Hausa novels

Yar Aikin Karuwai Book 2 Chapter 1-5 By Asma Baffa

Yar aikin Karuwai Book 2 By Asma Baffa

🌼’YAR AIKIN KARUWAI 2🌼
(MATAFIYA)

GARGADI GA MASU AUDIO WANNAN LITTAFIN NA RIGADA NA SIYAR DA SHI GA MASU SATA SU MAIDA SHI AUDIO BAN YARDA BA BAN AMINCE BA

 

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA GA
ZAINAB USMAN

 

Ina masu bukatar unique kitchen utensils . fabrics adult and children’s wears shoe’s and bag’s.
Da masu bukatar ahada musu lefe ko masu bukatar iya luggage’s din kawai duk inkazo
R&U EXCLUSIVE KITCHEN AND MORE.
Zaku samu duk abinda kuke bukata ko a awanne state kake zaa kawo

Masu bukata ga number. 0703 455 9202

https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx

 

Page din nan da
AIDA MAMAN TASNIM
Zai bude, nata ne ‘yar Albarka.

Gaisuwa ga
AUTARESS tawa

 

 

Lokacin da Suka tsaya a mota an wuce gamborin gala dake Maiduguri anyi nisa an nutsa ana ta wuce kauyuka masu hatsari, Rufaida ce ta Fara dirgowa daga cikin mota wacce da ganin Kalar motar tayoyin kadai kasan suna bin Sahara gata Samanta a bude yake Kamar akori kura amma katuwa ce motar idan ana ruwa sai dai a lulluba musu tempol,ga Rana ana kwalawa,tace Kaka dirgo kaima Kar zafi ya kashe min kai mu dai ko Makkah ko kafar katako,Makkah ko a buhun kunama sai munje Inshaallah ba gudu ba ja da baya,mutanen motar ne Suka firfito Dan guzirinsu na ruwa da na ci suka Fara Dan gurgura,Kaka yana gefe Rana ta ishi tsoho yace Jikalle dakko mana ruwan muma mu jika makoshinmu,baki Rufaida ta zumburo tace tun yanzu sai ka shanye mana guzurin ba a san ranar tashin motar nan ba fa,Wani matashi Wanda bai da aiki sai kallon Rufaida Kamar maye yace ke da Allah ki bawa bawan Allah ruwa ya Sha ke wacce irin azzaluma ce ne,Cele tace kaci darajar a hanya muke cikin Niyyar shiga Makkah nake bazan ce komai ba,Ido matashin ya zaro yace yau naji fitsararriya rashin kunya Zaki min,Kaka ne yace in Banda shishiginka Ina ruwanka da ita,matashin yace haka ma zaka ce na barku ta kasheka yace naji dan ubanka jikata ce fa matsiyacin yaro.
Ana haka Kawai mota ta tashi Rufaida ta kwarara ihun murna tayi tsalle tare da fadawa motar tace Kaka Miko hannunka,tsoho ya taka da kyar tana taimaka Masa ya shiga shima Suka zauna sannan ta dakko ruwa ta bawa Kaka ya Sha sosai ta mayar Bayan ta Sha itama,Chin chin da Tayo da meet pie na guzuri suna tafiya ita da Kaka suna ci tana kallon mutane dai in ka cika kallonta ma Sai tai maka gwalo Wai su kayan dadi suke ci,suna gama ci ta ebo dabino Suka ci sabo dabino Yana rike cikin matafiyi ko yaya kaci sinadarinsa Yana rike mutum na wani dogon lokaci,suna tafiya sai da dare yayi sosai Suka karasa wani kauyen suna murna za a huta amma Agent din ciki wacce tana gaban mota da wasu maza biyu Suma suna gaban mota Suka ce ba a tsayawa a wannan kauyen hatsari ne da shi kuyi Addua ma mu wuce lafiya,Rufaida aka jawo carbi ana hailala da istingifari tana cewa Allah ka tsallakar damu Allah Makkah ko a buhun barkono ne ka kaimu.

Suna tafiya a garin suka iske gawarwakin mutane birjik a gefen Hanya an karkashe su gasu nan,Cele ta tsorata da ganin gawar mutane birjik bata taba gani ba,suka ci gaba da tafiya har dare yayi sannan Suka zo wani kauyen da shi kuma ana yawan ruwa ba a tsayawa a wajen ruwa sai ya shanye motar gaba Daya su kansu mutanen wajen a saman dutse suke Kan tsauni,ana sauri za a bar wajen ruwa ya kece me karfi gashi ba batun ma a rufa musu tempol Dole sakkowa sukayi da yawansu sosai sabo da shake suke dam a cikin motar wasu sun iya daukan guzirinsu wasu basu iya dauka ba,ga wata Mata harda danta karami a baya dan wata uku,Agent dince ta karbar Mata yaro sannan ta sakko daga motar Suka hau gudu suna gudun tsira,Kakan Cele ya Fadi ya tashi Cele ta daukar musu guzirinsu ta Goya jakar a baya,suna gudu Kaka ya sake faduwa ta dawo ta dagashi ta taimaka Masa Suka ci gaba da gudu Allah yasa Cele Riga da wando ta saka amma rigar iya gwiwa, sai da Suka Yi tafiya me uban Nisa sannan Suka samu saman tsaunin da zasu fake,sai lokacin aka tuna da wata tsohuwa tukuf,aka dinga tambaya Ina Baba Ina Baba,Cele tace ai kuwa an barta a mota,sai da ruwa ya tsagaita Agent da driver da maza Uku Suka koma wajen motar tasu wadda ruwa ya shanyeta gaba daya,Baba suka hango Allah yasa iya kanta ne ruwan bai shanye ba,Suka Yi dabara aka dakkota.

