Hausa novels

Ruwan Zuma Page 51 Hausa Novel

(51)  Washe gari da misalin k’arfe goma na safe jirgin su Ammi ya sauk’a a Kano, Alhaji Abdul shi da kanshi ya je ya d’aukosu suka fara ajiye kayansu a gidan sannan ya kawo su zuwa gidan Haydar.  Har cikin gidan ya shigo da motar suka fiffito sannan ya kira maigadi ya shigar da wasu ledoji manya har da akwati cikin gidan, daga nan kuma ya fara k’okarin juyawa zai fita Ammi ta dakatar dashi tana cewa, “Ina kuma zaka je? Ka ce mini kaima baka ga Jaririn ba.” Murmusawa yayi wanda iyakarta fatar baki yace, “Sai daga baya zan zo Ammi, yanzu dai Baba ya gama ya fito mu tafi.” “Ka fito mu shiga tare, menene amfanin zaman ka a waje?”Fad’in Baba yana tsareshi da ido.  Ganin da gaske sun kafe dole sai ya shiga yasa yayi ajiyar zuciya yace, “Haydar ba zai so ganina a cikin gidansa tare da matarsa ba. Ko haihuwan nan bai fad’a mini ba sai a bakinki na ji Ammi, bana son in yi abun da zai k’ara tunzurashi ya k’ara tsanata. Gaisuwan da muke yi ma na godewa Allah kuma ya isa haka, ku yi hak’uri ba musu nake yi daku ba illa gujewa fitina.” Yana rufe baki Haydar ya fito daga k’ofar falonsa yana ganinsu fara’arsa ta yawaita ya tako zuwa gurinsu.  Ammi ya fara runguma yana cewa, “Na jima ban ganki ba Ammina.”   Yayin da ita kuma take murmusawa tana cewa, “Kai dai Ali baka girma. Da d’anka kake sakalci?” Saketa yayi ya koma gurin Baba wanda ya mik’a mishi hannu suka gaisa kana ya dubi Alhaji Abdul wanda har lokacin yana cikin mota yace, “Sannunka. Ya yau?” “Lafiya kalau. Mun samu k’aruwa.” “Eh.” Kawai Haydar ya fad’a fuskarsa babu wannan fara’ar ta d’azu. “Allah ya raya mana Baby boy.” Alhaji Abdul ya mishi addu’a kana ya tayar da motar yayi reverse zai je waje ya jira Baba. “Baba, Ammi mu shiga ciki ku ga Bundle of joy.” Haydar Ya fad’i hakan yana jawo hannun Ammi wacce ta bishi bayan ta lura da halin da Baba ya shiga bayan ya ga yanda Haydar ya yi treating Yayansa.  Babu musu suka bishi a baya zuwa falonshi kana ya bud’e k’ofar da ke tsakanin falonsa da na Laila ya je ya kar6o Baby a hannun wasu bak’i ya mik’awa Ammi.  Ammi tana ganin yaron fuskarta ta washe sai murmushi take yi bakinta har kunne. Baba ma da yake gefenta murmushin ne shinfid’e a fuskarsa yana shafa kan yaron a hankali cikin so da k’auna. “Yana kama da kai sosai Ali, lokacin da kake jariri fuskarka sak irin nashi sai dai ya fika girman jiki ne.” Fad’in Ammi tana duba yaron wanda ke bud’e idonshi a hankali yana juya kanshi zai nemi nono. “Ya farka ko? Yanzu zai saka kuka idan ba’a bashi nono ba.” Fad’in Haydar yana duban bakin k’ofa in da Laila ta shigo sanye cikin hijabi tana aiko musu da murmushi tana cewa, “Marhaba, sannun ku da zuwa.” Kana ta fara k’ok’arin zama a k’asa Ammi tayi saurin dakatar da ita ta ce, “Kul, zauna a sama. Kina jego ai zaman k’asa ba naki bane Laila.”   Laila da dama tunanin yanda zata zauna a k’asan take yi ta mik’e ta zauna a kujera a hankali don har lokacin tana jin ciwon d’inkin da aka mata.  Ammi ta mik’awa Baba jaririn wanda da kyar ya iya rik’ewa sai da ta gyara mishi kan yaron don tangal-tangal yake yi. “Rabon dana rik’e jariri har na manta, ina ga tun haihuwar Abdul.” Maganar Baba kenan da yasa kowa a mamaki. “Lallai abun ya jima.” Fad’in Ammi cikin tausayawa mijin nata, saboda tana tuna irin kwallafa rai da yayi a cikin Haydar amma Allah bai bashi ikon rik’e d’an nashi ba sai da ya girma har yayi aure.  Gaisawa suka yi cikin marmarin ganin juna, sannan Baba ya rik’e kan yaron ya fara mishi addu’a yana tofa mishi har na wasu mintuna sannan ya gama ya mayar wa Ammi yaron ta k’ar6a. Baba ya tashi tsaye yana cewa, “Mun ga jariri Allah ya raya mana shi. Lu’a idan kin gama ki kira Abdul ya dawo da ke gida.” “Zan mayar da ita Baba.” Haydar yayi saurin fad’a yana tashi tsaye zai raka Baba. Ammi ce ta mishi wani mugun kallo sannan tace, “Maganarka za’a bi ko ta Babanka?” Sai a lokacin Haydar ya gane yayi laifi yayi saurin gyara zancen sa da cewa, “Ina nufin kar ya wahala ne wajen zuwa d’aukoki, tun da ni ina nan sai kawai in mayar da ke. Amma ku yi hak’uri in hakan bai muku dad’i ba.” Baba murmushi yayi