Hausa novels

Halysaah Page 173 By Khaleesat Haydar

HALYSAAH PAGE 173…Jay ya kalli Ajay yace “We are almost there, in few minutes time za mu isa, ga bridge din can a gaban mu….” Ajay yace “I am not asking if we are there or not Jay, tambayar ka nake me za ayi a kan bridge din?” Jay yace “Mutumin nan da muke magana da shi ne, yace ya bar wajen accident din, he is heading to Abuja now, ya kusa bridge din shi ma, zai bani wayar Walid da number me chemist din da za mu kira….” Kiran da ya sake shigowa wayar Jay ne yasa bai karasa maganar da yake yi ba yayi picking call din ya kai kunne, after some seconds Ajay ya warce wayar daga hannun Jay da sauri jin yana fadin motar da suke ciki da color din motar, Ajay na masa wani kallo yace “Turn this car Jawwad, this is nothing but a plan, ka juya motar nan let get out of here, meyasa bai bar wayar wajen me chemist din ba zai taho da shi? Meyasa yake tambayar ka motar da kake ciki da color? Ka dinga tsayawa kayi tunani before kayi duk abinda zaka yi mana” Jay ya kalli Ajay yayi shiru alamar he is also reasoning with what he just said, Jay yace “Bazan tsaya kan bridge din ba, let just go down the bridge and find the nearest U-turn, i am not stopping….” Sai ga kira ya sake shigowa, Jay ya kalli wayar sannan ya kalli Ajay, Ajay ya daga kiran ya sa handsfree, daga daya bangaren mutumin yace “Motar ku ne ya wuce yanxu kun hau bridge ko? Just park one side gani nan zuwa” Jay yace “Mu hadu cikin Lokoja, i am not stopping anywhere around here….” Ajay yayi saurin katse wayar yace “C’mon Jay, you don’t have to tell him ur move” Ko rufe baki Ajay bai yi ba motoci biyu dake bayansu suka wuce su a guje, lokaci daya suka yi cornering dinsu dai dai saman bridge din ta yanda babu space da za ma su iya escaping wajen, Jay was startled yayi saurin taka brake yana kallon motocin sannan ya juya ya kalli Ajay, Ajay ya dinga kallon yanda suka yi cornering dinsu within few seconds baya ko kiftawa, Calmly yace “Buge su mu tafi kawai Jay, hit the car…..” Jay ya kallesa looking speechless don bbu ta yanda za su bar wajen ko da ya buge motar da ta tare gabansu, gardawa kusan goma ne suka fiffito daga both cars din duk fuskokinsu a rufe suna pointing ma motarsu bindiga, gaba dayansu suka nufi motar a guje, Jay ya jinginar da kansa daieran motar a hankali yace “Innalillahi wa Inna ilaihi raji’un” Ajay ya kallesa yace “Ba na gaya maka ba, i know this is definitely a plan….” Jay that was so confused yace “But what did they want from us?” Ajay yace “What did Walid want from us dai, don duk shirinsa ne wannan” Jay ya juya ya kallesa, Dai dai nan daya a cikin thugs din ya zagayo ta wajen da Jay yake yana nuna masa bindiga cikin daga murya yace “Come down or I shoot” Kan kace me sauran ma duk suka zagaye motar suna nuna masu bindiga suna cewa su fito daga cikin motar ko su fara harbi, Ajay dai sai bin su da ido yake don ya ma rasa ta inda zai fara, bai ga alamar za su iya da su ba cause they are all armed, he saw no way out in this situation, ya juya ya kalli Jay yace “You know what? Zan fita in samesu, use that opportunity and run away from here” Jay ya kallesa da sauri ya fixgosa ganin zai bude motar yace “Noo, are you out of ur senses, baka ganin they are all armed? Me zaka iya masu?” Da ido Ajay ya sake bin thugs din dake ta masu hayaniya su bude motar, Calmly yace “Look Jay, koma bayan motar, let me take over the steering, i will manage to get out of here” Kamar sun san maganar