Hausa novels

Mejo Najeeb Page 21 By Autar Alheri

“Yana shiga yawuce bathroom yasakarwa kanshi ruwa tareda lumshe blue eyes ɗinshi yana sauke numfashi ahankali yanajin daɗin yadda ruwan kezuba ajikinshi,,atake yashiga tunanin yanayinda yakasance aciki lokacinda yana tareda Isseta, wani irin lallausan murmushi yasaki wanda yaƙara bayyanarda kyawun fuskarshi Hakan yabawa dimple ɗinshi damar lotsawa. Ido nazaro ina kallon inda zallar kyau da kwarjini yake tafiya da ƙafafunshi🤩, araina nace dama mejo najeeb na murmushi? Tab dijam Ashe dayasan yadda yake ƙara mishi kyau wlh dabezauna ɗaure da fuska ba😥 kai agaskiya soja beyiba😏Shikuwa sosai yakejin farin ciki aranshi wanda besan daliliba kawaidai yasan yaji daɗi sosai ajikin wannan aljanar yarinyar wadda besan miyasa take saurin gigita mishi lissafiba muddin zeganta to zeji ajikinshi tabbas shiɗin namujine domin se mazan takarshi tamotsa, amma ya,ajiye Hakan amatsin kasan cewarta aljan kuma mutum..tunowa yayi da lokacinda yake kissing ɗinta yana tsotse ko ina abakinta ɗan yamutsa fuskarshi yayi tare da miƙa hannu yaɗauki towel ze goge bakinshi, komi yatuna sekuma yayi murmushi kawai yana mayarda towel ɗin ya girgiza kanshi, kana yashiga yin wan kanshi, seda yagama tass kana yafito ɗaure da towel aƙugunshi wurin mirror yanufa, datinaninta fall ranshi. mai kawai yashafa tare da fesa turare yaɗauki kayan baccin shi yasanya, kan gadon yahaura yayi kwanciyarshi aiko cikin sauƙi bacci yayi awun gabadashi cikeda mafalkin Maryama..🤩 Tofa wata sabuwa akace inji ƴan caca🤔Wannan matarce Wadda ta tsorata alokacinda maah tabawa Isseta maganin da tashafawa mejo a ƙirji…to yanzuma itace a tsaye tsakiyar ɗakinta tana kallon duk abinda ke faruwa tsakanin Mejo Najeeb da Isseta acikin madubin tsafinta wani irin ihun tasaki tare dayin jifada kwaryar hannunta tana faɗar “inaahhh ƙaryane wlh sam baki Isaba laweesatt ƙarya kikeyi wlh bariganin kin haɗa mejo da wannan yarinyar nicenan zan kasance ajalinku dagake har itaa domin kuwa najeeb nejeeb nejeeb nawane ni kaɗai, tafaɗa kusan sau ukku kana tazube awurin tana rusar kuka….dariya taji abayanta wanda yayi sana diyar ɗagowarta tana duban me dariyar, wani mushirikin tsoho ne kemaƙale ajikin Bangon ɗakinta yana dubanta Shima kamar yadda take kallonshi….cikin sauri tataso gareshi tana faɗar “kaganiko tsijuju kaga abinda suke shirin aikatamin ko? Laweesat naneman ruguza min komai tana neman lalatamin shirin danayi shekara da shekaru ina gina abuna?? Wlh awannan karon bazan bartaba tsijuju doline na nuna mata akwai banbanci ko tsakanin mutum da aljan akwai bil’adaman dayafi aljani hatsa bibanci, sabida Hakan zan nuna mata kalar nawa hatsabibancin afili wanda yafi nata, taƙara zancen tana huci wani irin abu na fitowa daga cikin kanta yanabin jikinta.Tunda fara magana wannan tsohon data kirada tsijuju yakafeta da jajayen idanuwanshi masu mugun ban tsoro kafin yace “aiko dakin tabka naki kuskuren idan kikace zakiyi jayayya da gimbiya laweesat domin kuwa ita ɗin mutuniyar