yace, “Duk yanda kayi ya yi daidai Aliyu Haydar. Sai anjima.” Da haka ya fita daga falon Haydar ya mara mishi baya har zuwa gurin motar ya bud’e mishi suka tafi. Yana dawowa cikin falon ya samu Laila na bawa jariri nono yayin da Ammi tayi shiru fuskarta babu fara’a ko kad’an. “Ammi lafiya na ganki haka? Baki da lafiya ne?” Shine Abun da ya fara fad’a yana neman zama a kusa da ita. “Koma can Ali.” Tace dashi tana nuna mishi gurin da ya zauna tun d’azu. Babu musu ya koma ya zauna amma hankalinshi ya tashi da yanayinta yana ta kallonta. Ammi ce ta fara magana bayan ta mayar da hankalinta kanshi ta ce, “Yanzu kai abun da kake yi ya dace? Haihuwa aka maka amma ka kasa sanar da d’an uwanka jininka sai dai ya ji a gari? Yaushe ka zama mai rik’o haka? So kake yi ka zama mara godiya ga Allah ga duk abun da yayi maka?” Laila ce ta d’ago kanta ta dubi Haydar wanda ke mata ido alamar ta tafi, ba shiri ta d’auki d’anta ta mik’e Ammi ta dubeta tace, “Ina zaki je? Ai laifin bashi kad’ai bane har da naki, zauna.” Laila komawa ta yi ta zauna tana cewa, “Wallahi Ammi ina fad’a mishi hakan da yake yi bai dace ba, k’arshe kafa mini doka yayi ya ce kar in sake d’auko mishi maganar baya so. Na yi iya bakin k’ok’arina domin in nuna mishi fushin da yake yi da d’an uwansa yayi yawa har ina bashi misalin tsakanina da Yaya Madu yanzu babu gaba sai zumunci mun ajiye komai a gefe tamkar ba’a yi ba. Ki yi hak’uri Ammi amma abun ya fi k’arfina ne shiyasa na yi shiru.” Ta k’arisa maganan tana kallon Haydar wanda ya had’a girar sama da k’asa kansa a k’asa yana murza yatsun hannunsa. “Ali kaine mai taurin kan kenan?” Ammi ta watso masa tambaya wacce tasa ya d’ago kanshi yana rage tsumewan ya ce, “Ammi don Allah idan zaki mini fad’a ki daina yi a gabanta bana jin dad’in hakan. Yanzun ma ban ga amfanin zamanta a nan d’in ba tun da ni zaki yiwa fad’an ba ita ba.” “Zaka nuna mini abun da ya fi dacewa kenan kamar yanda ka so nunawa Babanka d’azu ko? Yaushe ka zama haka ne Ali? Wallahi wannan ba tarbiyyar dana baka ba kenan.” Shiru yayi ya sadda kanshi k’asa bai ce komai ba, Laila kuma na ganin haka ta dubi Ammi tace, “Na yi bak’i wanda suka zo ganin jariri na taho nan bamu gaisa ba Ammi.” “Tsoron Alin kike ji shine kike neman guduwa daga nan ko?” Ta wutsiyar ido Laila ta kalli Haydar ta ga da gaske baya son kasancewarta a gurin kana ta mayar da dubanta ga Ammi ta girgiza kanta ta ce, “Ba haka bane Ammi.”“Tashi ki tafi.” Fad’in Ammi tana jin sanyi a ranta ganin Laila na bawa d’anta girma a matsayinshi na mijinta. Tana fita Ammi ta dawo da dubanta ga Haydar wanda shima tafiyar Laila yasa ya sassauto kad’an ta ce, “Meyasa kake mu’amala da Abdul kamar ba jininka ba? Ina son sanin laifin me yayi maka da har ka kasa koyan hak’urin zama dashi.” Shiru Haydar ya sake yi a karo na biyu wanda hakan ya fara bawa Ammi haushi ta ce, “Baka ji ina maka magana bane kana shiru Aliyu Haydar?” Yanda ta kira dukkan sunanshi yasa ya gane ranta ya 6aci bana wasa ba. Tashi yayi daga in da yake ya zo ya zauna a k’asa kusa da k’afafunta ya dubeta fuskarsa gwanin ban tausayi ya ce, “Ammi ba wai zan yi musu da ke ko kuma in nuna miki abun da kike fad’a ba gaskiya bane, sai dai ina buk’atar lokaci ne kafin in fara sake jikina dashi. Abubuwan da yayi sun yi yawan da ban hak’uri ko yafiya ba zai sa a yi saurin mancewa da su ba.” “Idan ban manta ba kace Laila da Abul ya cutar ba kai ba, kai kuma idan za’a duba gata yayi maka ba kad’an ba duk da cewa yayi niyyar cutar da kai a k’arshe amma Allah bai bashi sa’a ba. To ita Lailan ma da ya cutar da d’anta ta yafe mishi sannan har take nuna maka rashin amfanin abun da kake yi. Abdul yayanka ne wanda jinin da ke gudana a jikinshi shi yake gudu a naka, shi kuma uban naku ko bai nuna maka a fuska ba wallahi a zuciyarsa ba zai ji dad’in yanda kake yiwa d’ansa ba duk girman laifinsa. Wani irin rahama ce Allah bai maka ba fiye dashi? Wani irin fifiko ne Allah bai maka ba? Allah ya baka Matar da Abdul yake so shi kuma ya hanashi. Allah ya bayyana maka danginka kamar yanda kaci buri ba tare da iyawarka ba. Allah ya wadataka da arziki da nitsuwa, ya kare ka daga