Hausa novels

Halysaah Page 148 By Khaleesat Haydar

HALYSAAH PAGE 148…Khaleesat na kishingide tama repiving message din da Safiyyah tayi mata tun safe, nwa take i sosal amma duk abinda ta kal bakinta sai taji sa kamar magani, ga dal abinci iri ini da aka cika mata amma duk basu da dadi a bakinta sai watermelon kawai take ta sha, ta daga kai a hankali jin an bude kofar dakin, ajiye wayar hannunta tayi da mamaki tana kallon Noor babu ko kiftawa, Noor ta tafi da sauri ta rungumeta cike da farin cikin ganinta tace “Aunty” Khaleesat na gyars kwanciyarta har sannan mamaki kwance fuskarta tace “Ke da wa ku ka zo Noor?” Noor na murmushi ta zauna gefenta lace “Ni da Nenne da Aunty Murja” Khaleesat ta zaro ido tace “Yau ku ka zo ko yaushe?” Noor tace “A’a 3 days ago muka zo, muna gidan Aunty Murja all this while” Khaleesat felt so happy seeing her sister, amma kuma deep down bata so zuwan su tana cikin halin da take ciki ba, gashi ko zama sai ta daure take iya yi, a hankali ta kamo hannun tace “Umman mu fa?” Noor tace “L tana gida Khaleesat tace “Baba yace a gaisneni?” Noor na murmushi ta gyada máta kai, Khaleesat tace “Islam kuma taki ta biyo ku ko?” Noor tayi dariya tace “Tace ita bazata je ba” Khaleesat ta jawota jikinta tace “How about Aunty Farida?” Noor tace “She is at home too” Nenne ce ta shigo dakin da Aunty Murja, Khaleesat tayi murmushi tana kallon Nenne tace “Shi ne baku ce min za ku zo ba Nenne” Nenne ta zauna kan Carpet tace “Meye hadin biri da gada Khaleesah, ni wajen Murja na zo duba mara lafiya, tana ta yawo gwanin sha’awa a keker guragu da Mijinki ya siya mata me tsada irin na kasar waje wallahi, kamar ma keken da kansa yake tafiya fa” Khaleesat ta sauke kai bata ce komai ba, nan da nan mood dinta ya canza bayan Nenne ta ambato mata Ajay, Nenne dai ta ci gaba da bada labarin keken yarinyar Aunty Murja da kuma uwar kudin da Ajay ya bada a dinga kula da lafiyan yarinyar, gashi yarinyar ta dawo fes da ita kamar ba me lalura ba, To cut the conversation Khaleesat ta kalli Aunty Murja dake ta murmushi tace “Aunty ya Aunty Murja tace “Alhamdulillah Khale Ina ta son zuwa amma ban san ko kun dawo daga Amurkan ba, sai da Nenne ta zo take gaya min ai kun dawo tuntuni…” Khaleesat ta dan yi murmushi tana wasa da duvet din jikinta, Nenne tace “Ni banda ma Murja ta hadani da Allah mu taho mu duba ki ai baza ki gan mu a gidan nan ba Khaleesat, mun ma yi ta kiran mijinki daxu bamu samesa a waya ba, ashe ma baki ji dadi ba yanxu Hajiya ke gaya mana ai baki da lafiya” Ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Nenne tayi kasa da murya tace “To me yake damunki? Na ma ga kin yi kyau kin kara haske, idanuwanki ne dai suka fada” Sai kuma ta kalli Noor tace “Ke Noor tafi parlor tunda kun gaisa mu ma yanxu za mu fito” Mikewa Noor tayi ta nufi kofa ta fita daga dakin ta kulle kofar, Nenne ta kara yin kasa da murya tace “Ko ciki ne da ke?” Khaleesat ta hade rai taki bata amsa, Nenne tace “Ba hade rai ba ki bude baki ki min magana don duk nasan halin da kike ciki tunda ke munafuka ce algunguma warce bata san ciwon kanta ba, yanxu idan baki gaya ma İyayen da suka