Hausa novels

Kurkukun Kaddara Takun Farko Chapter 76 By Hafsat Bature Complete Novel

💋KURKUKUN ƘADDARA💋

Cigaban page 76

“Nifa lafiyata qalou, Nagode da kulawar ku agare ni, nayi missing É—inku sosai,” Cikin sanyin murya ya furta hakan, A hanzarce Batul ta miÆ™a hannu ta kunna fanfo ruwa ya soma zubowa, tarba tafin hannayen ta tayi Ruwa ya taru a cikinsu ta wanke mashi fuskar shi tare da zuba mashi ruwan a bakin shi Ya kuskure shi, Bayan ta kammala ta ruÆ™o hannun shi “Mu koma É—aki Mubeen” Sai da suka taimaka mashi tukunna Ya iya miÆ™ewa, fitowa su ka yi daga Cikin toilet zuwa É—aki, A saman gadon Shi Ya kwanta Yana faman sauke ajiyar zuciya, kewaye da gadon shi suka tsaya suna tottafa mashi addu’o’i, hakan ba Æ™aramin daÉ—i ya yi mashi ba, bayan sun samu komai ya lafa suna shirin komawa su zauna Kwatsam Gabriel Ya farka Hananyen shi biyu daddafe da kanshi Ya fasa wata irin gigitacciyar Æ™ara da ta janyo hankulan su Gare shi, Jikin shi sai kerma yake yi musamman la66ansa, Sambatu ya ke yi na fitar hayyaci, A hankali Su ka soma tafiya suna tunkarar gadon shi, A kewaye da gadon shi suka ja burki suna ambaton sunan shi Muryoyin su a tsorace

“Gabriel! Meke damun ka? FaÉ—a mana ina ke yi maka ciwo,” Shiru bai tanka masu ba, Hankalin Azeeza duk yafi tashi don tuni tafara sharar Æ™walla, tsananin tausayin shi ne ya kama su, musamman da ya daddafe kanshi sai ya tuna masu da Danish, duk idan ciwon shi ya tashi haka ya ke yi masu ya dinga fasa Æ™ara,

“Gabriel are u okey? Kan ka yana maka ciwo ne”? Azeeza ce ta ke tambayar shi, Deeja tace “Ku É—an jira in jaraba yi mashi Karatu kamar yarda Angel ta ta6a Yima Danish wata’Æ™il shima yaji sauÆ™i, ta Æ™arasa maganar tare da hawa saman gadon ta matsa kusa dashi ta tallabo kanshi da yatsun hannayenta tare da É—ago dashi, Saitin kunnan shi na dama ta kai bakinta, Kafin a tsanake ta soma Yi mashi karatun qur’ani, surorin da ta haddace akanta, fatiha, iklas, Falak da nasi, da wasu ayoyi irinsu Ayatul kursiyyu, Amanar rasulu da sauransu, A nutse Deeja take karanta mashi su cikin kunnan shi, su Parveen duk suna a tsaye bakin gadon suna kallon shi azeeza tana zaune daga gefen shi, ga dukkan alamu natsuwa ta fara shigar shi, don tun da ta fara Jikin shi ya daina kakarwa, natsuwa ta fara shigar shi, A hankali ta zame Hannayenta daga saman kanshi,

“Da sauÆ™i jikin naka”? Tayi maganar tana kallon fuskar shi, sai faman lumshe idanuwan shi ya ke yi, daÆ™yar ya iya buÉ—e baki Ya amsa mata da cewa “Am ok, Ina fata mun same ku lafiya,” har suna haÉ—a baki wurin furta mashi “Muna Lafiya” parveen tace “faÉ—a mana su wanene mu, don ni ban yarda ka dawo dai dai ba,” A hankali ya ke kallon fuskokin su É—aya bayan É—aya Ya soma faÉ—a masu sunayen su