kirkice amma wlh kisani hadiman ta sunfiki iskanci sunfiki zama kafiran asuli a zalunci da rashin imani, iname shawar tarki akan kibari mubi komai asannu sedai babban abinda Zaki kula dashi Anan shine kisaka mishi ido sosai shida wannan yarinyar dayake tare da ita domin kuwa renon laweesat ce itada muƙarrabanta kiyi ƙoƙarin hanashi keɓewa da ita domin tunda yanzu ita bayajin tsanarta har wannan abin yafara shiga tsakaninsu to yadace muyi gaggawar kammala aikinmu. Dan nisawa yayi kana yace “kisani doline yakasance kece macen dazefara sani arayuwarshi muddin yasan wata macen kafin ke tofa daga ranar kifara ƙirga kwanakin tonuwar asirinki domin duk abinda kikasan anyi tun abaya to zewarware ne kuma zekoma kanki sabida Hakan karki kuskura kibari yakusanci koda wata dabance balle wannan yarinyar domin inada tabbacin laweesat da biyu tabawa najeeb ita, sabida Hakan kikulaa kikulaaa kikulaaaaa kafin lokaci ya ƙure mikiiiii,,,yana gama faɗar Hakan yaɓace batt kamar be wanzu awurinba……wani irin numfashi taja kafin tace “tabbas kuwa zanyiwa tukkar hanci Sam bazan bari laweesat tasamu damar rusamun shirin dana ɗauki tsawon shekaru inayinshiba sam bazan bata wannan damar ba wlh doline najeebullah ya kwanta dani kafin kowacce mace aduniya domin samun damar ƙarasa aikina kodan cikar burinaa,,tana gama faɗar Hakan tasheƙe da wata mahaukaciyar dariya kana tashiga haɗa kayan tsafinta seda tagama tukunnah tafice daga ɗakin tana saƙa da mugun zare..Isseta baiwar AllahKiran sallar farko na asuba tafarka inda ciwon marar ne yatasheta domin har baƙon yakawo ziyara, daƙyar tasamu tamiƙe sabida yadda jikinta yayi mata tsami domin kuwa mejo beyi mata da kyau ba duk ilahirin jikinta ciwo yake mata Musamman Nashanunta da hips ɗinta sekuma lips domin sune abinda yabaje hajarshi akansu…Hakan tasamu ta isa bathroom ɗin wanka tayi daruwan zafi sosai kana tawanke kayanta da suka lalace tareda bedsheet ɗin gadon, seda tagama bayan ta gyara banɗakin tafito ɗaure da towel a ƙirjinta tanufi mirror,,,,,ranta kuwa fall mamakin mejo da al’ajabin abinda yayi mata, seda tagama shafe shafenta ne taɗauki wata doguwar riga tasaka bayan tasaka pant domin dai itakam bra bazata sawuba sabida sunji maza twins ɗin nata…bayan tagama saka kayane takwanta ta duƙunƙune wuri ɗaya tunda ba sallar zatayiba kuma gaya marar namata ciwo haryanzu, anan baccin wahala ya ɗauketa zuciyarta fall mamakin mejo.Mejo NajeebSeda haske yafara fitowane tukunna ya falka, cikin mamaki yakebin inda yakwana da kallo kafin abinda yafaru jiya yaƙara dawo mishi arai, dan murmushi yayi yana shafa lallausar sumar kanshi kafin yaɗago idonshi suka sauka akan window ɗakin, ai a 360 yamiƙe tareda nufar bathroom yana istigifari agun uban giji akan wannan makara dayayi sam baze iya tuna ranarda yamakara sallar asuba ba arayuwarshi amma yau kam gashi yamakaro, kuma yasan duk sharrin wannan aljanar yarinyar ne…alwala yayi agagguce yafito kaitsaye yanufi sallaya yashimfiɗa kana yatada sallar. Se bayan ya idar yayi