Uncategorized

Matar Makaho Part 6 Complete Hausa Novel

MATAR MAKAHO

Chapter 6

By Rukayya Ibrahim

Khadija ce a zube a kasa cikin ruwan cab’alin rijiya,salame na ruwan cikin ta,ta hakikance sai jibganta take

Sake hannun yayan khadija nayi Da wani irin gudu nayi Kan salame,don na fahimci Yan gidan nan in har baka koma irinsu ba zasu kasheka,yarinya sa’ar khadija Amma khadija ta sake jiki tana dukanta Koh martani Bata mayarwa sai k’okarin Kare kanta,kafun na Isa ba zatoh ba tsammani sai kawai Naga  Iro ya kwashe salame da kafa daga Kan khadija yayi ball da ita sai da ta zube a Gefen  rijiya bakin ta ya sare simintin rijiya,kafun kace me tuni ya rufe salame da duka sai a lokacin Yan gidan suka firfito,Abu kamar Wasa fad’a ya zama babba,don fadan yanzun Kam mutane sunkai biyar suke dambe,kama khadija nayi wance tunda Iro yayi ball da salame take gefe tana kuka duk jikinta sai rawa yake, “khadija  tashi mu shiga kofata sannu”

Mikewa tayi a hankali,suka nufi kofar shashensu

Al’ameen Kam Yana tsaya Kamar andasa sa don baya gane kome tsabar yanda surutai da koke koke  ke tashi a tsakar gidan,sai raba ido yake kawai

Muna zuwa saitin inda yake hannu kawai nasa na Kama NASA Muka shiga cikin kofar tare,

Sake hannunsa nayi, 

Ruwa na iba na Kai Mata band’aki na Kama hannunta muka shiga, kanta na wanke Mata kafun na fita na barta tayi wanka

Kaya na makala Mata a jikin kofar band’akin,

Tana fitowa.

D’aki Muka shiga zaunar da ita nayi da sauri na d’auko D’an kwalina na d’aura Mata akanta dake ta zubar da jini”khadija meya hadaku meya faru?

Wallahih   Aunty Ina fitowa kofarki kawai nazo wuce gindin rijiya,Daman salame na iban ruwa kawai ta kwashi kafafuna na zube shine tahau kaina tana dukana,kallifa Aunty ta fasamin Kai,ta fad’a tana Kara karfin kukanta

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 1 HAUSA NOVEL”


“Kiye Shuru khadija,share hawayen ki yanzun za’a bi Miki hakkinki wallahih in sunsan wata Basu San wata ba” nace Ina duba inda na aje wayata

In Raina dubune yau ya baci na gaji da bala’in Yan gidan nan da Talaucin da muke ciki zamuji Koh da tashin hankali’wayana na d’auka tunawa da nayi,da wani school mate nawa lokacin da na shiga jami’a shi Kuma Yana final year insa,yanzun police ne yana da babban mukami a hukuma, muna mutunci sosai kamar yan   uwa danayi aure ne dai bamu sake magana dashi ba.

Me zakiye Sumayya? Al’ameen dake zaune a kujira yayi tagumi ya tambaye ta 

“Mataki Zan d’auka”

Wani irin mataki?

Akwai Wanda Zan Kira wallahih Koh tantama banayi  daga gidan nan direct sai prison Koh station bazata shiga ba Kuma sai naso za’a bada belin ta”. 

Wa Zaki Kira?

“Wani friend Ina ne”

Toh wallahih ba’a gidan nan ba

“Ban gane ba’a gidan nan ba kenan kana nufin abarsu suci bulus kenan kaga yanda suka fasawa yarinya Kai kace a barsu”

Ina dai kanwata aka fasawa Kuma nace bana bukatar ki d’auki mataki

“Ok nuna mini kake khadija ba kanwata ba koh”fine shikenan gaka ga Yan gidan naku,Daman nice bare”nace Ina aje wayata na fita waje sosai maganar Al’ameen tamin zafi Wai kanwarsa Kuma yace baya bukatar mataki,watoh ba ruwana kenan a maganar

Al’ameen Kam harga Allah Bai Fad’a,don wani abuba kawai ya fad’ane don ta janye maganar rufe salame,baisan maganar zai Mata zafi harta fassarasa wani iri ba

Khadija Kam sosai taji Bata kyauta ba a  sanadin ta ma’aurata sun samu sabani,mikewa tayi ta fita  waje,

wajen da Sumayya ke zaune ta karasa

Aunty bara naje kasuwar

“Khadija Wai kina nufin kudin nan na hannunki”?

Ni na d’auka ma Koh kin yasar dashine tuntuni”

Ah ah Aunty Daman a bakin zanina na soke Kuma Allah ya taimakeni Bai fad’ ba

“Ok kibar zuwa cefenen”nace Ina karban kudin hannunta

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 2 HAUSA NOVEL”


Ah ah Aunty maganar Yan lallen fa,don Allah Aunty karki fasa lallen nan,Akan abinda ya faru.

“Ah ah khadija rike 1k innan kije chemist a Miki dressed in wajen Naga har yanzun jini Bai tsaya ba”

Toh Aunty na gode tace tana mikewa zata fita

Khadija tsaya muje na rakaki, Sumayya ki kawo cefenen Inna rakata chemist sai na wuce kasuwar, Al’ameen yace

Kala bance Masa ba don haushin sa nakeji sosai,hakurin sa yayi yawa shiyasa ake cutar sa kullum

Aunty Yaya na magana Wai zaije kasuwan,

“Ka barshi kawai gobe Zan aiki Yan lallen suje kasuwa su sai mini abin hadin”

Toh Aunty ki basa kudin cefenen sai ya sayo muku,ya iyya zuwa kasuwa, khadija tace cikin rashin Jin Dadi ganin yanda na Had’awa yayanta fuska

“Ungo”na Mika Masa 6k

Matsowa yayi Yana lalube ya karbi kudin a hannuna

Me da me Zan Saya?

“Ka tamabaye khadija na Mata lissafi “

Ok yace cikin sanyin jiki don wallahih Bai d’auka maganar zatayi zafi haka ba

Suna kokarin fita Asma’u na shigowa da kawayen ta,suka gaisa da Al’ameen kafun suka shigo,khadija kuma suka fita

Shimfid’a musu darduma nayi,suka zazzauna

Tashi nayi naje na chanja kaya,na manna Gam a faranti,na kwaba lalle,Muka fara

Khadija ta dawo lokacin kusan karfe 10

“khadija ki shige d’aki kije ki kwanta Naga an kawo NEPA ki huta kinji”nace Mata Ina kallon kanta da aka mannawa plaster

Toh Aunty tace tana shigewa d’akin, kwanciya tayi a kujira,banci ya d’auke ta

Al’ameen Kam kasuwa ya wuce yaje yayi sayayan kayan abinci,Amma Sam yau Baya cikin walwala tunda suka D’an samu sabani da Sumayya,don shi Sam bayason yayi abinda zai bawa wani haushi harya kullace sa abin damunsa yake

Yan matan sunata Hira,inama Amarya lalle,saiga Al’ameen ya dawo da laidodi a hannunsa na sayayyan kasuwa,mikewa nayi na karbi laidan gudun kar na tozartashi a gaban su,kitchen na shiga da laidodin shima bayana yabi 

Yan Mata Kam sai ido suke bin MAKAHO da MATARSA suna mamaki

Muna shiga kitchen in,na aje laidodin 

Sumayya Naga Yan sana’ar sunzo Koh Zaki kawo na girka Mana abincin? in yaso

“Kai bazaka fita bane”?

Zan fita Amma sai bayan azahar

“Toh ka iyya girkine? koh da wani idon zaka girka Mana abinci muci”?

Eh na iyya girki,sai ki jera mini Abubuwan da Zan girka Zan iyya

“Bana bukata”nace Ina Shirin fita

Jin Amsar da ta Bashi ya tabbatar har yanzun haushi takeji,hannu yasa a hankali ya rikota Jin zata fita a kitchen in

“Ka sakeni”nace ba Wasa a muryata

Sumayya kiye hakuri in abinda na fada Bai Miki Dadi ba

“Ka sakeni nace maka”

Am sorry

“Ka sakeni”

Baki hakura ba?

