Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 5 By Hafsat Bature

💋Kurkukun Ƙaddara💋

E5
Boss Bature✍️

“Ke da ubanwa ku ka yi wannan”?
Ƙura mashi ido magen tayi tana Cigaba da yin kukan Yunwar da take yi, wurgi yayi da ita, tare da naɗe hannun rigar shi Ya fuce daga gidan, kaitsaye Ya shiga Gidan Uxair, tun a bakin gate mai gadin Gidan Ya soma tambayar shi”Yalla6ai Lafiya”

Baiko tanka mashi ba Idonshi Ya rufe, Angel kawai Yake nema Ko sallama bai tsaya Yi ba Ya faɗa Cikin Falon Gidan, Ganin bakowa Yasa shi fara kwala mata Kira”Angel!Angel!Angel!!’ tamkar makoshin shi zai 6allo,

Da gudun gaske Aneelerh ta fito daga bedroom ɗinta Jin muryar Taj Cikin tashin hankali,

“Me ya faru ne”?tayi tambayar tana kallon shi,
“Where is Angel”?
“Ɗazu ta shigo bata Jin dadin jikinta, yanzu haka bacci take yi adakin”bata kai ƙarshen maganar ta ba, Ya wuce ta a fusace Ya faɗa dakin, Can ya hangota saman gado a kudundune tana ta sharar bacci,”

Hannu biyu yasa ya Cakumeta, da sauri aneerlerh ta biyo bayan shi Tana tambayar shi Meya faru ne,

Da budar bakinshi sai cewa yayi”kashe ta zanyi,”

Yana faɗin hakan ya nufi hanyar fita da ita, gida Ya koma da ita a dakin su Ya jefar da ita saman gado, sai lokacin ta farka tana kallon shi da manyan idanuwanta,

“Daddy what”?

“Zaki Ci ubanki ne” ya faɗi hakan tare da Janyo pillow Ya hau saman gadon Ya turmushi fuskarta dashi, Mutsu mutsu ta shiga yi, tana kokawar fitar da numfashinta, sae faman harba ƙafafunta take Yi, tana neman Ceto,Amma Taj sam Babu alamar zai sarara Mata, Saboda Baya acikin Hayyacinshi Dagasken kasheta Zai yi,

Faɗowa ɗakin aneelerh tayi ko takalma babu a ƙafafuwanta, Anan ta same shi Saman Gadon Ya danne angel Da pillow, A gigice ta fasa ƙara, Tare da yin kukan kura Ta haye saman Gadon, Da iya ƙarfinta na ƙarshe Ta cakumi wuyan jallabiyar jikin Taj tare da Yin Wurgi dashi gefe guda Ya faɗa saman mattress din,

Cikin shessheƙar kuka take fadin”Taj ban sanka da haka ba, meyasa zaka yanke hukunci Cikin fushi ne? Meye ribar ka idan ka kashe Angel?yarinyar da ba ta wuci 7years ba, idan ka yi hakuri Wata rana zata daina ne,

“Wlh bazan ƙyaleta ba Kafin ta kashe ni, Ni zan fara kashe ta,” ya ambaci hakan tare da yunƙurawa Ya miƙe Yana ƙoƙarin Cakumar Wuyan angel da ta sume, da sauri Aneelerh Ta sanya hannu ta ɗauketa, tana ƙokarin sauko wa da ita daga saman gadon, A ƙokarin Ya damƙo angel Ya janyo wuyan rigar Aneelerh gaba ɗaya aneelerh tayi baya ta faɗa saman faffaɗan kirjinshi, Angel kuma ta yi gefe ɗaya saman gadon,

Karo na farko da jikinta ya fara ta6a namijin da ba muharraminta ba, shi kan shi bai yi tsammani hakan zata faru ba, saboda ba ita yayi niyar Janyo ba, Angel da ke a hannunta Yaso Ya damƙo, hatta mayafin da aneelerh ta rufe kanta dashi ya warware sumar kanta mai tarin yawa ta sauka har saman kafadarta, wani irin yanayi mara misaltuwa ne ya ziyarci kowan nan su, ƙoƙarin miƙewa aneelerh ta yi sai dai ina wani magnet ne ya ruketa, Runtse idanuwanta tayi da karfi ta soma ambaton a’uzubillahi minasshaiɗanirrajim, tun da ta ambaci hakan sai ga shi ta samu ƙwarin guiwar Raba jikinta daga Na taj, aikuwa A gaggauce ta hanzarta sauka daga saman gadon, ko mayafin ta bata tsaya ɗauka ba ta watsa da gudu tabar ɗakin,

