Hausa novels

Matar Hariji Page 21 Romantic Hausa Novel

Duk yanda yaso tayi masa bayani taqi sai kuka kawai da takeyi da yayi Mata mgn hakanan ya qyaleta suka oma gda yaci gaba da tattalin ta duk wani motsinsa akan idonta baya sakaci da duk wani abu daya shafeta qauna yakewa cikin na musamman.A wannan tsakanin ne tafiya ta taso masa zuwa Germany lkcn tana tsakiyar laulayi yaso tafiya da ita amma tayi fur tace ita bazataba ya mayar da ita kano, dolensa badon yasoba ya kawota Kano kwana biyun da yayi a part din Mubaraka ne itakam zaman doya da manja akeyi ita dashi tunda ta lura da samuwar cikin na Hauwah ta dauki kishin duniya ta dorawa cikin.Ranar da ya bar dakinta ranar ya tafi amma saida ya nemowa Hauwah wata dattijuwa da zatake kula da ita saboda tsaro, farin ciki gurin Muneef kam baa cewa komai kura ta mutu ya huta gda ya dawo nashi.A ranar itama Mubaraka bata kwana a gdanba gdan wani Alhnta ta kwana ta zubewa Nanny din yaran su a cewarta bikin qawarta akeyi, itadai Hauwah tana samanta tana fama da kanta bata sanin wainar da ake toyawa sosai.A hankali ta fara fahimtar wani abu wata rana ta sauko daga saman wajen biyar na safe daga ita sai rigar bacci tunda ta fito ya kafeta da ido tare da qara lafewa a kujerar da yake kwance, itakam batama lura dashi ba ta wucce ta shiga kitchen din da niyyar dauko fresh milk saboda tashin da tayi taji cikinta kamar anyi mata yasa.Kitchen din ta shiga hakan ya bashi damar miqewa zumbur yabi bayanta batayi aune ba kawai saijin mutum tayi a bayanta ya dora hannunsa a saman weast dinta, zabura tayi tayi baya tare da qwallah qara yayi saurin rufe mata baki ta hannunsa tare da murdawa qofar key.Jikinta tsuma yakeyi tanaja da baya da sauri shikuma yana binta har takai qarshen kitchen din, yana wani murmushi yana lasar lebe ta wawuro wata shafceciyar wuqa tayi kansa yaja baya da sauri hakan ya bata damar murda mukullin ta bude qofar ta fita da gudu har suna karo da Ladi me rainon yaran gdan riqeta tayi da sauri tace.“Hajiya meye hakan?” A firgice ta qwace ta nufi saman a guje tana rusa kuka ta fada dakinta ta datse da mukulli jikinta na rawa tana kuka hatta abinda ke cikinta hautsinawa yakeyi haqoranta sai haduwa sukeyi. Ta dauki wayarta cikin kukan tashin hankali ta latsa number Lameer Ring daya cikin saa ta shiga ya daga da sauri yace “jiya kinyi bacci da wuri maman twins banji muryarki ba…” Kukanta ne ya katse masa maganar yace.“Meye kuma ya faru yanzu” cikin kuka tace “karo na uku kenan yanayimin haka Lameer nagaji da wannan akuyancin na qanin ka tunda ka tafi Laraba tacemin a gidannan yake kwana ban yarda ba ban gasqatata ba sai yau Lameer me yake nufi danine meye yakesa kullum burinsa ya ketamin haddi”Tunda ta fara mgnr ya miqe tsaye yana auna kalamanta da kalaman Sabon maigadin daya canza da yace masa Alh kullum sai qaninka yazo gdannan nayi yunqurin hanashi Hajiya babba tace karatu yake koya mata”Gabansa ne ya fadi sosai yace “me…me yayi miki?” Nan ta kwashe komai ta fada masa yace “ok ki shirya kayanki yau zansa azo a daukoki zuwa Lagos ku tafi da Laraba very soon zan dawo idan na dawo zansan abinyi”Kashe wayar yayi ya Kira ta Hajiyansa cikin tashin hankali yace “Hajiya Ina dan iskan yaron nan yake kwana” katseshi tayi da cewa “wlh bansani ba wani lkcn idan abin nasa ya juyo sai ya daina kwanan gida kwata²”Kashe wayar yayi ya kira wayar Mubaraka lkcn suna manne da juna yana bata labarin rashin sa’arsa na cimma buqatarsa gurin Hauwah da sauri ta daga tace “sai yau ka tuna damu?” Bai tsaya sauraron qorafinta ba yace “meye