Halysaah Page 39 By Khaleesat Haydar
Jay ya karasa har inda Ajay ke tsaye yace “I think we can take our leave now, nan da friday sai a basa makullin sabon gidan, we just hope he will accept it” Shi dai Ajay bai ce masa komai ba don bai ma san me yake cewa ba, ganin yanayinsa Jay yace “Hey Bruh, are you alright?” Jin Ajay bai basa amsa ba ya kalli wayar hannunsa that was still vibrating yace “Who is calling you?” Ajay ya sake kallon screen din sannan yayi picking dab da kira na biyu zai katse, kunne ya kai wayar yayi shiru yana sauraron yaji abinda Aunty Farida zata ce, muryar Khaleesat yaji a hankali tace “Good evening, Plss can i speak to my Housemate?” At first shiru Ajay yayi, can babu yabo babu fallasa yace “About?” Khaleesat ta girgiza kai murya can kasa tace “Ba komai, kawai dai ina son zan masa magana ne” Jay dai kallon Ajay kawai yake don bai san da wanda yake wayan ba, a takaice Ajay yace “Don’t you have his digit?” Bai jira cewarta ba ya katse wayar ya mayar aljihu, Jay yace “Who is that?” Banza Ajay yayi masa ya bude driver seat ya shiga ya tada motar fuskarsa a daure, Jay ya daga shoulder sannan ya zaga ya shiga gaban motar shi ma bai sake kulasa ba, Ajay ya ja motar suka bar anguwan motar dake bayansu na biye da su. Bayan sallahn magariba Malam Ali na zaune tsakar gida tare da Nenne da duk matansa sai yaran gidan gaba daya, Nenne ce kadai zaune kan kujera er tsugunno, sauran duk kan tabarma suke a zaune kowa na jiran jin dalilin zaunar da su da Nenne tayi, Umma dai na kusa da bakin kofar dakinta da su Islam da Noor a jikinta, Nenne tayi gyaran murya tace “Da farko dai nayi farin ciki ainun da dawowan ɗa na daga furson a karo na biyu, ina kuma rokon Allah ya sa iya bakin wahalarsa kenan sannan muna fatan yayi zuwan karshe furson, wa ennan samari da suka zo suka tsaya mana kuma har suka kubuto da Ali Allah Ubangiji ya masu albarka don da farko na zata makaryata ne kawai en neman suna, duk da dama inda naje ance min za a roki Allah ya kubutar da ɗa na, nafi tunanin ma rokon Allahn da aka yi ne kawai hakan ta faru ba wai don samarin nan ba, mun dai gode koma ya ya ne, sannan shawaran da zan bada shi ne muyi bulaguro mu koma kauye gaba dayanmu na en shekaru kafin komai ya lafa, mu ma hankalinmu zai fi kwanciya da hakan don Alhaji Musa da tsinannen ɗan sa ba barin mu za su yi mu zauna lafiya ba, duk da kotu ta wanke Ali amma Allah kadai yasan wani sharrin za su billo da shi don mutane ne wa enda babu Allah a ransu, wallahi sai su iya sa wa duk a kona mu cikin dare muna bacci, kunga ance zaman lafiya yafi zama ɗan sarki shi sa cikin rufin asiri mu tattara komatsanmu ko zuwa gobe da magariba ne Ali ya mana shatan katuwar tirela mu koma kauyen mu” Mama Zubaida da Mama Shatu da suka saki baki suna kallon Nenne kusan a tare suka ce “Kauye kuma Nenne?” Nenne na kallonsu da kyau tace “Kwarai kuwa kauye, don dama can ne asalinmu, na gaji da tsallaka kogi cikin kwale kwale zuwa nema ma Ali taimako wataran inje in kife, gwara tun da sauran mutuncinmu mu bar garin nan” Mama Zubaida na girgiza kai tace “Inaaa, ai bazata saɓu ba gaskiya, sai dai ni a bar ni a nan in ci gaba da kasuwancina ina rufa ma kaina da ‘ya ya na asiri, akan matsalar da buzuwar matarsa da er ta suka jawo baza a cucemu a mayar da mu riga ba, bazai