Hausa novels

Abban Sojoji Takun Karshe Book 3 Chapter 90 Complete Novel

Father of soldiers

🔥TAKUN ƘARSHE🔥

_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_

Not edited,

“zan cigaba da aiki a ƙarƙashin ka,”ta ƙarasa maganar,tana faman sauke ajiyar zuciya,
“Good,”ya furta hakan tare da miƙe wa daga zaune,Ya jingina bayanshi a jikin pillow,har time ɗin idanuwanshi na a lumshe bai buɗesu ba,
“Now you are under my control, you must follow my rules,”dakatawa yayi da yin maganar,tare da kai hannu ya zaro hanky daga front pocket na rigar shaddar jikinshi,
Miƙa mata yayi tare da cewa”Oya,goge wannan fentin dake a saman lips ɗinki,from now bana buƙatar naga make up a face ɗinki,in dai zakiyi aiki a part ɗina,”

Download>>> Auren Karin Kasa Book 1 Complete Document

Hannu tasa ta kar6i hanky ɗin,tare da kaishi saman lips ɗinta,a hankali ta shiga goge jan bakin da tasha fa,
Cigaba da magana yayi”i won’t restrict ur life,You still ave ur right,don na aure ki ba hakan yana nufin zaki ɗauki kanki as a married women ba,No just normally zakiyi rayuwarki,Kuma zaki iya kula duk wanda kikeso koda namiji ne i don’t care about that,’
Zaro ido waje sehrish tayi tana kallon fuskarshi,cike da mamakin jin abunda yace mata,Lamarin sgr ya fara bata tsoro,sae ka ce ba musulmi ba!da aurenta kuma ya amince mata ta kula duk wanda takeso?Anya bai fara shaye shaye ba?kodai yana da Iska ne ajikinshi?Abun yayi confusing ɗinta sosai,
“Idan ma kina da tsafta ki ƙara akan wadda kike da ita,part ɗina ya kasance kullum a tsaftace ya ke,”
Kasa kunne sehrish tayi tana sauraron shi,guiwowinta har sun fara yi mata raɗaɗi,magana yake yi tamkar baisan motsa la66ansa,balle har yayi sauri ya kammala ko ta samu ta miƙe,
“Banason wani ya ƙara girkamin abincin da zanci,da hannunki zaki girka mun,sannan ba kowani kalar abinci nake ci ba,Ki nemi bayani a wurin Asmee,”
Dakatawa ya ɗanyi da maganar,hannu ya miƙa tare da ɗauko wayarshi dake ajiye saman side drawer ɗinshi,ya shiga daddanata,
Ganin haka yasa sehrish tayi sauri Zama dirshin a ƙasan,kota rage raɗaɗin da guiwarta keyi mata,
“Where’s ur phone”?yayi tambayar tare da ɗan dakawata,da dannar wayar da yake yi,
Da sauri tace”na barta a bedroom ɗinmu,”
“Okey,”ya ambaci hakan tare da kai hannu ya buɗe drawer chest,memo ya ɗauko tare da biro,Ya buɗe empty page,a natse ya shiga yin rubutu asaman paper ɗin,.
Zugudum sehrish tayi,aranta tana tunanin ko taya zata iya gane hand writting ɗinshi?kwanakin baya,daya ta6a yi mata rubutu bata iya gane komai ya rubuta ba,har haroon ya yaudareta,
Bayan ya kammala rubutun,Yayi tearing paper ɗin tare da miƙa mata,hannu tasa ta kar6a,
“Phone number ɗina ne,Cos at anytime zan iya kiranki,even in the midnight indai ina buƙatar wani abu”
Amsa mashi tayi da toh,
“Your work will start from tomorrow!U can leave now,”
Jiki asanyaye sehrish ta miƙe dakyar take ɗangyasa ƙafarta tana tafiya,har sae da takai bakin ƙopar bedroom ɗin nashi sannan ta ɗan dakata da yin tafiyar,juyowa tayi tare da aza idonta akanshi,a lokacin harya sauko daga saman gadon,yana ƙokarin cire kayan jikinshi,da alama wanka zaiyi.