Suna dawowa inda su Cele suke aka hau jinyar Baba Kamar zata mutu ana so ruwa ya tsotse na Hanya su samu su iya fitar da motarsu daga cikin tabo,sai da Suka kwana biyu a saman tsaunin duk sun fita a hayayycinsu ga ruwa ga sanyi sai da suka samu ruwan ya dauke sannan mazan suka dinga canja kaya dama jakan kayansu duk ta Leda ce wacce ruwa bazai Shiga ba,Sauran matan Suka dan fake daga Bayan tsauni Suka canja Kaya Suka shanya kayan jikinsu,Cele tana zagawa zata canja Kaya maza wasu samari suka dinga leka ta,tana daga Riga Suka yi Ido hudu da wani matashi Mustapha nan take tace uwarka ka kalla Mustapha shege me idon ungulu Mustapha ya koma inda yake da sauri,Agent ta hau zaginsu tana dura musu ashar sannan Cele ta samu ta canja wasu riga da wando t-shirt fara da jean blue duk a gwanjo ta siyo abinta sabo da tunanin tafiya irin wannan sai da Riga da wando,cikin Yan matan wata Wasila tace kin huta wallahi Rufaida da nasan haka tafiyar take Nima duk kana nan Kaya zan kwaso,Cele tace ai ni Nan da Kika ganni akwai maths Ina da tunani da lissafi kayansu duk ya Fara bushewa sabo da rana ta kwalle,a ranar Kuma Baba tsohuwa da ake jinyarta Allah ya karbi rayuwarta suna sauri sai mutanen yankin Suka samu a ciki akwai musulmai sosai Suka Basu Gawar Baba suyi Mata sutura su binne ta,suka koma motar tasu kafin ta tashi sai da Suka yini tun safe suke abu Daya sai kusan dare sannan ta iya tashi,bayan ma ta tashi fitar da ita daga tabon sai da Suka hadu aka turata sosai sannan Suka tafi,Cele sai ihun murna take Makka ko da kafar katako ne,tace Alherin Allah ya Kai Miki Saudiyya wuuuuuu tayi tsalle ta dane bayan mota ta kamo Kaka Wanda yaji wuya cewa yake mu koma gida nidai na fasa zuwa Jikalle,Cele ta bata rai tace wlh sai dai muyi shahada a Hanya amma ba gudu ba ja da baya iya wuya sai munje Inshaallah sai munyi kudi,Abdul yace Inshaallah ai Ina zuwa shayi Zan ta Sha muryata ta washe sai kiji yalla yalla…suna dariya Awwalu yace sai kaji Muna ciniki muna Kam Kam,2riyal laa laaa kamsa riyal,suna tafiya kowa ya zaro kayan cinsa Yana ci har suna sake kwana Suka yini Sallah ce kawai ke tsaida su a wasu kauyukan.

Wise tana girkinta a kitchen Papa ya shigo a hankali ya dade Yana kallonta Yana zuba uban murmushi,yanzu sai Fushi take yi da shi bata kulashi ta maza yayi ya rungumeta ta baya,Wise Ido ta lumshe yau sati tana gaba da mijinta an dade ba a hadu ba a hankali cikin kunne Papa ya Shiga furta Mata haba my Game changer,My play maker, Heroes in my book, uhm haba my best goal assistance Allah yaci gaba da tsare min ke,Nayi kuskure ki yafe min ki taya ni da rokon Allah ya yafe min,da me zanji da halin da nake ciki ko da fushin da kike Yi dani,I love you my wife,kalaman Papa sun sanyaya zuciyar Wise ba kadan ba sunyi tasiri a zuciyarta a hankali ta juyo a jikinsa suna facing juna tace na hakura nima me laifi ce na maka karya na shigo rayuwarka badan Allah ba karshe na fada sonka,na taba karuw….shiiiii…Papa ya furta yace bana bukatar Jin komai na San komai Kuma na gano Baku da kudin da kika Zo yaudara ta da shi daga baya na hakura na aureki a haka, bana fata naji zancen kin taba karuwanci a duniya magana ta wuce Allah ya yafe mana,Wise tace na gode lokacin da idonta ya ciko da kwalla,Yana Murmushi yace mene abin kwalla kuma,Wise a kirjin Papa ta kwanta tana nadamar karuwancin da tayi a rayuwa,yace Kinga gama Mana abincin tukun yunwa nake ji rabon da naci abinci ya tsirga min tun kafin Maman Sabreen ta ballo ruwa,Gama girkin muci sai kizo kici gaba da min Shagwabar taki,lokacin da Wise ta danji kunya kenan tun shigarta bariki har mamakin kanta tayi Wai taji kunya,Papa yana fita ta kirani na daga lokacin Ina gyarawa Nawwar kayansa na sawa tace Miracle albishirinki nace goro tace yau naji kunya abin mamaki papan Sabreen yayi magana wai naji kunya,Dariya ta bani nace to congratulations,ta kashe wayar ta Kira Star dake jikin Malam a kwance suna murza juna taji Malam Abulkhair yana wani nishi,Star tace karatu yake Dora min ke Zan kira…ta kashe wayar,Wise ta bi Wayar da kallo tace shegu bari na Kira Seraline Saliha ce ita ta Kira Sera bugu Daya ta daga tana cewa Hero plate din fa daka wanke bai fita ba haka ake wanke wanken,Sabeer Yana dariya yace kin sani Shiga kitchen ni ba aikina ba,ni fa eating you shine aikina,Seraline tana dariya tace Allah ya shiryeka,Wise wayarta ta kashe tace to bari na Kama dattijona nima na hutawa kaina da Yan Iska,Iyamami an warke ras ashe an dawo da ita gida,ita bata rabo da zaga bangaren yaranta sai kace yar iska tana ji da Yamma part din Wise uban kida na tashi a speaker amma ta wani dangala kafa ta tafi wajen Wai zataje wajen danta Yusufa zasuyi magana.
Tana shiga ta iske Papa a zaune yana cin abinci Wise sai uwar rawa take tika Kamar ba gobe ta juyawa Papa mazaunai Yana kala Yana washe baki yana nishadi,Iyamami ta Shiga ko sallamarta ba a ji sai da Papa ya lura ransa ya baci wai ita Kawai sai dai ta shigowa mutum Palo ba knocking,kidan ya kashe Wise bata lura da Iyamami ba ma ta koma ta zauna a cinyar papa,sai da yace Iyamami fa,ba tare da ta tashi a cinyarsa ba ta juya ta kalleta ita kanta Wise tana Jin haushin abinda tsohuwar take mata,kin tashi tayi ta kwanta a jikin Papa sannan tace Ina yini Iyamami,tsohuwar Hannu ta shiga tafawa tace ke mayyar maza dama ance cikakkiyar karuwa ce gashi Kuwa idona Yana ta gani,yanzu idan ba tambadewa ba Kamar Papa babban mutum Wanda ya haifeki ki zauna kina uban murguza Masa tuwon duwawu a gabansa kina karkada su wato harda tura Masa ya gani ke ga tabbatacciya, yanzu idan a Zamanin mu ne yaushe za ayiwa Yusufa wannan iskancin ai sai kunya da kunya amma Kai Yusufa laifinka ne Kaine ka bata Fuska ta rainaka wannan raini ne,da yarka kamar Sabreen ko kunya baka ji,Kuma ta ganni na shigo tayi zamanta ma a cinyarka daram wato na gani da kyau Kuma a haka ta gaisheni ba rusunawa ba komai wato na haifar Mata yaro a banza ko Kai Kuma sai wani gyada Kai kake yi Kamar na jinjirin jaki.