Hannah Hibba Deeja, Parveen, Eve, Yasmin, Batool, Rubina, Aziza, Sarah, Jamima…….” tunkan ya rufe baki yaga suna ta murna ganin ya dawo dai dai, haÆ™iÆ™a Yaji daÉ—in kulawar su gare shi, Sai dai abu É—aya daya faÉ—ar mashi da gaba rashin mutun É—aya acikin su, Yarinyar da ya Æ™wallafa rai akan son ganinta, don su dasa daga inda su ka tsaya

“Where’s ANGEL”? Ras gabansu Ya faÉ—i Jin tambayar da ya yi masu, Nan fa suka fara kallon kallon a tsakanin su fuskokinsu É—auke da matsananciyar damuwa

“Inna lillahi..! Mun manta da Angel! Tun É—azu da safe ta shiga toilet ta datse, Ba irin bugun da bamuyi ma Æ™ofar ba amma ta Æ™i buÉ—ewa, bamusan me ta ke yi a ciki ba”

Muryar Haris ce ya janyo hankalin su ga kallon shi, Farkawar shi kenan daga bacci Yana ji suna zancen Babu Angel, Jikin shi A raunane Ya yunƙura Ya miƙe zaune, Da sauri Deeja ta nufi gadon shi ta haye sama ta zauna tana kallon shi,

“Haris Sannu Ya jikin Naka? Ina fata ba inda ke yi maka ciwo” murmushi ya sakar mata yayin da ya ke bin ta da kallo, daga gani ba Æ™aramar kewar ta yayi ba,

“Deeja lafiyata qalou, Jiki na da sauÆ™i, Naji ana zancen babu Angel me ya faru da ita? Ko sun zo sun É—auke ta ne”?

Girgiza mashi kai tayi alamar a’a “ÆŠazu da safe ta shiga toilet yin wanka, bamusan meya faru da ita ba, mun jira ta buÉ—e mana Æ™ofa amma shiru, mun yi iyakar bakin Æ™oÆ™arin mu wurin ganin mun 6alle Æ™ofar amma taÆ™i buÉ—uwa,’ deeja na kai Æ™arshen maganar ta, Batul ta jefa masu tambaya “Haris Ina Danish É—inmu”! ÆŠago wa yai da idon shi tare da kallonta, Mamaki ne ya bayyana akan fuskar shi

“Kamar batul nake gani! Yaushe aka dawo da ke?” Murmushi ta sakar mashi tare da cewa “Tuntuni na dawo, Na yi kewar ku sosai,” Jinjina kan shi ya yi kafin yaci gaba da magana “Bansan inda Danish ya ke ba, saboda ba’a tare mu ke dashi ba, tsawon lokacin nan bamu ta6a Yin tozali da shi ba,” Idon Gabriel akan Batul Sai yanzu da ya dawo hayyacin shi ya gane ta, Yasan cewa Æ´ar uwar su ce da suke ta nema, kuma itace Yarinyar da ya gani a kwanakin baya saman Third floor Tana gudun ceton Rai! Baisan ya akai ta dawo ba, Sai dai yaji daÉ—in ganin ta da ranta da lafiyarta.

“Ƴar uwar mu ce Batul, nasan baka santa ba” Azeeza ce tayi mashi magana ganin yana kallonta, Numfasawa ya yi tare da saukowa daga saman gadon kamar zai kife kasa saboda rashin Æ™warin Jikin shi

“Ina zaka je”? Atare su Hibba su ka haÉ—a baki wurin yi mashi magana

“Inason ganin Angel, ku nuna mini Æ™opar toilet É—in da ta shiga, zan yi Æ™oÆ™ari in 6alle ta”

“Kana fama da kanka Gabriel taya zaka iya 6alle Æ™ofa, tafiyar ma daÆ™yar ka ke yinta, Pls Ka koma ka zauna bazamu bari ka Ƙara raunata kan ka ba, ” Hannah ce tayi maganar tare da ruÆ™o hannun shi, ba don ya so ba ya koma ya zauna daga gefen gadon shi.

Hankalinsu Ba ƙaramin tashi yai ba, sun gama murnar dawowar su Haris damuwar rashin Angel ta hana su sakat ga dare har ya gabato amma babu ita, Jamimah sai kuka take yi masu akan Su Je su buɗe ƙofa su ɗauko Mata Genie ɗinta Idan suna son zaman Lafiya, Sun saba atare su ke kwaciya bacci, kwanakin nan ita ke yi masu shimfiɗa a saman floor.