Download>>> Mijin Malama Complete Document

Gyaɗa kai kawai tayi tare da sanya ƙafa ta fito daga bedroom ɗin nashi,
Bata tashi jin hawaye ba,sae da ta hau saman staircase din,tana taka benen a hankali,bakomai yafi ƙona mata rai ba fa ce abunda ya ce mata,Zata iya kula duk wanda takeso koda Namiji ne shi bai damu ba,tsabar takaici kamar ta haɗiyi zuciyarta haka take ji,taci alwashin saita koya mashi hankali,kuma zata jajurce ne wurin ganin ta gudanar da aikinta kamar yadda yakeso,daga baya kuma ta shiga tunanin komai yasa ya hanata shiga part ɗinshi da makeup?mai jan bakinta yayi mashi ne da zaisa ta goge?da alama so yake ya dinga ganinta kamar gardi,shiyasa yayi mata hakan,

Ƙarasa saukowa tayi daga saman stairs din,sannan ta tsaya tare da juyawa tana kallon upstairs ɗin”

In sha Allah,Wata rana Sai kayi kneel down agabana,Kamar yadda ka saba sanya ni in duka agabanka,koda baka zubar da hawayenka ba,zakayi kukan zuciya ne wanda yafi ciwo,Wannan alwashine na ɗaukarma kaina,In har ban tabbatar da faruwar hakan ba,To ni ba jinin Abusufyan bace da abu!!kuma ban cika mace ba,”
Tana magana hawaye na shararowa akan fuskarta,ranta ya 6aci sosai

*ATAƘAICE*

Acikin waɗannan ƴan kwanakin Sehrish ba ƙaramin jiki taji ba,domin kuwa sgr baiyi mata da sauƙi,Aiki takeyi tuƙuru,ba ƙaramin ƙoƙari take yi ba wurin ganin ta kiyaye duk wani abu da zai haɗa ta dashi,Aranar monday abusufyan ya mayar dasu school,da kanshi yakaisu acikin motarshi,basu samu matsala ba,sae dai an wuce su abubuwa da dama,Domin kuwa suna dab da fara’a Exams,abubuwa duk sun haɗe mata,ko karatu takeyi hankalinta na akan agogo,don kada ta shiga lokacin aikinta batare da ta sani ba,tun da sanyin safiya take shiga part dinshi tunkafin ma ya tashi daga bacci,ta gyara mashi toilet ɗinshi da falonshi,bayan ya tashi daga bacci ya shiga wanka,ta zauna ta gyara bedroom ɗin nashi,Sannan ta shiga kitchen ta haɗa mashi breakfast ɗinshi,Mafi yawancin lokutta a makare take zuwa makaranta,Saboda aikin sgr,Sae yaga damar sallamarta tukunna,abun ba ƙaramin 6ata ma abusufyan rai yakeyi ba,sae daga baya ya dinga danasanin ƙulla auren yarjejeniyar da sukayi,kullum Shi yake ja masu yin late a school,saboda dole sai sun jira sehrish ta kammala aiki a part din sgr,sannan su wuce school,baiwar Allah suna dawowa daga school da zarar tayi sallah,ko abinci bata ci,indai sgr na a cikin gidan sae ta fara zuwa ta gyara mashi part ɗinshi ta kuma kai mashi lunch ɗinshi,ta kuma yi serving ɗinshi abincinshi har sai ya mula yasha iska tukunna ya sallame ta,sannan fa take samun damar cin abincinta,Cikin lokaci ƙankani sehrish ta soma fita hayyacinta,Duk ta rame,kullum ne sai ta farka tsakar dare,ta zauna tayi ta kuka ba wanda ya sani,ita kaɗae tasan irin raɗaɗin da take ji acikin zuciyarta,gashi in tayi kuskuren yi mashi laifi,Hukunta ta yakeyi da tsallan kwaɗi,babu wanda bai fara jin tausayinta ba acikin gidan,shiru kawai sukeyi,bakomai ne ya jawo mata hakan ba fa ce rashin Hajiya azeema domin kuwa tun sati daya da yin auren,Tabar ƙasar izuwa dubai inda tasaba yin harkokin kasuwancinta,Amma tayi mata alƙawarin cewa bazata wuce One month ba zata dawo nigeria saboda ita kawai,Duk da haka kullum sai sunyi waya da ita,kuma tana ƙara ƙarfafa mata guiwa,kullum tana kara tunasar da ita akan cewa Karta kuskura ta karaya tun yanzu,Taci gaba da hakuri wata rana sai labari,mahaƙurci mawadaci ne,Sannan ta dage da addu’a kuma taci gaba da kyautata mashi,sgr bai tsaya a iya nan ba,idan dare yayi dama wannan ƙa’ida ne saita kai mashi coffee da kayan marmari around 12,toh yanzu takai ga,sae tana bacci wuraren 1:30 na dare ko biyu,ringing ɗin wayarshi ke tashinta daga bacci,daga ta ɗaga zaice mata Coffeee,yana furta hakan zai katse kiran,Dolenta ne ta tashi takai mashi ga bacci a idanunta,duk in taje part dinsa a wannan lokacin zata same shi ne yana yin nafilfilin dare,ko kuma ta same shi bayan ya kammala yin sallar yana karatun alƙur’ani,a rana ta farko data fara ganinshi yana karatun kur’ani abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Ita duk a tunaninta babu ilmin addini akanshi,Ashe kullum saiya tashi in midnight don yayi sallar dare da kuma karatun alƙur’ani,tun daga ranar da ta fara ganinshi yana yin sallar nan,itama sai ta koma yin sallar daren da karatun al’kur’nin,saboda su dinga samun ladar atare,tunda ya katse mata baccinta,