Wise tace Iyamami kiyi hakuri mu ai zamaninmu daban da naku Kuma Banga shigowarki ba irin waje na Yara ai ba a shiga da ka haka sakaka idan da tsirara muke fa ai Kinga bai Dace kiga inda danki yake Shige da fice ba ko ni bazan ji Dadi ba ki kallar min Antainarsa ba sabo da kin Gama kallon rabonki lokacin da Kika haife shi har ya balaga yanzu hurumina ce ni kadai ya kamata na gani,Iyamami salati ta saki kamar me Aljanu tace karya kike karuwa baki Isa ki mallake min Dana ba Kuma sai an sakeki,Papa yace Dan Allah Iyamami ki ja girmanki bazan ji dadi ana fada Miki magana ba ba tsari Kuma ke Kika jawo,Kuka Iyamami ta saki tace shike nan ku kashe ni ku huta wayyo jama’a kuzo mace tafi uwa wayyo Allah laaaaaaa mace tafi uwa Yusufa ka nemi Albarka,nayi tur da Allah wadai da wannan auren,bazai Albarka ba ta juya tana bazai Albarka sai ka saketa,Wise ta kalli Papa Wanda ya zuba tagumi yace shike Nan Iyamami ta kwashewa auren nan Albarka Ina tsoro Kar masifa ta kunno Mana,Wise tayi Murmushi tace Inshaallah zaiyi Albarka ni Wise na sa Masa albarka,bari naje na lallashe ta,yanzu a Fushi take ko kaje ma sake kwashewa auren Albarka zata yi Kawai muyi Mata Addua Allah ya ganar da ita idan ta huce sai muje tare mu bata hakuri ai uwa ce tafi gaban wasa,daganan Suka fara tsotsar juna suna murza juna har zuwa bedroom Suka fada saman bed, Papa Yana Mata rada suna dariya kasa kasa.

Nawwar yana kwance a jikina saman bed Ina zaune a tsakiyar bed dinmu jingine nake da jikin gadon Mami ta Kira shi ya kashe tare da kiranta back,yace Mamita ta kaina yau sati biyu da Iddar ki Ina murna Mami,karka dameni cewa nayi zanyi aure a nan kace no to ya kake so nayi balarabe ne dan Yemen Ina sonsa gaskiya,Nawwar yace Mami kede kice kyau ya rude ki Kawai gaskiya Ina taya Baffa kishi wani zai aure Masa mata,wallahi Mami larabawan nan karfin sha’awa gare su Basu San hakuri ba Kar ya kashe min Mami,zanci ubanka Nawwar ni sa’arka ce kafa dameni Ina ruwanka,dariya yayi yace Mami Ina jiye Miki wlh tam Ina nan zaki min waya kice an sakeki larabawan Yemen ko Kuwait ba sauki,Tsaki Mami ta ja tare da kashe wayarta ta Kira Yan uwanta ta sanar musu ta samu mijin aure Mahmood Suka Mata fatan alheria.
Ni Kuwa Ina Jin Nawwar suna magana da Mami ya gama bance kala ba waya nake dannawa Muna chat da Star akan magungunan gyara Oven Ina dariya ni kadai sabo da iskancin Star ya isheni,tace wai maganin da na baki ki gwada sunansa Memory ba irin kidan da Nawwar bazai Kama ba,tace yau akwai kida Nawwar ba bacci,makwafta ma Sai sunji kidan da Nawwar ke ji,voice na Mata nace baki ga bakina ba Dan karami can ma wajen haka yake ance da ganina kin San da lafiyata,Voice ta min itama tace zo kiga Malam na goge Masa hadda wlh karatu ma ya daina yanzu Sam sai karatun Antaina,Nace Nawwar yace ku dawo makaranta wlh gobe kullum sai kunzo mun hadu a gidana anyi karatu na fadawa ma su Mandula Wai kinji munafukin yaron data Aura harda min iyayi Wai shi matarsa ba inda zata je baya son yawon nan zaman aure zata Yi ba yawo ba,Star tace ai yafi karfin Mandula wannan Dan yaron sai abinda yace take yi har kuka yake bata idan anzo harka,ki duba Iskanci irin na Mandula a barikin ma taci uban kowa ta zaga bariki bariki Wai Dan yaro 26yrs shine yafi karfinta tace ko a bariki bata taba haduwa da irinsa ba sabon karatu take Yi a kansa, dariya muke ta yi,Nawwar Wayar ya kwace yace kin dameni fa aikinku kenan kuyi ta tona Mana asiri ana kallonmu a banza,Muna waya da Mami baki min jaje ba zata yi aure kina jina,nace to Da da Maminsa ta ya zan zauna Ina shigar muku zance please ka bani wayar mu karasa,yace ta karfi ce kwaci na Fara bin hannunsa Zan kwace yana yawo da hannun na kasa kamawa har na zameshi a jikina na tashi tsaye a saman bed din,jawoni yayi na Fada saman bed din ba shiri.

Dariya nayi nace ka tuna min da wani da na taba gani a Kano Yana yanayi da Kai har irin muryarku,da sauri ya bata rai sabo da kishi,nace labarinsa Zan baka a wajensa na samu kudin zuwa garin nan na manta ban fada maka ba,Fuska ya sake daurewa yayi gefe da Kansa Yana cewa bana son ji,nace Allah sai na fada maka,banza ya min na Fara bashi zuwana Kano daga Kauye lokacin da Dagaci ya koreni,nace Ina ta bara kullum sai na canja kamanni ta hanyar shefe fuskata da bakin tukunya na samu na saka yagaggun Kaya,Watarana nabi ta wajen hotel Wai ko zan samu kudi tunda masu kudi ne ke harka a wajen Kawai wani matashi kyakyawa yazo wlh duk da ban San fuskarsa ba Kuna Kama har muryar sai dai shi a Kano na ganshi me zai kawo shi Nan,walet dinsa ya jefar lokacin ya siyo abubuwa da yawa a ledojin shopping mall,ya rigada ya shige ciki nazo Ni Kuma na tsincii walet din da kudi a ciki dollars lokacin ban San mene dollars ba hasali ma ni ko kudin Nigeria ne ban iya ha’inci ba,sai da na kwashe 5 days kullum sai na je Neman bawan Allah din bana ganinsa ranar Katsam ya fito na Gane shi ta hanyar kamshin turarensa,da sauri Nawwar ya juyo Yana kallona ya furta Ina jinki,naci gaba da cewa Kawai mutumin ya karba yaji Dadi har dollars ya irgo ya bani nace bana so gwara ya bani dari biyar ko dubu Daya,yace to jirani ya shiga cikin hotel din ya kawo min dubu talatin yace inyi hakuri ba cash a hannunsa ya min godiya Ni Kuwa na kwashe da gudu sai tasha washe gari da safe.