Komawa Cikin sashen toilet ɗin su ka yi, Don su ƙara jaraba ƙarfi ko sun samu ƙofar ta buɗe masu, Gabriel da haris sun so su taimaka masu Wurin buɗe ƙofar sai dai sun hanasu yin hakan saboda babu ƙoshin lafiya a jikin su.

Kukan Jamimah Ya karaÉ—e Cikin É—akin su, Hatta Javed da Naufal sai da su ka farka daga bacci saboda sautin kukanta daya cika kunnuwan su, TaÆ™i samun wuri ta zauna, Ga uban bargon data zumbula a jikinta, Angel ta rufe mata uniform a cikin toilet shiyasa take ta yin zarya da bargo, Kanta har ya fara sara mata, Gabriel ne ya miÆ™a mata hannu tare da ambaton sunanta, Kamar jira ta ke yi da gudu ta nufi gadon shi ya É—auketa saman jikin shi yana lallashinta, cikin shesshesÆ™ar kuka take ce mashi “Dan Allah kaje ka É—auko mini Genie É—ita, tun É—azu tana a cikin toilet, Æ™ofa ta rufe da ita sunÆ™i su taimaka mata, Uniform É—ina ma suna a ciki itace ta yi mini wanka tace zata Wanke mani su, in sun bushe sai in saka su a jiki na….” duk ta cika shi da surutun ta, shi kanshi hankalin shi ba a kwance ya ke ba, Kowa da abunda yake saÆ™awa a ranshi dangane da rashin Angel gani su ke kamar fa an É—auke ta shiyasa taÆ™i buÉ—e Æ™ofar, saboda babu alamun mutun acikin toilet É—in, Ko motsi wannan baka Ji.

Ina Angel ta shiga meya faru da ita?

abunda ya faru Lokacin da Angel ta zuÆ™unna a gaban tukunyar fulawar nan, Hankalinta ba’a kwance ya ke ba, tun da ta fahimci Furen Danish, Azalzalar da zuciyarta ke yi mata akan taje ta nemo shi taga a wani hali ya ke ciki shi yaja hankalinta, miÆ™ewa tayi a fujajen ta nufi glass window É—in nan ta sanya Hannu ta sauke glass É—in ta dire shi Æ™asa Jikin bango, duk da irin tsoron da take ji hakan baisa ta fasa Æ™udirinta ba, Bayan ta janyo bokiti ta haye sama sai da ta fara Ambaton Bismillahi da kyakkyawar niyya tare da wasu addu’o’in neman tsari masu Æ™arfi Kafin ta daddage ta haura tagar ta duro ta bayanta, tsananin tsoro ne ya kamata da firgici Amma a haka ta daure ta cije saboda idanuwan ta a makance suke bata ji bata gani burinta Kawai ta gano inda Danish É—inta Ya ke, Cike da Æ™warin gwiwa ta miÆ™i doguwar hanyar nan wadda zata sada ta da ground floor É—in Gidan kurkukun, Tana tafiya tana ambaton sunan Allah, Duk addu’ar da tazo mata a cikin bakin ta karanta ta take yi, hada É—an gudu gudun ta wurin yin tafiyar, lokacin da ta kawo Æ™arshen hanyar ta faÉ—o ta cikin babban Filin dake a kewaye da waÉ—annan Dogayen benayen, Ras taji gabanta ya faÉ—i tunawa da abunda ya faru da ita a rana ta farko da ta fara zuwa wurin, ba zata ta6a manta irin baÆ™ar wahalar da tasha ba, A tsananin tsoroce take Æ™are ma benayen kallo don ta ga ko zasu motsa kamar yarda su ka yi mata aranar farko, ganin sunÆ™i Motsawa yasa ta soma tafiya Cikin sanÉ—a tana tunkarar su, shiru baka jin hayaniyar komai, ita kaÉ—ai kwallin Æ™wal kamar ba mutane A gidan Kurkukun.