Download>>> Boss Lady Romantic And Comedian Novel Complete

A 6angaren Amrish kuwa,Daƙyar haroon ya samu ta amince zata koma wurin Mommynta da zama,Da kanshi ya mayar da ita gidansu,Sannan ya gargaɗi mommynta akan ta kiyaye 6acin ranta,itama amrishi ɗin sai da yaja mata kunne akan karta ƙara yunkurin kashe kanta,da haka ya samu ya sasanta tsakaninsu,har ta koma school,Ranar da suka haɗu da sehrish a makaranta kamar zasu haɗiye junansu saboda tsabar farin ciki,sun sha kuka sosai,saboda sunyi kewar junansu,abun ba’a magana,

Soyayyar junaid da jahad kuwa kullum ƙara ninkuwa takeyi acikin zukatansu,sun shaƙu sosai koda yaushe suna manne da junansu,baya gajiya da ɗaukarta su fita shan ice cream,Junaid ya iya soyayya sosau,yaci sunanshi romeo,saboda ya iya caring,ga zumuɗi kamar sabon ango,A ƙagare yake da aɗaura mashi aure da jahad,Bawan Allah duk safiyar Allah sai yayi shiga ta mutunci yaje gaisar da Abusufyan,hakan ba ƙaramin daɗi yakeyi ma abusufyan ba,tun daga haka ya gane cewa junaid zai ruke mashi ƴarshi dakyau duk da ƙuruciyarshi,amma yana da hankali sosai,

A 6angaren Marshal Omar kuwa,Hosana ta tada mashi 6alli,saboda sehrish tayi aure ita bai aure ta ba,duk yadda yaso ya shawo kan hosana akan ta bashi lokaci amma yarinyar nan taƙi yarda,ƙarshe tace mashi in har baije anyi maganar aurensu ba,zata tona mashi asiri ne,gabanshi ya faɗi ya shiga tunanin wani asiri ne hosana take ikirarin zata tona mashi,koda ya matsa mata akan ta faɗa mashi abunda take 6oyewa,sae cewa tayi ae Ya ta6a yi mata fyaɗe hada nuna mashi Zoben diamond ɗinshi daya manta a ranar,kuma tace zata sanar dasu Abbansu ne,Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,ƙoƙarin fahimtar da ita ya shiga yi akan cewa shi fa ba fyade yayi mata ba,kawai tsautsayine yasa yayi ƙoƙarin raping ɗinta a lokacin,daƙyar ya samu ya lallasheta,sannan ta haƙura,a hakan ma sai da yayi mata alƙawarin cewa za’a daura masu aure,

Karanta>>> Yar Harka Romantic Hausa Novel – Aihausanovels

lokacin da Haroon Ya ji Auren Sehrish da sgr,tamkar zai zauce saboda tsabar tashin hankalin daya shiga,don shi dagaske son Sehrish yake yi,daga baya ne ya gano cewar Auren Nasu na wata uku ne,tunda yaji hakan sai hankalinshi ya kwanta,Kuma yaci alwashin cewa Sai ya samu soyayyar Sehrish,in ba haka ba sai yabi duk hanyar da zai bi wurin ganin ya biya bukatarshi da ita,don ya jima da kwaɗayin son kasancewa da ita,tashin hankali,

Wannan kenan

A ranar wata Juma’a ne,Allah yayi ma modibbo rasuwa,Mutuwarshi tayi matuƙar girgizasu gaba ɗayansu,Musaman Ammi kamar zata zauce don kuwa har suma saida tayi lokacin da saƙon mutuwar nashi ya isar masu,Rashin lafiya yayi na rana ɗaya kuma Allah ya kar6i abunshi,Sunji mutuwarnan kamar kamar me,Ashe babu rabon komawarshi saudiya,duk da yaci nasara akan abunda ya kawo shi nigeria ya haɗa kan zuri’arsu,ya ƙulla zumunci mai ƙarfi atsakaninsu,Allah ya jiƙan Modibbo,