sharrin duk wanda ya nufeka da sharri, ya kuma wadata ka da samun mace tagari sannan ya k’ara maka da albarka d’a alhali shi wanda kake fushin dashi bashi da wad’annan abubuwan, Ali wannan bai isa ya nuna maka cewa Allah yana sonka ba? Idan kuma kana maganar girman laifi ne sai ka tuna ni da mahaifinka kuma wace irin rayuwa muka yi kafin mu sameka, idan zaka cigaba da fushi da Abdul akan abun da yayi a baya ya kuma rok’i gafararka to muma zaka iya cigaba da fushi damu akan halinmu na baya wanda baka son a furta.” “Ammi don girman Allah na rok’eki ki daina tuna mini wannan abun.” Ya yi maganar hawaye na taruwa a idanunsa yana kallonta. “Sai ka mini alk’awarin gyara tsakaninka da Abdul don laifinshi k’arami ne a kan namu amma ka iya cigaba da zumunci da mu bayan ka samu labarin komai.” Sadda kanshi yayi a k’asa wannan karon hawaye na zuba a fuskarsa ba tare da ya ce komai ba. Ganin hakan yasa Ammi taci gaba da magana cikin rarrashi tana cewa, “Wata biyar kenan har da d’ori da faruwar wannan abun Haydar, Abdul ya canja ya daina munanan d’abi’unsa hatta neman mata da yake yi ya daina. Wallahi kullum idan ya zo Abuja a gidanmu yake sauk’a baya zuwa gidansa ya kwana. Yana girmamani sannan yana bani kulawa tamkar dama duk tsawon lokacin nan ya sanni kuma muna tare. Idan ya zo gida har abinci yake dafa mana duk da girmansa, kuma idan ina buk’atar wani abu kafin in sanar da Babanku shi nake fara kira ya mini ba wani ba. Ya zama tamkar d’ana dana haifa da cikina Ali. Kullum kuma maganarshi in yafewa mahaifiyar shi abun da ta mini ni kuma ban fasa jaddada mishi cewa na yafe mata ba saboda na lura hakan yana sanyaya mishi rai yana jin dad’i. Ali rashin kula d’an uwanka da kake yi yana yiwa mahaifinku zafi sai dai bai ta6a furtawa ba, akwai ranar dana d’auko mishi zancen amma cewa yayi duk laifin Abdul ne ba naka ba, amma nasan ba zai k’i ya ga kayi hak’uri kun kulla zumunci tsakaninku ba. Ita Lailan da abun ya faru a kanta ma ta hak’ura sannan taci gaba da zumunci da yayanta duk da irin muguntar da ya yi mata a rayuwarta. Shin wannan ba zai zama ishara a gareka ba cewa komai na duniyan nan d’an hak’uri ne? Tun da yayi nadama na gaskiya sai ka bashi damar da zai gyara laifukanshi ta hanyar sauk’e fushinka a gareshi. Ka kuma k’ara duba ga Rahamar da Allah Ya yi maka sai kai kuma ka gode mishi ta hanyar yafewa bayinsa abun da suka maka. Ka yi alk’awarin kulla zumunci da Abdul ko kuka in cigaba da maka fad’a ina baka misalai da rayuwata ta baya?” “Are you trying to blackmail me Ammi?” Haydar ya fad’a yana goge fuskarsa yana murmushi kad’an. “Na san kafin ka saurari gurin blackmailing d’in ka saurari sauran bayanai na wanda su nake so ka d’auka ba wannan ba.” Gyad’a kai Haydar yayi kana ya ce, “Zan gyara Insha Allah. Nagode da rashin nuna gajiyawarki wajen d’aurani a kan gaskiya Ammi. Allah ya bar mini ke ya k’ara miki lafiya da nisan kwana.” “Amin Amin Ali. Allah ya baka ikon gyarawa kaima.” “Amin Ammina.” Da haka Ammi ta tashi tsaye tana cewa, “Bari in shiga can don ban gaji da kallon mayunwacin maigidan nawa ba.” Haydar murmusawa yayi kana ya tashi ya shige d’akinsa don shirin zuwa office wanda a yanzu shine ya zama mai mallakin Lu’a Ventures. Ammi kuma har d’akin Laila ta shiga ta samu su Ajidde da Sabrin da wasu daga cikin ‘yan uwa a d’akin ana hira. Ganinta yasa suka fad’ada fara’arsu wanda Sabrin har tashi ta yi taje ta rungumeta tana cewa, “Oyoyo Ammi.” Sai da suka gaggaisa sannan Ammi ta nuna ledojin da aka shigo dasu ta ce, “Wannan daga Baban Ali ne da ni. Wannan kuma kayan Ali ne da muka saya tun ina d’auke da cikinsa sai kuma Allah yasa bai sakasu ba, shine muka kawo d’ansa ya saka.” Cikin al’ajabi ‘yan d’akin suka kalli akwatin wanda daga ganinta dama suke mamakin yanda aka samu akwatin daa amma kuma mai kyau da sabuntaka. Sabrin ce ta bud’e akwatin tana ciro kayan wanda sai k’amshin Comfort detergent suke yi alamar an wankewa tana mik’awa sauran ‘yan d’akin suna dubawa. “Ammi kun iya ajiya, wallahi kamar basu shekara talatin ba. Mun gode Allah Ya saka da alkhairi ya kuma k’ara bud’i.” Fad’in Laila tana k’arban wani daga hannun