Hausa novels

Halysaah Page 126 By Khaleesat Haydar

HALYSAAH PAGE 126….Khaleesat bata fasa rokon Ajay cikin rikicewa ba muryarta na rawa tana cewa don Allah ya barta ta tafi bandaki amma yaki ɗaga ta, da kyar take numfashi saboda weight dinsa da ya sakar mata amma ko lura da situation din da take ciki bai yi ba he was just smooching her tenderly all over her neck kuma iya abinda yake yi mata kenan sai hannunsa da yaki cirewa a kirjinta stroking it back and forth, kana ganinsa kasan he was so lost in the moment don tuni idanuwansa suka sauya launi suka dawo kamar na me jin bacci, Khaleesat ta dade bata shiga irin shock din nan da ta shiga ba don yayi mugun tsoratata, ganin abun ta dinga yi kamar a mafarki don in ance mata Ajay will do this bazata taɓa yarda ba, this was the least thing she expected from him, bai ma yi kama da wanda zai iya yi mata haka ba, kokarin sauke hannun rigar baccin jikinta yake yi cikin zafin nama, nan taji wani sabon strength ya zo mata ta fara kokuwa da shi trying so hard to push him off her cikin tashin hankali tana rokonsa amma sai da ya sauke rigar kasa gaba daya giving him full access to her radiant chest, nan ya kara birkicewa gaba daya, and it seems he was just after the chest a duk jikinta, bata san sanda ta dinga matse laps dinta ba tana cewa zata je restroom amma bai ma san tana yi ba, kawai vibration din wayarsa dake kusa da su ne ya dawo da shi duniyar da ya tafi, lokaci daya ya fada gefenta da sauri yana sauke numfashi looking so disoriented after realizing what he was doing, cikin few seconds ya sauka ƙasan carpet din dakin, tuni Khaleesat tayi using wannan opportunity din ita ma ta koma can daya side din gadon ta sauka kasa da sauri ko ina na jikinta na rawa tana kare kirjinta da hannunta, Ajay ya mike kamar ana hankadasa ya nufi kofar fita daga dakin almost stumbling over his feet, bai tsaya bangaren nasa ba kawai ya nufi part din Jay ya bude kofar ya shiga ya wuce bathroom dinsa, Khaleesat na ganin Ajay ya fita ta mance da wani Legend ta tashi ita ma ta maida rigarta ta fice daga part din cikin firgici ta koma dakin da take zama da gudunta, har sannan jikinta bai daina rawa ba, gaba daya ya tsorata ta, this was something she never saw coming saboda trust din da tayi masa, ta shiga bandaki da sauri tana duba laps dinta jin kamar period dinta ne ke zuba, after almost 15 mins ta fito daga bandakin duk jikinta a sanyaye ta jingina da bango tana shesshekan kuka, gaba daya ji tayi bata da sauran kuzari, she was so weak, har lokacin kuma ta kasa yarda da abinda ya faru don gani take kamar mafarki ne, after a while ta bude press din dakin ta ciro kayanta tana goge hawayen da yaki tsaya mata, cikin few minutes ta gama shiryawa har sannan bugun zuciyarta bai dawo dai dai ba ta nufi kofa da sauri ta bude ta fita, tsabar yanda take a rikice ta ma mance da wani kare a gidan, burinta kawai ta ganta out of the House, a haka ta sauka downstairs, luckily karen ma baya parlon ta nufi kofa ta fita kamar warce ake kora daga gidan ko waigawa bata yi ba. Wajen karfe tara Safiyyah ta bude kofar apartment dinsu jin ana danna bell, pajamas ne jikinta alamar she was still on bed, da mamaki ta dinga kallon Khaleesat daga sama har kasa tace “Ke kuma daga ina haka da sassafen nan?” Khaleesat taki yarda su hada ido kawai ta shiga cikin parlon tana kokarin hadiye kukan da ke neman kubuce mata, Safiyyah ta bi ta da kallo don ko jaka babu a hannunta balle waya gashi gaba daya ta ganta a firgice, can dai ta kulle kofar ta bi bayanta don dakinta ta nufa, zaune ta sameta kan kujera ga tsoro bayyane a fuskarta, Safiyyah tace “Wai me ya faru ne? Ko jikin Ajayn ne?” Kamar jira Khaleesat take ta fashe da kuka tana