Halysaah Page 40 By Khaleesat Haydar
Har mahaifin Abdul ya gama bambamin da yake yi a parlon Momy kamar zai ari baki bata ce masa komai ba illa rungume hannu da ta yi tana zaune kan kujera tana girgiza kafa fuskarta babu fara’a, Meemah dake zaune parlon ita ma dai bata ce komai ba fuska a murtuke, Alhaji Musa yayi bala’in sa me isarsa sannan ya juya zai bar parlon a fusace, sai kuma ya sake dawowa yana huci yace “Ina wawan Abdallan yake? Ina yake yaga abinda rashin tunaninsa da rashin daukan shawarar sa ya ja min” Momy ta tabe baki ita ma cike da takaici tace “Ai Alhaji yau kwana uku curr rabonsa ma da gidan gaba daya, kuma ba a samun sa a waya, ya kashe wayar” Rai bace Alhaji Musa yace “Duk shi ya ja min wannan bala’i ina zamana, wa yace masa dama ana harkar arziki da talaka? Sam ai ba a shige ma talaka duk yanda yake kuwa, tun asali zuri’ar da yake son in hada da wancan barawon mutumi ba wai nayi na’am da hakan bane, kawai bani da yanda zan yi da Abdallah ne” Momy ta gyara zama zuciyarta na tafarfasa tace “Atoh dai, har na gaji da nanata wannan sentence din da kayi Alhaji, ai ba a abun arziki da talaka don tun asali dama a tsiyace ya zo duniya kuma a tsiyace zai koma, kana zaman zaman ka gashi Abdullah ya ja maka asaran makudan kudi har da su taran kotu, wai kai da aka zalunta kai ne kuma da biyan tara saboda rashin adalci, ai Abdul bai kyauta mana bai duba mana ba, ace shi bazai dau maganata a matsayina na uwarsa ba? Babu yanda banyi discouraging dinsa kan tsinanniyar yarinyar nan ba na nuna masa ba ajinsa bace yaki saurarata wallahi, kyanta ne kawai ya rudesa wato kyan ɗan maciji, har tayin er aminiyata nayi masa amma firr yaron nan yaki, to ga dai abinda ya ja mana” Meemah tace “Ni duk ba wannan ba Momy, kawai so nake in san wasu ‘ya yan shegun ne suka tsaya mata haka har suka maida case din kotu? Sannan ga auren ma suna kokarin kotu ta rabasa ta karfi da yaji, kun ga kenan mun tashi a tutar babu, kuma babu tantama duk yanda aka yi ma su suka boye yarinyar, su waye en iskan nan ne?” Alhaji Musa na safa da marwa a parlon yace “Don kotu ta kori karar nan ba shi ke nufin na bar wannan mutumi da ya salwantar min da dukiya ba, mu zuba mu gani da shi, sai na lahira ya fi sa jin dadi wallahi” Daga haka ya bar parlon kamar zai tashi sama, Momy ta sauke wani ajiyar zuciyar takaici tana girgiza kai tace “Abdallah bai duba mana ba wallahi, ya kaskantar da mu a idon duniya kawai, wai yau talaka ne ya ci nasara a kan mu a kotu, this is a big slap to us, kuma ko uban menene dalilinsa na dinga kashe waya ba a samun sa oho? Ni taran da aka ci Alhaji ne ma yafi ƙona min rai wallahi, ga mari ga tsinka jaka, ki sake kiran wayarsa kiji ko zai shiga” Meemah tace “Baza fa a samesa a waya ba Momy, mu da ganin Abdallah sai ya cika burin dake ransa kema ai kin san halinsa, gwara ma ki saka ma ranki salama mu bi sa da addu’a kawai” Momy ta kalleta tace “Wato kin san inda yake kenan?” Meemah tace “Ke dai kawai ki bi sa da addu’a Allah ya basa nasaran abinda ya saka a gaba Momy, amma shegiyar yarinyar nan ai kamar ta shigo gidan nan ne babu me hana hakan, don baza mu yi biyu babu ba” Momy ta tabe baki tace “Har ga Allah ni so nayi kawai ya hakura da er matsiyatan nan Meemah, kada tsautsayi ma yasa a hada iri da ita mu shiga uku, hada iri da