Nawwar yace ai nine,kamar Wasa na dauka tashi yayi ya dauko wallet din cikin wata akwatinsa karama yace ba ita bace wannan? Na karba na duba sosai nace wlh itace,ya jawo locker ta jikin mudubi ya dakko turaren yace Kinga turarensa da nake sawa lokacin Kuma tunda na dawo na siyo sababbi na daina shafawa,karba nayi na fesa a jikina na bude baki nace wallahi kaine,yace to meeting naje kano sati biyu nayi a can green park hotel,nace shine wlh Ina mamaki da murna na dirgo daga saman bed Muka rungume juna sosai Yana dariya yace amma lokacin gaskiya matata Yar kauyis ce,dariya nayi nace ba wani yace kinyi wani daurin dankwali kin zamge kai me kunya bakya iya kallona fa,nace ai daga nan sai bariki,yanzu ai matar tawa ba kunya gareta ba,nace duk ta gudu ai gashi ka sake lalatani,gashina yake shafawa yace Yar amana ta ya daukeni yace zauna muyi kallo,baki na turo Ina shagwaba Ina Masa magana da Ido dariya yayi yace na gane ke Yar nan zalamarki yanzu tayi yawa,Murmushi nayi Ina sake rungume shi na tura shi saman bed yana min wani kallo me rudani,Hannu nasa tare da cire Yar guntuwar rigar da na saka daga ni sai pant sai bra,Muka Fara zuba kauna yau nice ke Jan ragamar komai ko da Muka tsunduma cikin harka Ina samansa Ina twerking yau sai da na gogewa Nawwar hadda,yaji Dadi fiye da kullum sai lallabani yake Yana nan da ni.

Mairo tun a ranar da Suka Isa kasa me tsarki wacce ta musu Hanya ta kaisu gidanta Wanda su wajen goma ne a gidan gidan nasu duk kazanta ko Ina ba a gyarawa ga Makkah suna da kuda,a cikin gidan duk Inda ka bi sai kudaje buuuu buuuu suna tashi ba kyan gani,Mairo tace kuda haka sai kace Muna gaban me balangun da bai Fara gashi ba,ku Kuwa ku samawa kanku lafiya ku dinga gyarawa ji yanda Muka wuce hadaddun wurare amma sai a nan Muka yada zango ,Agent din ta bata rai tace Zaki ma Yi bayani sai nan gaba tukun gaki da ciki Wai watansa nawa ne ma? Mairo tace wata bakwai kenan,gashi nan fa ya girma Amma kamar tumbi Allah ya taimakeki ,sauran takarin ne Suka Zo dukkansu dattijai dasu suka dakumi Sadiya Suka hau Yi Mata kiss a kumatu Salamu Alayki muaaah muahhh,kowacce haka Suka dakumi Mairo itama Suka rungumeta suna marhababik marhababik muah muuaaah….suna magana suna jefo larabci,Mairo tace zanyi fitsari,muje Kinga wagga hammam can wai toilet,ta fara takawa a hankali agent Hajiya Marwa tana furta shuwayya shuwayya….Mairo dai ta shiga toilet to ba Dan laifi an wanke.

Bayan sun huta na sati daya nan kuma Hajiya Marwa tace to akwai Sana’a iri iri ba Zama a nan Kuna gani kullum sai mun fita a garin nan neman kudi,dakin Marwa inda aka sauke su kaya ne zukumi zukumi irin na Yar hajja duk gumama iri iri ba masaka tsinke,a cikin gumamar Wanda mu anan akafi sani da gwanjo amma na larabawa ciki Suka zabi suturun sakawa,ita Mairo kudin Sana’ar ma aro aka Bata tsabar talauci, ta fara yin fura da nono amma da Yogourt suke amfani suna kaiwa gidajen masu Ibada Wanda Suka Zo Ibada Saudiyya ko dakin ka’aba ba a kaisu ba sabo da gudun kame dole sai lokacin da aikin Hajji yazo sannan kowa Yana da yanci lokacin zasu iya su sauke farali har Umrah amma duk da Haka Hajiya Marwa tace zata kaisu suyi Umrah kafin lokacin aikin hajji.

Su kuwa Wanda Suka je ta kamfani maza masu ilimi sunfi yawa su already dama suna da aikin da zasu yi,wasu ana kaisu kamfanin wani balaraben suna aiki wasu kuma gidan gonar wani,shima idan aka Kai mutum Kawai suna wajen aiki sai sun dade suke samu su saci hanya su fito a haka suke samu suyi aikin hajji kafin su samu yancin fita,Yan unguwar su Sadiya da aka musu hanyar aiki Suka tafi ta kamfani Suma suna da yawa ciki akwai Nazifi ,Shamsu,Isa duk makwaftan Sadiya ne Suma Babar su Sadiya ta musu hanyar kamfanin,Nazifi shi gidan gona aka kaishi inda aikinsu tsike Apple su shiryata kwali kwali,Shamsu kuwa shi bangaren kula da shanu aka kaishi sai Isa Wanda wani kamfani aka kaishi Wanda suke sarrafa Alkama a maidata flour suna ta aikinsu hankali kwance su Kam sun bi ta tsari sai dai wasu aikin nasu da wahala Kuma ga kudin kadan ake bar musu suna biyan Agent kudi Wanda a tafiya 1.5million aka ce zasu bada amma suna zuwa garin Suka ce 5million zasu biya dole,bangaren Mairo ma haka aka maida kudin sabo da zalunci irin na Agent da suke yi Babu tausayi ba Imani kana aiki amma kullum a biyan kudi kake.

Dake a can ne ba wahala washe gari aka daura auren Mami da Mahmood Balaraben Yemen Wanda ke da shagon Jallabiyya a Madina ana daurawa Amarya ta tare a gidan balarabe shi ya dakko abarsa a mota,Dake su suna da gata a kasar har motoci suke siya,gasu su dake larabawa ne business ya Kai wasu Saudiyya, wasu Kuma suna wasu kasashen sakamakon gomnatin kasashen su Ambassador dake me hankali ne yasan me yake sai yaje kasar da yake jakadanci ya samowa Yan kasarsa aiki na kirki me kyau a bashi vacancy,duk me son aiki sai yaje a bashi form a kasarsa ya cike da takardun da ake bukata sai a zabo su a kaisu wasu kasashen daban daban haka har Yan Bangladesh haka Ambassadors dinsu keyi amma Banda na kasar mu Nigeria Kai ka Isa ya Nemo muku aiki tunaninsa kullum ya danne kudaden talakawa ga inda zai amfanar da Yan kasarsa amma ya kasa, sai dai a kyale talakawa suna shiga kasashe ta gurbatacciyar Hanya Wanda ba a San inda Suka nufa ba suna zuwa suna bata sunan kasar a banza Kuma ga inda aikin jakada yake,kasashen kirki gasu nan suna samowa Yan kasarsu job opportunities daban daban aiki me kyau bana wulankaci ba a wasu kasashen suna tura yan kasarsu marasa aikin yi.