girgiza kai tace “I regret listening to you Safiyyah, kin cuce ni wallahi, nayi dana sanin sauraronki, dama kin saba fadin abinda ba shi ba, kin saba zama ki kirkiro karyarki ko kunya baki ji” Safiyyah dake ta kallonta kamar me son gano wani abu ta zauna gefen gado tace “Ikon Allah ni Safiyyah, Wani abu ne ya faru kike kirana da makaryaciya da sassafen nan ko gama bacci banyi ba karar bell da kika danna ya tasheni” Khaleesat ta fashe da matsanancin kukan da yafi na farko ta rufe fuskarta da tafin hannunta cikin rawan murya tace “Don me zaki ce min kinyi mafarkin bashi da lafiya kika sa na shirya da daddare naje gidan alhalin lafiyarsa kalau? Ai ni ban san haka halinsa yake ba wallahi, and i trusted him with all my heart ban taɓa expecting haka daga garesa ba, a duk duniya he is among the people I trust with all my soul cause I feel secure with him, amma ni ban san haka yake ba, kuma har naji na tsanesa, I hate him because of this, he betrayed my trust for him” Safiyyah ta saki baki tana kallonta, can ta ɗan yi murmushi tace “To da kika je wani abu ya faru ne a gidan da kike irin wannan maganganun? Yau naga karfin hali, In ma wani abu ne ya faru naga dai mijinki ne, ko dai mantawa kike ku ma’aurata ne?? meye abun tashin hankali in ma nuna maki yayi shi mijinki ne?” Khaleesat ta wani kalleta da sauri, cikin few seconds tayi maza ta gyara zancenta tace “Ban gane abinda kike nufi ba, karen nan ne fa ya sake bi na ba wani abu ba, what are you talking about” Tana fadin haka ta mike ta tafi ta kwanta gefen gadon Safiyyah alamar bata son conversation din kuma, Safiyyah dai sai kallonta take tana murmushi don bata ga alamar gaskiya take fadi ba, can tace “Gaskiya karen nan bai kyauta ba gashi ya kora ki da sassafe, a can gidan kika kwana kenan?” Khaleesat taki ce mata komai ta hade rai, mikewa Safiyyah tayi ta fita daga dakin zata je kitchen, ita dai tasan ba haka nan Khaleesat ta taho gidansu da sassafe ba kamar warce aka koro, ina ma ace abinda take zargi ne ya faru kuma ace har ciki ya shiga da sai taga karyan iskanci wajen Khaleesat, bayan ta koma dakin tace “To ko dai in hada maki ruwan dumi a bandaki ne? You look stressed” Mikewa Khaleesat tayi ta zauna tana mata wani kallo tace “What are you talking about, wai kina tunanin ni zan taɓa yarda da shi ne no matter what Safiyyah? You think i will accept him as a husband bayan kin san abinda ya faru? Ai ni ba er cin amana bace kuma nasan halacci, don haka kar ma kiyi tunanin ko wani abu ne ya faru don nasan ki da banzan tunani, to babu abinda ya faru wallahi, kuma babu abinda zai taɓa faruwa cause we are not meant for each other, in ma zaki dena tunanin dake ranki ki dena, banda ma karen yasa na yar da makullin apartment dina a parlorn gidan kin zata zaki gan ni gidan nan ne, ba sai ma ya sake ganina a gidan zai yi attempting komai ba….” Safiyyah dai kawai tayi murmushi don tasan duk wannan nonsense din nata ya kusa zuwa karshe yau ko gobe, Ita dariya ma take bata, wai ba er cin amana bace ita, to amanar wa za a ci? Da ba don tasan Khaleesat na da ilimin addininta dai dai gwargwado ba da babu abinda zai sa bata yi tunanin ko dai islamiyya ne bata taɓa zuwa ba duk tsawon rayuwarta, wani lokacin in Khaleesat ta yi wata maganar sai tayi ta mamaki kamar warce ake controlling da battery don ko nazarin abinda zata furta bata yi, kanta tsaye take fadin duk abinda ya zo bakinta, wai ita ba er cin amana bace, Safiyyah ta taɓe baki tace “Samu kika yi, me yasa bakin ki wasn’t this sharp for Abdul?? I wish zaki san value din da mijinki yake da shi wajen yan mata da yanda suke rubibinsa da burin mallakansa a matsayin miji da baki dinga shirmen nan ba, all because of Jawwad that is