“Ka sakeni”

Toh innaki fa,ba Matata na rike ba

“Matar ka ai da Ina da wannan matsayin da gaske da bazaka nuna mini banda matsayi agun khadija ba”

Amma ba nace kiye hakuri ba,yace Yana jawota jikinsa

“Nima ai bance maka naji haushi ba”

Amma gashe sai fushi kike

Haka dai Kai kake gani,nikam sakeni Rana yayi bamu karasa lalle ba

Bana gani sai dai ji

“Oho maka dai”

Mana dai,ba ni kadai ba

“Toh sakeni Mana”,nace Ina banbare jikina a nasa

Sumayya abinda yasa Kika ga naki ki d’auki mataki,da hukuma toh a gidan nan Babu Mai tsoron station Koh prison don ba bako bane agunsu, bare ya saka musu tsoro don kinsa an rufe salame,wata fitinar kika kunna,zaman gidan nan sai ya gagare mu

“Kai kake tsoron fitina bani ba’ akan gaskiya na Koh Ina zanje”

In Miki girkin?yace Yana kauda maganar

“Ka bare Zan girka”

Toh shikinan,yace Yana saketa,

Tsayawa nayi ya rigani fita a kitchen in,

Ya Kama hanyar kofar fita a shashen mu

Nima fita nayi,”am please bara na d’aura Abinci, Rana yayi sai nazo mu karasa”

Aunty bara na d’aura miki,wata Yan Mata a cikinsu tace

“Ah ah ki bare kawai”nace Ina tunanin karfa Bata iyya girki ba ta Bata mini kaji a banza 

Kai Aunty Koh dai kina tunanin ban iyya girki bane?

Ba haka bane,Daman Ina tunanin karna takura Miki ne,Amma  tunda kina sonyi shikenan,ki tuka semo laida babban duka,

Kitchen ta shiga

 ni Kuma d’aki na shiga naje na leka khadija har lokacin bacci take

Sai azahar  na kammala lallen Amarya,na tashe khadija mukayi sallah abincin da farida kawai Amarya ta girka na zubawa yayan Khadija nasa, na zuba na Daren mu, sauran na zuba ma kawayen, na ibawa Amarya na zuba Mana da khadija,sosai Tuwon yayi Dadi,bamu Gama ciba aka turo yara da kulolin Abinci daga gidansu Amarya shinkafa muka dad’a,

yaran na baiwa na yayan Khadija su Kai masa

Ganin da sauran lokaci yasa nama farida lalle (wance tamin girki)

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 3 HAUSA NOVEL”


Sai la’asar Asma’u tayi wanka sosai na zuba Mata light make-up tayi kyau Kamar me,ganin kawayen nata d’aukar ta hoto yasa Nima na fitar da wayata,na d’ad’auki hotonan lallen ta da kwalliyar da na Mata duk da hoto nason gida Mai kyau Amma wanka na gyara hoto ma ba gida kawai ba

************

Bayan tafiyar Amarya da kawayen ta, wanke wanke nayi na share kofar don yayi kaca kace,kowa yasan gidan Mai lalle in ta Tara customers,yanda yake baci

Wanka nayi,donna gaji sosai yau innan,vest nasa na d’aura zani don ba kowa a kofar nawa khadija ma ta tafi gida,don yau ba zuwa program Kai ya fashe

Bayan sallar mangariba ya dawo Kamar kullum wanka yayi mukaci Tuwon da farida ta dafa Mana da rana

Bayan sallan isha’i yau Koh jiran ya dawo masallaci banyi ba na kwanta don gabaki d’aya bacci nakeji ba kad’an ba ga gajiya sosai.

Yana dawowa ya tarar tayi bacci shima gadon ya hau don tabbas yau yasan ta gaji,tabata yayi yaji alamun bacci take,a hankali ya cire mata vest in jikinta daga ita sai wandon bacci,shima kayansa ya cire dagashi sai guntun wando a hankali ya rumgumeta,kome a hankali yake gudun karya ta tashi,sosai yaji wani irin yanayi Mai matukar shauki a tare dashe,amam haka yake dannewa,har bacci ya dauke sa

Misalin karfe 3 na asuba kamar a mafarki naji ana tattaba min kirji da sauri na bude ido,tashi nayi na zauna jina ba riga,sake taba jikina nayi don na tabbatar Aiko da gasken bani da riga,

“Wai meyasa kwana biyun nan ka chanja ne kanamin abinda ranka yake so”?

Mutum da halaliyarsa, ya Bata Amsa Kamar Wanda tama Dole

“Ka tashi mini a wajen kwanciya”

Ina kenan?

“Gado”

Naki, gaskiya yanzun bazanna kwana ni kadai ba alhalin Ina da mata.

“Don Allah nikam ka tashi, kaga yanzun ma Banga rigata ba ga d’akin duhu”

Saiki kwana haka

“Akan wani dalili Zan kwana ba riga,Kuma karka sake ciremin riga in Ina bacci banaso”

Inna cire fa?

“Au tamabaya ma kake sai me?

Eh tambaya nayi

“ka Dameni sai surutu kake sani tsakar dare”

Wani dare ai na yau ya wuce sai dai na gobe

“Ka tashi nace”

Naki

“sauka zanyi na bar maka d’akin ma in baka sauka ba”

Toh na hanaki ne

Mikewa nayi na sauka akan gadon nayi hanyar kofa Koh riga ban dashi,

Ba riga Zaki fita waje?

“Ai baka fini ido ba”nace Ina kokarin bude d’aki, kawai ji nayi y………..

  

Ji kawai nayi ya rumgume ni ta baya,

zare ido nayi jinsa shima ba riga,mannani yayi da jikin kofar shi koma ya rumgume ni sosai ya d’aura kansa a kafad’ata

“Wai menene haka don Allah” ?

Dadi ne,ya Bata Amsa

“Dad’au matau”    

Jin Amsar da ta Bashi yasa ya juyo da ita da karbi ya rungume ta

Ware ido nayi jina sukutum a kirjinsa dukan mu ba riga

“Wayyo Allah meye haka” 

Mele,shima ya Rama

“Nikam.ka sakeni”   

Bakinsu ya hada,a hankali yake kissing in lips nata na sama

Bansan garin Yaya ba Koh yaushe ba na tsinci kaina da Kama lips nashi na kasa Nima na shiga tsotsa

Jin ta Kama Masa lips yasa a hankali ya zame bakinsa cikin nata,ai da sauri yaji ta kamo kansa ta sake maisa bakinsa cikin nata 

Sosai suka shiga farantawa junan su Rai ,

ba zatoh Koh tsammani   muka zube a kasan cafet,nice a sama shi koma a kasa,

da sauri ya birkitota kasa Yana lalube da D’an kokarinsa zai zame Mata wandon baccin da ke jikinta

Da sauri na Kama hannunsa Jin aika aikan da yake so yayi

Don Allah ki bari musamu nutsuwa

“Nidai wallahih ah ah”

Please kinji

Kokarin mikewa na fara a jikinsa,

Da sauri ya kamota,Ina Zaki

“Anafa Kiran sallah”   

Sakinta yayi Jin da gaske Kiran Assalatu ake

Mikewa nayi a hankali daga jikinsa Jin ya sake ni,”d’akin ba haske fa”

 

Ki kunna glop Mana

“Bana gani” 

Ok bara na lalubo glop in

“Toh,Ina rigana”?

Bara na kunna wutan sai ki duba,yace Yana mikewa daga kasan cafet

Mikewa yayi Yana lalube ya Isa wajen makunnen NEPA ya kunna

D’akin ya gauraye da haske,da sauri na rufe kirjina da hannu sai koma nayi tsaki tunawa da nayi bama gani yake ba

Menene kike tsaki kuma?

“Banga rigana ba”

Riga Koh vest?

“Oho”

Wai kikam wace irin matane Mai tsewa

“Green in Mata ka aura”

Toh Green Sumayya,mu fita kar ashiga sallah?

“Kai ka fita Mana Koh na d’aureka ne”

Toh Green sumy

Lalle mutumin nan ya Raina mini wayo,ji kawai nayi ya kamo mini hannu Yana kokarin fita Dani a d’akin cikin lalube

“Ban saka rigaba ka sakeni Mana pls”

Sakin ta yayi Jin Wai Bata da rigan da gaske

Bayan fitar shi rigana na d’auka na fitoh Jin harya kammala Alwala ya wuce masallaci

Bayan idar da sallah dukan mu bacci muka koma 

Misalin karfe 7:00 na safe aka doka Mana sallama a kofar d’aki,bude ido nayi a hankali ganin Yana kokarin sauka a gadon yasa na gyara kwanciya

Amsa musu yayi ya zura jallabiyar sa ya fitoh,

Ina kwana yayan Khadija?

Lafiya Alhamdulillah

Gun Aunty Sumayya mukazo,Yan matan sukace

Ok,bara na kirata yace Yana komawa d’akin

Hawa gadon yayi,ya yaye blanket inda ta rufu 

“Menene”?