Mahmood dama burinsa ya auri baka duk da cewa Mami Fara ce amma ba irin nasu bane,dama shi baya son baka ko da Yar Africa ce to ace tana da haske shi ta masa, gida irin na larabawa komai yaji a gidan ba abinda babu a Hawa na hudu Mami take sauran duk gidajen larabawa ne Dake dogon building ne sosai, Mami bata Jin larabci sai turanci,shi Kuma Yana Jin turanci, Alwala Suka yi tare da gabatar da Nafeela sukayi adduoi duk da shima balarabe ne Kawai amma baida wani ilimin addini sosai,Kayan ci da sha ya kawo irin nasu na larabawa,Mami Iya gasashen Naman ta iya ci da Madara,Yana bata a baki yana Mika Mata wata tare da furta laban Hajji,Mami tace ta koshi sannan ya kyaleta,wanka ta shiga,daya bedroom din ya koma yayi wankansa a can sai ganinsa tayi ya dawo sanye cikin kayan bacci masu kyau Yana kamshi dama ga larabawa gwanayen turare gashinsa yaji gyara sai sheki yake.

Kallon Mami Kawai yake duk idonsa yayi ja har wani ruwa idon ke fitarwa sai da Mami ta tsorata,daure take da guntun towel ya kasa jira ta shirya,towel din ya fisge tare da yin jifa da shi, ya dauki Mami ya dorata saman bed,bakinta ya laluba ya fara kissing dinta a haukace Yana gurnani har wani shidewa yake,yanda yake bin Mami da tsotsar Boobs dinta kamar zai tsinke Mata su azaba Kawai take ji,shi kuwa ba ji ba gani,Har hakuri take bashi tana cewa please take it easy on me amma Ina sai gurnani yake Kamar zaki sai uban larabci yake ya manta Bata ji ashe masifa yake Mata Wai ya biya Sadakinsa tunda ya saka Mami a sako ya shigeta duk da tana da niima sai da taji zafi kasancewar ta dade rabonta da abin tunda Baffa ya dade bai kwanciya da ita,shi Kuma wannan balaraben Kamar mahaukaci haka yake abu,ba tsayawa Kawai aiki yake,tun Mami tana daurewa har ta gaza su dama yawancinsu Basu san su tsaya ba harijai ne,ya dade Yana Abu Daya sai larabci Kawai ke tashi a dakin Wai yabonta yake,Mami dai ta gaji ta fashe da kuka tana so ta gudu amma ba dama,tuni ta daina turanci shima ya daina sai larabcin dadi ita kuma ta koma Neman agaji da hausarta tana wayyo zai kashe ni,na shiga uku,ga mazaunan Mami sai Mari suke Sha duk sun Dade sunyi jajir, har da Kiran Nawwar ka ceceni ‘ya’yana amma Ina ba kowa,sai da yaji wa Mami rauni sannan bayan ya kawo ya lura amma ko a jikinsa Kawai Alhmdllh yake furtawa yana Jin dadinsa,Mami tana ta kuka sai Kuma yazo ya lallasheta Yana labbata har ta gasa jikinta ya bata magunguna ta Sha ta kwanta sai baccin wahala.

Cikin dare Malam Balarabe sai ya sake dawowa Yana lalubar Mami,Mami da Hausa tace baza ta yarda ba Suka Fara kokawa sai masifa yake da larabci Wai ya biya sadaki,Mami dai taki yarda suna kokawa Kawai ya kifa Mata Mari ta dafe kumatu ya turata ta kwanta har tana bige kanta da karfen gado nan azaba ta sha babu romancing na kirki sai azaba nonuwan Mami sunyi jajir sabo da azaba ga mazaune sunyi ja Suma suna ta Shan mari,haka kamar ran Mami zai fita sabo da yanda yake binta ba sauki duk da ta Saba tayi haihuwa nawa amma wannan balaraben na daban ne Sam Kamar marar Kai haka yake,Yana aiki Mami tace wallahi sai ka sake ni bazan iya ba na Saba da tsohon mijina 30mnt ya kawo,shi yasa idan mace ta Saba da Namiji daya to da salonsa zata Saba idan harijine haka zata Saba,idan ma bai dadewa haka zata Saba,to da guda dayanta ta Saba,tace sai da Nawwar ya fada min wai yaran Zamanin nan Ina suke sanin Kan ta duniya ne gashi ya sani ya fada min naki ji,yayin da Mami take Shan azaba mu Kuwa Muna can Muna Shirin bikin Santana da Jamcy.

Cele suna mota suna tafiya ruwa iska rana duk ta Kare a kansu duk sun fita a hayaccin Yan kwanakin duk sunyi zuru zuru sun rame, Amma a haka har nishadi suke yi suna wake wake da tafi sun kusa shiga Sudan suna bi ta Sahara duk sun Saba da juna duk da cewa wasu matan a ciki maza suna kawo musu hari,Samira ma Saura kadan Mustapha da Awwalu suyi Mata fyade Allah ya kiyaye Agent tace wallahi za a barsu a hanya shine suka samu lafiya Sabo da wasu ma fyade ake musu idan mazan ciki sunfi matan yawa.
Suna Shiga Sudan aka musu check in suka wuce kowa ka gani sai Murna tunaninsu ruwa ta sha,sai da Suka sauka a wata state ta Sudan sannan Agent tace to idan da me kudi sai ku Kama Sana’a har Allah ya kawo lokacin shigar mu Makkah,Cele tace na’am me Kika ce? Kinjini ai ku fito mu tafi Suka firfito da kayansu ta nunawa maza gidan da zasu zauna wani watsatsen gida shima a State din a Kauye suke sabo da wane mutum ba a shigar musu city haka Kawai,gidan maza dakin Dattijai daban dakin matasa daban,haka gidan da Suka je na wata ce wacce itace ogar Agent din da ta taho da su a gidanta aka sauki mata duk a daki daya aka gwamitse su,ga wasu matan da yawan gaske duk an kawo su sunfi wata a gidan suna ta Neman kudi a garin,Cele Allah yasa an iya Neman kudi,kwana uku suna fita suna ganin garin da hausawanmu da yawan gaske sai ta Fara danwaken Siyarwa ta fito da shi sai a warwashe a siye tas ga tsadar tsiya amma haka ake siyewa,kullum sai ta je ta gano lafiyar kaka tace ya dinga Fitowa inda ta kawo danwaken suna siyarwa tare,a cooler take Fitowa da shi dake komai sai da ta siyo dake Africa ne suna da abubuwa da yawa Wanda muma Muna da shi sai dai nasu Dake yankin Sahara ne Kai musu akeyi mutanenmu da Neman kudi, Su Samira sai mamakin kazar kazar din Cele suke Kamar ta San gari Sam a gidan ba a ganinta har wata state din take zuwa sabo da masifar neman kudi,Agent din gaba daya dariya Cele take basu daga zuwa gari sabo da Yar ta kife ce Kamar Yar kasar haka take abu, Hajiya Marwa Agent taga ta dawo da waken suya Kuma da kasko da kayan suyar awara komai dai ta hado,tace Allah de ya biya irinku muke so wallahi Yan ta kife ke ko hutawar ma bakiyi ba daga zuwa kwana goma ke tuni kinyi nisa a sana’a, kuma kina kallon garin Kika San me zakiyi Wanda Kika iya kina da basira,Cele tace gobe ma Sai awara naga har University ce a nan ga hausawanmu nan faca faca ko Ina gobe da Yamma sai awara danwake da safe, Cele washe gari ana gama siyar da danwake ta dawo gida ta yanka awararta ta soya a gida ta zuba a wani botiki ta Kai wajen makarantar duk da nisa Cele tana kaiwa sai kudinta cas ta dawo dauke da Madara ta gari da flavour da komai tana yin wanka tayi Sallah sai tazo tayi Albishir na siyarwa shima makarantar take kaiwa idan zata Kai Awara Mata har maza siye Albishir din nata akeyi,hausawanmu maza Yan makaranta sai son Cele suke kafin kace me Cele tayi suna kowa yace ya sunanta Kawai Cele duk da Cele aka Santa sai samari takeyi amma Ina kudi tazo nema kawai.
Alawar Madara ma yi take ta siyarwa sai Neman kudi takeyi sai da tayi nisa matan da Suka zo Su Samira Suka samu Rufaida Suka ce Cele koya Mana muma sana’ar, Cele da bala’inta tace dake ni na kawoku garin ni wa ya nuna min gari kowa yayi ta kansa ko Ina nake zuwa Kuma ai Kun sani, Yau Awarar Cele da yawa tayi abarta ga shegen tsada amma haka aka siyeta tas ta samu kudi sosai,Albishir ya Kare,Alawar Madara ma haka gidansu ta shigo da kudinta cas tana irgawa a gaban matan gidan sai da ta gama irgawa a gabansu tana wani gadara ta daga rigarta vest ce wacce tun a gida aka Mata aljihu me zip ta saka kudinta,Ogar Agent tace ke a waye kike Kamar kin taba zuwa wata kasar,Cele tace baki ga kalata bane jiki duk shayi tana gyara Riga,dariya sukayi,Cele tace ba time,wanka tayi ta canja doguwar rigar data siya a kasar duk kayansu dama sun wanke su tas, fita tayi ta samu restaurant ita da Kaka ta siya musu abinci me kyau Suka ci abinsu Cele kudinta take ci.