sabrin wanda ya burgeta ainun. Wani kayan idan aka ciro sai su yi dariya ana tuna wa aka taba sakawa irinshi da yake su abun nasu ma na yayi ne. Sai da suka gama ganin sauran kayan sannan Laila ta d’auki wanda yafi burgeta ta sakawa jaririn ta kaishi gurin Babansa wanda ya fito zai tafi aiki. “Dama yanzu nake da niyyar shiga in miki sallama. My bundle of joy, ko in tafi da kai ne?” Ya fad’a yana ajiye jakar hannuna ya kar6i yaron daga hannunta. “Baka da abu da zaka bashi ya sha da kun tafi tare.” “Wa yace bani dashi? Na k’irjin nawa fa?” Ya k’arisa maganan yana mata signa. “Sarkin magana, ai babu ruwan nono.” “Baki matsa yanda ya kamata bane.” Dariya Laila ta yi tana kad’a kai tace, “Baka ga kayan jikinshi ba?” Zama Haydar yayi kana ya kwaye abun da aka lullu6e jaririn dashi yana kallon kayan yace, “Ban sayi wannan ba. Waye ya kawo? Kuma kamar irin wanda yaran daa suke sakawa ne.” “Naka ne wanda su Ammi suka saya maka baka saka ba shine ta kawo.” Haydar shiru yayi ya k’urawa kayan ido sannan ya ce, “Yayi mishi kyau sosai. Bari in tafi.” Ya mik’a mata yaron sannan ya mata sallama ya tafi. Da rana bayan azahar Meenat ‘yar d’akin Ammi ta iso gidan mai jego, da saurinta ta rungume Ammi tana cewa, “Nayi kewarki Ammi.” Itama Ammi murna ne fal a fuskarta tana tambayar lafiyanta da kuma bayan rabuwa duk da cewa suna waya tun bayan da Ammi ta bar unguwar ta fara zama a gidan Ummii. Meenat ta gaishe da sauran ‘yan d’akin sannan aka mik’o mata jaririn tana kallonshi, a ranta kuma cewa take yi da itace mahaifiyarsa amma Babanshi ya k’i aurenta. “Baffa da kyar ya barni na taho wallahi, sai dana fad’a mishi cewa kece kika ce in zo kuma kina zuwa gaishesu sannan ya barni.” Fad’in Meenat ga Ammi. “Ai ban yi tsammanin zaki zo ba, na fad’a miki zuwan nawa ne kawai amma akan cewa gobe zan je na dubaku da duk ‘yan unguwa. Ina su Zaliha (Matar da Ammi ta ta6a taimako har Haydar ya nema mata gidan haya bayan mijinta ya gudu ya barta da ‘yaya. Bayan Ammi ta bar gidan tasa Haydar ya d’aukota ta dawo gidan da zama.)” “Suna can lafiyansu kalau. Ai ban fad’a mata kin zo ba.” Ana la’asar Ammi ta musu sallama a kan sai washegari zata dawo, Haydar da dama ya dawo gida ya fita zuwa waje in da Alhaji Abdul ke jiran Ammi ya kwankwasa mishi glass d’in window ya bud’e yana mamakin ganinshi. “Ka zo dauk’an Ammi kenan?” Haydar yayi maganar nevously yana kallon yayan nashi wanda yake cikin mamaki. “Eh, tace mini tana fitowa.” “Ka shigo ka ga Baby.” Haydar ya fad’a yana jin kamar zai shak’e da yawun bakinsa. Domin zai iya cewa wannan ne karo na farko da suke magana wacce bata shafi kasuwancinsu ba. “Kar ka damu ba sai na shiga ba, saboda na san Ammi ce ta matsa maka. Bana son a yi maka dole a kan abun da baka so.” “Ammi bata san da cewa zan maka magana ba.” Ya fad’i hakan yana kallon bakin gate in da Ammi ta fito tare da Meenat suna hira gwanin ban sha’awa. Alhaji Abdul ma bin su yayi da kallo amma hankalinshi yafi karkatuwa ga yarinyar da ke manne da Ammi tana mata magana kamar ta dad’e da saninta har tana d’aura kanta a kan kafadarta tana dariya. ‘She’s so young and innocent’. Ya fad’a a ranshi. Kafin su Ammi su iso gurinsu ya bud’e marfin motar ya fita yana cewa, “Ok to. Mu je.” Fuskarsa d’auke da murmushi domin ya gane cewa hakan yin kan Haydar ne ba wai tilasta mishi aka yi ba. Ammi da ta gansu tare sai da zuciyarta ta buga tana fatan Allah yasa Haydar ba maganar banza ya mishi ba akan fad’an da ta mishi d’azu. “Ammi ku shiga motar, bari ya ga Baby sai ya zo ku tafi.” Gyad’a kai kawai Ammi ta yi don ta kasa magana suka wuce gurin mota, Meenat kuma mamaki take yi dalilin da yasa wannan mutumin da zai mayar da su gida yake kallonta don dai tasan yayi sa’an babanta babu k’arya. Haydar a falonshi ya sauk’ar da Alhaji Abdul sannan ya d’auko mishi ruwa a cikin fridge d’in da ke falon ya ajiye mishi a gabanshi yana cewa, “Bari a kawoshi.” Alhaji Abdul tsabar murnar wannan karramawar da Haydar ya yi mishi kasa cewa komai yayi illa gyad’a kai da yayi yana murmushi tamkar zai tsaga fuskarsa gida biyu. Wai yau shine a gidan Haydar har yana kawo mishi ruwa? D’aukan