Gargadar So Chapter 27 By M Shakur
Sosai take yarfe hannunta sabida yanda yake mata zafi jini na diddiga takasa motsi daga wajen tana kuka har saida security guard sukazo wajen daya rikeda bag nata da phone yace “Ma’am is everything okay your hand is bleeding we believe this is your own” yamika mata jakanta da wayanta, hannunta mai lafiya takai ta goge fuskanta tass but dudda haka idanunta sunyi jazur alamun kuka sannan takai hannun daman kasa tana kokarin mikewa dan bayanta ciwo yake mata da dabara ta iya mikewa tsaye but tsabagen yanda batada karfi kawai ta luuuuu tai baya runtse idanunta tayi gam kawai ta sadakar tafadi charab taji an tareta tafada kan hannun dataji daya a waist nata daya a shoulder ta, ga kamshi mai bala’in dadi dake ratsa hancinta, almost 10secs tayi batai motsi ba kuma ba’a saketa ba kafin gently tafara bude idanunta dahar yaji yaji suke mata sabida kuka ta sauke rinannun idanun nata acikin na Khaleel dake kallonta awkwardly gadan toothpick abakisa tana iya hango kirjinshi sabida yanda baisa boturan gaban shirt nashi ba as usual, wani irin zabura tayi tafita daga jikinshi cikeda tsana tajuya ta karbi wayan nata da bag daga hannun security zata wuce cikin yar iskan voice yace “so you’re into gurls? I see no wonder kike tsani maza” tsayawa tayi tana kallon gefenta zuciyanta namata radadi, Khaleel yazo gefenta yakai hannu yana zare toothpick daga bakinshi cikeda neman tsokana irin na yan iskan yara yakai hannunshi gaban fuskanta yana waving yace “I feel sad she shatter your heart” yamata wani dan iskan kallo yanadan murmushi, Hawwa kawai ta tawuce da sauri tana share fuskanta dan yau batada karfi, daga murya Khaleel yayi yace “seeing you like this is so satisfying” bude motanta tayi ta shiga ta tada motan taja da mahaukacin gudu tabar eatery kuka kawai take hannunta na mata radadi har lokacin jini na fita though ba sosai kaman d’a ba.Ana magrib a masallaci takai gida Baba bayanan yana masallaci, fitowa tayi ahankali cus bayanta namata ciwo tarufe motan tashiga gida, daki tawuce ta zauna gaban madubinta tana jawo drawer tadauki spirit tazuba a tsakiyan hannu kara tayi tana fashewa da kuka sosai sannan tasa auduga ta goggege ciwukan hannunta, bottle water dake wajen tadauka tana kallo sai alokacin ta tuna tana azumi goge fuskanta tayı da bayan hannu takai ruwan baki tasha, ta lallaba tamike tafito tadauro alwala tadawo tahau kan dadduma tai salla, ta kwanta kan dadduma tana kallon saman dakinta bini bini tana goge hawayen dakebin fuskanta, saikuma chan tamika hannunta tadauki wayanta tai dialing number Ni’iman amman baya shiga busy busy taje watsapp tamata message baya shiga taga bata ganin DP dinta yau, blocking dinta kenan tayi.Rawa hannayenta suka fara cus in wildest dream nata bata taba tunanin Ni’ima can block her ba, tadauka duk maganganun datake dazu fushi ne, blocking dinnan hit Hawwa daban kawai tafashe da kuka tayi harta godema Allah, kawai saitaji rayuwan yamata daci, bazatai karyaba harda Ni’ima as part of the reason da bata damuwa da rashin aure, sabida tana debe mata kewa, waya, chatting, labarai abinda yafaru wajen aiki da sauransu, zuwa outing all those abubuwa makes her forget about actual problem nata, kanninta duka sunyi aure banda ita, gabaki dayan layinsu itace babban dabatai aureba kannin kanninta sunyi aure, hannunta dake mata zugi da Ni’ima ta taka da takalmi tadaga ta kalla sai kawai ta lumshe idanu hawaye na zubomata daga ido masu zafi tawani kanannade kanta a dadduma kaman macijiya ahaka aka kira isha’i ta lallaba tayi tareda shafa’i da wuturiWayan takara dauka tasake dialing number Ni’ima but busy wayan nata tadaura akan fuska tafashe da kuka mai zafi hawaye na diddiga akan screen na wayan for all this years da abubuwan dake faruwa da ita bata taba feeling broken ba like yau, yau jitayi da defense system nata da will of power nata da komima ma yayi breaking she’s weak, cire wayan tayi daga kunnenta tai dialing number Ammi ringing daya Ammi tadauka tace “Hawwa yaya how is your Monday? Kindawo daga aiki? Ya Baban naki ince bai cigaba da rigima dake b…….” Rage murya tayi sabida yanda takejin sheshekan kukan HawwaLumshe idanu Ammi tayi rabon dataji kukan Hawwa haka tun zamanin rasuwan mahaifiyarta cikeda so tace “Baba ne” girgizamata kai Hawwa tayi tace “Ammi Ni’ima tarabu da…da….d…..” takasa magana ma tsabagen kuka zuciyan Ammi bugawa ya shiga dan wlh tanason Hawwa sama da nata yaran ma bata wasa da ita, dasauri Baffa dake gefenta yace “Malam yasake mata wani abu ne?” Girgizamai kai Ammi tayi tamai alamu daya dakata tana sauraron yanda Hawwa kemata kuka batama iya magana ahankali Ammi tace “Hawwa