A hankali taj ya lumshe idanuwan shi, ya yin da hancin shi ke shaƙar mashi ƙamshin turaren Jikin aneelerh daya gauraye Jikinshi, bakomai Ya tuna ba face Matarshi da ta gudu tabar shi, maca ce mai matuƙar son ƙamshi, shima kuma ma’abocinsa ne, baisan Ya akai ba Ya tsinci kanshi da tariyo yarda Aneelerh ta faɗo saman ƙirjinshi, da kuma yadda yalwataccen gashin kanta Ya zubo har a jikinshi,da kuma daddaɗan ƙamshin turaren ta,

Ganin Zuciyar shi na ƙokarin Zayyana irin kyawun surarta ne yasa shi saurin Ambaton A uzu billahi minasshaiɗanirrajim, Astagfurullah Ya Allah,

Miƙe wa Ya yi zaune Duk kasala Ta rufe shi, saukowa yayi daga saman gadon ya fito palour, babu kowa Hakan ya tabbatar mashi da cewa Neelerh ta gudu, frigde ya buɗe ya dauko Swan Mai sanyi ya dawo bedroom din shi, daga gefen gadon Ya zauna, buɗe murfin yayi ya tarfa ruwan a hannunshi Ya watsa ma angel asaman fuskarta, nan take Taja dogon numshi,

Slowly ta buɗe idanuwanta akan fuskar shi, Suna hada ido ta fashe da matsanancin kuka,

Natsuwa yayi yana kallonta ko kusa baiji tausayin kukan nata ba, tun da ya lura Ba son shi take Yi ba,

Cikin shessheƙar kuka tace “You want to kill me because you don’t love me, yanzu da na mutu Allah zai kamani, so kake in shiga wuta ko? ta yi tambayar tana kallonshi, har lokacin idanuwanshi na akanta baice uffan ba,
“Kana Jina ka share ni ko”

Gyaran murya ya ɗanyi can kasan makoshin shi ya furta”Dama kina tsoran Mutuwa”!
A tsiwace tace “Eh mana,malamin mu ya karanta mana wani hadithi wanda ke magana akan mai munana ma iyayensa ba zai shiga aljanna ba, A wuta za’a babbaka shi……”

Ƙiris Ya rage taj ya ɗan murmusa”So you know that but u keep hurting me ko”?

Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan, Ganin tasha Jinin jikinta sosai yasa shi kwantowa Yayi mata rumfa da faffadan kirjinshi, cikin sanyin murya ya soma magana Yayin da idanuwan su ke kallon Cikin na Juna,

“Angel, zan sanar dake wani abun da baki sani ba ba ki da wanda yafi ni a duniyar nan, ba ki ta6a tambayata mahaifiyarki ba, Bansani ba ko kina tunanin Namiji yana iya haihuwa ne, Shiyasa kike ganin kamar ni na haife ki, Baki da abun wulaƙantawa Irin mahaifin ki,” shiru ya ɗanyi yana nazarin wani abu, ita kuwa ta kasa kunne tana sauraronshi,

Cigaba da magana yayi”Angel, mahaifiyarki a wulakance ta haife ki, Cikin bathtub tabar min ke, Cikin Jini kina ta kuka, Ni ina bacci kukan ki ne Ya tashe ni haka naje na sameki, Na ɗauke ki na rungume ki ajikina, duk da jinin da ke ajikin ki, Ni ban gudu nabar ki ba, kuma ban bari kin wulaƙanta ba, Sai da na tsaya akan ki angel da taimakon Allah har kika kai wannan lokacin, Tun da ki ke ƙuntatamun dai dai da na rana ɗaya ban ta6a Tunanin na tafi nabarki ba, kuma ban ta6a tunanin in sanya hannuna wurin ta6a lafiyar jikin ba amma angel……”kasa ƙarasa maganar Ya yi jin yadda ta rushe da kuka kamar ranta zai fita, ɗagowa Ya yi zaune yana kallonta.