goran ruwan yayi ya bud’e duk da cewa baya jin k’ishi ya bud’e ya fara sha yana jin kamar RUWAN ZUMA yake sha don bai yi tsammanin akwai ranar da Haydar zai bashi ruwa ba. Yana ajiye goran Haydar ya shigo hannunsa d’auke da Baby yayin da Laila ke bayanshi itama tana tahowa. Alhaji Abdul shima bai iya rik’e jariran ba sai da Haydar ya gyara mishi. Murmushin da yake yi kuwa k’aruwa ta yi yana kallon fuskan Baby yana jin kamar a bashi kyautarsa. “Da gaske yana kama da kai. D’azu da Baba ya fito yake fad’a mini har ya tura mini hotonsa. Allah ya rayashi a kan addinin musulunci yasa addini yayi alfahari dashi.” “Amin Amin.” Su Laila suka amsa. Kallo d’aya da Alhaji Abdul ya yiwa Laila bai sake d’ago kanshi ba har suka gaisa ta fita. Haydar na lura da hakan sai yaji sanyi a ranshi don ya lura da gaske yayan nashi ya canja. Wayarsa ya d’auka ya yiwa Babyn hoto yana cewa, “Wanda Baba ya d’auka bai fito sosai ba hannunsa na karkarwa kuma camerarsa bata da kyau.” Dariya ce ta su6ucewa Haydar ba tare da ya sani ba kana ya girgiza kai yace, “Zan fad’a mishi.” Alhaji Abdul dad’i ne ya k’ara lullu6eshi ya ce, “Kar mu yi haka da kai.” Shima yana dariya. Sai da suka nitsu sannan Alhaji Abdul ya dubi k’anin nashi with serious face, yace, “Nagode daka bani wannan daman kuma I promise baza ka ta6a regretting hakan ba. Thank you.” “Allah yasa.” Kawai Haydar ya fad’a kana ya kar6i yaron bayan Alhaji Abdul ya mik’o mishi suka fita tare. Har bakin motar ya rakashi sannan ya k’ara musu sallama ya koma gida. A hanya Ammi ta fad’awa Alhaji Abdul in da zai kaisu wato tsohuwar unguwarsu zata mayar da Meenat gida. Shi dai tun lokacin da yarinyar ta gaisheshi ya ji ya kasa nitsuwa yana ta kallonta ta wutsiyar ido don a gaban motar ta zauna kamar yanda Ammi ta umurceta ta yi. Suna isa suka shiga ciki wanda minti goma da haka suka fito tare Meenat d’auke da jaka a hannu ta matafiya tana ta murna. Mutumin da ya gani a bayansu yana magana da Ammi cikin mutuntawa yasa ya gane shine Babanta. Hakan yasa ya fito daga cikin motar ya mik’a mishi hannu suka gaisa Ammi na cewa, “Wannan d’an maigidana ne Alhaji Abdul, kuma Yaya yake ga Ali.” “Masha Allah, ai kullum na tuna cewa kin samu ‘yan uwanki sai na ji dad’i a raina. Ali kam ba’a ganinshi ya daina ziyartarmu, tun lokacin da ya kawo Zaliha gidanku ya tafi bai k’ara zuwa ba. A fad’a mishi Ina mishi murnar samun k’aruwar da yayi.” “Insha Allah zan fad’a mishi kuma zan aikoshi ya zo. Ai kun wuce makwabta a gurinmu sai sai ‘yan uwa. Allah ya bar zumuncin da ke tsakaninmu.”“Amin Amin.” Fad’in Baban Meenat yana gyad’a kanshi. Da haka suka yi sallama suka shiga mota Meenat sai murna take yi zata je gidan Ammi hutu har na sati d’aya. A gidan Alhaji Sammani na Kano Alhaji Abdul ya ajiyesu sannan ya tafi ya barsu zuciyarsa cike da tunanin wannan yarinyar Ammin. Washe gari driver ya kai Ammi da Meenat gidan su Laila wanda basu wuce minti talatin ba suka tafi akan zata je ziyaran dangin mijinta sai an kusa suna zata zo. Ammi ta zaga duk dangin Alhaji Sammani a cikin kwanaki hud’u tare da Meenat ‘yar d’akinta. A rana ta biyar ne suka k’ara komawa gidan Haydar in da ake hada-hadan suna washe gari, Ammi ta kai kayan sunan da ta yiwa Baby akan cewa ita baza ta zo suna ba. Ana sallan isha Haydar ya mayar dasu gida, har zai tafi Ammi ta tsayar dashi ta ce, “Baza ka fad’a mini Sunan yaron bane har sai na tambaya?” Murmushi yayi har hakwaran shi na bayyana ya fad’a mata. Cikin farin ciki ta nuna yayi k’okari sannan ya mata sallama ya koma gida. Misalin k’arfe sha d’aya da rabi Laila ce zaune a bakin katifar Haydar tana had’a kayayyakinta da zata saka washegari ranar suna, tun da ta san d’akinta ba zai mata dad’in canja kaya ba saboda jama’a. Haydar ne ya fito daga cikin band’aki ta ce, “Baka fad’a mini sunan Bundle of joy ba Haydar.” “Yayana na yiwa mai suna.” Ya bata amsa yana kwanciya a gefenta ya jawota yana tura kanshi jikinta. Zuciyarta ce ta buga ta k’arfi domin bata ta6a tsammanin zai yi hakan ba, ya rasa wanda zai yiwa takwara sai Alhaji Abdul? Duk da cewa ya canja halinshi sannan ta yafe mishi, kuma tana son mijinta yayi