ya isa, kukan ya isa haka? So kike hankalina yatashi nashigo hanya da daddaren nan?” Girgizamata kai Hawwa tayi Ammi tace “calm down Hawwa komi yayi zafi maganinsa Allah, kowace kaddara daga Allah yake, it’s okay Hawwa na, it’s okay kinji, ya isa hakanan ya isa”Akwai wani kalan natsuwa da kalaman Ammi ke bata ahankali tasoma rage kukan Ammi tace “meya faru tell me everything” da kyar ta iya fadama Ammi komi dudda kuka nafin karfin maganan nata but still Ammi manage to understand komi, wlh deep down tasan za’ai haka, ahankali ta zauna abakin gadon idanunta sun ciko da hawaye da sauri Baffa ya girgiza mata kai alamun kartayi she will break Hawwa even more, hadiyesu tayi tace “Ni’ima is angry I understand don’t pay attention to much to maganganun ta, itama ko’ina take im sure tanachan tana kuka kalan wannan dakikeyi, kunyi building strong relationship da Ni’ima da banjin zaiyi breaking hakanan ba just give her some time Hawwa, and stop crying”Ya isa ya isa, Ammi tai maganan cikeda tausasa zuciya maganganu masu dadi tashiga gayama Hawwa ahaka bacci yayi awon gaba da ita anan kasa kan dadduma. Ammi ta katse wayan takalli Baffa dayaji komi tace “nakira Ni’iman?” Gyadamata kai yayi dialing number Ni’ima tayi wayan yayi ringing harya katse ba’a dagaba saita sake kira but busy itama ansata a blacklist takira kusan 5times but haka zata sake kira Baffa yace “ya isa! Basai kin sake kiranta ba, bakomi rayuwa ce, bari zan ma abokanen aikina magana idan zan iya samana Hawwa wani aikin ağarın nan saita dawo nan zaria ta manta da damuwanta”Around 5 ta Hawwa ta tashi cikinta namata ciwo dana yunwa dana MP, bayanta shima na ciwo, kayan aiki ta da bata cire jiyaba tacire ta daura zani tafito, wanka tayi da brush da alawala tadawo ta shirya yau cikin simple office gown black tasa tai salla, tadauki black shades tasa cus idanunta sun kumbura sosai tawuce tafito Baba na masallaci, warming Mota tayi kafin taja motar tabar anguwan, Awani eatery ta tsaya tasai abinci, koda ta shigo office nata tabude abincin tagumi tayi tana kallon food din, saiga hawaye sharewa tayi dasauri takai hannunta tasake daga wayanta tai dialing number Ni’ima but busy tayi blocking nata true true, ijiyan zuciya ta sauke gwanin ban tausayi ta debi rice din takai baki da kyar ta hadiye baya mata dadi bakinta is just dry, rufe takeaway tayi ta ijiye agefenta tai shiru tana kallon waje daya tunani kawai take, rannan takasa komi har saida aka bata break cus tace batada lpy and kowa yagani kam she looks sick da kyar take tafiya DIG yace taje taga Dr tahuta cus Hawwa is strong bata fashi, she’s serious da aiki he needs her healthy.Around 1 takoma gida Baba na zaune awaje ya gantaDa sauri ya yunkuro yana kallon yanda tai parking tafito ahankali tana daukan jakanta da kyar, ganin yanda fuskanta yayi jajir hakama hancinta yasa dasauri yayi wajenta kafin tama iso yace “meyasameki awajen aiki Hawwa?” Ahankali asanyaye tace “banda lpy ne Baba” dasauri ya shiga kama crutches nashi a hammata yakai hannunshi yana taba goshinta yace “subhanallahi sannu Hawwa kinsha magani konasa asayo miki”? Ahankali tace “eh nasha” cikeda damuwa yace “assha sannu, sannu kinji, kawo jakan muje ciki” yakarbi jakan yana ratayawa a kafadansa sukai ciki…Har gaban dakinta saida yaga tabude ta shiga ciki sannan yawuce kitchen da kanshi ya shiga bude bude yadebo mata shinkafa da miya a kwano da zafinsa yafito yazo gaban dakin yana bugawa yace “nashigo”? Ahankali ba karfi a muryanta tace “eh” kofa yabude ya shiga da plate na abincin a hannunsa tashi zaune tayi dan tana shiga kwanciya tayi ko kaya bata cireba yabata abincin yace “ci, ci idan zazzabin bai kwanta ba saina kaiki asibitin su Ni’ima” sunan Ni’ima da Baba yakira kawai saiga hawaye sha hankalin Baba yatashi da sauri yaja kujera ya zauna gaban fadin yana ijiye crutches dinsa yace “Hawwa menene eh? Meke damunki? Wlh na hakura tunda kin nuna baki kaunar Alhaji Kabiru nimadai naga yamiki tsufa nafasa bari ki aureshi kinji, kiyakuri kome nagaya miki kwanakin baya eh Hawwa na, ya isa kukan, dena dena” yakai hannunshi yana sharemata fuska ta bala’in bashi tausayi, yashafa kanta yace “to ya isa ci abincin abinki ko kadan ne” yanda Baba yadamu yasa tadebi kadan takai bakinta da kyar tahadiye, yanda yaga tanayi yasa yace “kawo abincin bari naje nasayo kaza sai asoya miki kici abarbada cabbage da yaji da tumatir haka mahaifiyarki keson kaza” murmushi tamai kadan, tashi yayi yana dafa bango yasa mata filo akan gadon yace “kwanta da kyau kinji” kwanciya tayi yace “karki rufa jikinki na zafi” gyadamai kai tayi Baba yadauki abincin yana kallonta yawuce yafita yana gyaramata labule.


