Haihuwa Da Hanji Page 58 Hausa Novel
Alhamdulillah komai ya cigaba da tafiya normal bayan nan, ta cigaba da lectures ɗinta cikin kwanciyar hankali kuma tana samun duk wani kyautatawa daga zuri’ar na mijin nata kaman yadda shima yake kara samun kusanci da iyayenshi, Mai martaba ya sha jinya kan ya warke ya tara matan yayi ta basu haƙuri a ganinshi komai ya faru ne sanadin aurenshi da suka yi, sun nuna haka ƙaddarar su take sai dai Fatan Allah yayi musu sakayya akan Adama, Zarah da bata san komai ba sai da aka warware daga farko ji tayi duniyar yayi mata zafi damuwa yayi mata yawa ta tattara ta koma wurin mahaifiyarta da dukkansu har yan uwanta kunyar abinda mahaifinsu ya aikata ya sa ba sa iya ko fitowa, Ammi bata neme ta ba haka Aisha don tunda har ta yi niyyar auren Rayyan ne don ta cutar dashi su ma suka ji ba za su iya cigaba da hulda da ita ba amma Aisha tayi kuka kaman ta mutu, ta ɗauki zarah kaman ‘yan biyunta ne bata zaci hakan daga gareta ba.Maganan yanke hukunci sai da suka yi wata biyu suna cikin na uku garƙame cikin azabtarwa kan aka yankewa Fulani Adama hukuncin kisa ta hanyar rataya, Makama da asirinshi ya dawo mishi ya haukace damuwarshi kawai a barshi yayi ta tafiya ji yake kaman kwakwalwarshi zai fashe idan bai shiga duniya ba dukan da yake yiwa Madaki yasa aka raba musu ɗaki, shi Madaki da sauran hadiman an yanke musu life imprisoment iyalan su sun yi kuka kaman ba gobe amma bahaushe ya ce tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan yi wa dukan tsiya.Soyayya tsakanin Saleem da Aisha yayi nisa don har ya turo mai martaba yace za su yi fixing rana sai a haɗa da na Ameer da ya kasa komawa da Abeeha dake shirin gama makaranta, Jiddah dai da tayi mugun kewan su sai dai a haɗu a yi ta waya. Yau ya kama ana ya gobe Afeefah za ta gama First semester examination ɗinta kuma Rayyan ya tabbatar mata a satin za su fara shirin tafiya Kaduna don ta matsa mishi sossai akan komawa ga su Suhail da kuma su kawu Dukda shi baƙin cikin kawun bai taɓa wankuwa mishi a rai ba sai dai bai hanata ba don haka mai lalle ta nema Ammie ta turo mata har sashenta.Tana zaune da dogon wando da wani shirt Black na ma Rayyan ɗin ne daga ganin girman da yayi mata amma ta fi jinta comfortable ciki, ta ɗaura Black dan kwali a kanta an gama lallen kafa da hannun duk an saka leda su Aisha na gefe suna ta hirar su da ta shafi rayuwa har jan ya kama aka cire mata sai aka zana mata baƙi a bayan hannun don ta ce jan kawai ya isa a kafafun yarinyar kwararriya ce kuma lallen ya mugun kamawa yayi maroon sharrr kaman ka sace kafafun in ka gani, Rayyan ne yayi sallama ya shigo duk suka mishi sannu da dawowa daidai an gama baƙin kenan ya tsaya yana kallon hannun kan ya ce “Wai tunda na bar ku kina nan wurin zaune?”Ta karkata kai fuska a ɗan Shagwaɓe tace “Kwalliyar kenan sai wahala duk yunwa ma nake ji babu hannun cin”Ya kalli hannun nata sai ya nufi kitchen, Aisha da Abeeha suka kwashe da dariya suna tafawa”Sai da ke Matar mijinta”Aisha ta faɗa tana dariya.Abeeha tace “Ku tashi mu tafi yanzu bai wuci abinda zata ci ya je nema mata ba kan ya dawo ya kora mu ko su makanta mu gwara mun yi ta kanmu salin