Baki kikaye,Kamar Yan lallen ne fa

“Gaskiya bazan tashi ba suje su dawo anjima”

Ah ah Sumayya wulakanci ba kyau ki lallaba dai ki tashi kinji Green sumy

“Wallahih Inka sake fad’amin sunan nan Mai rabani da Kai sai Allah”

Me Zaki mini ai Babu abinda Zaki mini sai abinda Allah yaso

“Hmm” kawai nace na mike,fitowa nayi na shimfid’a musu darduma muka gaisa Yan matane guda biyu Amma ba kawaye bane,

“ban fa Saya lalle jiya ba bansamu D’an aika ba gashi 8:00 ake bude kasuwa Koh zaku karba kuje ku sayo”?

Eh Daman mu biyu mukace bara muzo kafun a Gama Mana kafun sauran su karaso,ba damuwa a bamu kudin bara muje mu sayo in 

“Ok bara na kawo muku kudin”dakin na shiga na d’auko musu kudin,suna fita wanka nayi na kimtsa kofata yayan Khadija ya ibo Mana ruwa,

Shinkafa da wake dafa duka na dafa Mana direct harda na Rana 

Bayan mun karya fita yayi, ni Kuma muka fara lalle,

Sai kusan 3 na karasawa matan lallen su dukansu su bakwai kowa hannu hannu na Masa ja da baki,sai kwalliyar walima 

Gaskiya yauma ba laifi na damka kudi Mai tsoka sosai..

Naso.muyi cefene Amma yau khadija batazo ba ni koma ba fita nake ba bare na aiki yaro

Yayan Khadija Kam Yana fita yaje ya bude mangoron sa duk sun rube haka ya zubar dasu don Koh ya bude ba Saya za’a yi ba haka yayita zama har yamma don yasan tabbas Sumayya zata sama musu na abinci Amma yanajin kunya ace kullum ita ke ciyar dashi 

Haka yayita zama sai mangari ba ya mike bayan yaje masallaci ya kamo hanyar gida jiki a sabule

Bayan sallar mangari ba ruwa na Ina na shiga wanka

Yana shiga gidan da sallama ya shigo kofar Jin shuru Bata Amsa ba ya zata Koh tana d’aki ne,ruwa ya Iba ya shiga ban d’akin

Goga soso nake a zaune kawai naji mutum ya shigo bayan gidan

A matukar tsorace na kwana Kara,”wayyooo”

Shikam zuciya D’aya ya shiga bandakin Bai d’auka tana ciki ba shiyasa ihun yazo Masa unexpected,yasa ya gigice, Sam Bai d’auka dalilin shigarsa bane yasata ihun,d’auka  yayi Koh wani mummunan abune ya same ta

Subhanallah Sumayya lafiya? yade?

yace Yana matsowa inda yaji ihun nata

“Wallahih Inka zo inda nake saina kwara maka  ruwan nan”,nace cikin tsawa Ina d’aukar bokatin ruwan wanka na in,damuwa na kawai na ja towel inda na makala a saman kofar band’akin,na d’aura

Sai yanzun ya gane dalilin ihun nata,manna Mata hauka kawai yayi ya Kama cire riga

“Wallahi ka fita a toilet innan na ratse Zan kwara maka ruwan nan”,duk tabi ta rikice

Ikon Allah waini idone Dani bare na kalli abinda kike boye wan

Kuturu,kawai nace,Ina daga boket in ruwan ganin Yana matsowa inda nake

Jii kawai yayi shaaaaaaaa Sumayya ta kwarara Masa ruwa,Bai d’auka da gaske take zata kwara Masa ruwan ba,

Nikam ganin Yana ta faman sharte ruwan fuskar sa yasa,na ruga zanyi waje da gudu Koh Kaya bansa ba ,

Ai.jin gudunta yasa ya bita shima da gudun 

Ina kokarin fita a band’akin kawai naji ya jawoni ciki, Allah yasa Ina kusa ta towel jawosa nayi a hannusa

Wallahih Sumayya baki Isa ba ki kwaramin ruwa Kuma ki.gudu

Ganin fa na shiga hannu,inda Allah yasoni ma na d’aura towel in”don Allah kayi hakuri yayan Khadija kuskure ne”

Kuskure ai baki isaba kinji na rantse

Kuka na fara ganinsa in yaci serious,Babu Wasa a fuskarsa da gaske yake b barina zaiyi naci bulus ba

“To Kayi hakuri”

Naki,ke Inna Miki Abu ai baki hakura

“Wallahih inayi kaji yayan khadija”

Bazanfa hakura ba malama

To me koma Zan maka Koh dukana zakayi ne?

Ah ah wanka Zaki mini

“Wanka”😳?

Eh Kinga Daman ba gani nake ba kullum.bayana baya fita

“Nima ai bana ganin bayana kuma ni ban iyya ma manya wanka ba”

Ah ah kina kallo Mana,Kuma Zaki koya

“Wallahih ni banason irin abinnan,  nace maka ka sakeni kanaji fa ana Kiran isha’i Kuma sai magana kake sani a bayan gida kasan ba kyau fa”

Tsakanin nida ke waya fara magana a ban d’akin nan tunda ba idone Dani ba, ba kallo Miki abin zanyi ba me na ihu harda kwara mini ruwa🤥

“Toh kayi hakuri kaji yayan Khadija wallahih mantawa nayi baka kallo”

Da gaske kina mantawa bana gani?

“Eh sosai ma,ai ba kowa.ke.ganinka yasan baka kallo ba”nace don ya barni

Ok wayo Zaki mini kenan harda wani yabona toh naki wayon in Kinga na barki kin fita toh kin zabi Daya a cikin ukun nan,

Koh ki wanke mini baya

Koh ki wanke mini Kai

Koh ki haske mini gemu

Lallai mutumin nan yaga wajen baccina nice ma Zan wanke Masa baya Kai Koh aski,

Toh Zan maka aski Amma sai gobe kasan yanzun dare ne bazaiyi kyau ba gashi ba NEPA Kai Kuma bakada shaver”

Kinyi Alkawari Zaki aske mini gobe?

“Eh”

Toh wanke mini

“Toh,ka sake mini hannu Mana saika zauna na wanke maka”

Na sakeki ki gudu

“Allah bazan gudu ba”

Ban yarda ba

Yace Yana Jan hannuta,ya zauna akan kujiran hannunsa na rike da nata

“Toh a hakan Zan wanke maka Kai kana rike da hannuna”

Ai Inna sakeki nasan guduwa zakiye

“Allah bazan guduba”

Toh tunda kikace Allah na sakeki,yace Yana sake Mata hannu

“Ina abin wanke Kai in”?

Gashe yace Yasa hannu a k’wandon soson nasa ya d’auko guntun soda,gashi nan

“Kana nufin da soda Zan wanke maka Kai”?

Eh man ba Yana kunfa da cire datti ba

“Uhmm Ina zuwa”,nace Ina kokarin nufar kofar band’akin

Kinye alkawari fa Zaki wanke mini,shine kike son gudu

“Abu Zan d’auko na dawo”

Toh yace Yana kokarin cire jikekken rigansa

Ina fita a band’akin na shiga d’aki bude akwatina nayi na d’auko Abubuwan wanke gashi, na Mata masu kyau da shaver,na dawo ban d’akin wayata na kunna na jinginasa da jikin gini matsowa  nayi inda yake zaune daga shi Sai wando dogo na jeans

Rangwafawa nayi na fara wanke Masa gashinsa sosai na zuzzuba Masa Abubuwan wanke Kai gashinsa mai yawa irin na Fulani,sosai ya fita nasa Masa Abubuwan laushin gashi cikin Yan minutes gashinsa yayi masifar kyau, shaver da na d’auko na saka Masa a fuska zan aske Masa gemu

Ke sumayya ragewa fa zakiye ba askewa ba 

“Na sani ai”nace Ina gyara Masa gashin gemun

Ina Gamawa nace NASA”ka duba Koh yayi”

Ina Naga idon dubawa sai dai na taba,ya Bata Amsa Yana tana fuskar sa, gaskiya kin iyya gyaran fuska

“Uhmm kasan me”?

ah ah saikin fada

“Ai…….ban karasa ba Jin ana kokarin shiga masallaci sallan isha’i yasa ban karasa maganar da nakeson Yi ba,

“kaYi sauri ka kwara ruwa ana shiga sallah”Ina maganar na fita a band’akin

Jin fitarta yayi wanka shap shap ya tafi masallaci

Yana fita ruwan wanka na Kuma ibo wa na Shiga band’aki,Ina wanka inata tunanin shin yau meke damuna ne Abubuwan da suka faru sai bani mamaki suke

Ina fita na shiga d’aki bayan nayi Alwala sallan nayi na kwanta akan kujira don yau ba karamin gajiya nayi ba don Koh girkin dare bansamu nayi ba gashi inason zuwa gidan Goggo Amina na duba Kan khadija yau kwata kwata ban ganta ba

Sai kusan 8 ya shigo d’akin, Sumayya kin kwanta ne?