da Ajay yayi suka sakar ma Tyre biyu bullets, Jay sai da yaji kansa ya sara masa, lokaci daya suka kara sakin bullets a back seat, Ajay ya kalli Jay, kawai ya bude motar ya sauka kafin su ci gaba da harbin, wannan yasa Jay yayi saurin bude motar shi ma ya sauka ya tunkaresu don baya son Ajay yace zai yi halinsa a wajen, bridge din ya dawo babu mota ko daya both hawa da sauka alamar dai anyi alerting sauran motoci masu zuwa cewar it’s not safe up there kowa ya ja ya tsaya a kasan gadan, Tunda suka sauko a motar thugs din ke pointing masu bindiga, Ajay dai bin su da kallo kawai yake daya bayan daya, Jay ya dake yace “What did you people want from us?” Wani me katon murya a cikinsu yace “Da kai muke ta waya yanxu?” Jay yace “Ni ne, me ku ke bukata?” Thug din yayi wani dariya yace “To an yi hatsari mun dauke wayar wanda yayi hatsarin for our interest, mu bamu san sa ba, we have nothing to do with him, tuni yan gari sun kai sa asibiti, he look rich shi yasa muka bibiyi yan uwansa ta wayarsa” Yana fadin haka ya wurga passport din Walid da wallet dinsa fa sauran tarkacensa a gaban Jay….” Calmly Jay yace “Me ku ke bukata daga gare mu? Say what ever it is….” Mutumin ya kara wani dariya da karfi, sai kuma ya hade rai yace “Kudi” Jay yace “Transfer ko Cash” Mutumin na wani murmushi ya kalli sauran thugs din dake tsaye still pointing their guns at Ajay and Jay, yace “Transfer, dauko waya ka mana transfer, sharp” Duk wannan abun Ajay na tsaye yana kallonsu, kusan dukkansu da bindiga me lafiya a hannunsu, Jay ya kalli Ajay suka hada ido sannan ya juya zai koma gun mota, wani a cikinsu ya bisa a baya yana pointing masa bindiga har zuwa gun motar, Ajay dai ya bi su da kallo just to make sure Jay is safe, Jay na dauko wayarsa daga cikin mota yaji harbin bindiga twice, dagowa yayi da sauri daga cikin motar idonsa ya sauka kan Ajay da ya dafe chest chest dinsa yana kallon mutumin dake opposite dinsa, Jay bai san sanda yayi wani kara ya saki wayar hannunsa da gudu ya zaga zuwa inda Ajay yake, kafin ya iso nan har Ajay ya durkusa on his knee yana kallonsa, lokaci daya rigar jikinsa yayi drenching da jini, Jay ya duka gabansa cikin rudewa ya rungumosa cikin tashin hankali yace “No pls, hold on Junaid, hold on plsss” Ajay na son bude baki yayi magana amma ya kasa, and he began gasping and struggling for breathe, sai ga jini na zuba bakinsa, Jay bai fasa kiran sunansa ba cikin tashin hankali yana rike da shi, sai kuma yayi saurin cire rigarsa hannunsa na rawa ya toshe dai dai wajen gunshot din sannan ya zaunar da shi yana cewa “Hold on piss Ajay… Pls hold on” Yana ganin Ajay ya fara rufe ido ya kara rungumosa cikin tashin hankali yayi wani kara yace “Noo, don’t do this to us Junaid, I know you to be very strong, hold on plss, hold on a little za mu je asibiti yanxu….” Ajay ya ja numfashi da kyar as if trying to hold on a little kamar yanda Jay yace masa amma numfashinsa ya fara failing dinsa ya daura kansa saman kafadar Jay that was trying to give him all possible first aid a moment din, still Breathe Ajay ya bude baki ake care of Jeeddah” Daga haka yaji yana kalmar shahada, after that kuma a ya dinga yi yana kiran sunansa da kartı cıkın rikicewa, da grip din bindiga daya daga thugs din suka bugi kan Jay sannan su uku suka fincikosa hakan yasa ya sake Ajay, double ya dinga ganin yanda Ajay yayi baya ya fadi bayan ya sakesa, yayi wani kara that echoed to a far far distance yana kwala sunansa, sau uku suna