there enjoying his marriage….” Mikewa Khaleesat tayi ta shige bandaki ba tare da ta tsaya ta ci gaba da sauraronta ba. Har bayan la’asar Khaleesat na kwance dakin Safiyyah gaba daya mood dinta a dagule throughout, sai juye juye take yin kan gado, gashi har sannan her body was still weak from what happened in the morning, duk yanda ta so distracting brain dinta daga incident din hakan ya ci tura, don duk bayan mintuna kadan abinda ya faru sai ya fado mata a rai taji kamar it’s happening at the moment, she still feels his hand gently moving round her chest, she still feels his rapid breathing on her chest, wani lokaci kuma taji kamar bakinsa na wuyanta don har sai ta kai hannu ta shafa wuyar jifa jifa, Safiyyah ta idar da sallah ta juya tana kallonta tace “Lokacin sallah fa ya wuce Madam” Khaleesat dai tayi shiru don ko magana taki yi da Safiyyah all through, a hankali ta sauka daga saman gadon ta nufi bandaki zata yi alwala Safiyyah ta bi ta da kallo, ta girgiza kai tana ɗan murmushi, dai dai nan wayarta ya fara ring, ta dau wayar ganin Ajay ne ta mike ta fita daga dakin, a parlor tayi picking call din nasa, maganar few seconds suka yi sannan ta fita can waje, gaban apartment dinsu ta gansa yayi parking yana jiranta, ta karasa har kusa da motar ya mika mata makullin hannunsa ta amsa sannan ya ja motarsa ya wuce. Sosai Khaleesat ta ji dadi bayan da Safiyyah ke sanar mata ai kamar akwai spare key din apartment dinta da Housemate ya taɓa bata da dadewa ta ajiye, Khaleesat tace “Don Allah kawo in ga ko shi ne, ko dai key din old apartment din mu ne” Safiyyah ta mike ta bude wani jakanta ta ciro makullin da Ajay ya kawo ta nuna ma Khaleesat tace “Duba ki ga, ban san ko na tsohon apartment din bane” Khaleesat ta wara ido ta amshi makullin tace “Ai kuwa na new apartment din ne wallahi, amma naji dadi sosai, let me just be going to my apartment dama na gaji” Safiyyah tace “To wayarki da kika baro can gidan fa?” Khaleesat ta hade rai tace “I don’t want to talk about that” Safiyyah tace “To amma ki jira mu ci abinci don nasan ko kin koma ba abincin zaki ci ba” Daga haka Safiyyah ta fita daga dakin, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo da plate din shinkafa sai robobin drinks biyu, na zobo da wani me kamar kunun Aya, Safiyyah tace “Zan sha Zobon ke ki sha wannan” Khaleesat bata ce mata komai ba ta fara cin abincin a hankali duk da bata da appetite kwata kwata, kadan ta ci ta ajiye cokalin, zata dau ruwa ta sha Safiyyah tayi saurin cewa “To baki sha drink din ba ai” Khaleesat ta kalli robon drink din tace “Maman Aslam ce tayi?” Safiyyah tace “Eh mana, kin san lokacin tana Nigeria shi take siyarwa online, manyan mutane ke siyan natural drinks dinta, a nan ma ana saka order” Khaleesat ta bude ta sha kadan to feel the taste, can ta kalli Safiyyah tace “Kamar ba kunun Aya ba ai” Safiyyah tace “Mix nutritious kunun Aya ake ce masa, sai kin ci gaba da sha zaki ga ya ma fi kunun Aya dadi da gardi, shegen tsada fa garesa shi yasa na dauko daya kawai kar gobe ta kulle fridge dinta” Khaleesat ta ci gaba da sha don yana da zaƙi sosai, bayan ta sha ya wuce rabi ta ajiye sauran Safiyyah ta hade rai tace “To waye zai shanye wannan din da kika rage, salon ta kullaceni in taga na dau mata abu kuma bamu shanye ba” Khaleesat ta dau sauran ta shanye don bata son jaraban Sophie, bayan ta ajiye empty goran ta mike ta fara shirin tafiya Apartment dinta…. Tun da Khaleesat ta isa gida take kwance kan 3 seater a parlor tana jin jikinta duk a mace, weakness din da take ji har yafi wanda ta yini take ji yau, ta ma rasa gane yanayin da take ji a jikinta, kan kace me ta dawo kamar mara lafiya, wajen karfe bakwai da rabi ta mike zaune da kyar