“Eh Amma idanuna biyu”

Jin muryar ta saitin kujira,yasa ya nufo inda take 

Ina kallonsa harya ido wajen kujiran Yana kokarin zama mini akan kafafu da sauri na mike zaune na nade kafafun nawa”yanzun zama mini zakaye akan kafafu daban d’aga ba ka karyamin kasusuwa Koh me”?

Au kafarki nagun ne?ya  tamaya 

“Kaji nace maka Ina kwance sannan kazo zaka zauna akujiran”

Sanann yanzun kana tambaya ta Ina kwance ne”

Sorry yace Yana zama a inda ta d’aga kafartata, Sumayya!!

Na’am

Sumayya Ina Mai baki hakuri nasan tabbas band’auke Miki nauyin da ya rataya akaina a matsayina na mijinki b Ina Mai neman afuwanki wallahih Sumayya bani dashine shiyasa yau kwana biyu ban baki kome ba

“Ba kome ai nasan baka dashin ne sannan ni don na samu na sai Mana abinda zamuci ai ba kome wata Rana Allah zai baka kaima sauka sai mana”nace Ina kallonsa

Nagode Sumayya Allah ya saka mini da alkhari

“Ameeeeeen Daman jiranka nake kazo muje mu duba jikin khadija kasan yau ban samu zama ba tun safe”

Amma bakin gaji ba ki bari gobe Mana sai muje

 “ah ah  muje dai, gobe ma akwai masu zuwa kwalliyar bud’an Kai dana dinner har dare Ina busy”

Ok toh yace Yana mikewa

Hijjab nawa har kasa na d’auka nasa da karamin purse

D’aukar sandar sa yayi ya tsaya Yana jiranta a kofar d’akin

“Yau fa bazaka tafi da sandar nan ba atoh”

Akan me?

“Akan zaka fita Dani”

Ke asuwa?

“Asu masu ido” nace Ina kamo hannunsa ba musu  ya aje sandar

Tsaya na rufe kofar, yace

Sake Masa hannun nayi ya rufe mana kofar,Yana rufewa sake kama Masa hannun nayi Muka fita a shashen mu 

Tsakar gidan kaman ba dare ba duk jama’ar gidan na zazaune wasu a taburma wasu a kujira,nidai ganinsu baisa na sake hannunsa ba

Ke fasuma Wai me kika ganine a tare da miskini kike zaune dashi kamar auren tsafi,d’aya daga cikin Yan gidan Tama Sumayya gogar zana 

Ai toh auren tsafinne Mana inba haka ba mutun da arziki ya zabi Talauci,fasuma ta bata amsa..

Nikam ban tanka musu ba Donna fahimci Yan gidan nan sai shiriyar Allah don mutum Kam sai wani ikon Allah,tunda mutuwar inno Bai saka sun tsakaita da dambe da cacar baki ba ai hukuma ma bazata iyya dasu ba, kamar yanda Al’ameen yace

Waje muka fita,Ina rike da hannunsa muna tafiya,duk.inda muka wuce sai an bimu da kallo bare ga mazan unguwan da Basu sanni ba suna Daijin kwatance a bakin matansu,duk.madalisan da Muka wuce bin mu ake da kallo ga hasken sola ya haska Koh Ina, a hakan har muka shigo layin su Goggo Amina, na saima Khadija kankana da lemo,

da sallama a bakina na shiga gidan,don shi yace bazai shiga ba sai ammasa iso

“Assalamu alaikum”

Waalaikumu salam barka dai Sumayya sannu da zuwa Goggo Amina ta fad’a tana shimfid’a mini taburma

“Yauwa Goggo Ina wunin ku”

“Lafiya Alhamdulillah Sumayya kece da Daren nan”

Eh Goggo tare muka taho na fad’a Ina sunkuyar da Kai,(Wai kunya🤥)

Shine ya tsaya a waje ai aikin muhammad kenan kamar gidan bakonsa ne,kice ya shigo

“Toh Goggo” nace na koma kofar gida

“Ka shigo”nace Ina juyawa

Toh kin hanani rike sanda sanna kin tafi kin barni

“Yanzun bazaka iyya shiga da kanka ba”?

Eh bazan iyya ba

Uhmm kawai nace na Kama hannunsa da yake dare ne koma ba NEPA sai da muka kusa isa kusa da Goggo na sake Masa hnnu,

Zama nayi a taburman shi Kuma ya zauna a kujira,

Goggon Ina wuni?

Lafiya Muhammad hala kunzo duba khadija ne?

“Eh wallahih Goggo shuru yau najita bata zoba shine muka taho mu duba Koh kan nata ne har yanzun”?

Wallahih Sumayya ta fad’amin abinda ya faru,zaman gidan mu sai hakuri kuma.ku Kara hakuri kinji kome zai wuce

“Ba kome gaggo”

Aiko khadija kam.na kwance a d’aki yau Koh fita batayi ba Kai na ciwo ga zazzabi duka,Daman khadija akwai raki ku shiga ku duba ta,inji Goggo

Mikewa mukayi, muka shiga d’akin

Khadija ce a kwance tana bacci,

Fita mukaye don bamu tashe taba 

“Toh Goggo zamu tafi ga wannan ba yawa Allah ya Bata lfy wannan Kuma 5k ne yayanta ya bani Wai na baki koh gobe saita je asibiti”nace Ina aje laidan da na shigo dashi,hade da mikawa Goggo kudin

Wai Al’ameen d’awainiyane har haka daka bare Koh chemist taje goben sun Kara Mata wasu magani Koh na 200 ma

Al’ameen Kam mamakine ya kamasa yaushi ya samu kudi har 5k da zai bawa khadija,Amma Sumayya tace in jisa,

“Goggo taje asibitin dai zaifi tunda jiya chemist in ta fara zuwa ba’a dace ba”na fada Ina taka kafar yayan Khadija Jin yayi shuru baice kome ba

Am am gaskiya ne Goggo ki karbi kudin inyaso taje asibitin

Amma kudin yayi yawa ai muhammad

Ba wani yawa Goggo In change ya rage ku rike zai D’an rage muku wasu Abubuwan 

Kai Amma mungode muhammad, Sumayya Allah ya saka 

“Ameeeeeen” har muna hada baki dashi

Fita mukaye daga gidan Goggo Amina kafun na rike Masa hannu

Jin tayi hanyar titi ba hanyar gida ba yasa yace Mata Sumayya Ina zamuje koma bafa nan bane hanyar?

Sai da Kai zanyi nace Ina tare keke napep…………

Keke napep na sayar ban kulasa ba

Hajiya Ina Zaki?Mai napep in ya tambaye Sumayya.

“MEGA restaurant” na basa Amsa

Ok hau muje

Sumayya restaurant Kuma?Koh dai banji daidai bane? Al’ameen ya tambaye ta

“Daidai kaji,yau agun zamuci abincin dare,banyi girki ba”

Sumayya ai akwai wajen Saida abinci Koh round about ana sai dawa basai munje restaurant ba.

“Nidai gun zamu Kuma sai kaje”   

Wai hajiya bazaku hau bane? Koh nayi tafiya tane? ,kun tsaidani Kuna Bata mini lokaci ga dare nayi  

“Yi Hakuri.

 yayan Khadija muje”  nace Ina Kama hannunsa muka shiga keken        

 A MEGA restaurant, Mai keke ya saukesu

Biyansa nayi kudinsa bayan mun sauka,Kama hannunsa nayi muka shiga ciki,

Al’ameen Kam binta kawai yake baida baki ,sai dai yaji sun shiga wani waje Mai mugun sanyi sai Kuma D’an motsen jama’a d’aid’ai ku

Har lokacin Ina rike da hannunsa,D’aya daga cikin kujerun dinning table dake wajen,na nufa ja Masa kujera nayi”ka zauna”nace Ina zama a nawa kujeran

Ok , yanzun cikin inda muke nan shine restaurant in? ya tambaye ta Yana zama

“Eh Mana Hala baka taba zuwa ba”?

Nasan restaurant Amma bana shiga.

“Toh yau ka shiga”

Waiter ne yazo, sannunku da zuwa mega restaurant,ga list nan ka duba abinda za’a kawo muku,yafada Yana mikawa Al’ameen Takardan hannunsa

“Yauwa bani Anan”nace Ina karban list in.

“Me za’a kawo maka”? 

Duk abinda kike so, Al’ameen ya Bata Amsa

“Tamabyar ka fa nayi”

Amsa na b’aki 

“Ok toh a kawo maka tuwo Koh shinkafa Koh doya”?