Har ta kai bakin benan ta soma Jin sautin Wata shaƙaƙƙiyar murya tana ambaton sunanta, A gigice ta juya tana kallon bayanta don taga wanene Sai dai bata ga komai ba, Sautin dariya mai kama da haniniyar Doki ta dinga Ji a cikin kunnuwan ta, Tuni zufa ta wanke fuskarta sharkaf, Can kuma ta dinga jin kukan jarirai Enyaaa enyeeh, Da sauri ta toshe kunnuwan ta da tafin hannuwan ta, bugun zuciyar ta na ci gaba da hauhawa, Jikin ta ya hau rawa, Saboda taurin kai irin nata a haka ta soma hawa benen la66anta na kerma wurin ambaton sunan Allah, ba zato ba tsammani taji Matattakalar Benan ta soma Motsawa, hakan ya sa ta daddage ta watsa da gudu tana haura matattakalar Yayin da benan ke mayar da ita baya har tuntu6e take yi ta kife Ƙasa, Staircases ɗin suka dinga janyeta suna mayar da ita baya kamar zasu saukar da ita daga saman gadon, Cikin zafin nama ta ɗago da kanta tare da miƙewa ta dinga gudu zufa na bin jikinta har sai da Allah ya bata nasarar kaiwa ga Second Floor, Ta ƙarfi ta buga tsalle ta haye sama tana faman Haki, sumar kanta duk ta rufe fuskarta, Ƴan hanjin Cikinta sai kaɗawa su ke Yi, A hankali ta yunƙura ta miƙe tsaye tare da juyawa tana kallon benan, Wani abun mamaki Gaba ɗaya ya daina motsawa sauke ajiyar zuciya ta yi, Angel da kasada taci gaba da tafiya Saman hawa na biyu, Sai faman baza ido ta ke yi tana ƙarewa ginin kallo, tsarin shi yadda kasan Ƴan hanjin Cikin mutun saboda kwana kwanar da ke gare shi, A dai dai Bakin wani corridor taci burki tana leƙa Ciki, Ɗakuna ta hango A jere Kusan guda Huɗu biyu suna fuskantar biyu, Ƙofofin su a rufe su ke sai dai bata da tabbacin Ko an sanya masu Kuba.

“Ya Allah ka tsare ni daga sharrin duk wani abun cutarwa, Ya Allah ka haÉ—a ni da abunda nazo nemo Cikin sauÆ™i ba tare da nasha wahala ba,” acikin zuciyar ta take ambaton hakan, É—aga kafarta tayi tare da nufar Ƙofofin, Hannu ta kai ta É—an ta6a Jikin Æ™ofar farko ba zato ba tsammani taji Æ™ofar tana lilo alamar a buÉ—e ta ke, Sai da ta fara karanta addu’ar neman tsari ba tare da Jin tsoro ba, ta faÉ—a ÆŠaya daga Cikin Æ™ofofin, wurga Æ™afar ta ke da wuya wani uban wari ya daki hancin ta, Idanuwan ta a zazzare ta ke Æ™are ma ÆŠakin Kallo, tamkar Igiyar Shanya ce kewaye A cikin shi ta kowane 6angare, babban abunda yayi mugun É—aga mata hankali Gangar Jikin Matasan Ƴan mata ta gani da maza Wanda basu haura shekarun su Batul ba, zindir babu kaya a jikin su, An É—aure wuyan su sagale Jikin Igiyoyin nan kamar kayan wanki da alama Sun gama amfani dasu, wasu An cire nonuwan su,wasu kuma an cire gaban su,Wasu Idanuwan su aka kwalkwale Yayin da wasu kayan Cikin su aka wawake, Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!!