ya tasheki da wuri?” Tsaki tayi tace “nifa natsani tuhuma kaji na fada maka” bai kuma cewa komai ba ya kashe wayarsa.Duban Muneef tayi tace “ina tsoron wannan bagidajiyar yarinyar ta ballo mana ruwa fah” dariya yayi yace “habadai ita mahaukaciyar inace da zata fada masa” share mgnr sukayi sukaci gaba da sharholiyarsu inda ita kuma ta fara hada kayanta wani yaronsa yazo ya daukesu daga gdan ba tare da kowa ya sani ba.Shikuma cikin sirri ya turo aka maqala masa C.C camera da takeyi masa record na komai batare dasun sani ba, saida aka dauki sati guda sannan Mubaraka ta kirasa lkcn taje gdan Hajiya suke qyanqyasa masa wai wani mutum yazo har gida ya dauki Hauwah har Hajiya tana fadin ai dama tasan zaayi haka duk macece zata iya hqrn da Mubaraka takeyi dashi.Shidai bai nuna shine yasa akazo aka dauketa ba hasalima cewa yayi zaisa a nemeta, su Mubaraka duniya ta samu shima maigadin kudi take basa batasan leqen asirinta yakeyi ba yana ganin takunta tayi wanka ta qyafe wani Alh birni yazo ya dauketa.Da dare kuma Muneef yazo susha shagalinsu, yau tun safe ta shirya zuwa gidan Hajiya abokin shedancinta babu lfy tana zuwa suka gaisa da Hajiyan ta miqe tace bari taje ta duboshi, Hajiya bata dauki komai ba tabita da kallo ta bude qofar ta shiga ta mayar ta rufe yana kwance ya bude idonsa ganin itace yasasa bude mata hannu ta shige jikinsa tana kissing dinsa tace “inata missing dinka jiya nasha magunguna na tsumu najika shiru Saida mukayi waya da Hajiya take cemin bakada lfy”Shima shigewa yayi jikinta yana lasar lips dinta yana tura hannunsa cikin rigarta yace “nima nayi kewarki yanzu sai muyi qara’in rayuwa” zaro ido tayi tace “hajiya fah” kanne mata ido yayi yace “manta da ita” daga haka suka soma fajircinsu sunma manta da a Ina suke, ita kuwa Hajiya tananan zaune taji Shiru tayi yawa sai tayi kamar ta miqe saidai ta share candai taga abin yayi yawa kuma ta tuna da wani gani da tayi musu suna kissing din juna, ai saita zabura ta miqe tana fadin Mubaraka yamma fah tayi kizo ki tafi gdan…..”Maganarce ta maqale saboda abinda idanunta ya gane Mata taja baya da sauri tare da kurma ihu tana fadin “innanillahi wa innah ilaihirraji’un me zangani ni jikar me sabulu Muneef Mubaraka lahaula wala quwwata illah billahil aliyul’azeem matar yayanka yau nayi baqin gani ni maryamu meye ya kawoni ne…..” Zunbur suka daga junansu kowa yana neman abinda zai sitirta jikinsa kafin su gama kimtsawa Hajiya tayi waje batakai ga zama ba jiri ya debeta ta fadi qasa tim daidai lkcn da Alh yake shigowa gidan ya qarasa da hanzarinsa ya dagota yana jijjigata.Fitowar muneef da mubaraka yasa Alh binsu da kallo kowa sai rawar jiki yakeyi na alamun rashin gaskiya shidai bai tsaya sauraronsu ba ya dauki Hajiya ya fita da ita zuwa ga likita, aka shiga dubata.Kwanan Hajiya uku batasan waye ke akanta ba a rana ta hudu ce ta samu kanta Koda ta farfado taga muneef a kanta kuka ta kamayi tana girgiza masa kai tana nuna masa hanyar waje tun daga wannan rana bata yarda yazo inda take balle mubaraka wadda da tazoma hanata shigowa tayi.Takasa fadawa kowa abinda ya faru sai aikin kuka da nadamar abubuwa da yawa.Sati daya da faruwar lamarin Lameer ya diro 9ja Lagos ya sauka gurin gimbiyarsa zuciyarsa wasai, itama tayi murnar ganinsa sosai ta rasa Ina zata ajeshi don murna, ya sunkuceta yana dariya ya shige da ita bedroom nasu ya kwantar da ita a gado yace “nayi missing kyakkyawar kulawar matata nayi missing farin cikina”Rungumeshi tayi tace “nafika kewa babe kullum sai nayita juyi ina rungume pillow”

Back to top button