Gaba ɗayansu suka shirya zuwa Damaturu domin halartar jana’izarshi,Banda su sehrish saboda Exams da sukeyi a school ta Second term,amma matasan gidan dukansu abbansu ya tattarasu sun tafi can,gidan ya rage daga Azmee sae su sehrish,baƙaramin daɗin tafiyar sgr sehrish taji ba,Duk da ranta na bata cewar daƙyar zai wuce 1 week bai dawo cikin gidan ba,ta dan samu hutu,Kullum daga taji dirar mota jiki na rawa zata je ta leƙa ta window taga wanene ya dawo,Fargabarta kar ace shine ya dawo,da zarar taga bashi bane,Daɗi take ji,duk da tayi kewar shi sosai,Ko bacci takeyi sai ta dinga jin muryarshi acikin kunnanta yana cewa”Oya kneel down” har mafarkinshi takeyi,❤
Yau Ya kasance wata ɗaya cuf da yin aurensu,batare da sgr ya soke yarjejeniyar ba,yanzu kwana biyar kenan da tafiyarsu Damaturu,dama abbansu yace sai sun zaga dangi,tunda sun jima basu je sun sada zumunci ba,

*Boss Bature*

❤🤍❤

Wuraren ƙarfe 3 na rana,sehrish na kwance saman gadonsu,tayi nisa acikin baccinta,baiwar Allah ba ƙaramar gajiya ta kwaso ba,Yau suka kammala Exams ɗinsu,tunda suka dawo daga school Ko Uniform ɗin jikinta bata samu ta cire ba,ga yunwa na cinta amma ahaka ta kwanta saboda baccin da take ji,

Jahad kuwa tana a garden suna video call da junaid,tun bayan da suka tafi,kullum ne saiya kirata video Call,idan suka fara wayar nan sai sunyi fiye da one hour suna magana,Idan da daddare ne kuwa ya kirata suna kaiwa har wurin asuba,basu runtsa ba,Soyayyarsu ba ƙaramin burge sehrish takeyi ba,wani sa’in sai taji dama itace take samun irin kulawar a wurin sgr,ɗan tahalikin nan tunda suka tafi kullum ne saita tura mashi Text message amma babu reply,bai ta6a mayar mata da amsa ba,kuma hakan baisa ta daina tura mashi ba,