Kowaccensu ta Kama Sana’a suna fama har Suka kwashe wata uku a Sudan Sannan akace su shirya lokacin shigar su Makkah yayi,masu kudi suzo a tafi dasu ta jirgi Wanda basu da kudi Kuma to fa ga mota a hakan ma har ruwa sai an haura ta komi,Cele tace Nawa ne kudin jirgin? Aka fada Mata ta cire nata da na kaka ta bayar, kwashe su aka kaisu can bayan gari waje ne kamar kurkur aka basu uniform ja Riga da wando Kamar yan gidan kaso kowa da number dinsa a jiki a nan ma Sai da Suka kwashe kwanaki sannan ranar da zasu tafi aka fara Kiran number har Cele da Kaka Suka Shige jirgi,na mota ma aka Kira wasu da yawa aka jera su a motoci,Suma kasar akwai kudin da suke karuwa da shi shi yasa suke yarda ana haka ma’aikatan wajen duk Yan kasar Sudan ne.

Cele a jirgi sai zare Ido akeyi da passport dinsu da visa duk an buga musu ta sudan, a hakanma Makkah ta wata state din aka shigar dasu maimakon ta Jiddah sabo da hanyar ta Barauniyar Hanya ce,Cele su a birnin Riyad aka sauke su Kawai aka musu check in duk kudin Aljihun su suke ci a hakan ma, suna fitowa Cele taga birni iya birni ta zazzagi kasar Sudan tas tace ga inda ake arziki tace Kasar da Annabawa sun zauna a cikinta ai ta musamman ce,ga cikamakin Annabawa anan kasar yake,mu Kuwa wanne Annabi ne ya biyo ta kasashenmu,sai masar itama a daban suke map ne ya cuce su ya watso su Africa amma a nan haka suke, akwai wacce aka hada su Cele zata musu jagora zuwa garin Makkah ta fito tace ga Taxi tana jiranmu kuzo muje Suka karasa,Balaraben yace su shiga inda aka Yi rashin sa’a sai kawai Cele ta Fara shiga motar ashe mazane Larabawa a ciki mutum biyu Kawai kafin Kaka ya shiga sunga an rufe motar an fisga a million anyi gaba da Cele ,Kaka ya Fadi ya fashe da kuka Yana shike Nan Jikata ta fada mugun Hannu mene amfanin zuwana Yana ta kuka,Matar da sauran maza da matan hausawa suna bashi baki cewar za a ganta Inshaallah,tace kaga dattijo tashi mu tafi wallahi a state dinnan basa barin baki sai wane da wane sai Wanda ya Isa shike Zama a nan sai ka jawo Mana a kamamu,Kaka Yana kuka yace tunda Naga motar nan baka wuluk glass dinta ma baki wuluk ba a ganin kowa nasan ba Alheri bace wata taxi Suka tare Suka shiga Suka nufi Garin Makkah,Kaka dai cewa yake gwara a kamani a maidani Najeria mene amfanina me Zan iyayi na Sana’a a kasar nan dama da jikata na dogara,wannan zuwa bai min ba shi yasa nace mubi ta Madina garin manzo aka ki ji idan Madina ne su suna kaunar mutane da bako gashi yanzu kun jawo min Ina Zan Sa kaina,sai dai nayi bara Kawai a kasar nan ba wata Sana’a da Zan iya ni bara zanyi na koma almajiri Kaka harda shanye Hannu ya sagale shi yace na koma nakasashe,wani abin idan ya fada dariya ma yake basu.

Cele kuwa tana fara musu ihu tana kururuwa Kawai suka dan hura Mata wani hayaki a Fuska shike nan jikinta ya mutu tana kallon kowa sannan kowa na kallonta duk abinda ake tana gani amma motsi baza ta iya ba ko yatsanta ta gagara motsawa,wani asibiti Suka wuce direct,suna yin waya matar Ahsan Maheerah ta fito sanye da kayan likitocinta tana zuwa da Allurarta cikin sirinji Kawai ta Bude mota Cele tana kallo ta Mata Allurar gaba Daya sai ta koma ganin duhu daga nan bata sake sanin inda take ba,Nurse ta Kira Suka Zo aka dora Cele a kai aka jata cikin asibiti dama duk sun San da zancen dashen cikin da za ayi su tunaninsu ma budurwar da yardarta za ayi tunda ance a kawo wacce ta taba haihuwa biyu ko Uku tasan Kan komai amma Maheera ita tafi son kyakyawar mace Kar a kawo Mata wacce ba me kyau ba ta haifo musu yaro kalarsu duk da cewa tasan balarabe za a haifo tunda maniyyunsu ne,ba ruwanta da yardar mace ta taba haihuwa ko a’a Kawai ita a kamo Mata ko wace,Wanda Suka Yi aikin ta biyasu kudade masu kyau,Ahsan Yana da tausayi da Imani bai San da hakan ba sam,ita dama Maheerah bata ganin bakar fata a mutum ganinsa take a wulakance Kamar ba Allah ne ya halicce shi ba su Kawai sune mutane akidar yahudawa ce da ita.