Hannu ta ɗaura akai tana faɗin “Wayyo Allah na nashiga Uku,Na bani Na lalace!” hankalin shi ba ƙaramin tashi yayi ba,njin yadda babyn shi take Kuka,

Lallashinta ya soma ƙokarin”Am really sorry daughter, I don’t mean to hurt u darling, Na faɗa maki ne don ki ɗauke ni da muhimmanci, don ki san cewa Ina sonki, kuma ina buƙatar tausayawa daga gare ki,” bata tsaya sauraronshi ba, Ta sauko daga saman Gadon da gudu ta nufi toilet ta shige taja ƙopar ta rufe,

A hanzarce Ya sauko daga saman godon cike da fargabar karta kashe kanta, tura ƙopar yayi ya ji tayi Locking dinta,

Bubbuga ƙopar ya shiga yi yana ambaton sunanta”My angel am sorry, kada hakan Ya ta6a zuciyarki, kinsan ina sonki, banason zubar hawayen ki”

Daga Cikin toilet ɗin yajiyo muryarta Cikin shesshekar kuka tana faɗin”I hate my self daddy, cikin toilet aka haife ni, kuma ta gudu tabar ni saboda bata sona……”
Runtse idanuwan shi Yayi tare da ɗan Cizon lips ɗinshi Calmly ya kira sunanta”Angel pls forget about it, Tunda kina da ni don me zaki damu kanki? Ni ne mom dinki kuma daddyn ki,
Zuƙunnawa Yayi agaban ƙopar, yana ji aran shi cewa tana zaune a gaban ƙopar, tsit ya ji ta daina kukan
“Pls say something to me, ko naji sanyi acikin zuciyata”
Shiru bata tanka mashi ba,
“Ki buɗa mun ƙopar”
Sai Lokacin yajiyo muryarta can ƙasa ƙasa”daddy inaso na mutu, kodan saboda nadaina 6ata maka rai”
Cikin matsananciyar damuwa Yace”idan kika mutu angel shi ne zan shiga Damuwa wadda zatayi silar mutuwata nima, saboda kece Oxygen ɗin da nake shaƙa,”

Yakai ƙarshen maganar tare da kwantar da kanshi jikin door ɗin, don Yaji daɗin Jin muryarta

“I made a mistake daddy, I won’t hurt you anymore,”

Saboda tsabar Mamakin Jin abunda tace har saida Ya ɗan dago da kanshi, yana kwalkwale kunnanshi wai koda Ya samu matsalar hearing ne,

“I love u daddy” ya kuma Jin ta furta mashi aruɗe yace”Repeat it pls”
“I love u daddy”
“sake maimaita mun naji”fuskar shi ɗauke da murmushi Ya yi maganar,
Sake maimaitawa ta yi kamar yarda ya nuna yana son ta yi ma shi,

“I love U daddy, Bani da tamkarka a duniyar nan”
Wani irin ihu ya saki, Irin wanda Ƴan kwallo ke yi idan sunci nasara akan wasan su,

A ƙagare Yace”Come out pls, ina so naji ɗumin ki a jikina”

Yana jiyo alamun tana buɗe ƙopar kamar jira yake yi, tana ƙarasa buɗe wa Ya janyo ta Jikin shi yayi hugging ɗinta very tight, hannun shi na acikin sumarta, Wani irin farin Ciki ne Ya lullu6e shi kamar wanda a ka yi ma Albishir da gidan Aljanna,’ dole Taj ya yi farin ciki cos this is the first time da angel Ta fara furta mashi kalmar tana son shi a mtsayina mahaifinta, Ya ji tausayinta sosai, bai ta6a tunanin akwai lagwanta ba sai yau, da ta ji cewa mahaifiyar ta ta gudu ta barta, Jikinta ya yi sanyi, da yasan da haka da tuni ya faɗa mata, da duk wannan abun bai faru ba,

daukarta Yayi asaman bayanshi, yakaita Cikin motarshi, atare da ita suka je masallaci, Ya barta acikin mota, Bayan ya kammala sallar, ya dawo Ya shiga motar yayi driving ɗinsu zuwa Restaurant, komai take so shiyasa aka kawo masu, sai da suka ci suka ƙoshi, sannan Suka dawo gida, A palour suka zauna saman Sofa tana rungume ajikin shi, Suna kallon tashar Mbs 3, dama best channel ɗinta ce saboda suna sanya Cartoon, tafi sha’awar kallon Cartoon da kuma zombie,

Tuni bacci ya dauketa ajikinshi, asaman kafaɗar shi ya ɗauke ta Ya nufi bedroom dinsu, don ya kwantar da ita, a hankali Ya tura kopar ɗakin Ya shige, A saman gado Ya kwantar da ita, Sai da ya fara daukar wayar shi dake ajiye agaban mirror, Tukunna Ya haye saman gadon ya janyo ta a jikinshi, Yana shafa sumar kanta, cikin magagin bacci ya ji tana fadin”I luv u daddy” murmushi ya ɗan saki, Tare da manna mata kiss a gefen fuskarta
“Luv u too My own daughter”