Karanta>>> Abban Sojoji Book 2 Complete Novel

Cikin bacci ta dinga jin jiniyar motoci acikin kunnanta,A firgice ta farka tana faman zare ido,tsoranta kada ace Sgr ne yadawo Cikin gidan,Sai da tadawo cikin hayyacinta sosai sannan ta gane cewa ashe wayarta ce ke ringing,Wata irin nauyayiyar ajiyar zuciya ta sauke,Hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman pillow,sae hamma takeyi saboda yunwar da take ji,duba screen ɗin wayar tayi,Sunan Daddy ne ya bayyana,Murmushi ta ɗan saki tare da answer kiran,ta kara wayar a kunnanta,
“Assalamu Alalikum daddy,”
Muryar abusufyance ta amsa mata da cewa”Wa’alaikum salam,Daughter ya kike?tun ɗazu inata jaraba kiran wayar jahad line busy,ke ma kuma na kira wayarki kusan sau biyu tana ringing ba’a ɗaga ba,dafatan kuna lafiya,”
“Bacci nakeyi ne shiyasa banga kiranka ba,Jahad kuma tunkafin na kwanta,ta sanar dani cewa junaid ya kirata,nasan yanzu haka dashi takeyin waya a garden,”
“Okey,hosana fa?tana ina ne?itama na kira layinta a switch off,”
“Daddy hosana fa,bata amfani da wayarta,tun ranar daka siya mana su bata ƙara bi takanta ba,tafi mayar da hankali akan laptop ɗinmu,yanzu haka ma kallo takeyi acikinta,”_
Abusufyan yace”Na kira ne dama don inji ya ku ke,”
Murmushi tayi kafin tace”Alhamdulillah daddy,muna lafiya,fatan kaima haka”?
..”ina lafiya nima,Ya Exams ɗin taku?kunyi abun kirki ko?
dariya ta ɗanyi tare da cewa”Yau dai muka kammala,Result muke jira yanzu,amma fa daddy kasan a ƙurarren lokaci muka koma school,duk an wuce mu a karatu,duk yadda kaga result ɗinmu kawai kayi shiru da bakinka,ka sanya mana albarka,”
Tana jiyo muryar abusufyan ta cikin wayar yana dariya,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace”Oh,kina nufin cewa ba kuyi abun kirki ba ko?oh ni abusufyan kada ace ƴa’ƴana basu da ƙoƙari,”
“A’a daddy ae ba laifinmu bane,yakamata ayi mana uziri,saura fa two weeks a fara exam ka mayar damu school,”
Abusufyan yace”hakane kuma fa,baki tambayeni yaushe zan dawo ba?ko bakiyi missing ɗina bane”?
Muryarta da ƴar shagwa6a tace”I really missed u alot daddy,kamar na janyoka ta cikin wayar nan,inyi hugging ɗinki,”
Dariya yayi sosai kafin yace”this Week zamu dawo ae,zuwan bazata zanyi,kuma a washe garin ranar da nadawo zamuje kano,Zan ɗauki ɗaya daga cikin ku mu tafi kano,saboda inaso muje gidan makwabtan nan naku ya ma sunansu?
Da sauri tace”gidansu maman sadeeq”?
Yace”eh nan nake nufi,zamu je ne domin munyi bincike akan mahaifiyarku,Nasan zamu samu ƙarin bayani a wurinsu,”
Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskar sehrish,fuskarta dauke da murmushi tace”daddy inaso dan Allah ku tafi tare dani mana,”
“Kina tunanin cewa Babban yayanku zai bari na tafi tare dake ne”?
Shiru tayi tuni idanunta sun ciko da kwalla,muryarta tamkar zatayi kuka tace”Amma daddy,ni ya kamata a tafi tare dani,saboda zanfi gane kwantancen gidan nasu,”
“Shikenan idan har kinason mu tafi tare dake,toh ki fara sanar da babban yayanku,idan har ya amince zamu tafi atare,in kuwa ya hanaki zuwa sai dai ki haƙura mu tafi tare da Jahad,”
Jikinta ne yayi sanyi harma ta fidda rai don kuwa tasan cewa Daƙyar ne sgr ya barta ta tafi kano,
Cikin sanyin murya tace”Shikenan daddy,zan jaraba tambayarshi idan ya dawo,Allah yasa yabarni,wlh dana ji sosai,”
Sun jima suna waya dashi kafin sukayi sallama,ajiye wayar tayi asaman side drawer,sannan ta sauko daga saman gadon,direct ta wuce toilet domin yin wanka,within mins ta fito jikinta sanye da bathrobe,ta saki gashin kanta a bayanta,yanzu tsayinshi yakai har mid back ɗinta,
Gaban mirror ta tsaya,tare da ruƙe qugunta,bakowa bane ya faɗo mata a ranta ba fa ce Sgr,a duk lokacin daya sanya bathrobe ɗinshi ba ƙaramin kyau rigar take yi mashi ba,yadda kasan donshi akayi rigar,

Hannu tasa tare da janyo gashin kan nata,ta dawo dashi ta gabanta,tana kwaikwayon yadda sgr yakeyi in ya fito daga wanka,ta daure fuskarta kamar yadda yake tamke fuskarshi,a ƙarshe ta fashe da dariya,
Tana cikin rahar nan,hosana ta turo ƙopar ɗakin nasu,Ta cikin mirror take hangenta,Hannunta na ruke da system ɗinsu,jikinta na sanye da doguwar riga ta material,
“Sehrish ga lunch ɗinki can a dining,Aunty azmee ta ce idan kin gama baccin lalacin naki kije ki ci,”
Ta ƙarasa maganar a yayin da take zama daga gefen gadon nasu,
Juyowa sehrish tayi tare da kallon hosana tace”daddy ya kira wayarki a switch off,wai ina kike ajiye ta ne”?
Yatsina fuska hosana tayi kafin tace”Oho,nima bansan inda take ba,nemanta na keyi ruwa ajallo,dan Allah ki tayani nemanta,inaso in kira Ya Omar,nayi nayi da jahad ta kira munshi amma taƙiya,dama kece mai ɗan mutuncin,”