talaka ai ci baya ne Meemah, don ni har cikin raina naki jinin talaka wallahi balle in hada zuri’a da su” Meemah tace “To ai dama bama fatan a hada iri da ita Momy, personally bazan ma bar hakan ya faru ba trust me, kawai ta shigo gidan ta gane Allah daya ne, ke kuma ki fara masa fafutukar wani auren da wuri wuri” Momy dai tayi shiru, can ta tabe baki tace “Allah ya sa ya saurareni to” Meemah tace “Haba dai zai saurareki, da kaina zan masa magana, a samar masa yarinya dai dai class dinsa” Momy tace “To ai shikenan, yanxu tracing din matsiyaciyar yarinyar ya sa a masa kenan?” Meemah tace “Ko ma dai menene mu dai mu zuba ido mu bi sa da addu’a kawai Momy” Mikewa Momy tayi tace “Bari in je in lallaba babanku, na dade ban ga ransa ya baci irin haka ba, haba ai abun da bacin rai, wai ace talaka yayi nasara akan ka a kotu bayan kai ne me gaskiya ai abun da ciwo” Daga haka ta wuce sama, Meemah ta dau wayarta tayi dailing number da take samun Abdul da shi ta tashi ta shiga dakin dake parlon. Da asuba ko sallah ba ayi Malam Ali ya fito da er jakar da yake tafiya da shi bayan ya mulke jikinsa da basilin saboda sanyin da ake, bin dakunan matan nasa yayi duk ya kwankwasa masu kofa, Mama Zubaida da Mama Shatu suka fito suna kallonsa da mamaki suka ce “Lafiya Malam?” Mama Zubaida tace “Ko tafiya kauyen ne ya taso?” Shi dai bai tanka su ba ya dinga goge takalminsa da yayi ƙura, Umma ce karshen fitowa ita ma ta tsaya tana kallonsa ta kasa cewa komai don tasan manufarsa, ko baccin kirki bata yi ba daren jiya tsabar yanda hankalinta ya tashi, Nenne ce ta shigo gidan yafe da zaninta tana ganin Malam Ali tace “Yauwa ko sallah kar ka jira kayi idan kaje tashar kayi a can Ali, ga er soyayyiyar nama da gurasa na kullo maka ka ci a hanya” Mama Shatu tace “Tafiya zai yi ne Nenne?” Nenne tace “Babu ruwan ku, ku dai ku yi masa fatan Allah ya kiyaye hanya” Malam Ali ya amshi kullin nama da gurasan da Nenne ke mika masa, yana kallon matan nasa yace “Toh sai Allah yayi min dawowa” Mama Shatu tace “To ai shikenan, Allah Ubangiji ya tsare Malam” Mama Zubaida ma tace “Allah ya tsare duk da muna da hakkin ka sanar mana inda zaka je da asuban fari Malam” Nenne tace “Bazai sanar ba Zubaida, uban me sanin inda za shi zai kara maki?” Mama Zubaida ta juya ta koma daki, Mama Shatu ma ta tabe baki ta koma dakinta, Nenne ta kalli Umma tace “Wato ke ce isasshiyar da bazata yi masa Allah ya kiyaye ba ko Zahra’u” Shi dai Malam Ali tuni har ya fice daga gidan, Nenne na nuna Umma tace “Mugun abun ku zai kare maku da ke da er ki wallahi, babu wanda ya isa ya salwantar min da ɗa na lokacinsa bai yi ba” Daga haka ta bi bayan Malam Ali da sauri zata rakasa bakin titi ya samu adaidaita sahun da zai kai sa tasha. That same day bayan an idar da sallahn asuba Jay ya shigo parlorn Mai martaba da sleepy face ta dalilin kiran da yayi masa, ganin irin zaman da Abba yayi kamar yana fadarsa ya gane serious issue Abban zai yi discussing da su kenan, ya kalli Ajay dake parlon zaune shi ma alamar kiran sa Abban yayi, Aunty ma na zaune parlon, Jay ya sauke kansa ya karasa kusa da Ajay ya zauna kasan lallausan carpet din parlon, dabi’ar Abba ne sai ya iya minti biyar zuwa goma kamar me nazari kafin ya fara magana in ya tara ku, Jay ya sunkuyar da kansa ya lumshe ido, Ajay ya ɗan