ma taɓa yiwuwa bane gaskiya” Mama Shatu ta cafke tace “Sai dai ya tattara matarsa da ‘ya yanta su kuma kauye Nenne, amma mu kam muna nan tunda ba mu da ‘ya yanmu muka jawo magana ba, dama mu ke ciyar da kan mu balle mu ji tsoron zamu rasa abinci” A fusace Nenne tace “A yaushe ku ka fara ciyar da kan naku munafukan Allah? ba sai bayan da ku ka tsiyacesa da fararen kafafuwan ku ba tukun? Ai ko Alhamdulillah kowa zai ma Ali shaidan kula da bautata ma iyalinsa banda jarabawan shegun mata da Allah ya hadasa da, ku ne nan ku ka ja masa karayar arziki, dama ance min dukkanin ku babu alkhairi a tare da shi gwara ma Zahra’u, wallahi ce min aka yi in dai zai rabu da ke da Zubaida to arzikinsa zai dawo kaca kaca har fin na ɗa, Zahra’u ce kadai matarsa ta arziki aka ce min, da zai ji ta nawa ma duk ya sallameku in ga inda za ku koma idan ba kauyen ba, ke Zubaida kin manta kauyen da uwarki da ubanki suke sai sati sati ake kawo ruwan pampo? Kin manta ko wutar lantarki ba a ja maku har yau a kauyen ba? Kauyen da muka je na dawo ina ta amai da gudawa amma har kina da bakin kushe namu kauyen da babu abinda babu? To wani ɗan iskan ne ma yace Rano kauye ce tukunna? Sannan ke shatu baza ma a kira garin iyayenki da kauye ba sai dai ace daji, haka nan muka dawo kano maguzawan mayu suka kamani da kyar aka samo kaina ba don Allah yayi da sauran shan ruwana a duniya da tuni na rasu wallahi” Shi dai Malam Ali yayi tagumi yayi shiru bai ce komai ba don tun kan Nenne ta kawo wnn shawara dama yake jin gwara ya koma garinsu don bai san da me Alhaji Musa da ɗan sa za su billo ba kuma, shi dai bai yarda kotu zata wankesa akan kudaden nan masu yawa ba gani kawai yake dadin baki su Ajay suke masa, Nenne tace “Yau ga samun waje kai, ita Zahra’u me yasa bata kushe shawarata ba sai ku masu fararen kafa, ko da yake ita ta guduwan er ta da ta shiga duniya ma take, mu bar ta taji da wannan ma” Mama Shatu tace “Wace er ta? Ai wallahi ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba Zahra’u tasan inda er ta take, mu dai ne kawai aka rena ma wayo aka raina mana hankali” Mama Zubaida tace “To ai ba ma sai kin rantse ba Shatu, kwarai kuwa Zahra’u tasan inda Khaleesat take” Nenne dai sai kallon Umma da ko kallon kishiyoyin nata bata yi ba take, a hankali Nenne tace “Lallai biri yayi kama da mutum, na kuma yarda da maganarku don Zahra’u da na sani da har yanzu tana nan kan darduma sanye da dogon hijabi tana rike da carbi tana kuka ba dare ba rana duk ta fita hayyacin ta, kawarta Uwar Salame da makociyarku sha’awa me daddawa su yi ta shigowa suna dannarta su zazzauna kusa da ita kamar me takaba, amma ina lura da ita yau kusan sati uku kenan tana ta harkar gabanta kamar babu abinda ya faru, nima dai ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba tasan inda Khaleesah take” Malam Ali ya gyara zama yana kallon Umma cikin lallami yace “Kiyi ma girman Allah Zahra’u ke da er ki ku rufa min asiri yanda Allah ya rufa maku, duk inda er nan ta tafi kiyi masu waya ta dawo ta amshi auren mijinta hannu bibbiyu, dama Allah ya riga ya kaddara Abdul ne mijinta mu din banza ne za mu canza hakan? don girman Allah ta rufa min asiri, ina cikin tashin hankali har yanxu wallahi don ban san kuma da me Alhaji Musa da ɗan sa za su dawo min ba, rufin asirina shi ne na damka