zumunci dashi bata ga cancantar da yayi a mishi takwara ba. Sai dai baza ta nuna mishi hakan da yayi bai mata dad’i ba saboda ya fita iko da yaron fiye da ita. “Haydar me kake yi haka?” Ta tambayeshi da taji ya zuge zip d’in rigarta yana neman cireta gaba d’aya. “Dabarun mata nake son a mini, na so in yi hak’uri amma kullum na ganki sai kin birkita mini lissafi da kyan ki da kuma k’amshin da baya barin jikinki Laila.” “Haydar jego nake yi fa.” Ta fad’a tana rik’e hannunshi wanda ke wasa da k’irjinta. “Sai aka ce kar mace ta biyawa mijinta buk’ata in tana jego? Ba fa jikinki zan shiga ba Laila.” Shiru ta yi bata motsa ba, hakan yasa ya dakata daga abun da yake yi ya koma can gefe ya kwanta kamar wani abun tausayi. Hakan ba k’aramin tausayi ya saka mata a ranta ba, sannan ta san abun da yake buk’atan ba laifi bane don ta mishi. Kwanciya ta yi tana manna mishi k’irjinta a bayanshi tana cewa, “Mik’o mini Vaseline d’inka.” Washegari da asuba aka rad’a sunan jariri a masallaci aka raba goro, dibino da sweets. Mas’ud sai da yayi hawaye da ya ji shi aka yiwa takwara, ai kuwa har gida ya biyo Haydar yana mishi godiya kamar zai had’iye shi tsabar murna da farin ciki. Laila tana zaune a falo a lokacin gari ya fara haske tana magana da wad’anda aka yi hayansu zasu yi girki akan kulawan Marwa da Hajja ta ji shigowan su, wanda hakan yasa k’irjinta ya buga don za’a fad’a mata sunan d’anta Abdul K’adir ne. Sallamarsu ta yi kana ta k’ak’alo murmushi ta gaishe da Haydar tana kallon Mas’ud wanda ya ke cikin farin ciki kamar wanda aka yiwa babban kyauta ta ce, “Kai kuma me ka samu kake ta murna haka?” Mas’ud kallon Haydar yayi cikin rashin yarda yace, “Dama bata sani bane?” Girgiza kai Haydar yayi yana mik’awa Sabrin sauran dibinon wacce itama ta kasa kunne tana son jin sunan k’anin nata. “Ni ya yiwa takwara Kalti. Duk mutanen duniyan nan ni kad’ai ya za6a ya sakawa d’anshi sunana.” Sabrin zuwa ta yi ta rungume Mas’ud cikin tayashi murna sai dariya take yi ta kasa tsayawa guri d’aya, ita kuma Laila kasa motsi ta yi tana kallon Haydar idanunta sun ciko da hawaye ta ce, “Meyasa ka za6eshi?” “Saboda shi ya bani aurenki ya kuma mara mana baya ba tare da ya kyamaci tarayyarmu ba Laila. Mas’ud ya cancanci fiye da haka, ya zama d’an uwana, abokina kuma mai sunan d’ana.” “Nagode sosai Baban Mas’ud Allah ya saka maka da alkhairi. Nima Mas’ud ne ya zama tamkar k’ashin bayana duk tsawon shekarun da muka d’auka muna rayuwa. Yayi mini komai ya kuma so duk abun da nake so ciki har da kai Haydar. Ka wanke mini zuciyata kuma ka cika mini wani buri nawa wanda tun ina da k’uruciya na yi alk’awarin yi wa Mas’ud takwara sai Allah yasa ban saka haihuwa ba sai yanzu. Nagode sosai.” “Ki daina mini godiya saboda ke kika wahala bani ba Laila, and you deserve more than that.” “Awnnnnn. Allah ya barku tare lovebirds.” Fad’in Sabrin tana narkewa a jikin Mas’ud irin abun ya burgeta d’in nan. Dankwalon Laila ta aika mata kana ta share hawayen fuskarta ta shige cikin d’akinta in da ta jiyo kukan Mas’ud junior. Bikin suna ya k’ayatar don dangi da abokan arzik’i sun taru ana ta hidima cikin farin ciki da annushuwa. Duk wanda ya zo aka fad’a mishi sunan yaron sai ya kad’a kai ya ce, “Dama Mas’ud ya fi kowa cancanta.” Dangin Haydar kuwa zuga suka yi na kwansu da kwarkwatansu suka zo a lokaci d’aya wanda yasa dole aka bud’e musu falon Haydar saboda yawansu. Kayan da suka taho dashi kuwa sai da Laila tace yayi yawa a rage amma suka k’i. Aunty Aisha ce ta ce, “Ana haihuwa a zuriyar Aunty Hadiza da kuma Babana amma ba’a ta6a yi a zuriyar Baffa Sammani ba sai wannan karon. Wannan kad’an ma kika gani don ga makullin gida da mota daga Alhaji Abdul ya ce a bawa d’anshi.” Laila kasa magana ta yi sai ‘yan uwanta ne suke ta godiya tare da saka albarka aka mik’o mata keys d’in ta rik’e tana cewa, “Allah ya saka muku da alkhairi ya kuma bar zumunci.” “Amin Amin.” Suka amsa kana aka fara shigo musu abinci da drinks kamar ba zai k’are ba. Rengem kam wannan karon bata samu shiga ba saboda abincin Shuwa irin su Danderu, Shurba da Gahwa su suka ci saboda basu ta6a cin irinshi ba kuma ya burgesu. Ana