Download>>> Dr Bobby Hausa Novel Document

Harara sehrish ta watsa mata tare da cewa”Sai yau kikasan da haka?bayan kinsaba cewa nafi kowa tsiwa,bayan duk acikinmu ni ce innocent,”
Marairaice mata fuska hosana tayi,”pls rishi komai ya wuce,dan Allah ki bani aron wayarki yanzu dai in kira Ya omar,2 days banji Voice ɗinshi ba,Ni fushi nakeyi dashi ma,ko ya kira yaji ya nake,amma bai kira ba,”rai a6ace tayi maganar,
“Kada ki isheni da surutu,don nasanki bakya gajiya,ga wayar nan ki ɗauka,salon ki cinyemun katina,”
Cike da zumuɗi hosana ta ajiye system ɗin asaman gadon,sannan ta ɗauki wayar da sauri ta fuce daga ɗakin,
Gaban wardrobe ta koma tare da buɗewa,tana neman kayan da zata sanya,shirt ce ta ɗauko off shoulder Ash colour tare da dogon wandon Jeans,batare da 6ata lokaci ba ta zura kayan ajikinta,bayan ta kammala sanya kayan ta koma gaban mirror, tana shafa powder,sannan ta ɗan shafa lip gloss,murza la66an tayi,tana cikin sharce sumar kanta,Jahad ta turo ƙopar ɗakin,
Hannunta ruƙe da wayarta,fuskar nan awashe sae faman sakin murmushi take yi,
Juyowa sehrish tayi tare da kallonta tace”Sai yanzu kika kammala shan Love ɗin?Ni wannan soyayyarta ku tana ɗaure mun kai wlh,ko gajiya bakuyi,yadda kasan Romeo da juliet,kullum kuna a manne da juna,”
Jahad tace”da alama baƙin ciki kikeyi mun Allah,”
“In rasa dawa zanyi baƙin ciki sae dake?kin manta wa nake aure?Ni fa matar Surgeon general ce,ke fa?Ni har kunya ma nake ji,ki rasa dawa zakiyi soyayya sae wannan shagwa6a66an…”
Tunkan takai ƙarshen maganar jahad tace”Auren da yanzu saura 2 month ya mutu!dashi har kike tutiya,”
Gaban sehrish ne ya faɗi rasss!lokaci guda jikinta yayi wani irin sanyi,yayin da idanunta suka ciko tab da kwalla,
Ita kanta jahad,bataso ta faɗi hakan ba,ranta ne ya 6aci saboda ta tsani a kushe mata baby Junaid ɗinta,Wannan ne yasa har ta faɗi maganar da tayi,
“Jahad!ni kike faɗa ma haka”?
Da sauri jahad tace”dan Allah kiyi haƙuri,wlh bansan na faɗi hakan ba,raina ne ya ɗan sosu,”
“Kinayi mun fatan aurena ya mutu kenan”? Tayi tambayar hankalinta aɗan tashe
“Dan Allah rishi kidaina faɗin wannan maganar,nace maki ba a son raina na faɗi hakan ba,”tayi maganar tare da ƙarasawa wurin sehrish ɗin,ta ruƙo hannunta,
“Pls kada ki bari hawayen nan sun fito daga cikin idanunki,kinsan cewa bazan ta6a yi maki fatan aurenki ya mutu ba,kuma wlh ban faɗi hakan ba donna 6ata maki rai ba,” fuskar jahad tamkar zatayi kuka saboda tausayin sehrish,
Tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,cikin sanyin murya ta wanda ya karaya tace”kin faɗi gaskiya jahad,bai kamata inyi prouding da aurenshi ba,Ni sam na manta ashe yau saura 2 month babban yaya ya sake ni,ni nama ƙosa ya sake ni in huta,’
Hannu jahad tasanya tana share mata hawayenta”in sha Allah Babban yaya bazai ta6a sakin ki ba,banayi maku fatan rabuwa da junanku,Nafison ku kasance atare na har abada,Daso samu ne kawai wani abu ya shiga atsakaninku,Ana saura sati daya auren ya mutu,aga kina amai kinga shikenan babu zancen saki,Sae dai a fara tanadin suna,”cike da zolaya jahad tayi maganar,aikuwa nan take sehrish ta fashe da dariya,
Ganin tafara dariya yasa jahad taci gaba da tsokanarta”gaskiya naƙosa in ganki da ciki,cikin ma na babban yayanmu,Wayyo Allah na bansan wani irin farin ciki zanyi ba aranar,zanso naga babynku,wlh ba ƙaramin kyau zaiyi ba,idan ya biyo kowannanku,”
Fuskarta ɗauke da murmushi tace”Najima ina burin wannan ranar,bazan 6oye maki ba jahad,inaso inga nima na haifi ɗan babbyna,Amma nasan ba yanzu ba,”