Aban doya 

Ok,mikawa waiter in nayi hade da basa amsa”ka kawo plate biyu D’aya na doya da miyar kaza,D’aya Kuma fried rice with chicken  yaji vegetable sosai,in Kuna da exotic a had’a mana da ruwa”

Ok ma, an gama,ya karbi takardan in ya wuce

Sosai mutanen restaurant in suka bisu da ido tun shigarsu kowa yake gulman su da ido wasu Kam har kasa hakuri sukaye sunayi da baki,abin mamaki ya Basu ganin matsiyacin MAKAHO Koh suturar arziki Babu a jikinsa,mace Kamar Sumayya tana rike da hannunsa Koh tantama Babu daga ka gansu kasan ma’aurata ne,Amma kallo D’aya zakama Sumayya kasan ba karamar classic bane 

Bayan an kawo Mana abincin,tura Masa nayi nasa a gabansa shukali na Mika Masa”ungo shukalinka abinci na gaban ka”

Abinci muka faraci a nitse idon mutane na Kan mu sosai har abin ya takurani

Sumayya!!

“Na’am”

Nikam wajen nan akwai mutane sosai ne?

“Eh akwai Amma ba sosai ba kasan yanzun dare ne”

Amma dai kallon mu suke koh?

Mamakine ya kamani Amma na maze, “ah ah ba Wanda ke kallon mu kowa harkar gabansa yake,Amma meyasa ka tambaya”

Jikina ya bani ana kallo nane tunda muka shigon nan

“Aiko ba Wanda ke kallon mu”,na basa amsa

Taima ke kike kallona.

“Akan me Zan kalleka Kuma”😒?

Waya sani Koh kyau na Miki,Kinga dogon hanci

“Ina abin yake bare a yabasa”

Abinci muke ci muna Hira har muka Gama Amma dukan mu bamu cinye duka ba,

list aka akawo mana,na duba kudin mu dubu 3,800 ne, bude Purse nayi nabiya kudin, ordern ice cream nayi aka Mana takeaway a laida

Mamakine ya Kama Al’ameen yanzun abincin da sukacin nan shine 3800 ,ai cefenen dubu uku da dari takwas zai musu wata ma suna dafawa.

Suna fitowa a restaurant in ganin titi ba napep yasa Sumayya duba wayar ta

Karfe 10:3 na dare ne,”asaifa mun jima a wajen nan 8 fa Muka bar gida”

Gaskiya Kam Kuma bana majin dirin machine sai mototi

“Ba machine Kam sai dai mu taka da kafa”na basa amsa Ina Kama hannunsa muna tafiya inda Allah ya somu ma tsakanin sintali da mega ba nisa sosai 

“Nikam azumi saura wata nawane”?

Saura sati nawa dai?ya Bata Amsa

“Satitika kenan baikai wata ba?Ashe shiyasa aketa aure aure”

Gaskiya Kam saura sati uku da kwana hudu

Lalle kam,”kasan yanzun haka gobe, za’a yi bud’an kan Amarya da yamma,sai ayi fitan Angonci duka,da dare Kuma dinner,Kuma nice duka Zan musu kwalliya, shiyasa nake son in Allah ya kaimu gobe sai ka nemo mini yaro yaje Mana kasuwa Ina son Gama girki da wure”

Yaro Kuma wani yaro.kike ga Zan iyya aika a unguwan mun nan har kasuwa ,sai dai naje kawai tunda khadija ba lfy.

“Toh Allah ya kaimu,ni chemist ma nakeson mu shiga nasai maganin gajiya,Amma dare yayi”

Ah ah Sumayya da kankantan shikarunki karki Bata shi dashan maganguna, don kina aikin gajiya,in Kika riga Kika saba,toh zai biki Koh yaushe kikaye aiki sai kinsha 

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 4 HAUSA NOVEL”


“Gaskiya ne Amma wallahih bayana ya tokare ni sosai,gashi yanzun ma sai tafiya muke da kafa”

Da kafa suka taka har sintali suna tafiya suna Hira,Dayake gidan Adara ba’a rufesa Koh karfe d’ayan dare ne yasa suka samu kofa a bude,

Shigan su, suka shige shashen su bakin su d’auke da sallama

Al’ameen ne ya bude d’akin 

Muna isa ruwa na iba duk yanda nake tsoron toilet in dare yayi Amma zafin da nakeji Bai barni naji tsoron ba,

band’akin na shiga na kwara ruwan na fito,

d’akin na shiga.

Al’ameen na zaune a Kan kujera Yana jiran Sumayya ta fito shima ya shiga Wanka don yaukam ba NEPA an d’auke

“Assalamu alaikum”nace Ina shigowa d’akin

Waalaikumu salam, gaskiya yau Kam Alhamdulillah akwai.zafi Kam

“Gaskiya ni a waje ma zanyi shimfid’a yanzun”

Ok.bara nayi wanka daidai kinyi shimfid’ar?yace Yana fita a d’akin ban d’aki ya shiga bayan ya ibi ruwan shima

Yayan khadija na fita na saka.kayana saboda zafin da ake have vest na saka ,da wandon bacci fankalele shara shara har kasa,kayan shinfid’a na fitar na shinfid’a mana darduma a baranda na shinfid’a zanin gado da filoluka, kwanciya nayi a gefe tsabar gajiya Koh hula ban saka ba,bayana sai damuna yake koh bacci na kasa.

Yana fitowa d’akin ya shiga 3quiter yasa Koh riga baisa ba ya rufe kofar, ya nufi inda yake kyautata zaton agun ta musu shimfid’a

Ina kwance Ina kallonsa harya matso inda nake kwance hannu yasa ya tattaba shimfid’ar sai Kuma ya fara laluben Kan shinfid’ar  bayan ya xauna.

Jin ya tabata yasashe Hawa Kan shinfidar kwanciya yayi a Gefen pillow n da ta d’aura kanta akai

“Bakaji pillow da na aje maka bane”

Naji Mana Amma a naki nakeson kwanciya

“Kaga ka rabu Dani jikina ciwo yake mini”

Hannu kawai naji yasa a bayana Yana mammatsa mini baya,naso hanasa amma Jin yanda message in ke kauda tsamin da bayana yake mini yasa nayi Shuru

Yana ta mamatse Mata baya da kafa duka har yaji tayi bacci, gyara Mata kwanciya yayi,daga kefuwarda tayi shima ya kwanta a Gefen ta bacci ya d’aukesa.

Misalin karfe biyu na dare ya farka Jin iska na kad’awa ga kamshin kasa na tashi bude ido yayi sosai, ya mike zaune hannu yasa ya taba Sumayya Aiko tana kwance Koh juyawa Bata sake ba tun gyarata da yayi, Sumayya!! Sumayya!!

“Ummmm menene”nace cikin magagin bacci don harga Allah yau dai baccin gajiya nake

Ana iska ga hadari,ki tashi mu shiga d’aki

“Da wani idon kaga hadarin ni wallahih ka barni nayi bacci”,na fada Ina gyara kwanciya

Sumayya ruwane fa da gaske

Shuru na Masa abina na koma bacci 

Jin Taki tashi yasa ya mike key ya d’auka ya bude d’akin, d’aukarta yayi a hannu a hankali yake tafiya Yana lalube harya shiga da ita d’akin,Kan gado ya haura ya kwantar da ita,Jin an Soma yayafi da sauri ya fitoh a d’akin shimfid’ar su ya tattara ya Kai d’aki randar robansu ya zubar da ruwan ya hada da bokataye ya jejjera a bakin baranda,daidai lokacin aka fara ruwa sosai Kamar me .

Alwala yayi ya shiga d’akin sallaya ya d’auka ya shimfid’a wa yayi ya Tada kabbara,lafilfilu yake har kusan karfe uku na dare kafun ya kwanta shima a gefenta 

 *Washe gari*

Kamar kullum yaukam da safe kudi na basa yasai Mana manya manyan gongomin Madara da bornviter  na sai suga Rabin kwano Lipton kwali d’aya na had’a da cornflakes,dashi muka karya ya fita

Al’ameen kam yasan baida abinda zaiyi haka ya fita yaje ya zauna a bakin titi ya rasa mafita Allah ya gani Yana iyya bakin kokarinsa wajen niman abinda zai rufawa kansa asiri,Amma abin yaki yasan kome na Allah ne Kuma Bai manta dashi ba a hakan ma yana kara godewa Allah tunda Sumayya nada rufin asiri da ace Bata sana’a a war yanzun da kayan abincin ta ya fara karewa baisan yanda zaiyi ba.

