Hausa novels

Halysaah Page 128 By Khaleesat Haydar

HALYSAAH PAGE 128…Karfe tara da rabi Khaleesat ta shigo wajen Aunty Farida tana sanye da hijab har kasa zata yi mata sai da safe, kana kallonta zaka yi tunanin she is sleepy by mere looking at her eyes, nan kuwa ba baccin take ji ba, Aunty Farida tace “Kin ci abinci ne?” A hankali Khaleesat ta gyada kai tace “Na ci” Aunty Farida tace “To ga fruits” Ta girgiza kai tace “Na koshi” Aunty Farida ta nuna mata ledan dake kusa da akwatinta tace “Hajiya Zaliha ta bada a kawo maki sakon can” Khaleesat ta karasa wajen ta duka zata dau ledan taji sallaman Ajay baki kofar dakin, kawai ji tayi gabanta ya fadi ga wani tashi da tsikar jikinta yake, ya karaso cikin dakin bayan Aunty Farida ta amsa sallaman sa, yace “Sai da safe Aunty, hope baki bukatar komai?” Aunty Farida tace “A’a ba abinda nake bukata Junaid, Allah ya tashe mu lafiya” Yace “Ameen” Juyawa yayi ya fita daga dakin, sai a sannan Khaleesat ta dago ta koma ta zauna inda take zaune, a hankali take bude ledan taga hadaddun turarruka ne na humra da oil perf, tun bata bude su ba kamshin ya gama gauraye ko ina na dakin, dama tun safe take ta jin wani kamshin a dakin ashe wa ennan turaren ne suka cika ko ina, ta ɗan yi murmushi tace “Nagode sosai, zan mata godiya ta WhatsApp, muna chatting once a while da ita” Mayar da turarurrukan tayi cikin leda zata mike Aunty Farida dake kallonta tace “Ba bangaren mijinki za ki ba, sai ki shafa turaren ai” Nan da nan ɗan fara’an dake fuskar Khaleesat yayi escaping, ta ɗan kalli Aunty Farida dake ta kallonta, hakan yasa ta bude turaren ta shafa kadan a hannu ta goga a hijab dinta, Aunty Farida tace “Dama ance maki na kaya ne ko baki da hankali ne?” Khaleesat dai bata ce komai ba, Aunty Farida tace “Cire Hijab din” Ba musu ta cire hijab din, doguwar rigan bacci ne jikinta da ya wuce gwiwa, sanin babu inda zata je sai dakinta ta shafa turarurrukan sosai a jikinta sannan ta maida Hijab dinta, bata kara minti biyar a dakin ba tayi ma Aunty Farida sai da safe ta koma dakin da take ta cire Hijab dinta ta kwanta bayan ta kara AC din dakin don ita kadai tasan abinda take ji a jikinta kuma har yafi yanda take ji daxu. Khaleesat na kwance wajen karfe sha daya taji an bude kofar dakinta, sosai taji gabanta ya fadi, amma taki juyawa taga wanda ya bude kofar cause she is backing the door, gabanta ya dinga faduwa after imagining Ajay ne, jin an kulle kofar yasa ta juya da sauri, Aunty Farida ta gani hakan yasa ta mike zaune tana gyara hulan kanta ta sunkuyar da kai, Aunty Farida ta nufeta tana kallonta cikin nutsuwa ta kwantar da murya tace “Khaleesat ki gaya min menene matsalar ki da Junaid? Kar ki boye min komai ki gaya min gaskiya” Khaleesat dai ta ki dago kanta tayi shiru, Aunty Farida tace “Ina sauraron ki dota, ko kina da wanda zaki gaya ma matsalar ki da ya wuce Umma ko ni?” Hawaye ya cika idon Khaleesat, cikin sanyin murya tace “To Aunty ai ni ban ce ina son sa ba aka aura min shi fa” Calmly Aunty Farida tace “To shi cewa yayi yana sonki da aka aura masa ke Khaleesat? Shi ma ae bai ce yana so ba” Khaleesat na goge idonta tace “To tunda ba ma son juna ba sai ya rabu da ni ba, ni kallon yaya da kuma Friend dina kawai nake masa” Still speaking calmly Aunty Farida tace “Idan ya rabu da ke kuma sai ayi yaya kenan Khaleesat?” A hankali tace “Sai in auri wanda nake so” Aunty Farida ta gyada kai ta kara kwantar da murya tace “To wanene wanda kike son?” Hawaye sosai ke sauka idon Khaleesat taki cewa komai, Aunty Farida tace “Jawwad ko?” Khaleesat ta fashe da kuka a hankali tana gyada mata kai, kawai jin saukan wani wawan mari tayi a fuskarta, bata gama recovering ba Aunty Farida ta kara mata wani lafiyayyen marin, gigicewa tayi ta dafe duk kuncinta ta fashe da kuka sosai zata sauka daga kan gadon ta daya side din Aunty Farida ta fincikota ta gwabje bakinta tana huci tace “Mahaukaciyar banza kawai shashasha gantalalliya warce bata san ciwon kanta ba, dama jira nake mu kai karshen zancen kafin in ci ubanki, mu za ki kunyata ki tozarta? Tarbiyyar da aka maki kenan a gida? To je ki auri Jawwad din don ubanki tunda ke karya ce mara zuciya warce bata san darajan iyayenta ba balle nata, banda kaddara ke har kin kai class din Junaid kike tunani da har zaki ce baki son sa? Uban me zai yi da ke banda shi din me biyayya ne ga ubansa? Wallahi yafi karfin ki ta ko ina, kuma aurenki da Junaid yayi babban taimako ne gare ki da rufin asirin ki, amma har kike da shegen bakin da zaki bude kice baki son aurensa, ko Jawwad din ne