askar dinshi kana Takoma yayi wanka, yana fitowa yashafa mai kawai tareda fesa turarukanshi masu masifar ƙamshi, sa’annan yaɗauki kayanshi yasaka red color ɗin riga me gajeren hannu kana yasaka farin wando yaɗauki takalma red yasaka, “wow Masha allah agaskiya mejo Najeeb kyakkyawa ne nagaban kwatance domin kowacce irin sutura yasaka kyau take masa, cer key ɗinshi kawai yaɗauka yafita yana amsa wayar general aliyu inda yake gayamishi yazo gida Hajiya mama tace ba’agidan yakwanaba. Suna cikinyin wayar yafito harabar gidan inda su captain Umar suka taso suna gaidashi..hannu kawai yaɗaga musu kana yashiga motar yayi mata key yafice daga gidan…sukam da kallo suka bishi suna mamakin kwanan dayayi anan domin sudai tun ranarda yace sufara tsaron gidan koganin shi basuyi yazoba balle yakwana. Se ayau ɗinnan, haka dai suka share tunanin suka shiga sha’anin gabansu tareda zaman jiran matar gidan takawo musu abin kari🤩Yana fita kaitsaye hospital ɗin Doctor ziyad yawuce…doctor ziyad nazaune yana duba wata marar lpy mejo yashigo office ɗin…dukkansu ɗagowa sukayi suna kallonshi,,,shiko ko kallonsu beyiba yawuce bathroom ɗin dake cikin office ɗin yayi zamanshi yana jiran doctor ziyad ɗin yashigo…seda yagama sallamar wannan matar kana yashiga yasameshi. “morning friend ya ƙarfin jikin naka? Doctor ziyad yafaɗa yana bashi hannu suka gaisa, kana yace “im better now, yafaɗa kamar bayaso. “Au really?🤨 Cewar doctor ziyad cikin mamaki..hararar shi mejo yayi kafin yace “of course, tukunna yaƙara da fadar”maganin ciwon cikin mata zaka bani, yaƙarasa zancen yana ɗan yamutsa kyakkyawar fuskarshi.”Tofa subahanallah waye ba lpy ummi ko Mansura? Yatambaya cikin damuwa…Shikuwa banza yayi mishi kamar bejishiba, ganin Hakan yasa doctor ziyad faɗar “kaifa ɗan iska ne mejo kanaji mutum nayima magana zaka sharehi waima tukunnah jiya miyasa kagudu batareda kajiraniba?? Ko kana gudun natuhumeka ne akan fitinarka tayi yawa. Yafaɗa yana ƴar dariya…Shikuwa aɗage ya kalleshi kana yamaida idonshi akan wayarshi dayake chat da general faruk…”Humm mejo kenan wlh to bari ingayama tunwuri kanemi matar aure domin wlh wannan Condions ɗin naka idan Kaci gabada zama ahakan za’a iya samun matsala sabida bakowanne magani ko injection ketasiri ajikinkaba kuma wannan matsalar zata iya taɓa ƙwayoyin halittarka please kakula Dan Allah, yaƙarasa zancen in seriously…ganin yadda yake maganar dagaske ne yasa mejo bashi hankalinshi har ya kai ƙarshe domin aduniya Allah yajarabeshi dason yara Hakan yasa yajinjinawa doctor ziyad kai kawai batareda yace komaiba amma dai ga dukkan alamu ya yadda dazancenshi. Ledar maganin doctor ziyad yabashi tareda yimai bayanin yadda za’ayi anfani dashi.. “okay thanks shine abunda yafito daga bakinshi tare da Miƙewa yabar office ɗin.Hanyar gida yaɗauka seda yakusa ƙarasawa yatunada Batada lafiya fa, balallene zata iya tashi tanemi abunciba tunowa da Hakan yasa yajuya akalar motar zuwa wani gidan abinci dake kan hanyar, seda yasiya mata abinci merai da lafiya tare da