alin”Afeefah na ce musu su tsaya ko ta kanta basu bi ba suka tarkata suka tafi sai gashi ya dawo hannunshi rike da wani plate.”Duk ka kora min ‘yan hirar Ya Saraki…””Dama wani amfani suke dashi a gareki idan ina nan? Babu so Haaa ki ci abinci”Murmushi ta saki tana bude baki ya saka mata Nan-bread guda biyu da ya sanyo a plate ɗin da curry chicken da ya zuba a gefe, da hannunshi yake bata yana tabbatar da bai ɓata mata jiki ba har ta ƙoshi ya bata ruwa ta sha kan ya shiga duba lallen.”Kin yi wa lallen nan kyau ainun Boɗɗi na”Tayi murmushi tana sake kallon lallen “Ko kuma shi ya min kyau dai ko Ya Saraki?”.”Wai dama baki sani ba?””Mene?””Ado biyayya yake miki, Kwalliyar da kanshi ke kike mishi kyau ba shi yake miki kyau ba..”She’s just blushing don bata gajiya da sauraron dadadan kalamanshi yana ɗan wuya ya sake bakin don haka idan ya sake yana zubowar tana amfani da damar ta adana a cikin zuciyarta ta yadda ko baya nan in ta tuna fuskarta kan zama ya cika da tarin murmushi.Washegari kuwa aka kai ta paper yadda aka saba motoci biyu har gaban exams hall su jira ta gama a dawo da ita gida, yau ko da ta fito bata gansu ba, daga jikin hall ɗin ta tsaya sai ta ga call nashi tayi picking ya ce mata ta taho yana kallonta fuskarta cike da fara’a ta nufi motar nashi don a yau da kanshi ya zo ɗaukar ta.Idanunshi da ya zura mata tun tahowarta ya lumshe a sadda ta yi masauki gaban motar kamshinta mai sanyi da natsuwa na ratsa shi”Hey Assalamu Alaikum”Ta furta a hankali tare da miƙa mishi hannunta ya ɗan murmusa kan ya miƙa nashi ya shigar cikin nata yana kallon tsakiyar idanunta ya furta”Wa’alaikissalam warahmatullah”Cire hannunta ta so yi sai ya gimtse yana mata kallon baki isa ba kuma ai dariya ta ɗan yi, ya miƙa hannu gefenshi ya zaro wani rose Red nd green dake fidda sassanyar kamshi ya miƙa mata.Da hannu ɗaya ta karɓa ta kai hancinta tana lumshe ido fuskanta ɗauke da murmushi tace “and this?””I am bribing you a ban dama in fitar dake outing”Dariya ne ya ɗan kufce mata “seriously? Ai na zaci saurayi da buduruwa ne ke fita date ba mata da miji ba”Tayi tambayar tana wara fararen idanunta a kanshi ya kai hannunshi ɗaya kan kumatunta ya shafa “Babu laifi a hakan…. Afeefah ki na da kyau fiye da duk wani abu mai kyau, kina da daraja fiye da duk wani abu mai daraja a kullum soyayyarki ƙara yawa take a zuciyar Ryan, I will always love you again and again…kullum sabunta kanshi soyayyar ki ke yi so i have to be very caution”Tayi murmushi mai cike da tarin alfahari tana sake shinshuna kyawawar furen dake hannunta.Motar ya ja suka fice daga makarantar.”Kin ce za ki yi sayayyar su Suhail should we start with the shopping ko mu je ki sha ice cream?”Tayi murmushi tana sake jin alfahari zuciyarta fal godiyar Allah tace “Lets start with the shopping”Kai tsaye shopping din ya kaita a tare suke tafiya hannunshi rike da nata ɗayan yana tura chart na shopping din ita kuma tana duba abinda zata ɗauka.Tsaye yake sai dai bayanshi a jingine da stall ɗin kayayyaki inda suke babu wasu yawaitar mutane, ita ke sayayya shi ya zuba mata idanu yana aikin kallo, sanye yake da full Black Jean nd top ya saka facing cap da ya zauna mishi