cikin hira sai ga Umma da Muna wanda daga ganin yanayin fuskarsu zaka gane dole ce ta saka suka zo. Laila ce ta tar6esu cikin fara’a don ta yi mamakin ganinsu, tana tuna rabonta da Umma tun lokacin da su Haydar da Nazifi suka kai Abul Maiduguri. Umma bata bari suka gaisa ba ta ce, “Yanzu ‘yar nan da girmanki tsofai-tsofai da ke sai da yaro mara asali nan ya miki ciki? Kuma don rashin ta ido har tara jama’a kuka yi ana hidiman suna? Ni kam in ba don Nazifi ya matsa mini ba bazan zo ganin wannan kayan takaicin ba.” Sosai Laila ta ji zafin kalaman Umma saboda cikin baynar jama’a ta yi maganar ciki har da ‘yan uwanta da kuma abokan arzik’i. Kunya ce ta rufeta ta ji kamar ta rufe idonta kowa ya 6ace a gidan. “Cikin shege shi ake 6oyewa ake kuma ala wadai dashi ba cikin sunnah ba wanda ya fito daga tsatso na gari. Girman mace kuma ba shi zai sa idan ta haihu ta zama abun kaico da nunawa a idon duniya ba. Sannan zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana ha-maza-ha-mata sai ya yi. Wanda kike kira mara asalin ga can ‘yan uwansa a falon can ki duba ki gani in sun yi kalar takaici, sannan ki gyara halinki don kullum tsufa kike yi amma masifa da bala’i ke cinki kin kasa kwantar da hankalinki, k’arshenta a haka zaki tafi in baki yi babban rabo ba. Allah ya kyauta.” Wannan fad’in Hajiya Maryam kenan wacce dama tun asali take cike da halin Umma a kan Laila. Umma kamar zata yi magana amma ta rufe bakinta babu kunyan idanun mutane ta shiga falon Haydar ta ga jama’a birjik wanda gani d’aya zaka musu ka gane ‘yan gayu ne na k’arshe, gefensu kuma can akwatuna ne shida da kuma ledoji kala kala wanda ta tabbatar kayan suna ne a ciki wanda aka kawowa Laila. “Su basu d’auki haihuwata a matsayin kaico ba shiyasa suka mini hidima irin haka har da kyautar mota da gida Umma.” Laila ta fad’awa Umma wanda ita kad’ai ta ji kana ta d’aga muryarta tace, “Aunty Aisha ga Kakarsu Abul da Sabrin ta zo gaisheku.” Nan idon ‘yan falon ya dawo kan Umma suna binta da murmushi ana d’aga mata gaisuwa tana cewa, “Lafiya. Lafiya. Lafiya.” Kawai amma mamaki ne shimfid’e a fuskarta. Jiri ta fara gani ta yi saurin dafa k’ofa tana rufe idanunta. Hakan yasa ‘yan d’akin suka farga wasu suka yiwo kanta aka rik’eta ana mata sannu. Hajiya Maryam ce ta bada shawaran a mayar da ita gida wai hayaniyar ce bata so. Hakan kuma aka yi, ana neman wa zai mayar dasu gida Aunty Aisha ta ce, “Ga can Ahmad a waje ya kaisu mana. Ga motoci birjik a waje har sai an tsaya ana nema? Mu ma ai ‘yan uwa ne.” Muna dama bata bi Umma zuwa falon Haydar ba don tana da masaniyar bayyanar dangin Haydar da kuma cewa wai ‘yan uwa ma suke shi da Laila. Aunty Aisha ce ta kama kafad’ar Umma suka fita da ita waje Muna na rik’e da silifas d’inta tana binsu a baya kamar zata tsala ihu. A cikin motar Aunty Aisha aka sakata ta zauna sannan aka kar6o jaririn daga hannun su Ahmad aka mik’awa Umma wanda sai k’amshi yake yi ya cika yayi kyau cikin kayan alfarma. “Na ga har zaku tafi baku ga jaririn bane shine na kar6oshi a hannun dangin babansa. Tun lokacin da suka zo yaron yake hannunsu, to abun ka da gudan jini suna marmarinsa. Wannan d’in sunanta Aunty Aisha kuma ‘yar Baffan Haydar ne, wanda zai mayar daku gida kuma d’anta ne. Ahmad idan ka sauk’esu akwai kayansu a booth ka cire musu.” Hajiya Maryam ta d’age yaron a cinyar Umma ta rufe musu k’ofar. Cikin girmansa Ahmad ya ce, “To Aunty Maryam.” Kana ya ja motar suka fara tafiya bayan ya kunna a.c. Muna da Umma kuwa suna bayan mota a.c na bugarsu sai zare idanu suke yi, Umma ce ta yi k’arfin hali ta ce, “D’an nan ku d’in dangin mijin Laila ce?” Murmusawa Ahmad yayi bai kawo komai a ranshi ba ya ce, “Eh, shi kawuna ne k’anin mamana. Ina zan kai ku?” Umma ce ta mishi kwatance ya kaisu har bakin k’ofar gidan sannan ya fitar musu da take away d’in su tare da souvenirs ya kai cikin gidan sannan ya fito ya koma gida. Yana fita Umma ta saka kuka wanda ya sa Nazifi ya fito daga d’aki yana tambayar ko lafiya? “Ashe an gane dangin mijin Lamla shine baka fad’a mini ba? Kai wannan abun bai mini dad’i ba ta bani kunya a cikin jama’a ana ta mini dariya.” Dafe kai