Hausa novels

Kanwar Maza Book 3 Complete Novel Document

Kanwar Maza Book 3 By A'isha Adam (Ayushercool)

Description/Story:

Kanwar Maza Book 3 Complete Hausa Novel Document Written By Ayushcool

 

Description

Wani irin tausayinsa ne ya kama Aliyu, duk yadda adam ya so ɓoye hawayensa kasawa yayi, ya barsu suka din ga zuba son ransu.

Da ƙyar Aliyu ya ɗan yi gyaran murya ya ce “Kamar yadda ka ce kai musulmi ne ka yarda da ƙaddara, to Yakamata a ga hakan a aikace, ka yi haƙuri in sha Allah sirikinka zai fuskance ka, Allah ya yi mata rahama”.

Mama ce ta yi sallama a ɗakin tana faɗin “Aliyu ya tashi kuwa?”.

Ta tarar da su a zaune, mama ta ce “Alhamdilillah ala kulli halin, Allah mun gode maka, sannu ka ji?” Ya jinjina wa mama kai yana share hawaye.

“Ayi haƙuri, a fawallawa Allah, yaronka mahaifiyarka da sauran makusantanka suna buƙatar ka, ita tata ta ƙare ta yi shahada sai fatan Allah ya karɓi shahadarta, ayi haƙuri, Aliyu je ka ɗaki ka kawo ruwan shayi da abinci ya samu ya saka wani abu a cikin sa”.
Aliyu ya tashi ya fita, yana fita lokitan dare ya shigo, ya dudduba Adam aka bashi maganinsa na dare, likita ya jaddada masa ya kula da magani da dokokin da aka saka masa.
Sam Adam ba ya fahimtar abun da likitan yake faɗa, mama ta miƙa masa kofin shayi cikin kulawa ta ce “Daure ka sha, ka ga an baka magani, dole sai ka ci abinci” kallon mama kawai yake yi, wato duk in da uwa take uwa ce, yadda ta ke ta nuna kulawa a kansa sai ya ji daɗi, duk da tarin damuwar da yake ciki.
Duk da ba zai iya tantance manufar kulawar da mama take bashi ba, amma tun da ya taso kulawa ɗaya ce yake gani ta zahiri, wato kulawar ammi ban da haka galibi masu yi masa murmushi suna yin sa ne da biyu.

Da ƙyar ya karɓi kofin shayin, ya ɗan sha kaɗan ya ajiye, mama ta yi ta masa nasiha, da rarrashi cikin siga ta dattaku da manyance.
Ya ɗan murza zoben hannunsa ya ce “Da ke da iyalinki, babu abun da zan iya ce muku sai godiya, a rayuwata na daɗe ban ga mutane masu karamcinku ba. Amma dan Allah ku yi haƙuri da abun da zan faɗa, ina son zan karɓi yarona, dan Allah a rarrashi mamansa, na san zata tsaneni fiye da da, amma ni ba zan iya da rigimarta ba, a bata haƙuri zan ɗau yaron nan zan tafi da shi wurin kakansa, sai hukuncin da ya yanke a kanmu”.

A take mama ta ji babu daɗi, domin ita kanta ta shaƙu da jaririn ba kaɗan ba, ya shiga ranta.

A zahiri ta ce “Babu laifi, Ubangiji Allah ya raya shi bisa tafarkin addinin musulunci, ya jiƙan mahaifiyarsa. Amma ina fatan ba zaka rabamu da shi gaba ɗaya ba, dan a halin rumaisa bana jin za ta iya haƙura”.

Yayi murmushi ga hawaye na zuba daga idonsa ya ce “Za ta saba in sha Allah, ba zata damu sosai ba amma yarona yana buƙatar kariya ta musamman, ba zan manta soyayyar da ta nunawa gudan jinina ba”

Jiki a sanyaye mama ta ce “Babu laifi, Allah ya jiƙan mahaifiyarsa, kai kuma ya baka lafiya” da haka mama ta yi musu sallama ta koma ɗakin da rumaisa take. Ta kwanta tana facing ɗin Sabir, tana ta baccinta, ta saka hannu ta riƙe masa nasa hannun suna bacci.

Tausayinsu ne ya kama mama, amma babu yadda ta iya, haka ta shiga harhaɗa wa sabir kayansa, a daren ta haɗa komai cif a wuri ɗaya.
Suma ta haɗa musu nasu kayan, dan ta ji likitan yana cewa washegari zai sallami rumaisa, tun da ita ma ta warware sai abun da ba a rasa ba.

Sai da ta kammala, sannan ta yi alwala ta tayar da salla.