a ranta tana addu’an Allah ya sa akwai pad a gidan cause she is expecting her period is here, tashi tayi tana tafiya a hankali ta wuce sama zuwa dakinta, ta ciro pack din pad a cikin kayanta ta dau daya ta shiga bandaki, after taking her bath ta dauro alwala ta fito ta saka doguwar riga ta dau Hijab dinta a cikin press sannan ta shimfida darduma ta tada sallah, tana idarwa ta kwanta kan darduman ta lumshe ido. Washegari haka Khaleesat ta yini a sama tana bacci don daren jiya bata wani yi bacci isasshe ba, da yamma bayan tayi wanka tayi sallan La’asar tana kitchen tana dafa tea taji kamar an bude kofar apartment dinta, sosai gabanta ya fadi ta juya da sauri tana kallon kofar kitchen din duk da ba ganin wanda ya shigo parlon zata yi ba, a hankali ta kashe gas ta koma gefe ta tsaya taki fita daga kitchen din duk da hijab din da tayi sallah ne jikinta har sannan, tana ta tsaye har na minti goma daga karshe ta dake ta leka parlon, yana zaune kan kujera ya saka face cap idonsa sanye da Black glasses yayi keeping serious face, sosai taji gabanta ya fadi ta koma kitchen din da sauri ta jingina da cabinet kamar zata yi kuka, har cikin ranta taji tana tsoronsa kuma yanxu, ta kara tsayuwan wani minti biyar a kitchen din kafin tayi karfin halin fitowa ko ta kan shayinta bata bi ba don har taji shayin ya fita ranta, ko da wasa bata yarda ta kalli inda yake zaune ba kanta a kasa ta nufi stairs tana tafiya a hankali zuciyarta na bugawa, ya bi ta da kallon gefen ido ta cikin Glasses dinsa ba tare da ya juya kansa ba, sai da yaga zata haura stairs yace “Kee” Cak ta tsaya jin serious tone din da yayi using, sai kuma ta juya kamar munafuka ta ɗan kallesa, lokaci daya tayi saurin sunkuyar da kanta tana wasa da hijab din jikinta, duk da ba ganin idonsa take ba amma wani irin kunya taji take ji, after some seconds ya mike ya nuna mata kofar fita apartment din calmly yace “Mu je” Bata san sanda ta sake kallonsa da sauri ba gabanta na faduwa, sai kuma ta marairaice kamar zata yi kuka tace “Ni dai wallahi nafi son apartment din nan don Allah kayi hakuri ka bar ni pls, we are starting exams upper week ina son in dinga karatuna quietly a nan, nafi gane karatun a gidan nan” Ya hade rai yace “Fita mu je na ce” Hawayen dake makale idonta suka zubo, cikin rawan murya tace “Don Allah kayi hakuri ka bar ni….” Tsorata tayi saboda tsawan da ya daka mata ya nuna mata kofar fita daga apartment din, bata sake masa musu ba tana goge hawayen idonta jikinta na rawa ta nufi kofar fita daga apartment din ya bi bayanta, har suka koma can gidan hawaye take, sosai hankalinta ke a tashe and she felt just like she is with a total stranger, a hankali take haurawa sama tana goge hawayen da yaki tsaya mata bayan sun shiga gidan, tana jin yana biye da ita a baya amma taki yarda ta juya saboda tsoro, zata shiga dakin da take zama taji muryarsa yace “Walk straight” Sai a sannan ta juya ta kallesa, har lokacin yaki cire glasses din idonsa da face cap kuma kallonta yake directly in the eyes baya ko kiftawa, kamar ta sani ta sunkuyar da kanta, Calmly yace “Ba ki jin turanci ne?” Juyawa tayi ta ci gaba da tafiya a hankali walking down the corridor kamar yanda yace, kawai taga ya wuce ta, sannan yayi knocking kofar wani daki yayi sallama, after few seconds ya cire face cap dinsa da glasses din idonsa ba tare da ya bari su hada ido da Khaleesat ba ya bude kofar ya shiga ciki leaving the door open, Khaleesat: da gabanta ke ta faduwa wondering who was inside the room ta ɗan leka cikin dakin before going in, wani ƙara tayi tana zaro ido with surprise ganin Aunty Farida zaune cikin dakin, bata san sanda ta nufeta da gudu ba ta tafi ta fada kanta ta kankameta.

Back to top button