Karanta>>> Idan Ba Ke Complete Novel Document

“Dont worry ur self,Very soon zaki haifa ma babban yayanmu twins ko triplet,tunda muma triplet ne,nasan acikinmu baza’a rasa wadda zata haifi ƴan biyu ba ko ƴan uku,”Acewar jahad,
Shiru sehrish ta ɗanyi tana murmushi,duk da tasan abune mai wuya amma taji daɗin maganar nan ta jahad,
“Inaso naje naci abinci,yunwa nake ji,”
Ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar fita daga ɗakin,Bin bayanta jahad tayi da sauri tare da ruƙo hannunta cikin nata,
“Mu tafi atare,nima ae banci abincin ba,”
Dining suka nufa,Wuri suka samu asaman dining chairs ɗin kowa ya zauna,Tray ne mai faɗi azmee ta ajiye masu asaman dining ɗin,Warmers ne guda biyu babba da ƙarama ta miya ajiye asaman shi tare da plate,sae drinks data ɗauko masu,
Da yake mutanen gidan duk basu nan shiyasa bata girka abinci dayawa ba kamar yadda ta saba,ita kanta ta ɗan samu hutu yanzu,
“Munyi waya da daddy,”sehrish ce tayi maganar a yayin da take ƙoƙarin buɗe warmer ɗin,
“Ya faɗa maki ranar da zasu dawo ne”?_
“A’a bai faɗamun ba,sai dai yayi mun albishir mai daɗi,”
Cike da zumuɗi jahad tace”Wani albishir kenan”?
Murmushi ta ɗanyi a lokacin ta kammala buɗe warmer ɗin,wainar shinkafa ce acikinta,
“Ya sanar dani cewa da zarar sun dawo daga damaturu,A washe garin ranar zasu tafi kano,wurin nemo oumman mu,”
Maimakon taga farin ciki akan fuskar jahad,sai taga idanunta sun ɗan ciko daa kwalla,

“Meyasa bakya farin ciki ne”?
“Sehrish farin ciki fa kika ce?Bana Farin ciki,Idan har kika ga nayi farin ciki,toh An samu oummaan mu ne da ranta kuma da lafiyarta,ina fargabar abunda zaibiyo baya,idan suka je nemanta,Kinsan yadda oumman mu take tsananin son mu sosai,Amma lokaci guda aka nemeta aka rasa,tsorona kada ace ya sayyadi ne yayi mata wani abun,dama yasha faɗin cewa zai kashe ta idan har bata daina bin ƙwaƙƙwafin da takeyi mashi ba…..”dakatawa jahad tayi da yin maganar,jikinsu duk yayi sanyi,
“Addu’a yakamata muyi mata akan Allah yasa su samota,Amma nikaina ina fargabar a wani hali zasu same ta,”
Duk sunsha jinin jikinsu,zuba masu wainar tayi acikin plate,sannan ta buɗe ƙaramar warmer ɗin,Miyar ganye ce,taji ganda lu6u lu6u acikin,Tuni ƙamshinta ya gauraye wurin,
Daƙyar suke iya cin abincin,kamar waɗanda akayi ma dole suci,