sossai saboda mutane kar su gane shi, takalman kafafunshi ma bakake ne, hannayenshi duka a zube a aljihu… Don tun dazu suke tsaye wurin choculates ɗin tana ta rawan ido.Ta ɗauko wani choculates tana dubawa sai kuma ta ɗan ɗago karab suka haɗa idanu kusan karo na biyar kenan a take ta Shagwaɓe fuska tana kallonshi ya ɗan saki smile yana ɗage mata gira guda”ya dai? Na miki ne?”Ya ƙarshe da wani kayataccen murmushi…”Ni ya kamata in ce haka ai tun da ni ake ƙarewa kallo.. Ni Allah watarana har muni na sai ka binciko”Ta faɗa cikin yanayin da ya saka shi faɗaɗa murmushin shi, choculates na hannunta ta ɗaga sama”Ina son picking wa su suhail wannan yayi ko? Ko me kake tunani?”Very naughty yana ɗan lashe lip ɗin shi na ƙasa ya furta”I am thinking of kissing you…”Hannu ta saka ta rufe baki tana zazzaro ido ya saki dariya mai sauti kan ya yunkura ya nufe ta, kalle kalle ta fara kan ta yunkura kuwa da gaske yayi pecking lips ɗin nata hannunshi na ɗan manna ta da jikinshi.”Ya Saraki waje fa muke””Ina ruwana”Ganin yana ta kallon fuskarta ta san zai iya aikata abinda ma ya fi haka don haka ta janye ta saka choculates ɗin tace su tafi ita kam ta gama, sai murmushi yake mata don ta bashi dariya yadda take zare ido kaman yayi komai ne gaban mutanen, shi ya biya kuɗin suka fice.Sossai suka zazzaga ya kashe ta da tarin soyayya wai murnar kamallah exams sai dare suka koma masarautan, a sayayyanta har su Ammie ta yiwa don haka tana idar da isha ta fito hadimarta tayi saurin karbar manyan ledojin hannunta suka nufi sashen Ammin don shi bai shigo ba tukuna, ta shiga sashen Ammin da sallama sai idanunta suka sauƙa kan zarah dake tsugune ƙasa sanye da hijabi tana kuka sossai.Gefe ta samu ta zauna bata ce komai ba har zarahn ta gaji da kukan ta fara roƙon su yafiya duk ta rame tayi duhu. Ammi ta sauke numfashi tace “Zarah ki daina kukan nan haka ni kam na yafe miki, wlh ban taɓa bambanta ki da Aisha ba Dukda na ji mamakin ƙudirinki a kaina amma tunda kin gane kuskuren ki Allah ubangiji ya yafe mana gabaɗaya”Aisha ma tace ai ya wuce. Ta kalli Afeefah zata yi magana Afeefah tace”Ni dai baki min komai ba wlh zarah. Allah ubangiji ya cigaba da ɗora mu duka bisa turban gaskiya”Suka amsa da Ameen kan ta miƙe ta fice suka bi ta da kallo.Afeefah ta gaishe da Ammie ta amsa cike da kulawa tana tambayarta exams “Alhamdulillah Ammie mun gama lafiya””Allah ya ba da sakamako na alkhairi, yanzu sai shirye shiryen tafiya Kaduna ko?”Kai ta gyaɗa Ammie tace “Masha Allah, Allah ya nuna mana. Akwai saƙo zuwa da safe za’a kawo miki sai ki duba ki ga idan akwai abinda kike son ƙari ko chanji duk sai a yi”Godiya tayi sossai kan ta miƙawa Ammie ledar hannunta daidai Rayyan ya shigo kenan tana cewa “Ammi mun je shopping ne sai na ɗauka muku da Abeey”Ta miƙawa Aisha nasu.Ammie ta buɗe ledar Dukda duk wani kyauta da za’a yi mata tana da halin yin fiye dashi amma kyautatawa abu ne mai daaɗi kwarai kuma ta ji daaɗi har ƙasan ranta Leshi ne mai tsadar gaske sai turare shima designer na Abeey, Abeeha da Zarah dogayen riguna ne egypt Abaya sai yan abun ciye ciye tarin choculates. Shi karan kanshi Rayyan fuskanshi ya nuna jin daaɗi ainun Dukda