A nan take likitoci Suka yiwa Cele dashen ciki tunda manniyin Kawai za a shigar cikin mahaifar,sai da Suka Yi aikinsu tare da Maheera itama likitar Mata ce kusan itace ma tayi komai,Wani likita yace amma Yarinyar nan kamar bata taba haihuwa ba Kamar ma bata sex,Maheerah ko a gefen kwalar rigarta ita tunda aiki yayi kyau shike nan,Cele sai da ta kwana tana bacci sannan ta farka taji dai Kamar an taba gabanta amma bata ji zafi ba,jikinta duk ta jishi wani iri ba yanda ta Saba Jin kanta ba,Wata nurse ce ta shigo ta iske ta tashi brush ta kawo Mata da toothpaste sababbi ta Shiga toilet tayi wanka da sabulun da aka bata Malam toilet tsabar tsafta Kamar ta gidanka,ta fito bayan tayi Alwala a saman tiles din ta kalli inda taga dama Kawai ta Fara rama sallolinta kaf Wanda tasan ana binta tun daga lokacin da tabar su Kaka,tana idar da Sallar gaba daya Kaka ya dawo Mata komai ya dawo kanta nan take ta fashe da kuka wiwi, Tambayarta nurse din tayi zata ci abinci da turanci Cele ma ba turanci take ji ba larabci take ji ba sai hausa sai Dan turancin data tsinta a bakin mutane ba uwar data sani ba karatu tayi ba iyakarta primary sai zunzurutun ilimin addini dake kanta,bata magana ga uwar yunwa tana ji aka kawo Mata shayi a Dan wani mitsil din glass cup bai fi kurba daya ba,sai kayan marmari a cikin wata roba anyi seiling nata,sai gurasa guda biyu da wani naman kaza Quarter sai shinkafa ta sha wasu irin kayan lambu kuma gata fara ko maiko babu sai Albasa Rabin guda ba yankawa ba komai a wanke,sai salat Kawai gindin aka yanke aka wanke ba yankawa sai chili pepper green guda biyu Zako zako Wai a haka zaka ci nan a haka sabo da an San Yar Africa ce aka Mata haka,harda lemon mango a wata kwalaba me kauri ba ma roba ko kwali ba,Cele bata fiye cin abinci da yawa ba amma duk da haka rainawa tayi ta daga Dan kofin shayin ta Masa kurba daya ta juye shi a bakinta ta hadiye.

Gurasar ta dauka tana masifa aikin banza Ina bredi ta dinga hada kazar da gurasar ta cinye,Yar shinkafar Yar kadan a wani container ta cinye nanma ta Sha fruits din ta shanye lemon ta shanye ruwan sai da ta cinye komai tas ta koma saman gadon sai bacci,da rana ma aka sake kawo wasu Kalar abincin,da dare ma harda tsiren larabawa na kaza a jikin tsinken karfen farko an saka zallar tsokar kaza sai na biyu katon tumatur a gaba kaza gabanta wani sweet pepper green,gabansa kaza gabansa wani yellow sweet pepper,gabansa kaza gaba katuwar albasa gaba katon green chili pepper,gaba kaza gaban red pepper sai Albasa katuwa sai kaza again haka yake a tsinken,sai wani Cheaps da kwai,Cele tace Kaka Allah sarki ta Fara hawaye tana cinyewa ta kwanta,sai da Cele tayi sati guda a asibiti sannan aka shigar da ita wata na’ura bata San Mene ba Suka tabbatar dansu a cikinta ma yayi nisa aiki yayi kyau,ita Cele taga ana ta taya Maheerah murna ana Mata congratulations da larabci, da Yamma bayan ta tashi a aiki mijinta Ahsan matashi hadadden gaske yazo daukanta a mota tace Cele ta fito tana harararta ta fisgo hannunta dama kayanta babu su kafin Kaka ya sa kayan a mota Suka sace ta,Ahsan ya dan kalleta kadan tunaninsa da yardata tana fada Masa aiki yayi kyau suna ta murna Suna Hira da larabci,Cele Kuwa ta zuba Masa Ido tunda take bata taba ganin balarabe har a tv bata taba ganin me kyansa ba ga iya wanka sai kamshi yake fitarwa na musamman gashinsa wani irin gyara aka masa Kamar Dan kasar amurka ,Kuma yau ba Jallabiya ya saka ba kana nan Kaya ne a jikinsa na Yan gayu tace a ranta ashe larabawa Suma suna swagg,Bayan motar Maheerah ta tura Cele tana harararta ta Shiga ta rufe sannan ta koma gaban mota ta zauna sai kissing din juna suke Yana tambayarta ya aikin tana Masa shagwaba ta gaji ita,wani shopping mall cele taga sun tsaya ta fito ta fisgo hannun Cele ta fito tana janta suka shiga ciki,Ahsan Yana Mata fada ta daina haka ba kyau,Abayoyi ta zabo wa Cele dai dai da ita masu kyau sunfi kala goma,da takalma flat Wai sabo da cikinsu baza ta sa me tudu ba,ta siyo har su kayan kwalliya dai body lotion da sauran duk takarkace na Mata har su Inners da kayan bacci komai an siya mata Kawai hand bag ce bata siya mata ba, wai ba inda Zan fita ai,har pakistain Ahsan ya siyawa Cele kala biyar masu kyau harda Riga da skert irin na larabawa kyawawa ganin Cele tana k kallonsu sun birgeta sai Kawai ya siya mata,duk abinda yaga Cele tana ta kallo sai ya siya mata,taga wani cup kato plactic Kuma na roba Amma design tace wannan da shi zan dinga Shan shayi,Ahsan yaji ta ambaci shayi tana daga cup din ya dinga dariya Yana mamaki ya kalli Cele yace Shay? ta daga Masa Kai ya dakko mata aka hada da cup din Suka je aka biya kudi Suka Shiga mota sai gidansu,Cele taga Aljannar duniya duk da su basuyin gida irin namu mutum ya shati fili Kawai yayi ginin da yaga dama su ba haka bane, Amma gidansu ya tsaru kana gani kasan me kudi ne tun daga layin da suke da kalolin gidajen dake yankin,gidaje ne Wanda basu fi hawa daya ba,Steps din benen ta wajen compound din yake sai ka bi ta nan sannan ka Shiga aihin gidan ma, compound Kuma harda parking space ko Ina yaji kayan alatu da flowers ado irin na larabawa, katon Palo ne na gaske yaji alatu an shirya Masa Aljannar duniya komai na ciki me tsada ne sababbi kuma kasancewar duk gaf da Ramadan ake canja kayan daki har cokali sai an canja latest duk shekara shima gidan sai an sake Masa sabon salon gyara,Sanyin ac Kawai ke tashi da wani kamshi,Yar aikinsu Yar bangaladesh me suna Ayusha tana ta aikinta ta Gama shirya dining abinda suke so ake dafa musu,Nan Cele taga asara Maheerah ce ta kalli abincin iri iri ta ja Dan ja tsuka tace taji yanzu bata son ci baza su ci ba,Ahsan ma yace abinda take so,dama su mazan su masu hankalin bautar Mata suke Yi kullum a wahala suke da matansu,Cele tana gani aka tattara abincin tas aka juye a Leda aka jefa a dustbin,Ayusha ta shiga kitchen itama Ayusha dake Yar waje ce har da wani kyamar Cele tana Mata wani kallon banza,Ahsan ne ya fito cikin Jallabiya fara yayi wanka ya shirya gata fitted inda ya bar Cele a tsaye haka ya sake fitowa bayan yayi wanka ya sameta a haka duk rashin kunyar Cele ta kasa cewa komai bakinta ya mutu,Ahsan kafadunta ya dafa da hannayensa biyu ya zaunar da ita a saman kujera Yana Mata murmushi, to dalilin Islamiyya dai ta gane da ya tambayeta sunanta tace Rufaida da Hausa Kuma ta fara Masa kwatance tana nuna gefen kofa tana cewa Nigeria Ismi Cele,Yace Cele da karyanyan harshensa yanda ya fada sai da ya bata dariya ta murmusa tare da daga masa kai da hausarta tace ae acan Nigeria Ismi Cele,Kai ya jinjina ya gane,Maheerah ce ta fito itama ta Sha wanka ta hade cikin wasu matsiyatan Kaya Ashe a gidansu kusan tsirara suke yawo Amma a waje sai ka gansu da Abaya da nikaf, wani mini skert ta saka na jean da Yar top me spaghetti hand Rabin nononuwanta duk a waje,tana da kiba Cele ta fita kyan diri nesa ba kusa har kyawun Fuska ma Sai ka zabi Cele baka zabe ta ba,hakoranta duk sunyi tsatsa sabo da mugun Shan Shan Zaki sunyi wani iri sun ciccinye dama basu fiye kyawun hakora ba,Ahsan kuwa kamar baya Shan zaki hakoransa farare tas kanana masu kyau shi Kam ta ko Ina Allah ya Masa baiwa,Tv ta kunna ta kamo wakokin larabawa masu rawa da gashi,Shi kuwa Laptop dinsa ya dauka kamfanin iPhone yana amfani da ita ya harde kafafu tana saman cinyarsa ga shayin Gahwa Yana korawa itama Maheerah shayin take Sha suna jiran abincin da suka ce Ayusha ta dafa yanzu,su dama masu kishi Basu barin Yar aiki ta zauna da wasu Kaya sai abaya Kuma Dole ta sa nikam a haka take musu aiki tana gamawa Kuma bata kwanar musu a gida sai dai ta tafi masaukinta da safe da wuri take zuwa kafin su fita ana yin Sallar asuba take zuwa haka Ayusha ma take Yi amma suna biyanta sosai ba mugunta,ba irin mu ba ki dauki yarki tayi ta wahala kina wulakantata yaran gida suna ci Mata mutunci gata kullum cikin wahala kina saka sutura me tsada dinki ma ki kasa Mata ko Yar Atamfa sai dai tayi ta Zama cikin tsumma,ta wanke kashin yaranki etc ki dauki dubu biyu ki bata a wata abin haushin har gidan manyan masu kudin Babu canjin albashi sai dai daiku.