haife ki matsalarki ba uban wa gare ki a duniya da zaki gaya ma? To da yake wannan kawar taki er albarka c ta gaya min halin da kike ciki tun aurki na farko ashe dalilin mutuwan auren kenan ma, mu zaki tona ma asiri wancan kin yi shiru an sako ki duk da gantalallen aure ne kuma sakin shi ne mafi alheri, wannan kuma auren da kowa ke alfahari da shi shima so kike ki kashesa? Ina batun aure babu kwanciya? Aure tsawon wata shidda amma haka Yariman ke kallonki shi bai gaya mana matsalar ki ba don shi din yaro ne me kunya da nutsuwa, ke kuma mahaukaciya kin ki magana mu san na yi? to bamu haifi er da zata tona mana asiri a duniya ba, don haka ga nan magunguna a jakana babu inda ban shiga ba da taimakon uban kishiyar Murja mun nemo maki taimako, an kuma tabbatar mana asiri ne a jikin ki shi yasa hakan ke faruwa, duk ma wanda yayi maki wannan asiri kina fara maganin zai koma kansa, tun da na shigo garin nan ban zauna ba sai fafutukan nema maki mafita nake duk ranan garin ya babbake min fuska, yanxu dakin naki ne nan? Sai ki samu akwati ki saka magungunan a ciki kar ayi tunanin wani mugun abu na kawo maki masarauta?” Khaleesat da har sannan fuskarta ke daure tace “Ni ba dakina bane nan” Hajja tace “Dakin waye nan din?” Khaleesat ta kai tace “Bangaren Hajja ne gaba daya Nenne ta ja bakinta ta tsuke tana rarraba Ido jin abinda Khaleesat tace, can dai kuma ta kara cewa “To babu wannan kamaran da masu kudi ke sakawa ya nannade maganar mutane?” Khaleesat ta girgiza mata kal, Nenne tace “Ba kuma abun in ce ki tashi mu je bangarenki ba ayi tunanin wani abu na kawo maki, ae da sai mu koma sashin ki tunda mun gaisheta” Khaleesat tace “Bani da lafiya ai shi yasa nake nan” Nenne tayi kasa da murya sosai tace “To ni dai ban san yanda zanyi da itatuwan nan ba, ban san yanda zan damka maki a hannu ba ki fara amfani da su cikin gaggawa, ba aburi in bude jakar ba ma yanxu aji kamshinsu a zata wani asiri ne” a hankali Khaleesat tace “Duk ranan da za ku koma Kano ai sai inje gidan Aunty Murja in maku sallama sai ki bani a can” Nenne ta hade girar sama da ta kasa tace “Ni da nake son in ga aikin maganin kafin in tafi? Ai sai naga kamun ludayin lamarin zan bar garin nan, Sai dai in kin zo da sunan yi mana sallama sai in baki sannan in zauna har sai naji yaya ake ciki idan kika yi amfani da su, don gaskiya wannan babban magana ce ba karam wallahi ko bacci ban yi ba ranan da Safiym ta gaya min, ana idar da sallah na sa Malarn Ali ya goyani a machine sai tasha, kin san ya siya machine sabuwa dal Khaleesat ta dan yi murmashi tace “Da gaske Nenne?” Nenne tace “Al Malam Ali Alhamdulillahi yanxu, kasuwancinsa na ta bunkasa a sannu sannu” Khaleesat tayi shiru, nan ta fara tunanin ba ma Abban nata miliyan goma daga cikin account dinta ya kara jari, don kudaden ciki yanxu sun yi 16M, a hankali tace “Nima in sha Allah zan zo Kano, ko kuma in bi ki mu koma tare” Nenne ta hade rai tace “Ki zo ki mana uban me, in ba jinyan laulayin ciki zai kawo ki ba babu shegen dake bukatar ki a Kano a yanxu dai” Khaleesat ta dinga kallon Nenne, Nenne tace “To shikenan tunda mun gaisa kuma kince zaki je can gidan