masu Khaleesah kawai, in har suka kasheni wallahi banza kawai za su kashe tunda ba galihu ne da ni ba, tunda aka maida ni furson din nan nake rashin lafiya me tsanani, yanzu haka maganar da nake yi kirjina kamar an aza min katuwar dutse, ku yi min rai ke da er ki” Kamar zai yi kuka ya kare maganar, Nenne na matsar kwallan da babu tace “In wani abu ya same ka dama da Zahra’u da er ta zan yi kuka wallahi, don su ke kokarin salwantar min da kai ta karfi da yaji” Umma da hawaye ya cika idonta tace “To wai ta yaya zan san inda Khaleesah take ni ba waya ba balle ku yi tunanin tana kirana? Ko kun ga ina zuwa wani waje daga cikin dakina ne?” Mama Zubaida tace “Na rantse da wanda raina ke hannunsa Zahra’u kinsan inda makirar er ki take, don haka sai dai ki rena ma wani hankali amma ba mu ba, duk abinda ya samu mijinmu dama har karshen duniya mun yi ta ja ma ke da ‘ya yanki Allah ya isa kenan, banda samun waje ita Khaleesah har tana da ta cewa da har zata bude baki tace bazata zauna da Abdul ba? Da me tafi Abdul din banda rufa mata asiri da yayi zai aureta? Mutumin da ya maida ta fess ya maida ta mutum ya kashe mata dukiya babu adadi don butulci da samun waje tace ita bata son sa kuma a ina aka taɓa tafka wannan iskancin? Wallahi ba a samu wanda zai ci ubanta bane shi yasa ta samu waje da yawa” Umma tace “Tun da har kuke tunanin nasan inda take kuma baza ku rasa sanin inda take ba ai, kilan ma za ku fi ni sani, don haka sai ku je ku fito da ita ku kai ta gidan Abdul din” Umma na kai wa nan ta mike ta shige dakinta, Mama Shatu tayi kasa da murya tace “Al-qur’an tasan inda take, da bata san inda take ba wallahi da har yau bata dena koke koke ba kilan har sai tayi rashin lafiya, kuma ni na ma fi zargin tana wajen kanwarta ne a garin Legas wallahi, in da ba haka ba ai da tuni mun ga Farida a gidan nan kamar an jefota amma gashi kusan sati uku har yau shiru Farida bata zo ba” Mama Zubaida tace “Ahaf ai mu ba yara bane” shi dai Malam Ali sai zazzare ido yake, Nenne tayi kasa da murya tace “Gaskiya na yarda da maganarku, don nima ina ta mamakin me yasa har yau farida bata zo ba, ita da ko tari yayarta tayi zata hawo mota ta kamo hanyar kano, amma ace an rasa Khaleesah yau sati uku shiru bata kamo hanya ba, ai da alamar tambaya” Malam Ali ya share zufar goshinsa duk da sanyin da ake shi ma yayi kasa da murya yace “To yanxu meye shawara? Ko ni zan shirya in tafi Lagos din ne?” Sosai hankalin Umma dake tsaye bakin kofarta daga cikin daki ya tashi don duk tana jin abinda suke cewa, Mama Zubaida tayi kasa da murya tace “Ai ban ma yarda da shiga dakin da tayi ba kilan er uwar zata kira, ko da yake bata da waya, kawai ina ga a gaya ma….” Mama Shatu ta ɗan tsunguli Mama Zubaida alamar tayi shiru, lkci daya Mama Zubaida tayi tsit, Nenne ta mike tana kallon Malam Ali tace “Mu je daga gefe mu yi shawara Ali” Mikewa Malam Ali yayi ya nufi can hanyar fita daga compound din Nenne na biye da shi, Mama Shatu ta mike tayi ma Mama Zubaida alamar su shiga ciki, suna shiga daki Mama Shatu tace “Ke ya muna neman maganar auren nan ya rushe gaba daya ko zai hakura yace a basa Labeebah ko Lamisah amma kike basu shawaran su je Lagos?” Mama Zubaida tace “Wallahi gaba daya na sha’afa kinsan kwakwalwar tawa, kuma kece kika kawo maganar Khaleesah, tun asali