buga masa kan bindigan da karfi before he passed out, suka sakesa ya fadi kan jinin Ajay, thugs din uku suka tafi kan Ajay da gudu suka dagasa within few seconds suka jefasa cikin ruwan dake karkashin bridge din, wani a cikinsu ya kalli ogansu yace “Oga baza a harbesa ba shi?” Ogan yace “A’a ko kwarzane ba ace mu yi masa ba” Kamar hadin baki kuma duk suka shige motocinsu gaba daya suka yi zoom off, sun bar wajen da minti kusan biyar sai ga motocin yan sanda biyu bayan anyi alerting dinsu operation dake faruwa saman bridge, Jay kawai suka gani kwance cikin jini, sai motarsu dake bude da wallet din Walid da Passport dinsa, suka dauke Jay zuwa asibitin cikin gari…. Wajen karfe bakwai na safe Khaleesat ta fito main parlor tana tafiya a hankali ta zauna kan carpet tana kallon Hajja a hankali tace “Ina kwana Hajja?” Hajja tace “Lafiya lau Jeeddah, fin jikin?” Khaleesat ta sunku ar da “Da sauki” Hajja tace “Yakumbo taje gaisheni yanxu take gaya min baki yi bacci ba daren jiya, nima zuwana gidan kenan, idan na samu ganin Mai martaba sai a kira maki likita ya duba ki” Ita dai Khaleesat kanta na kasa, Hajja ta kalli Yakumbo tace “Bayan kunun da take sha sai me kuma take iya ci?” Da ladabi Yakumbo tace “Babu wani abu da take ci sai Guava ranki shi dade” Hajja na kallon Khaleesat tace “Sannu Jeeddah” Ita dai Khaleesat bata dago kanta ba, Hajja ta sake kallon Yakumbo tace “To yanxu ta sha kunun ne?” Yakumbo tace “Yanxu naga dama mata yana kitchen, da yake sai kusan asuban nan ta samu bacci, shigowarki yanxu yasa na taso ta” Hajja tace “Wayyo, ai da baki taso ta ba, nima dalili yasa nayi sammakon zuwa gidan, debo mata kunun ta sha Yakumbo tace “To Ranki shi dade” Mikewa Tayi ta nufi kitchen da sauri, Khaleesat ta bi ta da kallo, daurewa kawai take zaman da tayi a parlon, ji take kamar an zare mata wani abu a jiki that’s making her feel extra weak tun jiya da daddare, ta kalli Hajja cike da karfin hali tace “Zan wanke baki in dawo Hajja” Hajja tace “To je ki dawo Jeeddah, Allah Ubangiji ya baki lafiya” Khaleesat ta daure da kyar ta mike a T S Virin da take ji ta bar parlon, kitchen ta shiga wajen Yakumbo dake juye mata kunu a flask, da mamaki Yakumbo tace “Ranki shi dade kina bukatar wani abu ne?” Ta jingina da kofa tace “Bai kira ki bane Mama?” Yakumbo tace “Ni nasan ya kira Gimblya, kilan ko matsalar network ne ya hana kiran shigowa” Khaleesat dai bata ce komai ba, kawal ta juya ta fita daga kitchen din zuwa part dinsa, Yakumbo ta sauke ajiyar zuciya ta ci gaba da abinda take, tun jiya ta damu tana son magana da shi a waya, ta kirasa ya kai sau biyar bal daga ba, shi ne ta sa Yakumbo ta kirasa ita ma din bai daga ba, duk da haka Khaleesat ta kasa fushi da shi, duk baccin da bata yl ba daren jlya lokaci lokaci take kiransa still no response, kafin bacci ya dauketa da asuba ma ta kirasa shiru, ita kanta Yakumbo ta kirasa da wayarta bayan sallan asuba amma bal daga ba, amma saboda bata son Khaleesat tayi fushi da shi sai take ta laka ma network, Hajja na ta zaune parlon sai ga Aunty ta shigo da sallama, tun shigowar Hajja gidan ta hadu da jakadiyar Aunty ta gaya mata tace ma Aunty ta taho bangaren Ajay ta sameta, most 15 minutes ago kenan, sal yanxu Aunty taga daman zuwa, zaunawa tayi kan Carpet Sarkanmu da Safiyah Hajja” Hajja tace “Yauwa….” Aunty tace “Ina kwana?” Hajja tace “Lafiya lau, Yusuf din bai tashi bane har yanxu?” Aunty tace “Eh baya jin dadi ne shi yasa bai fito ba” Hajja tace “Har yanxu