***********

Khadija ce ta shigo bayan sallan azahar lokacin Ina kanwa matan da suka zo make-up, Assalamu alaikum

“Waalaikumu salam” dukan mu muka amsa Mata

“Ah ah khadin Goggo idonki kenan”?nace Ina kallonta sanye take da atamfar dana Bata riga da zani sai gyle da takalmi harda jaka sai laida Mai tambarin asibiti a hannunta sosai tayi kyau fuskarta tayi fayau alamu dai batajin dadi,abinka da farin fata

Wallahih Aunty na fitoh asibitine nace bara dai nashigo yau Goggo takece mini kun shigo da dare Ina bacci.

“Eh wallahih mun shigo da yayanki nace abarki kawai kar a tasheki”

Allah sarki,tace tana gaida matan dake zazaune suna jiran na Gama wa Wanda

 nakema make-up 

“Khadija ki shiga d’aki Mana akwai NEPA ki jona kittle akwai kayan shayi asaman freezer”

Aunty bazan iyya shaba bakina ba dadi Sam shiyasa koh abincin dare ban iyya ciba Haka karyawa ma.

Ah ah khadija dadai kin daure kinsha shayin Daya fi Amma ace bakinki ba Dadi saiki kicin abinci,ai ko magani in ba abinci baya aiki,D’aya daga cikin customers nawa ta fad’a

“Gaskiya ne  khadija,ki shiga in kinsha saiki kwanta ki huta”

Toh Aunty tace tana shiga d’akin, kittle in ta d’auko ta zuba ruwa ta jona,shayi ta hada kad’an ta iyya Sha ta balle maganin Tasha  kwanciya taye  lokaci D’aya bacci ya d’auke ta

Sai kusan 4:30 na Kamala wa sauran kwalliyansu Daman Amarya tun 3 na yamma na Gama Mata saboda bud’an Kai,

Gaskiya yau  na damki rabona mutane kusan goma nama makeup heavy make-up

Simple make-up

Light make-up

Duk yau ba Wanda banyi ba sosai na samu kudi 50k yau na damka nan ma banyi na dinner ba kenan.

Misalin karfe biyar khadija ta mike zata wuce gida Aunty nikam Zan wuce sai gobe 

“Toh khadija Allah ya Kara lafiya ga wannan ki D’an samu abinda kike bukata ki Saya dashi” nace Ina Mika Mata 10k

 Aunty ki barshi kawai d’awainiyar tayi yawa jiyama fa Goggo tace mini kun kawo Mana 5k naje asibiti danaje in ma,Ina saurayin da nace Miki yazo guna?

“Eh na tuna har kikace bazaki fita ba”na Bata Amsa

Ashe Dr ne Ina zuwa na gansa shine ya sayo mini magani  kyauta,

“Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari”

Ameen Aunty

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 5 HAUSA NOVEL”


Hey

“Wancan yayan kine ya baki wannan Kuma nawane,ki karba khadija kid’an Saya Abubuwan da baki dasu”

Gaskiya Aunty nagode Allah ya saka da alkhari,tasa hannu ta karbi kudin

“Ameen khadija”

Yauwa aunty nace Koh Zaki aje mini tunda Naga azumi ya kusa Inna tashi zuwa kasuwa saina karba naje na sai kaya,samun na samu dinki da wure?

“Ah ah khadija insha Allah, Allah zai Bud’a Mana har yayanki ya sai Miki kayan Sallah, wannan dai ki sai Abubuwan bukata irinsu kananan Kaya da mayuka Turare pad omo sabulu ke dai irin Abubuwan bukatar Yan Mata haka”

Toh shikinan Aunty Daman bani da kananan Kaya sai na saya pant biyu Brz sai vest shima biyu Amma na gwanjo Zan Saya aunty sauran chanjen, Ina materials da ake yayi yanzun ana yankawa a dinka dogayen riguna dasu?

“Eh khadija”na gane su 

Yauwa yadi d’aya dari uku su Zan Saya kala biyar na dinka 

“Gaskiya khadija kinye tunani Mai kyau kema saiki samu na chanjawa kwana biyu”

Toh Aunty Zan tafi nagode Allah ya Karo customers

“Ameen khadija yanzun ma wasu na zuwa da dare maganar dinner aike alkhari ce tunda sanadin ki nake samun kudin”

Ah ah Aunty Allah ne ya tsaga da rabonki , shiyasa kike ci

“Hakane Kam khadija” nace Ina shiga kitchen da sauri nake na d’aura Mana abincin da zamuci

Bayan fitar khadija girki na Gama na juye Mana a kula,sai goshin mangari ba yayan Khadija ya dawo

Sumayya sannu da gida?

“Yauwa sannu yayan Khadija sai yanzun”

Eh wallahih ya aiki?

“Lafiya klau” nace Ina kallon sa ganin Kamar a cikin damuwa yake

D’azun Bashir wani makwancin mu ke tambaya ta Wai MATAR sace taji labarin Wai kina lalle ke kikama Asma’u na aure shine Wai yake tambaya ta zata samu lalle gobe,make-up jibi da Rana?

nace ya bari saina tambaye ki inyaso in mun hadu a masallaci anjima na fad’a Masa amsar ki.

“Lallen me za’a ma MATAR tasa”?

Suna ne haihuwa tayi jibi suna

“Gaskiya nifa bazanje home service ba,in mutum nason lalle Koh kwalliya yazo ya same ni a gidana”

Amfa Sumayya haihuwa ne ya za’a yi mace maijego tazo lalle gidanki?

“Wallahih yayan Khadija ni raini ne banaso a rayuwa na kar mutun yaga kaje Masa lalle ya Raina ka” 

Kai Sumayya ba wani raini ai sana’a ce ta kaiki ba maula ba,ki daure kije ki Mata kinji?

“Shikenan Allah ya kaimu goben Amma bansan gidansu ba da yamma ta tura yaro yazo ya kaini”

Sumayya har yamma?ya tambaye ta

“Eh man saina Gama aikina,Koh so kake na tafi da safene,jibine fa sunan”

Toh shikenan Allah ya kaimu yace Yana mikewa ,ruwa ya ibo a boket ya shiga bandaki

Muna idar da sallan mangariba Koh abinci bamu ciba Yan make-up na dinner suka zo su biyar ne dukansu harda Amarya heavy make-up suke so,Dole tasa na hakura dacin nawa zuba Masa nayi na d’auko Masa ruwa a freezer na jira Masa,a d’aki na fitoh waje,don ni bana saka baki a dakina Sam kowa ya zauna a waje kawai

Sai da yaye isha’i kafun ya shigo gidan, gaisawa sukaye da customers nawa,don na fahimci yanzun mutane na ganin kirmansa tunda kofarsa suka shigo

“Abincin ka na d’aki yayan Khadija”nace Masa ganin ya nufi d’akin kar yaje ya zubar da abincin tunda a kasa na jira.

Toh yace Mata Yana shiga d’akin

Make-up na Amarya na fara, Gamawa ta biyani akazo aka d’auketa saura hudun ma duk na Gama musu kafun 9:00,kudin da suka bani 25k Inna hada Dana d’azun kusan dubu saba’in na samu kenan Alhamdulillah yau kawai na tashi da kudi dubu sittin da biyar in aka cire 10k Dana bawa khadija

Wani tunanine ya fado mini akan kudin, murmushi kawai nayi na nufi d’akin

Ina bude labulin idona ya sauka Akan plate inda nasama yayan Khadija abinci nakai dubana garesa da mamaki ganinsa a………….

Al’ameen ne, Sumayya ta gani zaune ya zuba tagumi Koh abincin Bai d’and’ana ba.

Cikin mamaki ta karaso cikin dakin”yayan Khadija lafiya kuwa”? tace tana matsowa kusa dashi  

Firgigit ya dawo hayyacinsa,  Sumayya har kun Gama kwalliyar?

“Eh mun gama,Naga bakaci abincin kaba Allah dai yasa lfy Koh” ta Kara tambayar sa.  

Lafiya Sumayya jiranki nake  in kuka Gama saimuci”ya Bata Amsa

Da mamaki sumayya ke kallonsa”banace kaci ba”? 

Sumayya na kasaci ne, kece Kika nema Kika dafa Taya zanyi na rigaki ci bayan ke kina ta faman aiki.