*HAROON*

Fitowarshi kenan daga cikin bedroom ɗinshi,yana ƙokarin barin wurin,Yaji an ambaci sunanshi”Haroon”!gabanshi ne ya fadi,duk a tunaninshi Amrish ce ta kuma biyo shi,da sauri ya juya don yaga wacece,tun daga ƙasa har sama ya soma binta da kallo,Jikinta na sanye da atampa,riga da skirt ne sun matseta sosai,gaba ɗaya surar jikinta ta fito ɗass,bakowa bace wannan fa ce Hayaam,fitowarta kenan daga ɗakinsu na hotel da Omar ya kama masu,Ashe tun ranar basu tafi ba,Zama suka cigaba dayi acikinshi sun ƙara biyan kuɗin ɗakin,don aunty babba taci alwashin cewa babu inda zasu tafi,daga abuja sai Enugu wurin bokan nan,Yanzu haka kuɗi suke harhaɗawa,duk ta siyar da gold ɗinta,yanzu ma shirye shiryen tafiya sukeyi,
Sakin baki haroon yayi yana kallonta,da wata irin kasalalliyar Murya yace”Ke!me kikeyi anan”!?
Cike da kwarkwasa Hayaam ta ƙarasa gabanshi fuskarta ɗauke da murmushi tace”Kayi mamakin ganina ne?nikaina bansan da zamanka anan ba,yanzu kawai ina fitowa na ganka,kana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinka,”
Lokaci guda haroon ya saki wannan shu’umin murmushin nashi,a wayance yace”Amma nadaina ganinki a gidanmu,nayi tsammanin cewa kin koma gidanku ne?but me kikeyi acikin hotel ɗin nan”?
Shiru ta danyi tana tunanin abunda zata faɗa mashi,
Shi kuwa gogan gaba daya ya aza kwartayen idanuwan nan nashi akan Ƙirjinta,
“Naji kin yi shiru,idan ba damuwa mu shiga daga ciki mana,”yayi maganar yana nuna mata ƙopar daƙinshi,
Gaba yayi tabi bayanshi,buɗe masu ɗakin yayi suka shiga ciki,
A gefen gadonshi suka zauna,suna fuskantar juna,
“Kinyi kyau sosai,”yayi maganar yana wasa da harshen shi asaman la66ansa,
Murmushi hayaam tayi,batare da tace mashi komai ba,
“Ko kina buƙatar abunsha ne kona ci haka insa akawo maki”?
Girgiza kai tayi”a’a,a ƙoshe nake,bana jin yunwa,
ta6e bakinsa ya ɗanyi,kafin ya kuma cewa”Ƙamshin turarenki yayi mun,”
Dariya tayi tare da cewa”Allah ko”?
“Da zaki bani dama ko sau ɗaya ne,just inaso in ɗan shaƙi ƙamshinne a hancina,”
Batasan wanene haroon ba,saboda tasan halayen matasan gidansu,tayi tunanin cewa shima duk irinsu ne,hakan yasa tace mashi”Mezai hana,”
Matsawa yayi kusa da ita,tare da kai hancinshi saman fatar ƙirjinta,yana ɗan shinshinar ƙamshin turaren,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,zagayawa yayi da hannunshi ta bayan rigarta,abu kamar wasa,ya zuge zeep ɗin rigarta a hankali,saboda tafara fita hayyacinta,
ɗagowa yayi da hancinshi izuwa saman wuyanta kamar wani maye,haka ya shiga shinshina wuyan nata,da wata irin kasalalliyar murya yace,”Wannan turaren na wani company ne”
Shiru tayi batare da ta bashi amsar tambayarshi ba,dama da biyu yayi mata maganar don yaji idan har lokacin tana acikin hayyacinta,Shirun da tayi mashi ne ya tabbatar mashi da cewar,tafara fita hayyacinta,
Bata ankara ba,taji hannunshi ta cikin rigarta saman boobs ɗinta,A zabure ta kwace kanta daga jikinshi tare da ja da baya,tana ƙokarin gyara rigarta,ɗagowa tayi tana kallonshi,Murmushi ta gani akan fuskarshi,
Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ma,duk a tunaninta mutumin kirki ne shi ashe shima ɗan harka ne,
Miƙewa tayi da sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin,Hannu tasa ta ruƙo kopar zata buɗe,taji ƙopar adatse,hakan yasa tayi saurin juyawa tare da kallonshi,Nuna mata key ɗin yayi a hannunshi yana dariya,
Fuskarta aɗan ɗaure tace”pls,ka buɗe mun kopa inaso na tafi,Aunty laila na jirana,”
Mikewa haroon yayi tare da takawa izuwa gabanta ya tsaya,sannan yace”Ganinki da nayi gaba daya kin tayarmun da sha’awata,na kwaɗaitu da son kasancewa tare dake,kallo ɗaya da nayi maki na gane cewa ke ba ƙaramar ƴar bariki bace,Don haka kada ki 6oye mun true colour ɗinki,kizo kawai muyi harka,”
Zuba mashi ido tayi tana tunanin ta wata hanya zata 6ullowa haroon don ta samu ta tsere mashi,bakomai take ji ma tsoro ba fa ce aunty babba,saboda ta hanata kula maza,’
“Koda ace ina kula maza,bazan kula irinka ba,Kuma ni ba ƴar iska bace kamar yadda kake tsammani,Ka buɗe mun kopa in fita,in ba haka ba zanyi maka illa,”a tsiwace tayi maganar hada rufe idanunta,
Dariya haroon yayi tare da sanya hannushi ya ɗaga wandon jikinshi,ya tura key din acikinsa,sannan yace mata”Zoki ɗauki key din idan kin isa,ƙaramar ƴar tasha kafin kiyimun illa ni zan illata ki idan har baki taimaki kanki ba”
Tsabar takaici ne ya cika hayaam,tayi danasanin yi mashi magana,da duk hakan bata faru ba…

 

Back to top button