Cele tana Jin Kiran Sallah ta mike tace Salah,Maheerah ko kallonta bata yi ba Kawai tv take kallo,Ahsan ne ya nuna Mata dakinta har kayan da Suka siyo Mata shi ya tashi ya dauka ya Kai Mata dakin da Suka bata a matsayin nata,dakin yasha gyara,gado ne irin na larabawa na karfe amma designers ce har mudubin na daban ne kalar bed din sai wani slice Sip kana danna wani Abu zaka ga ya bude da kansa,harda katuwar plasma tv dinta,Cele tace ya ihali mutanen nan me suke nufi dani ne,tunaninta ma suman da tayi a mota ne yasa aka kaita asibiti Suka taimaketa.

A cikin toilet dinta tayi wanka ta fito tare da daura Alwala ta shimfida sallayar data gani Fitowa tayi tace Qibla,Ahsan ya taso ya nuna Mata tayi Sallar magriba shi Kuma ya fice masallaci Maheerah tana nan a zaune tana kallon wakoki,Ayusha ma tayi Sallah Banda Maheerah,Ahsan ya dawo Yana ta Mata fada Amma sai ta Fara kukan shagwaba Wai ya takura Mata ita wahala take Sha a gidansa,ya shiga lallabata Yana bata hakuri,Cele Kuwa Fitowa tayi tace bari naje Palo na Sha kallon haukar Maheerah,ta fito ta isketa tana ta hawaye tana kuka kanta a bisa kafadar Ahsan Yana aikin lallashi,dariya ta kama Cele ta dinga kyalkyala dariya tace Yasin da a Nigeria kike da kinci ubanki hannun mazan mu da tuni kinci duka uwarki aka Miki yau naga Yar iskar Mata shegen Kai kamar turmi,ita a larabawan ma cutar Mijinta aka Yi hakora duk cin Zuma Kamar tsohuwar langa, Ahsan Jin tana ta maganganu tana kallonsu da yarena ya tambaye ta da hannu Wai lafiya? Dariya tayi tace da hausa nace wannan Yar iskar matar taka ce ta nuna Maheerah da baki ya kalli Cele yayi Murmushi harda sa min yatsa a lips dinsa Wai shiiiii nayi shuru Kar na takurawa Maheerah,Baki cele ta bude tace an gaisheka Alhaji salmanu Sallamamme ko Alhaji Sallau ne,kaga mijin tace,ya sake tambaya da hannu Wai me nace? Tace ubanka nace Sallamamme baza ka Zama Namiji ba ta gwada Masa yanda ake Marin mutum da zancen kurame tana zuga shi tace ya mareta, kafada ya makale,Cele tace yau Naga dolon mutum ni Rufaida.

 

Ayi min sharhi yafi min godiya.

MASU JUYA LITTAFI AUDIO BA IZINI BADA YAWUNA BA,NA RIGA NA SIYAR DA SHI.

Masu bukatar sauraren Audio book dina ku duba YouTube channel
S ZARIA TV

Click Here To Read Chapter 6-10

https://chat.whatsapp.com/Dk4tpug5deM85rvWdb7KIR

 

AsmaBaffa
08061929616

Back to top button