dai? Jiya mun yi waya da shi yake ce min baya jin dadi shine har nayi sammakon zuwa in gansa yanxu” Aunty tace “Ai kam jikin ba dadi, sai da aka kira likitansa, da na barosa dai bacci yake, amma zaki iya zuwa ki gansa Hajja” Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace “Allah Ubangiji ya basa lafiya, bari dai ya tashi din ya fito” Hajja bata rufe baki ba sai ga Hajiya A’isha ta shigo parlon cikin gigicewa ta zo wajen Aunty bayan taje bangarenta aka ce ta taho bangaren Ajay, Hajiya A’isha bata san ma Hajja ta zo gidan ba, tana ganin Hajja ta taho ta zube gabanta tace “Innalillahi wa Inna ilaihi raji’una, wani labari ne wannan nake ji a gidan nan ni A’isha?” Aunty ta juya da sauri tana kallonta, Hajja da hankalinta ya tashi sosai ta mike tsaye tace “Kamar yaya A’isha?” Hajiya A’isha tace “Yanxu Hajiya Sumayya ta kirani wai Mukhtar ya kirata cikin kidimewa yana sanar mata rasuwa” Hajja ta dafe kirji tace “Wa ya rasu?” Aunty bata sapanda ta mike da sauri ba hankalishi tunanin gun Mai martaba ya tafiya Aa fashe da kuka tace “Ni ai ban san baku sani ba” Sai kuma ta mike zata fita parlon Haiia sashin Sarki taji Hajiya A’isha tace “Wai Junaid aka harbe daren jiya….” Hajja bata san sanda tayi mata wani tsawan ba cikin gigicewa tace “Wani magana ce wannan kike yi A’isha, wani Junaid din aka harbe?” Yakumbo da ta kasa shigowa parlorn tun zuwan Hajiya A’isha ta sake fruits din hannunta da ta wanke zata kawo ma Hajja jin abinda Hajiya A’isha tace, Aunty kuwa still tayi a inda take tsaye ko kwakkwaran motsi ta kasa tana kallon Hajiya A’isha babu ko kiftawa, Hajiya A’isha ta fashe da kuka tace “Innalillahi wa Inna ilaihi raji’un, mun shiga uku Hajja, wallahi harbinsa suka yi har lahira” Yakumbo tayi saurin juyawa ganin Khaleesat bakin kofar parlor ta tafi tayi saurin tareta tace “Ranki shi dade mu je ciki in baki kunun” Bata jira cewarta ba ta fara jan ta zuwa cikin parlon a rikice, Khaleesat ta warce hannunta tana kallonta babu ko kiftawa tace “Me ke faruwa?” Gaba daya Yakumbo ta daburce ta kara rikota tace “Mu je dai ciki ranki shi dade” Khaleesat bata san sanda ta warce hannunta ba ta fice daga parlon da sauri zuwa Main parlor, amma bata tarar da Hajja da su Aunty parlon ba, hakan yasa ta fice daga bangaren gaba daya ko takalmi babu a kafarta, Aunty suna isa sashin sarki suka tarar ya fita masarautar urgently don ko wayoyinsa bai dauka ba, suka tarar da Maryam da Khadijah sai kuka suke a parlon don a kan idonsu aka kira Mai martaba sun shigo duba jikinsa, Hajja dai na tsaye bata ko motsi sai bin kowa take da kallo, sai ga Kilishi da Gimbiya Firdausi da Hajiya Sumayya sun shigo kamar an hankadosu, Kilishi na cewa “Innalillahi wa Inna ilaihi raji’una, Allahumma ajirni fi musibati, Hajja shikenan Junaid, Innalillahi wa Inna ilaihi raji’un…..” Hajiya A’isha ce tayi saurin tare Hajja da tayi baya zata fadi, su Kilishi ma duk suka yi kanta aka rirriketa, duk Khaleesat na tsaye tana kallonsu kamar an dasa ta a wajen, taji kanta ya fara juya mata ta fara ganin kowa double a parlon, a bayanta take jin kamar muryar mu Hadiyah tana kuka alamar da Ummi suke waya tana cewa “Wallahi Ummi Ya Mukhtar ne ya kira, wai sun harbe Ya Junaid shi kuma Jawwad yana asibiti a lokoja din” Khaleesat taji komai ya tsaya mata cak, ta dena ganin haske sai duhu, banda Hadiyah da tayi saurin rikota da tuni zata b da kofa, su Aunty da Gimbiya Kansu da sauri….

Visit Kundin Hausa Novel For More Novel

Back to top button