Wata irin narkakkiyar zufa ce ta wanke ko’ina na jikinta da ke ta yin kerma kamar wadda ake kada ma mazari, duk ta bi ta furgice ganin komai ta ke yi tamkar a mafarki, Hannayen ta daddafe da kanta cikin fitar hayyaci ta fito daga Cikin É—akin, Maimakon tayi reverse ta koma Inda ta fito sai ta Æ™ara gaba saboda gushewar da hankalin ta yayi, A gigice Ta fito daga É—akin Wani irin jiri take gani a cikin idanuwan ta, Hannunta dafe da Æ™irjinta Zuciyar ta sai tashi take yi ga wani irin zazza6i da ya lullu6eta.

A bakin Ƙofar ɗaki na biyu ta faɗa tana faman haki, Karaf idanuwan ta suka sauka Akan Giants da ke gudanar da aikin su na Theatre, gadaje ne sunfi talatin Cikin Ɗakin mai faɗin gaske, kowani gado Yana ɗauke da mutun kwance saman shi, Sun fafe cikin su suna ɗibar kayan cikin nasu tare da ɗaura su saman table ɗin da ke a gefen su, A matuƙar razane ta juya tana neman hanyar da zata bi ta Fitar da ita daga Cikin Corridor ɗin, Allah Yaso basu lura da ita ba babu wanda Ya ganta don gaba daya hankulan su na akan aikin da suke kuma basu zaton wata matsala , Watsawa ta yi da gudu Ita kanta batasan inda take tunkara ba Sunan Allah kaɗai ta ke iya ambato a cikin bakinta, adaidai saitin wata ƙopa ta soma jin Wata kakkausar murya tana magana da wani irin gur6ataccen yare mara daɗin ji, A hautsine takai idonta Ƙofar Dogon labule ne launin Ja ya rufe ta, Yatsun hannunta na kerma ta ɗan yaye labulan.

Babban É—aki ne mai girman gaske kamar palour, komai Na cikin shi Red & black Colour ne, bangon É—akin Zanunnukan kan Æ™warangwal ne dana kunama, da na wasu halittu masu dogon harshe Da zaÆ™o zaÆ™on akaifu irin na shaiÉ—anu, Zanen su ne ta ko’ina gwanin ban tsoro, Mutane ta gani a jere sunkai su Talatin Kowannan su na sanye Cikin Jajayen dogayen riguna masu huluna, hannuwan su ruÆ™e da Æ™oÆ™una masu É—auke da jini, daga tsakiyar su wasu tiÆ™a tiÆ™an mutane ne kusan su Shidda, Yadda kasan Irin malaman Majami’u na Æ™asar India, Tumbur babu Kaya ajikin su, Sae dai wani Æ™aramin Jan Æ™yalle da su ka É—aure Æ™ugunan su dashi, ga wani uban tumbi da suka tara, Jikin su bulbul ansha Jini An Æ™oshi, Jan fentin da ke saman fuskokin su Ya rufe ainihin Suffar su sun koma kamar dodonni, Sun kewaye wani Dodon tsafi dake a zaune saman armchair, Wata irin halitta mai matuk’ar muni miyau sai zalalowa yake yi daga bakin shi, Zir Jikin shi babu kaya sai uwar yanar da ta nannaÉ—e gangar Jikin shi tayi mashi tamkar sutura.

A kowace kusurwa ta cikin ɗakin jajayen ƙwaryoyi ne a jere an rufe su da faifai, Ga wasu ƙananun Yara da basu haura 7 years ba mata zuƙunne saman gwiwowin su babu kaya a jikin su, gabansu ca6a ca6a da jini, daga gani amfani aka yi dasu.

Wani ikon Allah duk tashin hankalin da idanuwanta su ka yi tozali dashi baisa ta kurma ihu ba saida taga waɗannan yaran ƙananu tukunna sautin muryar ta ya dawo har ta ƙware Baki zata Kurma Ihu ba zato ba tsammani taji saukar hannun mutun saman bakinta, sosai Ya toshe mata baki! Batasan wanene ba hakan yasa ta zazzare idanuwan ta waɗanda su ka kaɗa su ka yi jawur dasu, tsoro da firgici ne.

 

Click Here To Download Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete

 

 

( mu hadu next page In Allah yakaimu da rai da lafiya, masu yi mun ya jiki ina godiya)

 

Back to top button