kallesa sanin sai ya iya bacci a haka, ai ko yaga baccin yake, Ajay ya ɗan tunkudesa da elbow dinsa, Jay ya bude ido da sauri yana gyara zama, shi dai Abba kallonsu kawai yake, At last Abba yayi gyaran murya cikin nutsuwa yace “First of…. Ina son sanin zaman me ku ke har yanxu a garin nan baku karasa gida ba?” Duk suka yi shiru babu wanda yace komai kansu a kasa, Calmy Abba yace “Ohk take ur time, amma kuyi kokari ku je gida kafin hutun ku ya kare, Secondly…. maganar da nayi da ku a Maryland naji babu wanda yace min komai a kai har yanxu, ga lokacin da na baku ya cika, nayi maku uxurin mantuwa shi yasa nake tunatar da ku yanxu…” Nan ma duk suka yi shiru babu wanda yace komai, shi ma Abban yayi shiru yana kallonsu yana jiran amsa a duk sanda suka shirya, sun san shirun da Mai martaba yayi amsarsu yake kira ko da zai dau 10min ko fin haka ma kafin su basa amsan he won’t mind zai jira su patiently, sanin halin Abban nasa yasa Ajay ya daga kai, Softly yace “Ayi hakuri ranka shi dade ba mantawa muka yi ba, in sha Allah we are working on that very soon” Mai martaba yace “Is that so?” Ajay ya sauke kansa don kalman Abba na nufin bai gamsu da abinda yace ba kenan, Shi dai Jay yaki dago kai, a hankali Ajay yace “A gafarce mu a ɗan kara mana lokaci Abba…” Aunty da har ta fahimci maganar da ake ta ɗan yi gyaran murya ta nemi permission din magana gun Mai martaba, ya gyada mata kai alamar ta fadi abinda zata fada, cikin nutsuwa tace “In na fahimci maganar da ake ranka shi dade, magana ce akan su fito da matan aure duba da yanda shekarunsu ke gaba ba baya ba, wannan magana kuma ba sabuwar magana bace don an fi shekara 3 ana yin ta amma babu wani progress, a takaice basa daukar maganar da muhimmanci, to amma dai ina ga ka ɗan sha’afa ne ur Highness, don shi Jawwad ai akwai maganar sa da Hadeeyah a kasa duk da ba wai maganar tayi karfi bane kuma wannan hadi, hadi ne me kyau da zai kara karfafa zumunci don mahaifiyar Hadeeyah jininka ce kuma ita ta kawo wannan shawara duk da Fulani wato mahaifiyar Jawwad uwar dakinta ce tun asali, shi kuma Junaid a yanda na lura da shi zai fi maraba da zabin ka garesa duba da nature dinsa da rashin choice dinsa, don haka shi Jawwad a tsaida maganar sa da Hadeeyah kawai ina ga hakan zai fi, shi kuma Yarima i think we should get him a princess from neighbouring states, ko ni zan iya jagorantar hakan don arranged marriage zai fi suiting dinsa duba da nature dinsa, kuma ina son a bar komai a hannuna ranka shi dade…” Ajay ya daga kai ya kalleta zai yi magana mai martaba ya dakatar da shi, Ajay ya sauke kansa, Speaking Calmly Mai martaba dake kallon Ajay da Jay yace “Za ku iya tafiya, Allah yayi maku albarka” Sai a sannan Jawwad ya dago kai ya kalli Aunty dake ɗan murmushi ganin Mai martaba yayi na’am da shawaranta, tuni Ajay har yayi disappearing daga parlorn fuska a murtuke, Jay ya mike shi ma ya bi bayan Ajay yana tafiya a hankali, bai taɓa sanin baya son Hadeeyah da aure ba sai yau da Aunty ke bada shawaran a tsaida ranan aurensu da ita, yasan kuma duk abinda Aunty tace kamar Abba ya aikata hakan ya gama ne, kawai yaji hankalinsa yayi mugun tashi yaji wani zufa na keto masa, dakinsa ya shige ya kulle da makulli ya jingina da kofar ya lumshe ido zuciyarsa na bugawa, Ajay na shiga dakinsa shi ma ya kulle da