tare suka Saya amma ko kusa bai san har da su Ammie ta yi wa sayayyar ba sai darajar ta ya ƙaru a idanunshi barin ma da ya ji adu’o’in da Ammie ke yi mata anan ya fahimci duk kudin iyaye kyautata musu na saka su farin ciki kuma hakan Allah ne kadai ya san irin ladar da zai baka bisa wannan murmushi da ka sanya su aiko ya ƙudiri aniyar cigaba da ganin wannan murmushi na Ammie, Sai kusan goma suka bar sashen.Bayan kwana biyu da gama exams ɗinta suka fito a shirye tsaff cikin shiga na alfarma, tafiyar har da Abeeha da Aisha don duk sun gama exams motoci shida ne ya kaisu Airport yana riƙe da hannunta cike da kulawa da so da kauna har suka sauƙa a filin tashi da saukar jirgi na Abuja, anan ma motocin alfarma bakaken prado sai sheki suke da securities ne suka zo ɗaukar su ya san aikin mai martaba ne don haka babu wani dogon nazari suka shiga zuwa gida, sun samu gidan a cike su Saleem da sisters ɗin shi ga Sulaiman da matarshi da Twins su fauza ga jidda an shirya musu abinciccika iri daban daban kasancewar tafiyar mintuna 40 ne ba wani gajiya suka yi ba nan Sulaiman da Saleem da kuma Rayyan suka zauna sitting room yayinda ‘yan matan suke ta hira a parlor babu wani nuna bakunta ko rashin sanayya kaman ‘yan uwa. Sai wuraren isha duk bakin suka tafi Aisha ta sauƙa ɗakin Afeefah na ɓangaren Mammi yayinda su Afeefah suka sauƙa sashensu.Washegari da safe suka fito a shirye tsaff suka shiga wannan motocin nan a jere suka Lula sai Anchau Shigowar su Layin su Aunty zee suka jera gabaɗaya securities ɗin suka fiffito aka buɗe musu kofa za ta sauƙa ya riƙe hannunta yana kallon gidan da ya fara ganinta ciki a sadda ta sallamar da Rayuwa, ita kanta tana tuna ranar da aka yi yunkurin kashe ta a wannan gida, tana tuna rayuwarsu da Aunty zee tana iya tuna ranar da ya fara tare ta a cikin jikinshi lokacin da ta yanke yin mai Dungurun gum da rayuwarta Wai HAIHUWA DA HANJI a sadda ta sallamar cewa barin ta duniyar shine maslaharta idan har ta tafi ai shikenan babu mai kallonta bare yayi mata sharrin maita ko zama annoba. Idanunta cike da hawaye ta kalleshi ya lumshe nashi cikin su fuskarshi babu walwala yace “Kin ga dalilin da ya sa bana so ki zo ko?”Ta mayar da kanta ƙasa ta san kuka kam sai ta yi shi kuma abinda baya so kenan sam.”Ki min alkawari ba za ki yi kuka ba”Tayi shiru bata ce komai ba, ya zame hannunshi yana sauke numfashi sai ta juya ta sauƙa ta nufi kofar kyauren gidan da ya tsufa mata ainun kaman ba gidan Aunty zee ba da yake fes fes, jama’ar unguwa dayawa sun fita suna kallon wanda ya zo don jiniyar masu take musu baya ya ja hankalinsu sossai.Sanye take da wani dakakken purple lace mai shegen tsada an yi mata dinkin Borno style straight skirt da bubu da yayi mugun kyau ta zuba accesories gold ne daga wuyanta zuwa hannunta mayafinta ya zauna mata sossai hannunta rike da wani sabon designer bag da ta dauka cikin kayan aurenta da har lokacin suke gidansu na Kaduna don bata tattare ba, sai takalmin ta mai ɗan tudu wannan vibe ɗin na manyan mata kuma hajiyoyi yan gatan mazajensu shi take bayarwa har ta tura kofan gidan ta sanya kai da sallama.Wasu yara biyu ta gani suna wasa sanye da wasu kaya da suka fi yanayi da tsumma sun yi dukun dukun macen gashinta kaman wanda yayi shekara bai ga ruwa ba, kafafunsu babu takalmi, ganin ta yasa suka tsaya suna kallonta kamannin fuskokin su yasa taji tayi bursting to tears, gabanta na tsananin faɗuwa ta ce “Suhail…! Suhailaah???”