“Karka Kara fad’amin irin wannan magana daga yau”

Don me?ya tambaye ta

“Saboda duk abinda na baka ni gani nake kamar kaika bani mukeci banason Kara Jin irin maganar nan,Ina zaune itdakai ne badon kome ba sai don Allah,rufin asirin ka nawa ne nawa nakane”ta fada tana kallonsa

Shikenan Sumayya nagode,

“Bana bukatar godiyan ka ka gode Allah”tace tana matsowa kusa da abincin budewa tayi tasa shukali”Bismillah muci”tace tana iba 

Toh yace Yana laluben nasa shukalin

Abinci sukaci Amma cikinsu Babu Mai magana kowa Yana cin abinci ne,bare Hajiya sumy 

Suna Gama cin abincin Al’ameen ne ya tattara Kwanukan yafita dasu waje 

Sumayya Kam wanka ta shiga,tana fita tayi Alwala,kayan bacci tasa ta kwanta 

Al’ameen Jin ta kwanta yasa shima fita wajen ruwa ya Iba yayi wanka.kamar yanda yazamo musu Al’ada wankan dare kafun su kwanta,Yana fitowa ban d’akin kofar shashen su ya rufe,ya shigo d’akin,rufewa yayi a hankali yake takawa Yana laluben gadon harya iso, Hawa gadon yayi ya kwanta a hankali,

Sumayya Kam mamakine ya kamata ganin sa a hakan Sannan yahau gadon ma Bai Saba Mata yanda yake Mata ba, watoh son mannuwa kusa da ita.

A hankali ta mirgina kusa dashi hannu tasa ta Kama NASA hannun”yayan Khadija”

Cikin sanyin halinsan nan ya amsa mata, na’am.

“Menene yake damunka ne Wai” ?

Ba kome Sumayya me Kika gani?ya tambaye ta Yana Mai dagota ya d’aurata a jikinsa gabaki d’aya

“Ba kome, yauwa nace kanada National ID card ne”?

Sai dai voters card bani da National ID card

“Ok shima zaiyi Daman inason na bude account a bank ne kasan banzo da details nawa ba”

Toh shikenan Allah ya kaimu goben saina baki 

“Zaka rakani bank in? Koh naje da kaina”ta fada tana gyara kwanciyar ta akansa 

Duk yanda Kika gani goben ne Zaki bank in Koh yaushe?

“Sai na Gama lallen da akayi booking innan”

Toh shikenan Allah ya kaimu saina rakaki,in khadija taji sauki Kuma sai kuje tare kinsan me?ya tambaye Sumayya

“Ah ah”

Khadija na son zuwa bank Kamar me haka lokacin kudin covid 19 ta dameni Wai sai naje mun bude account muma,mun cika Koh zamu samu kudi,Amma da mukaje bank hanani Shiga sukayi security Wai ba’a bara a banki,Kuma su tsaya su saurare mu sunki Haka suka kuramu waje.

Sosai naji maganar ta tabamin rai”aiko Insha Allah da ita zani taga bank,Amma kaima fa Dole zamuje tare tunda account Kai za’a budewa ba niba.

Toh Allah ya nuna Mana yace Yana zura hannunsa a cikin rigan bacci dake jikinta

Jin hannunsa a riganta unexpected yasa ta zabura sai Kuma ta koma ta kwanta a hankali ta lumshe ido Jin abinda yake Mata da hannunsa a cikin riga”kasan me”?

Ah ah ya Bata Amsa

“Nikam Ina ga Zan Saida laptop Ina da waya”

Akan me Zaki saidasu toh?

“Saboda Banga amfanin suba inba kallo ba me nake dasu shiyasa Zan sayar”tace. Tana taimaka Masa ganin Yana kokarin zare rigar Tata

Umm umm Sumayya waike bazaki ringa d’aukar kwalliya kina sawa a media ba Koh Allah zaisa asamu location naki Kinga ai sai afi saninki sosai a Jala

“Kasan ba kowa keson  asa hotonsa a social media ba shiyasa ban fara posted ba,Nima nayi wannan tunanin”

Eh ai tambayan su zakinayi Zaki d’aura hotonsu kiyi Tallah Amma fa Yan Mata banda matan aure, insun Amince shikinan,tunda wasu da yawa in sunyi kwalliyar ma post suke.

“Gaskiya ne Amma waya fad’a maka ana d’aura kwalliya a online?

Kuma ya akayi kasan ana Post”?Sumayya ta tambaye sa tana kakkama Masa gashin kai Jin wani magic dake bin jikinta a sanadin abinda yake Mata

Uhmmm ai inaji ana Hira koma ni lokacin da na makance ma waya tayi araha a hannun kowa ba,Kamar yanzun

Washhhh toh,uhmm tace tana zillewa daga kansa ta sauka a gefe.

Jin ta zame yasa ya bita shima, tana kwanciya ya kwanta akanta rumfa ya Mata da kirjinsa,ya had’a fuskarsa da Tata fuskar yayi Yana tsintsinar bakinta,dake kamshi 

“Wayyo ka sauka nauye”tace tana mutsu mutsu tana damke damtsen hannunsa

Shagwaba Koh bafa nauyina na d’aura miki ba

“Nidai ka sauka,kawai tsoro nakeji”

Tsoron me?ko ni dodone?ya tambaye ta Yana Mai Kara matsota garesa

“Ka sauka”

Naki,yace Yana Kara Danna kansa akanta

“Nifa bacci nakeji kaji muye bacci”

Nikam banajin bacci

“Nikam ai inaji Koh”?

Sai kiye ai na hanaki ne?

“Amma ai ka tokareni”

Shuru ya Mata yaki kulata sai bidirinsa yake a kanta jifa jifa tana taimaka Masa 

Jin abin NASA ya fara yawa yasa ta fashe Masa da kuka

A tsorace ya mike a kanta sauka yayi gefe cikin tsoro,yake tambayar ta,ke Sumayya menene,Yana tattabata yaji Koh lfy

Saura kad’an dariya ya kubucewa Sumayya Jin yanda duk ya tsorata dagajin kukanta kawai,ta rasa ma wani irin namiji ne Mai shegen tsoro haka

“Toh ba Kaine ba nace maka inajin bacci sai matseni kake”ta fada da muryar kuka tana kallonsa tana Masa gwalo ganin yanda sai zazzare ido yake kamar kace kittt ya ruga

Shine abinda ya saki kuka?

“Eh Mana”

Toh Yi hakuri kwanta toh.

Dariyace ta subuce mata Jin abinda yace Yana kwanciya a gefenta baima mannu kusa da itaba

Cikin mamaki ya Tashi zaune Jin tana dariya, Sumayya Anya lfy kuwa daga kuka saiki koma dariya?

Shuru tayi gudun karya harbo jirginta”babu kawai ji nayi kamar jakulkule ake mini a ciki”

Shuru yayi baice kome ba illah rufe ido da yayi Yana nazarin Rayuwa yau Wai shine da Mata,Ashe haka zama da mace yakeda Dadi duk halinda kake ciki muddin ka samu mace na gari ka Gama samun Jin dadi,duk halinda namiji zai shiga mundin dare yayi zata ga tayi kokarin kauda damuwar tasa Koh Bata cireba,zatayi iyya bakin kokarin ta taga ta d’auke Masa hankali

Jin yanda Sumayya keta motse yasa shi kiranta, Sumayya!!

“Na’am”ta amsa tana gyara kwanciya

Bakiyi bacci ba?

“Umm banyi ba”

Saboda me?

“Haka kawai”

Jin Amsar da ta basa yasa a hankali ya matso gareta,lumshe ido tayi Jin yanda tsikar jikinta ke tashi,Jin gashin kirjinsa na goguwa da bayan ta

Hannu yasa a hankali ya Kama waist inta d’an zabura tayi kad’an,yasa hannu ya maidata,watoh kukan shugwaba Koh?

“Bawani shugwaba,Kuma ni ba shagwabebbiya bace atoh”

Shugwabebbiyace Mana ai duk lukutaye akwai shagwaba

“Waye lukutar”?ta tambaye sa tana juyowa suka fuskanci juna

Daga Sumayya har Al’ameen wani yanayi sukaji a tare da junan su sosai kusancin su yayi yawa akwance da suken nan

Kece Mana, lukuta kiga nan naki fa Kato,yace Yana Kama Mata bombs,

Hannu tasa ta buge Masa hannu”ai naka yafi nawa girma”

Zare ido yayi Kamar tana ganinsa,ai Dana shiga uku ai,sai wando Mai shape za’ana dinka min.

Hhhhh Sumayya ta Kama dariya “Wai wando Mai shape waya ganka kana tafiya kana murgud’asu a cikin jallabiya”ta karasa maganar da kamo hannunsa dake Kan kirjinta don wallahih kirjin zafi yake Mata 

Shi Karan kansa Al’ameen abin sai da ya basa dariya,Amma yakiye, murmushi kawai yayi,Jin ta Kama Masa hannu kafarsa ya daura Mata akan kafa.

Kokarin mikewa ta fara har lokacin hannunsa na rike a nata Wai don karya taba Mata inda bataso

Jin tana kokarin tashi yasa sa tambayar ta,Ina Zaki Kuma dare fa yayi.

“Rigata nake nema”

Kiye me dashi?

“Me ake da riga”

 Sawa, ya Bata Amsa

“Nima sawan zanyi”

Nikam gaskiya banso kawai mu k’wanta haka.