makulli ya zauna gefen gado ya dafe kansa da hannu biyu, this is not the first time da Aunty ke kasalanda akan duk abinda ya shafesa gashi Abbansa baya basa listening ears ko me Aunty tace masa kawai haka za ayi abun nan komin munin abun, at this point he felt he is of no importance to his father, he felt dejected, and it’s been like this for so many years, he have no one to stand for him, a hankali ya juya yana kallon wayarsa dake vibrate, Number Aunty Farida ya gani a gaban screen din wayar, ya kalli agogo yaga karfe shidda da minti biyar na safe, request din Khaleesat na jiya da ta kirasa ya tuna, hakan yasa har kiran ya katse bai daga ba knowing she might be the one calling, kiran ya sake shigowa ya kalli screen din nan ma bai daga ba har ya katse, sau hudu kiran na shigowa continuously, hakan yasa ya maida attention dinsa kan wayar ya ɗan yi jim with different thought running his mind, ganin kiran ya katse an sake kira making it the 5th time of calling yasa ya dau wayar ya daga ya kai kunne yayi shiru waiting to hear who is on the line, a hankali ya mike jin abinda Aunty Farida ke ce masa ta wayar, bai san sanda ya zame wayar daga kunnensa ba rate din heartbeat dinsa na karuwa, da sauri ya nufi kofarsa ya bude ya fice daga dakin ya murda kofar dakin Jay yaji a kulle, knocking ya dinga yi non stop kafin Jay ya bude kofar da mamaki yana kallonsa yace “What is it?” Ajay ya shiga dakin yana shafa gashin kansa da wani expression yace “He tracked her to Lagos” Still Jay yayi a inda yake tsaye ko kwakkwaran motsi baya yi yana kallon Ajay, Ajay ya ja numfashi sannan ya zauna kan kujeran dakin ya lumshe idanuwansa ya jinginar da kansa jikin kujeran trying to calm himself, Jay was speechless and shock at the same time, da kyar ya ja kafa ya zauna gefen gadonsa ya dafe kansa da yaji yayi masa nauyi, kamar an tsikare Ajay ya mike yace “Book us ticket to Lagos” Daga haka ya fice daga dakin.*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788 👈🏻, it’s better ki ji tsoron Allah ki sauke nauyi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500*Akwai wani abu da yake iya faɗakar da tunani tun daga nesa…Wani ƙamshi da yake sa zuciya bugawa da sauri…Wani ɗanɗano mai narkar da zuciyar masoyi…Wannan shi ne ƙamshin *Scent Palace**Scent Palace*, da ke cikin birnin Gombe, shine gidan turaruka na musamman da ke kawo muku turaruka masu inganci daga cikin gida da waje masu ɗorewa, masu daɗin shaƙa, kuma masu burgewaIdan kina son turare da zai saka masoyinki ya ƙara zurfafa soyayyarsa gare ki ko kuma turare da zai sanya ki zama abar misali a wajen jama’a to *Scent Palace* shine mafita.Abubuwan da muke da su sun haɗa da:Turaren jiki (body spray/perfume) na mata da mazaTuraren gida da ɗakiTuraren motaTuraren wuta na gargajiya da zamaniEid Gift Boxes an tanada musamman domin ku da masoyankuMe yasa *Scent Palace*?✔ Ingantattun turaruka daga ƙasashen waje✔ Farashi mai sauƙi da rangwamen Sallah✔ Kyaututtuka da aka shirya cikin kwali na alfarma✔ Nationwide delivery *Scent Palace* ba kawai turare ba ne ƙamshi ne da ke ƙarfafa soyayya, daɗi, da kimaTuntube mu yau don odar ki:📍 Gombe📞 08038888936 Instagram/Facebook/WhatsApp:08038888936,08154812224*Scent Palace* Ƙamshin da ke bayyanar da ƙima! Ƙamshi ba wai kawai ƙamshi ba magana ce ta zuciya