bari mu tashi kawai mu tafi, kar a ga mun dade cikin dakin” Daga haka ta mike tana gyara yafin gyalenta tace “To tashi ki mana rakiya ko?” Khaleesat tayi shiru, Aunty Murja tace “Nenne a kwance fa muka sameta ba lafiya, mu yi tafiyarmu kawai in ta samu sauki sai taje can gidan namu” Nenne ta tabe baki ta nufi kofa, Aunty Murja tayi ma Khaleesat sallama sa murmushi ta bi bayan Nenne, Khai ta sauke idonta jin hawaye ya fara taruwa idon, a nake su zsunty murje suka lite uaja dakin, Hajja na parlor har sannan da Noor a gefenta tana cin Apple din da Hajja ta sa ta dauka, tana ganin sun fito ta mike ta koma wajen yayarta a daki, Hajja na kallonsu Wenne tace “Madallah har kun fito” Nenne tace “Mun fito ranki shi dade, unguwanmu da nisa shi ne nace gwara mu kama hanya da wuri kar yamma yayi mana a hanya” Hajja tace “A’a ba kwana biyu ku ka zo yi mana ba dama” Nenne na murmushi tace “Daga mu sai kayan jikinmu fa ranki shi dade, dama ziyara ce kawai ba wani abu ba” Hajja tace “Ikon Allah, duk tunanina za ku mana kwana biyu, amma ya kamata gaskiya ku dawo da shirin kwana” Nenne tace “Gaskiya ne Ranki shi dade” Daga part din Hajja masu aiki suka yi ma Nenne da Aunty Murja rakiya zuwa bangaren Mami don can aka kai masu abinci, nan din ma Nenne tace a koshe suke iya fruits kawai suka sha sai su alkaki da dublan da suka ci, ba yanda Mami bata yi dasu su ci abinci ba suka ki. Bayan sun yi sallan la’asar Mami tace “Ai Yariman ma ba shi da lafiya Hajiya, shi yasa ma zo gaishe ku ba yana can kwance sh Nenne tace “Subhanallahi, ai kuwa daxu nasa Murja ta kirasa ta sanar masa za mu shigo Gidan Sarki don hatta ita Khaleesat din bata san da zuwan mu ba wallahi, to Murja bata samesa a waya ba ashe bai da Isfiya bawan Allah” Mami tace “Wallahi kam bal ji dadi ba” Nenne tace “To Allah (Ubangiji ya basa lafiya, Allah ya sa kaffara ne” Marni tace “Ameen, bari in raka ku can bangaren nasa sai kuyi masa sannu” Nenne tace “Eh gaskiya kam ya kamata” Mami ta rakasu har part din Ajay suka zauna babban parlor, ita kuma ta karasa cikin Parlonsa, zaune ta samesa yana shan fruit ga darduma a shimfide parlon alamar sallah ya idar, he looks much better akan few hours ago, tace “Ka tashi baccin Junaid?” Ya sauke idonsa yace “Na tashi” Tace “Ya jikin fa?” Yace “Da sauki” Mami tace “Kakar Halysaah ce suka zo, ka fito ku gaisa za su koma ne yanxu” Ajay ya daga kai da sauri ya kalli Mami, ko me ya tuna sai kuma yayi maza ya sauke kai bayan sun hada ido, Mami na kula da tun safe yaki yarda ya hada ido da ita yanxun ma by mistake hakan ya faru, yayi kasa da murya yace “Mami ko dai ka kice ina bacci” Mami ta kallesa daga har kasa tace “Ko ba bacci ba, dalia tashi mu fita Malam, gida za su koma, Drivern da zai maida su ma na jira a waje” Ajay bai ce komai ba kuma bai dago kansa ba, Mami ta juya ta fita ta koma can wajensu Nenne, da kyar Ajay ya mike ya fita daga Parlonsa, yana shiga Main parlor ya zauna kan Carpet yana gaida Nenne da Aunty Murja kansa a kasa, Nenne ta amsa cike da damuwa tace “Sannu Ahmad, ashe baka ji dadi ba, Allah Ubangiji ya baka lafiya ya sa kaffara ne” Bai dago kansa ba yace “Ameen