KARANTA: “MATAR MAKAHO PART 6 HAUSA NOVEL”


“Jikinka Koh nawa?wato mu k’wanta haka ka karasani ba”

Sorry zafi yake mikine?

“Eh Mana duk ka mammasa mini jiki”

Amma ai kinji Dadi

“Banjiba”ta basa amsa tana mikewa zaune

Ai da sauri yasa hannu ya rike Tata hannun,yana kwance  Bai tashi ba,kiyi hakuri mu k’wanta haka ba abinda Zan sake Miki.

“Ai kasan bakyau kwana ba Kaya”

Menene a jikinki Koh tsirara kike yanzun?

“Rigan fa”

Ai nace bazan miki kome ba yace Yana jawota jikinsa matseta yayi a hankali ya jawo blanket inda ke Kan kadon ya rufe jikinsu.

***********

Washe gari Kamar kullum bayan Al’ameen ya dawo sallan asuba, sunnah TV Sumayya ta kunna musu daga ita harshi in suna kwance suna sauraron wa’azi.

Sai wajen 7:3pm Sumayya ta mike shara tayi yayan Khadija ya Mata wanke wanke, ruwan zafi ta jona abuta,Yana tafasa ta juye a boker tasawa yayan Khadija nasa, ta shiga ban dakin

 tana fita yayan Khadija ma wanka ya Shiga.

Vayan sun Gama shiryawa kudi ta mika masa 1k”ka sai Mana egg’s guda biyar sai bread na 500 Mai kyau ka hada Mana da butter “

Karban kudin yayi,ya fita.

Bayan ya sayo k’wai da bread, soya k’wai in Sumayya tayi ta hada musu cornflakes ga tie,jira musu tayi a kasan cafet,kamo hannunsa tayi suka zauna a kasa, bubude abincin tayi”karbi shukalinka”

Toh yace Ya karba shukalin ,tattaba plates in yayi Jin plate biyu ne ga bowl d’aya ga cups biyu,wannene abincin nawa Naga Kwanukan da yawa?

Duka zakaci d’ayan soyayyen k’wai ne d’ayan bread ne da butter a jikinsa sai Kuma bowl na cornflakes,sai cups na tie”nace Ina tura Masa plate in k’wai a gabansa”kaci kwai sai kana Had’awa da tie ga bread”

Shikam Al’ameen ya kasa magana Wai karyawane da abinci Kala uku shi Al’ameen,ganin Al’ameen bai fara ci ba ita har tayi Rabin cup na tie inta yasa ta aje kofin,hannu tasa a cikin k’wai in ta yagi babba ta tura Masa a baki

Shikam Jin abinci a bakinsa da Kuma yatsarta sai faman tura Masa take yasa sa cizon yasan kad’an,

Ai Kara ta sake hade da yarfa hannun nata”wayyo yatsana jini jini yake na bunu tace tana duba hannun”.

Da mamaki Al’ameen yace jinii ma Sumayya?

“Eh gashi shikinan ya gusuramin yatsa”

Mu gani

“Bazaka gani ba sai kace idone da kai”

Toh muji.

Bazakaji ba din,tace tana daukar kofin shayen ta

Jin tayi Shuru yasa sa gutsurar bread Mai butter,Wai zai Bata itama d’ayar hannun nasa yasa ya lalubo fuskarta,Jin fuskar Tata yasa ya fara lalubar bakinta da hannunsa

“Kasan Allah Inka samin hannun hagunka a bakina ba”tace ganin Yana ta tattaba Mata baki da hannun nasa

Kayya abinci Zan baki,yafada Yana Mika Mata gutsuren bread inda ke hannun damansa a baki,

Rufe bakin tayi Taki budewa.

Shikam sai goga Mata bread in yake a lebe gashi duk butter ya Bata Mata fuska

“Kanata Bata mini fuska da butter”tace bayan ta rike hannunsa

Toh ba kinki bude bakin ba sai kokari nake,

Kaga kaci abincin kan, ka barni naci nawa,tace Masa tana goge fuskar ta 

Toh ki bare na baki wanann kawai kinji

Ganin yanda ya nace Mata yasa ta bude bakin Yana saka Mata bread in da sauri ta datse hakorin ta,Wai don ta cije yatsarsa shima abin mamaki da sauri taga ya cire hannunsa kafun ma hakorinta ya Sauka akan yatsar,Yana dariya

Ai Daman nasan saikince Zaki Rama shiyasa Nima nayi taka tsamtsam da yatsana.

Shuru ta Masa Bata tanka masa ba.

Haushi ya shigane bakutuwa?

Kara ta sake tayi kansa “nice bakutuwa”

Jin ta hafto, yasashi Kare kansa, hannu yasa ya tare fuskarsa.

Ganin haka sai abin yayi mugun Bata dariya waishi harga Allah tunani yake wani abin zata Masa haryana tare fuska.

Jin shuru baiji tayi Masa kome ba yasashi fara laluben ta Aiko ya jita a kusa dashi,da sauri ya rikota, sorry kinji

“Ni……shuru tayi Bata karasa ba Jin sallama a kofarsu amsawa tayi ta mike kaci abincin kafun na dawo”

Toh yace Yana saka hannunsa ya d’auki cup inda ta aje masa…

Sumayya tana fita taga wata budurwa irin classic innan zata Kai kusan sa’ar ta kyakkyawace Amma baka Tasha kwalliya tana rataye da school back “sannuki da zuwa”tace Mata tana shimfid’a musu darduma”Bismillah ki zauna”

Yauwa Ina kwana?bakuwar tace tana zama akan sallayar

“Lafiya ykk ya gida”?

Lafiya Alhamdulillah,ya aiki?

Lafiya klau,Ina zuwa Sumayya tace tana mikewa d’akin ta shiga ta hada cornflakes da ruwa  Daya a fijrij ta hada a tire ta kawowa bakuwarBismillalahih ka  abin Kari ba nauye Kam”tace tana ajemata a gaba

La d’awainiyane haka Allah dakin barsa yanzun na fitoh gida zanje school ne ma nace bara na biyu dai ta gidanki

“Allah sarki Amma dai ki saka Koh albarkane yafi dai kikici bazanji Dadi ba”

Shikenan bara dai NASA albarkan tunda kin Masa tace tana iban cornflakes in da shukali uku tayi tace Alhamdulillah

“Badai harkin koshi ba”?

Alhamdulillah wallahih ya isheni,suna na kamila Ina zaune a unguwan gadi,Daman nazone wajen ki in Babu damuwa inason zan fara Training in make-up,Naga wanda kika ma kanwata a auren Asma’u shine nace tamin kwatancen gidanki  inyaso sai nazo inji.

“Toh gaskiya ni bana koyarda make-up saboda bani da shago sai gidana Kinga Kuma Ina da ayyuka yau da gobe”tace Mata tana tunanin ta yarda ne Koh karna yarda

Ba damuwa sister Nima Ina zuwa school Kinga saiki bani time inda zanna zuwa Koh ki ban number ki duk lokacin da kike free sai ki kirani Koh Kika samu Yan make-up.

“Shikenan yanzun dai ki bare Inna ma mijina magaa in ya Amince xakiji daga gareni”

Ok ba damuwa saiki bani contact naki Koh in ba damuwa sannan nawane kudin da Zan biyaki Kinga Inna koma Koh yaushe Kika kirani saina tawo dasu

Toh, make-up dai kashi kashine sanann yanayin kwakwalwar mutum wata a wata D’aya zata koye make-up wata biyu wata fiye da uku ma Bata iyya ba so ni bansan ya yanayin d’aukar kwalliyarki ba Amma dai inso samune wata uku kina koya”

Ok yanzun wata ukun nawa ne kudina

“50k Koh wani wata kudinki na wata uku 150k kenan”

Wai habba sister kudin nan yayi yawa Mana dubu dari da hamsin,

Gaskiya kenan Kinga a cikin kudin Zan Saya make-up kit sabo duka,saboda bazaiyu Ina baki na aikina kina koya dashi ba, sanan infa kika iyya a kwana uku Zaki iyya samun sama da kudinda Kika biya na koyo”

Hakane Kam Amma dai ki duba ki rage mini kinsan baban mu yace in zaiyu nida kanwata zai biyawa.

“Shikenan Zan rage dubu goma”

ok shikenan an gode saina jiki

Shikenan bara na baki number,daidai lokacin Al’ameen ya fito d’akin hannunsa rike da cup inda yasha shaye

What?? wa nake ganin nan Kamar  Muhammad Al’ameen Yusuf bakuwar tace tana zare ido

A matukar razane har bakin sa na rawa yace kamilaaaaa………..

Back to top button