Nazifi yayi yana tausayin mahaifiyarsa da irin tsanar da ta yiwa Laila har bata son farin cikinta. Dangin Haydar sai yamma suka tafi aka cikasu da take away da kuma souvenirs. Laila rufe side d’in Haydar ta yi suka koma sashenta aka cigaba da hidiman suna. Suna zaune ana hira sai ga Shema’u y’ar Tabawa ta shigo falon. Tun bayan rasuwar Babansu Tabawa ta sayarwa Madu takunta da na ‘yarta na gidan gadon nasu sannan suka koma Wudil in da iyayen Tabawa suke da zama. Tun auren Shema’u da su Laila suka je aka musu wulakanci basu sake komawa ba, haka suma basu nemesu ba a haka zumuncin nasu ya lalace. Bayan an gaisa ana tambayar bayan rabuwa Shema’u ta ce, “Marwa ce ta je har Wudil ta fad’a mana kin haihu tare da rok’on muci gaba da zumuncin mu kar mu watsar. Mama tace a gaisheku ciwon k’afa ba zai barta ta zo ba.” Da haka ta ciro rigar yaro da kuma zanin abunku ta mik’awa Laila tace ga abun sunansu ita da mamanta. Har cikin ranta Laila ta ji dad’in wannan kaya ta kuma kai cikin wardrobe d’inta da niyyar d’inkawa duk da cewa zanin wankanta ya fishi tsada. Sati d’aya shema’u ta yi a gidan Laila sannan ta bi Yayarsu Ajidde gidanta a kan itama zata mata kwana biyu sai ta koma Wudil, aka bar Laila ita kad’ai da mijinta da kuma Bundle of joy d’insu. Haydar bai dawo d’akin Laila ba yace ya gaji da je-ka-ka-dawo tsakanin sashenshi da nata. Dolenta ita ta shigo sashensa suna kwana tare, idan abun nashi suka motsa sai ya d’age Bundle of joy ya nemi a mishi dabarun mata tun da har lokacin bata gama bik’i ba. Wata biyu da haka Laila ta fara ziyara ga ‘yan uwa da abokan arzik’i a matsayin yawon arba’in. Daga nan har Wudil suka je gaishe da Tabawa in da suka kawo ta asibitin Kano ganin ciwon k’afar tata yana wahalar da ita. Shema’u ke jinyarta yayin da Haydar ya d’auke nauyin komai bayan yayi k’aramar musu da Mas’ud akan cewa shi zai biya. Tana samun sauk’i suka koma garinsu suna zuwa ganin Likita idan lokacin komawarsu yayi. Mas’ud Junior wanda ake kiranshi da sunanshi na yanka ya cika wata shida har yana rarrafe, yaro ne d’an lukuti kyakkyawa gwanin ban sha’awa kuma ga shiga rai. Kulawan da yake samu daga kowa yasa yake da son mutane da kuma son a d’aukeshi a fita yawo. A wannan ranar ne kuma Kaala Abdi ya kira Laila ya fad’a mata Abul yana hanya zai dawo gida. Laila kasa zama ta yi tsabar murna da kuma fargaban yanda Abul zai yi idan ya zo ya sameta tare da d’an Haydar duk da cewa yana da labarin ta haihu, zata iya cewa rabon da ta yi magana dashi tun ranar da ta fad’a mishi ta haihu ya d’auki fushi da ita yau wata biyar kenan. Ko da ta je Maiduguri dubashi kuwa bai d’ago kai ya dubeta ba balle d’an dake hannunta. Haydar ta kira a waya ta sanar dashi ya dawo gida yana tayata murna amma sai ya lura ita damuwa take ciki. “Menene damuwar ki Maman Mas’ud?” Ya tambayeta yana jawota jikinshi tare da d’ansu wanda ke wasa da gemun babansa. “Abul.” Kawai ta fad’a ya kuma gane me take nufi. “Karki damu. Insha Allah babu abun da zai faru. Me da me za’a shirya mishi?” Haydar shi ya taya Laila girkin da zata sauk’i Abul dashi duk ta bata da tabbacin ko zai ci. Har yamma liss suna zaune suna jiranshi suka ji k’arar bud’e k’ofa Laila tayi saurin isa bakin window tana lek’awa. Abul ta gani tare da Baba maigadi suna gaisawa fuskarsa d’auke da fara’a kamar bashi ba. Yayi k’iba ya tara gemu da saje yana rataye da jakarsa a bayanshi ya nufo mashigar falon Laila ta yi saurin sake labulen ta koma gefen Haydar ta zauna zuciyarta na bugu. Abul yana shigowa suka dubeshi cikin fara’a amma shi hankalinshi na kan yaron da ke hannun Haydar wanda ya tabbatar shine d’an mamanshi. Mas’ud junior na jin k’arar bud’e k’ofa ya kalli wanda ya shigo ya 6are baki yana dariya yana tafa hannayensa alamar a d’aukeshi a tafi yawo. K’arshe sauk’a yayi daga jikin babanshi ya rarrafa zuwa gurin Abul ya kama wandonshi yana ja yana gwalantoyi. Laila tsoro ne ya kamata kar Abul yayi kwallo da d’anta amma Haydar ya rik’o hannunta yana kallon yanda Abul ke battling da zuciyarsa game da yaron dake jan wandonsa yana mishi dariya bakinshi babu hak’ori ko d’aya.

Mun Fateey 👌

Back to top button