.Abeeha ce ta dafa ta ganin tana ƙoƙarin faɗuwa saboda jirin da ta ji ya ɗauketa a lokacin da suka amsa, waennan su ne yaran Aunty zee? Su Suhail ne haka? Innalillahi wainna ilaihi rajiun”Ina Babanku?”Cikin maganansu suka ce “Yana ɗaki kwance ba shi da lafiya”Da sauri ta nufi ɗakin da yake kwancen babu komai cikin ɗakin sai tantagaryan siminti, me ya faru? Ta fara tambayar kanta kan ta isa inda yake kwance kan taburma idanunshi a buɗe yana kallonta ta duka gangarshi “Uncle Usman!!”Hawaye na zubo mata babu kakkautawa a hankali yace “Afeefah?? Ke ce??”Hannayenta ta sa ta toshe Bakinta tana sakin kuka da gaske su ɗin ne cikin wannan hali?”Uncle me ya faru? Ina Hamdiyya? Me ya samu aikinka baka da lafiya ne?”Duk ta rasa ma me zata tambaya shima yana kuka yace “Ki yafe min Afeefah don Allah ki yafe min na cutar da ke, na kasa rike amanar da zainabu ta tafi ta bar mini ki gafarceni AFEEFAH””Baka yi min komai ba uncle wlh baka yi min komai ba hasali ma ka rike ni da amana tsawon shekara da nayi a gidan nan baka taɓa hantara ta ba, wlh baka min komai ba ni ban ga laifinka ba ko da ka zarge ni saboda ina da tambarin tun farko manne a goshina””Na kasa amincewa da cewa Allah ne me kashewa kuma mai raya wa, hankali na ya tashi ainun don bayan mun binne zainab kin dawo mun kore ki sai muka muka je asibiti da su Suhail za’a yi musu riga kafi a kuma ba mu madarar da ya kamata su cigaba da sha anan ne likitan ya ji maganan da muke yi da Hamdiyya da maiyya ce ta kashe zainabu yayi saurin taka mana birki ya kuma shiga yi mana bayanin abinda ya faru da zainabu wanda bamu sani ba, ya ce mata dayawa suna samun wannan matsala na Postpertum ko a samu taɓuwar mu’amala ko irin ciwon cikin wasu kam ma har a zaci sun haukace ne, ciwon cikin nata bamu farga da wuri ba sai da ya mata illah kwarai muka koma a sannan babu abinda za su iya ta rasu. Hamdiyya kuma dama ta jima tana yi mata hassada tana jin haushin yadda ta samu ciki ita tana zaune hakika ta yi yunkurin illa ta cikin tun kan su zo duniya Allah na kare su har ta haihu tana ganin kaman za ku haɗu ku kwashe dan abinda na mallaka da ke da zainabu ga yarana da farin cikin samuwar su bai ɓoya mini kuma dama ta jima tana sanyawa ranta ba sonta nake ba na aureta ne kawai don in haihuwa a yanzu da bata haihu ba matata ta haihu ta gama amfani kenan zan iya sakarta kowani lokaci hakan yasa ta ƙarfafa hassadarta a kanku musamman ke tana amfani da baƙanta miki tana kuntatawa Zainabu.A ƙarshe tayi sanadin da kika bar gidan nan anan ta fara rainon azaba ga yarana ba tare da na sani ba, duka zagi tun basu san kansu ba, ta bar su da yunwa ta bar su cikin ruwan wanka duka don ba ita ta haife su ba Allah ne ke kare su ban sani ba, a ranan da na san duk abinda take kullawa na shiga masifar tashin hankali marar misaltuwa musamman in na tuna abinda na yi miki daga nan jinina ya hau na samu matsalar shanyewan jiki, a