Kaka” Aunty Murja ma tayi masa fatan samun sauki, yace “Ameen, ya Jeeddah fa” Aunty Murja na murmushi tace “Tana nan lafiya wallahi Yarima” Basu fi minti biyar a part din Ajay ba Mami ta mayar da su bangaren Hajja za su mata sallama, tsadaddun atamfofi biyar Hajja ta sa aka debo ma su, sai turarurruka kusan kala goma, sannan ta hada da dubu dari a kan kayan, ta kuma dage in dai za su bar Bauchi su zo ayi sallama, Nenne dai sai godiya take mata haka ma Aunty Murja, Mami na kallon Nenne tace “Tunda za ku kara kwanaki a Bauchi ai da kun bar takwaran Hajja wajen yayarta tayi mata kwana biyu” Hajja tace “Gaskiya kam, ma naga ai duk anyi hutun makaranta Baby ma yau aka je daukota daga makarantar su, kilan ma sun kusa yanzu haka” Nenne tace “To shikenan ranki shi dade sai ta zauna din har zuwa sanda za mu koma in sha Allahu” A haka Mami tayi ma su Nenne rakiya zuwa gun mota….. Maganganu ne fal cikin Nenne amma ba daman yi, har sai da suka bar gidan a motar da zai maida su gidan Aunty Murja sannan ta kalli Aunty Murja tayi kasa da murya tace “Ke Murja wannan matar da ta mana rakiya fa kamar Uwar Jawwad ce in dal ba idona ke yaudarata ba, har gida fa tayi gayya suka je suka ci mana mutunci babu abinda suka mance basu gaya mana ba daga karshe tace dan ta bazai auri Bazawara ba, muka ci kukan mu muka gode Allah, to sai kuma gashi naga mun zo…..” Da sauri Aunty Murja tayi ma Nenne alamar tayi shiru ga dreba, Nenne tayi maza ta rufe bakinta tana zare ido, bata sake cewa komai ba a motar, amma fa kanta ya gama kullewa ganin irin tarban da Mami tayi masu, duk da a farko ta ma kasa hada ido da su, to ko dai kawai kamanni ne. Bayan tafiyarsu Nenne Dr din dake duba Khaleesat ta zo ta d tayi mata injections dinta sannan ta wajen karfe biyar Hajja ta mike tana kallon Noor dake zaune parlon don Khaleesat tayi bacci tun da aka mata allura, Hajja ta sa daya daga masu aikin dake Part din nata su kai Noor wajen Mami don ita part din Jay take son tafiya don yanayin da ta gansa daxu taga alamar magana ya shigo yi mata sai kuma ga kakar Khaleesat, Yana zaune Parionsa ta samesa yana kallo, ta zauna kan kujera tace “Ina Hadiyah?” Ya jinginar da kansa da kujera bayan ya rage volume din TV din without looking at her yace “I don’t know, kilan tana can cikin gida” Hajja tace “Maimakon ta zauna ta kula da kai baka da lafiya sai ta tafi gantali cikin gida?” Shi dai bai ce komai ba don shi rabonsa ma da ganinta tun wajen 12 na rana da ta shirya ta ci kwalliya ta tafi can wajen uwarta da yan gidan, Hajja tace “Amma jikin da sauki?” Yace “Na ji sauki” Tace “To an kawo maka abinci kuwa tunda ita gantalalliyar bata nan?” Duk da bai ci ba yace “Na ci” Hajja ta sauke ajiyar zuciya, sai kuma tace “Daxu ka shigo kamar zaka min magana sai ga baki sun shigo” Ya girgiza kal yace “A’a, naje daukan abinci ne” Hajja tayi shiru kallonsa, ya gyara zama yace “Na ji za ayi meeting bayan Magrib, don Allah Hajja ina son ki nema min alfarma gun Mai martaba Ina son zan koma UK in nemi aiki a can” a hankali Hajja tace “UK kuma Jawwad?” Mace “In sha Allah” Hajja ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace “Kasan bazai amince da haka ba Jawwad” Jay yace “In ke kika yi masa maganan nasan zai amince” Hajja bata sake cewa komai ba a Parlon, after a while ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace “Ka je can bangarena ka sameni nan da minti sha biyar” Daga haka ta mike ta fita daga parlonsa, bangaren Ajay ta nufa zata dubasa, ya fito daga kitchen kenan rike da cup din Coffee Hajja ta iso corridor din, ta bude kofar Parlonsa ta shiga ya bi bayanta, ta zauna kan kujera tace “Kajl dama dama kenan” Bai ce komai ba ya zauna sannan ya gaisheta ba tare da ya kalleta ba, tana kallonsa tace “How are you feeling now?” Shi dai bai dago kansa ba a hankali yace “Alhamdulillah” Hajja tace “Tunda jikin ka da sauki kaje ka duba matar ka” Sai da gaban Ajay ya fadi jin abinda Hajja tace, yayi yana juya Coffee din hannunsa da s a hankall, Hajja tace “Ko kuma ka tashi mu tafi, tana can bangarena…” Da sauri Ajay yace ‘A’a sal anjima Karfe shidda saura Jay ya shigo parion Mami ta dalilin kiransa da tayi a waya, zaunawa yayi kan kujera donsa a kan TV yace “Gani Mami” Mami dai ta ci gaba da dama fura da take, Noor na zaune kasan carpet tana kallon Tv, tun daxu take son komawa part din Hajja taje gun Khaleesat amma ta kasa gaya ma Mami, Noor ta gaishesa, jin bai amsa ba Mami tace “Ana gaishe ka” Bai cire idonsa akan TV ba Without interest ya amsa a takaice, Mami dai ta ci gaba da abinda take, ya kara kallon Mami don barin parlon yake son yi yace “Mami kin yi kirana” Mami tace “Fura da nono ne gashi nan ban gama damawa ba” Yace “A’a bazan sha ba, na koshi” Yana fadin haka zai tashi Mami tace “Ka jira in gama ka tafi da shi, duk sanda ka so sha sai ka sha” Shiru yayi bai ce komai ba amma ransa bal so ya tsaya din ba, after some minutes Mami ta kalli Noor tace “Je kitchen ki dauko cup in zuba maki Noor” Noor ta dan yi murmushi tana girgiza kal tace “Na koshi” hatta muryarta Mami jin sa kamar ne Khaleesat, Jay ya mike à Laka yace “Mami idan anyi sallah zan dawo Dai dai nan aka bude kofar parlon sai ga Hadiyah ta shigo, kallo daya tayi ma Mani sai kuma ta kalli Jay ta hade rai tace “Sni ne tun daxu nake neman ka ashe nan ka zo ka zauna…. Mami ta daga kai ta kalli Jay tace “Je ka, zan bada furan ma….” Hadiyan ta wani kalleta, sal kuma ta tabe baki ts juya ta fice daga parlon without noticing Noor, Jay ya nufi kofa ya fice daga parlon. Bayan Magrib Ajay ya dake ya fita daga part dinsa zai je bangaren Hajja, kansa a kasa yake tafiya slowly yana sanye da thick Jacket dinsa ya saka har hulan Jacket din da ya rufe har kusan goshinsa kamar wani Villain, hannunsa duk biyu na cikin aljihun jacket din, har lokacin jikinsa a sanyaye yake sannan ba wal wani karfi yaji ba sai karfin hali, duk baccin da ya dinga yi yau Khaleesat kawai yake gani a baccin nasa, condition din da take ciki ya tsaya masa sosai a rai duk da halin da shi ma yake ciki but gaba daya hankalinsa na kanta, he couldn’t sleep all through yesterday a haka ya isa part din Hajja kansa a ka bude kofar parlorn a hankall ya shiga cikl ya daga kai, ido hudu suka yi da Jay dake zaune parlon tare da Hajja.

Back to top button