Da asubar fari, sabir ya tashi yana ‘yan koke-koke, mama ta ɗauke shi ta yi masa wanka, ta bashi madararsa, ita kanta mama tana matuƙar ƙaunar yaron da tausayinsa, ta ɗauke shi ta goya shi a bayanta, ta yi sallar asuba, ta tashi ruma ta yi salla sannan ta fita daga ɗakin.
Harabar asibitin ta koma ta kira mai sunan baba, tana shiga ya ɗaga, ya gaida mama, ta amsa masa sannan ta ce “Babana, dan Allah da gari yayi haske ka taho asibitin nan, yau za a sallami rumaisa, kuma yau za su karɓi ɗan su, ka san halinta sarai, jiya da daddare babansa da ya farfaɗo ya ce zai karɓi ɗan sa ya tafi da shi ya gabatar da shi a danginsa, sannan ya sanar da rasuwar uwar ɗan”.

Mai sunan baba ya ɗan yi shiru sannan ya ce b”Babu laifi, zan shigo in sha Allah, amma a bita a hankali dan Allah, ko a bari na zo tukuna”

Mama ta ce “ai shi ya sa na ce sai ka zo ɗin”

Bayan sallar asuba, Adam ya karɓi wayarsa a hannun Aliyu, ya kira ammi, suka yi magana, ta ji daɗi sosai da jin muryarsa, tayi masa addu’a da fatan alkhairi.
Ya kira Bashir ma suka gaisa, tare da sanar da shi, ya je ya taho da Ammi.

Kiran jabir ne yake ta shigowa tun bayan da ya kunna wayar, kamar ya share sai kuma ya ɗaga.

“Wai ina ka shiga haka baka ɗaga wayata? Ya ake ciki ne akwai wani labari ne? Ko ka koma wurin yarinyar?”

“A’a ban koma ba, zan koma bacci yanzu zan zo gida in sameka anjima” bai ko tsaya saurarar mai jabir zai ce ba, ya kashe wayar ya ajiye, haryanzu ya kasa gazgata maganganun rumaisa, wai Aisha ta mutu, ganin abun yake kamar almara, sai yanzu ya gane ka rasa mutum ka ga gawarsa wata ni’ima ce, ba irin tunanin da bai zo masa a kan gawar Aisha ba.

Abun mamaki yau ruma taƙi komawa bacci, mama har tambayar ta ta yi ba zata koma bacci ba, ta ce ba ta ji.

Ta dubi in da mama ta haɗa kayansu ta ce “Mama wai tafiya zamu yi ne an sallame ni?”.

“Eh, in anjima za a sallame mu”

“Yeeee dama na gaji da zaman asibitin nan wallahi, yau sai gida, ga kayana ga na babyna nima na samu mai sunan babana, sai dai Allah ya sa kar yayi halin mai sunan kakanmu” tayi maganar da sigar tsokanar mama, amma mama ba ta tanka mata ba.

Har gari ya waye ruma idonta biyu, ta damu mama a kan ta bata sabir, amma mama ta hanata.

Wajen ƙarfe tara, Usman da mai sunan baba suka zo, ruma tana ta murna zata tafi gida, dan zumuɗi ta ce abincin ma sai ta je gida zata ci.

Usman ya din ga kwasar kayansu yana fitarwa, sai murna take yi yau ba kwanan asibiti, dan takardar sallama kawai suke jira daga likita.

Bashir ne ya shigo ɗakin rumaisa, ya kalleta yayi murmushi ya ce “Yau sai gida uwar rikici”

Ta yi murmushi ta ce “Ɗan uwanmu, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, jin godiyar nake ma ta yi kaɗan a baki, amma zan din ga yi maka Addu’a idan na yi salla”..

Yayi murmushi ya ce “Kai masha Allah, amma na gode ƙwarai da gaske, sister na asiya ma tana gaishe ki, ita ma ba ta da lafiya ne. Amma kin je kin duba baban sabir kuwa?”

Ta ɗan yi turus tana kallon mama, mama ta ce ‘Yanzu zan sakata a gaba mu je ta duba shi, sai mu tafi”.

Bashir ya ce “Yauwwa mama, dama ga ammi can ma ta zo sai ku yi sallama, ai bai kamata ku tafi babu sallama ba”.

“To ai yaya Aliyu ya ce bai mutu ba, har ya tashi”

“Haba rumaisa, idan da kara yakamata ki je ki duba shi, ko dan albarkacin sabir ɗinki”.

Usman ya ce “Sai ka lallaɓata ma, wuce mu je, kuma saura mu je ki yi rashin kan gadon naki, ya saka dogarai su saita miki zama”.

Suka ɗunguma zuwa ɗakin da takawa yake, suka tarar ammi na zaune a kusa da shi, ta riƙe hannunsa, tana share masa hawaye.

Ammi na ganinsu tayi murmushi ta ce “Kun fito? Yau ban ƙaraso mun gaisa ba rumaisa, hankalina ne a tashe”

 

 

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Back to top button