara lashe shi. Luuuu kawai yayi ya sake sumewa……..✍️

_😂😂😂 Gaskiya JJ kana bada maza a wannan al’amari . JJ na buƙatar addu’a fa🚴🚴🚴🚴😆🥱_

Click Here To Read Cuta Ta Dau Cuta Chapter 3 By Billyn Abdull Complete Novel

*_ALLAH ka gafarta ma iyayenmu😭🙏🏻_*

Back to top button