ma bai kamata mu ce komai ba gashi yanxu mun karkato da hankalinsu zuwa Lagos, sai fa Malam ya iya shiryawa ya kama hanyar Lagos wallahi” Mama Shatu tayi shiru, can tace “Ai ko in yaje lagos din nan shikenan tsarinmu ya lalace don taso keyarta zai yi su dawo kano ya mika ma Abdul ita, kinga shikenan mun tashi a tutar babu mun kai ma malamai kudadenmu a banza, tunda duk mun san Abdul din na sonta kuma hannu bibbiyu zai amsheta su fara rayuwar aure” Mama Zubaida tace “Toh kuwa ina ga da kaina zan kira Farida ince mata in har tasan Khaleesah na wajenta to tayi maza maza su bar gidan don Malam zai kama hanyar lagos tare da Abdul” Mama Shatu tace “A’a bari in shiga dakin Zahra’u in gaya mata hakan, tunda ga Nenne da Malam can sun kebe bamu san maganar da suke ba” Bata jira cewar Mama Zubaida ba ta fita zuwa dakin Umma, Zaune ta tarar da Umma bakin katifarta abun duniya ya isheta gashi babu waya hannunta, kuma in tace ta fita daga gidan ta amshi waya a makota tasan dole za a zargeta, kuma daxu da safe suka yi waya da farida ta wayar Mama Salame take sanar mata jibi za su Nijar da Khaleesat, Mama Shatu na kallon Umma tayi kasa da murya tace “Zahra’u, ga 1can Nenne da Malam suna shirya yanda za a tafi legas wajen Farida gobe da asubar fari, in dai kinsan Khaleesah na wajenta wallahi kiyi maza ki buga mata waya su bar gidan su tafi wani wajen, a ajiye batun kishi a gefe abinda baza ka so ma danka ba kar ka so ma ɗan wani, don duk mun san Abdul ba mutumin kwarai bane, kuma a zamanin nan an dena auren dole, mu ma ba a mana dole ba don haka baza mu yi ma ‘ya yan mu ba” Mama Shatu na kai wa nan ta juya ta fice daga dakin, Umma ta mike gabanta na faduwa ta ɗan leka tsakar gidan taga Nenne da Malam Ali tsaye a can lokon tsakar gidan suna magana kasa kasa…. Jay ya fito daga kitchen hannunsa rike da mug din shayi yana juyawa a hankali, Step Mom din Ajay ce zaune parlon cikin shiga ta alfarma, a ranan ta sauka gidan tare da jakadiyarta sun dawo daga kaduna, Jakadiyarta na dinning area tana yanka mata fruit, Jay ya tsaya dai dai inda yake don bata san ya fito daga kitchen din ba, da wani kallon tsana kawai yaga take bin Ajay dake haurawa sama hannunsa rike da laptop dinsa, after few seconds Jay ya ci gaba da juya shayin hannunsa yana kallonta, tana jin sound din cokali ta juya da sauri tana ɗan murmushi ta hau canza channel din TV, shi dai Jay ya karasa cikin parlon bai sake kallonta ba, Jakadiyarta ta taho ta ajiye mata fruit din da ta gama yankawa cikin ladabi take sanar mata ga kayan marmarin, Cike da isa Aunty ta dau Apple ta fara ci, ta ɗan kalli Jay ganin sama zai wuce shi ma tace “Gobe Abbanku zai shigo wani taro” Jay yace “Mun yi waya da shi” Daga haka shi ma ya wuce sama, ta wani taɓe baki ta bi sa da kallo, Jakadiyar da ta zube gefenta cikin girmamawa tayi kasa da murya tace “Ranki shi dade, Allah ya ja zamaninki, daxu bayan saukan mu gidan nan na jiyo mana wani labari, Allah ya sa zaki yi maraba da wannan labarin” A takaice Aunty tace “Labari akan me?” Jakadiyar ta gyara zama murya can kasa tace “Akan Yarima” Aunty ta ajiye Apple din hannunta ta ba jakadiyar gaba daya attention dinta tace “Me kika jiyo?”
Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it’s better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500