takaice Hamdiyya ta tattara komai ta sayar akan ba zata iya zama da ni ba ga jinya, ga rainon ƴaƴan da ba nata ba kuma bata da damar haihuwa, ko sati ba’a yi ba na samu labarin mota ta kaɗe ta ta rasa kafafunta ta kuma rasa rabin fuskarta duk kudin yana tafiya a jinyar da har yau bata warke ba. Kuɗin da Zainabu tayi ta ajiye miki a asusu da su na tsira sai waenda abokan arziki kan kawo da shi nake aika yaran nan su sayi abinci su ci ko makota su basu, bana iya yi musu komai ko wanka sai dai su je su watsa”Sossai Afeefah ke kuka, Allah sarki rayuwa amma Hamdiyya ta cika azzalumar matar uba kuma ko a yanzu ta ga ishara, Rayyan Aisha ta kira don Afeefah ta kasa daina kuka hankalinta ba karamin tashi yayi ba shi ya kira aka dauki uncle Usman yace a koma cikin Kaduna dashi a kaishi asibiti zai kira Sulaiman kan su juyo.Su Suhail na rungume da Afeefah suka fito zuwa mota yan unguwar na zuwa su gaisheta suna ta mamaki har wasu na tambayar ko Afeefahn Aunty zee ce ta gyaɗa musu kai, Rayyan ya zubar da dukiya don duk wanda ya nuna ya gane ta aka gaisa sai ya mishi kyauta daga nan suka nufi Dutsen-wai.”Afeefah!”Ta kalleshi ya riƙe hannunta ya sa hannu yana share mata fuska yace “kuka sam bai kamace ki ba, ko don zafin da nake ji a nan ya kamata ki sassauta”Ya ƙarasa yana nuna zuciyarshi. Ta gyaɗa kai ya ce “Na san burinki shi ne ki yi kuɗi, ba kuma don wani abu ba sai don ki tallafawa al’umma musamman na ƙauye irin cikin kauyen ku da ake rayuwa kara zube babu neman ilimi, babu sana’a ana rayuwa irin rayuwar dabobbi ko zamanin da chan baya, ina so in sanar miki cewa na ba da wannan gudumawa na buɗe miki Center na farko ina fata ya zama farkon buduwar tarin alkhairanki… Ina adu’a Allah ya sanyawa gidauniyarki daga na farko har na karshe albarka ya dafa miki ya kuma isar miki da ladan… Akwai Center da aka gama buɗewa a Dutsen-wai da Sunanki a yau za’a yi taron kaddamarwa a cikin wannan plaza akwai kayan aiki da malamai na Musamman da zasu ke koyawa mata sana’o’in dogaro da kai kaman su ɗinki da sauransu akwai kuma makaranta islamiyya da malaman da muka yi hiring na musulunci da za su tsaya tsayin daka wurin ganin sun koyawa matan wannan kauye da ma mazan addini akwai kuma babban masallacin juma’a a kusa da wannan plaza shi kam na Mammi ne ina Fatan duk Sallar da za’a yi ciki ladar ya isa gareta. Ba ni da alaka da kula da wurin daga yau duk naki ne ga takardun da ma komai da komai na plaza ɗin kyauta ne na musamman zuwa gareki”Jikinshi kawai ta faɗa don ta gigice ta rasa ma wani irin abu zata yi, kuka kawai ta saka mishi yana ta aikin rarrashi za tayi godiya ya manne Bakinta da nashi yana kissing passionatly sai da ya tabbatar ta daina hawayen kan ya saki yayi pecking goshinta “Anything for you my baby girl ki sani wannan ɗin mafarin nasararki kenan a rayuwa, duk wanda ya baƙanta miki a da a yanzu yana a karkashin kafafunki, na ji daaɗi da kika nufi saka musu da alkhairi bayan sun bi ki da sharri amma ki sani wannan yunkuri naki na basu ilimi makami ne mai girman gaske a duniyarsu ladar ki sai a wurin ubangiji”Daidai nan suka isa cikin Dutsen-wai ita ke kwatanta musu har kofan Gidan Kawu Labaran.