mijinki bazai taɓa iyawa da mugayen halayyarki ba yanda yake da zuciya haka, ni yanxu na ma dena ganin laifin azabtar da ke da Abdul yayi a gidansa, don Allah kadai yasan abinda kike masa lokacin, to bari ki ji in gaya maki takanas na shirya na taho America don in lallasa ki, kafin ki tona mana asiri gwara in karya ki, Muna zaune wata mata ta zo gida ta tada mana iska ta zayyano mana duk zaman da kike da mijinki nace zan kuwa zo in gyara maki zama tunda shi Junaid din yaki fada mana cin mutuncin da kike masa, kuma in baki yi hankali ba kan in bar kasar nan sai na maki shegen duka wallahi” Kuka kawai Khaleesat take kamar an aikota tana bubbuga kafa kamar wata er yarinya, a fusace Aunty Farida tace “Ohh daman kuka kika samu??” Gun Charger din laptop dinta ta nufa da sauri, Khaleesat na ganin haka ta fice daga dakin da gudu bata tsaya ko ina ba sai bangaren Ajay, yana zaune kan kujera a Bedroom dinsa yana kallon wani Movie a Plasma dake dakin, hannunsa rike da cup din Coffee da yayi making a nan dakin da kettle, sai gata ta shigo har cikin dakin ganin baya parlor, ta zube masa kasan carpet ta rushe da wani matsanancin kuka, ajiye cup din hannunsa yayi ya mike da sauri ya nufeta ya duka gabanta holding on to her shoulder yace “Kee, What happened? Me ya faru?” Jinin da ya gani kwance gefen lips dinta da fuskarta da yayi ja saboda marin da Aunty Farida ta lallafta mata yasa yayi shiru yana kallonta baya ko kiftawa, babu abinda ya fado ransa sai ranan da ta kirasa a waya tana kuka yaje kofar gidan Maman Fu’ad a Hotoro ya sameta ta fito fuskarta da shatin marin da Abdul yayi mata sannan jini ya kwanta idonta…. Sauke idonsa yayi bai ce komai ba don ya riga ya gane ita da Aunty Farida ce, baƙin ciki da takaici ya sa Khaleesat ta kara sautin kukan da take yi ganin yaki ce mata komai, bata san sanda ta tura hannunsa daga shoulder dinta ba a fusace tace “Idan baza ka ce min komai ba ka dena kallona” Tana fadin haka ta mike tana kara sautin kukanta zata tafi kan kujera tayi ball da cup din tea da ya ajiye bata sani ba, wani ƙara tayi ta zaro ido tana yarfe hannu tace “Wayyo kafana, na shiga uku….” Lokaci daya ya mike ya tafi kusa da ita da sauri yana kallon kafar yaga coffee din ya zubar mata a kafar, ya ja ta zuwa bandaki ya kunna pampo ya tara kafar a bakin tap din, gaba daya ta cika masa kunne da kuka kamar wata yarinya, kawai gani tayi ya dauketa bayan ya gama wanke kafar suka fita daga bandakin, nan da nan ta dena kukan da take ta turo baki tace “Ni ka saukeni” Bai ajiyeta ko ina ba sai saman gadonsa ya hade rai yace “Zaki sha mari” Gaban mirror dinsa ya tafi ya dauko ointment ya dawo ya duka gabanta sannan ya bude ointment din yana kallon kafarta, gently ya fara shafa mata salve din in a circular motion a dai dai inda ruwan shayin ya zuba, tayi saurin janye kafarta jin kamar an hadata da electric tsabar wani irin shock da taji, ta fara komawa baya a hankali tace “A’a ni bana soo” Ya wani hade rai yace “Ina wasa da ke ne?” Hawa saman gadon yayi ya fixgo kafarta, tayi saurin hade laps dinta waje daya kar taje ya ga inner wear dinta, bai ma san tana yi ba don idonsa na kan kafarta da yake shafa ma ointment din, a hankali ta koma ta rufe fuskarta da pillow still joining her laps tightly together, har sannan kuma bata dena jin shock da take ji ba, can ya ɗaga kai ya kalleta ganin yanda take yi da laps dinta, ya dinga kallon laps din…. Wani ƙara Khaleesat tayi ta bude ido da sauri jin hannunsa a lap dinta, ya daure fuska yace “Har nan shayin ya zuba ne?” Bata tsaya basa amsa ba ta fara kokarin sauka daga kan gadon da sauri don ta tsorata, yayi hanzarin fixgota ya mayar da ita ya kwantar yana kallon kwayar idanuwanta, nan da nan ta gigice masa ganin wai lap din zai yi separating tace “Nooo, don Allah ka bari mana, wallahi ba abinda ya zuba a nan, don Allah stop it, ta ya shayi zai zuba nan??” Yana kallonta da idanuwansa da suka koma lumsassu cikin husky voice yace “Ta sama” kunya yasa taki yarda su hada ido ta fara masa magiyan ita ba komai a laps dinta amma duk magiyanta bai sa ya fasa abinda yayi niyya ba don sai da yayi, ai ko tayi saurin rungumosa jikinta taki basa access din ganin abinda yake son gani, hakan da tayi yasa kirjinta yayi distracting dinsa daga can, cikin zafin nama ya sauke rigar kasa, jikinta ya dau rawa ta fara rokonsa wai zata je bandaki, amma ko sanin abinda take cewa bai yi ba, outburst dinta ma sai yafi nasa a wajen…..*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah, ur evidence via 07087865788*

Back to top button