Number Uzair Ya kira, tana fara ringing Uzair ya ɗauka,
“Aminina Yanzu nake shirin zuwa duba jikin ka”
“Na hutasshe ka ba sai kazo ba, Jiki ya yi sauƙi Alhamdulillah”
“Naji labarin abun kunyar da kaso ka aikata na kashe ƴarka, Ae ni har na yi shirin zuwa ɗaukar rahoto”
Fashewa Taj yayi da dariya”Ta
6atamin raine, ni kaina bansan nayi wannan yunkurin ba,”
“Yanzu Ina virus ɗin taka take”?a cewar uzair, don tun ranar da ta Sa ƴan sanda su ka kama su akan ƙazafin da ta yi masu na cewa su ƴan yankar kai ne, tun daga ranar Yake kiran ta da Virus,
Murmushi Taj yayi, tare da kai hannu ya shafa sumar kan angel, Virus ta yi bacci, Mutumina ka ta ya ni farin Ciki,”
Uzair yace”Meya faru”?
Nan Taj ya kwashe duk abunda Ya faru tsakanin shi da angel ya sanar mashi,”
Yana jiyo sautin dariyar farin cikin da uzair Yake yi,
“Ja’irar taji ƙamshin mutuwa, Allah yasa ƙarshen wahalarmu ce tazo, Amma fa nayi farin Ciki,

“Ameen mutumina”
Shiru suka ɗanyi,yana so ya tambaye shi aneelerh amma ya kasa,
“Muyi video call mana”acewar uzair,
Batare da musu ba suka canza Kiran zuwa Video call, A kwance uzair yake saman katafaren gadonsu, ya dan tada kan shi saman pillow, jikin shi na sanye da kayan Bacci,
“Show me her face” murmushi taj ya yi tare da haska mashi fuskar angel, ta sa ki baki da hanci tana ta sharar bacci,
Dariya uzair yayi”waya ga mashasha, wannan ae itace Laca sera jibi yadda ta saki la66a, a haka zata zama surukar mu,”
Fuskar Uzair ɗauke da murmu shi yace”cin mutuncin ya isa haka aminina, kai ka sani Wlh angel koda kuɗin mutun saida rabon shi, koda rabon shi sai in Allah ya nufa”
Jinjina kai Uzair Yayi tare da ɗan yatsina fuska yace”Virus ɗin”?

Taj na ƙoƙarin buɗe baki ya mayar mashi da martani, adai dai Lokacin Aneelerh ta fito daga Cikin toilet, Chest ɗinta ɗaure da farin towel iya guiwarta ya tsaya, Ta cikin Screen ɗin wayar uzair, Taj Ya hangota yanayin kwanciyar da uzair yayi ya juya ma Toilet ɗin ɗakin shi baya, wanda hakan yasa har Taj ya iya hango fitowarta,

Baisan ya a kai ba Ya tsinci kanshi da satar kallonta, Ya bar uzair sai faman zuba yake yi kamar kanyar da bata da daɗi, gaban mirror ta tsaya tana tsane sumar kanta da towel,

“Me kake tunani ne”? a firgice taj Ya mayar da hankalinshi kan Uzair, muryar shi na inda inda yace”Bakomai zan kwanta mutumina, Sae Allah yakaimu,” da sauri ya yi rejecting kiran tunkafin ma uzair ya yi mashi sallama,

Lumshe idanuwan shi ya yi zuciyar shi a cunkushe, duk yadda yaso Ya hana kan shi tunanin abunda ya faru tsakanin shi da aneelerh abun ya faskara, daƙyar ya samu bacci yayi awon gaba da shi,

Tun daga wannan Ranar Angel bata ƙara 6ata mashi rai ba, koda yaushe suna manne da juna wata irin shaƙuwace a tsakanin su, mutu ka raba takalmin kaza, tabbas Angel taba kowa mamaki, irin yadda take son mahaifinta, tarairayarshi take yi, biyayya take yi mashi sau da ƙafa, Xaman Lafiya ya wanzu a tsakanin su.

 

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

Mu haɗu a next page, saoda wadanda su ka ce bai buɗe ba yasa na rage yawan page ɗin, kar a manta da comment like and share

 

Comment like nd share

 

Back to top button