roghut dudda Cewar yasan baza’arasa kayan sanyi agidan ba amma Hakan yaƙara siya mata wasu tukunnah yanufi gidan….koda yashiga general parlor gidan yasa meshi yadda yabarshi ko fitilar perlor ba’akunna ba Hakan ya tabbatar masa dacewar bata sauko bakenan, haurawa yayi Saman benen zuwa bedroom ɗinta yatura ƙofar ahankali yashiga tareda maidata yarufe, wayar hannunshi ya haska yahangota can akwance akan gadoƘarasawa yayi kusanta yazauna bakin gadon kana yatsura muta ido kawai yana kallonta, tunani yakeyi ta inama ze fara tadata ayadda yaga taduƙunƙune wuri ɗaya kuma ta kwaɓe fuskarta yatabbatar masa dacewa ba daɗin baccin takejiba,,,Yajima ahakan yamun ya yaye blanket ɗin ahankali seda yakusa zameshi daga jikinta ne yaji tariƙe daƙarfi tana wasu surutai wanda ya kasa jin abinda take faɗa amma kuma se motsi bakinta keyi,,,cikin sauri yakara kunnenshi Dede bakinta anan yaji tana faɗar “kabari please zafi sukemun dan Allah yah najeeb kayi haƙuri nipples na zafi wayyoo Allah maah zetsinkamun nono na kigayamai yabari please, taƙarasa zancen tana ƙara matse jikinta tare da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba…ido mejo yazaro jin abinda take faɗa kamin kuma wani shi’umin murmushi yasuɓuce mushi yana shafa lallausar sumar kanshi..tinani yakeyi aranshi dama tasan Sunanshi ne takeyi kamar batasanshi ba?? Yayiwa kanshi wannan tambayar….sekuma wata zuciyar tace kobata san sunanka ba aitaji su general aliyu na faɗa kuma agabanta maahh tafaɗi cikakken Sunan naka. Jinjina kanshi yayi alamar ya yadda da abinda zuciyar tashi tagaya mishi,, hannunshi yaɗora akan kyakkyawan gashin kanta daya zubo har godon bayanta besan miyasaba kawai yatsinci kanshi dashafa gashin kan nata yana lumshe kyawawan blue eyes ɗinshi, Yajima ahakan kamin yabuɗe idanun nashi akanta aiko suka yi ido huɗu shida ita,,domin tinda yaɗora hannunshi akanta tafalka sedai kunyarshi da haushin abinda yayi mata jiya yahanata cemishi komai….cikin sauri yajanye hannunshi yareda ɗaure fuskar kamar besan minene dariya ba shi adole karta renashi,, miƙewa yayi kamar wanda aka tsikara yanufi barin ɗakin seda yakai bakin ƙofar kana yabuɗe baki cikin cool voice ɗinshi yace “ga abunci nan kitashi kici sekisha magani yana gama faɗar Hakan yafice daga ɗakin….da kallo Isseta tabishi domin yayi mata kyau acikin wannan shigar tashi, sedai zuciyarta fall mamakin shi yadda yakeyin abu yakoma kamar bashi yayishiba,,seda taji tashin mota alamar yabar gidan kenan sa’annan tamiƙe daƙyar tanufi bathroom wanka tayi sosai tareda brush kana tafito tagyara jikinta domin tuni baƙon nata yakawo ziyara,,,bayan tagama duk uzurintane tasaka kayanta tukunnah taɗauki abuncin taci domin sosai taji daɗin siyo matashi dayayi tunda bazata iya dafawaba..seda taƙoshi kana tasha magani, sauran da bata taɓa ba taɗauka takaiwa su captain Umar kana tadawo tashiga gyaran gidan domin sosai taji daɗin maganin datasha…Shikuwa mejo yana fita gidansu general aliyu yanufa.Nigar Acikin garin maraɗi….!

Back to top button