Hausa novels

Abban Sojoji Chapter 6 Complete Hausa Novel

“`The father Of Soldiers“`

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

 Kallon juna suka shiga yi, ganin cewa ya toge yasa ɗaya da cikinsu sake yi masa magana cikin lallami ” tell me why do u want to go out ? if u need something i can go and buy it for you ,”

Jin hakan yasa junaid jin sauƙi aransa, hannu yasa ya zaro kuɗi kusan dubu goma ya miƙa masa sannan ya cije ya daure ya ce “pads nake so na mata kwali guda sannan panties dozen ɗaya bansan size ɗin ba amma karya wuce na ƴar 17 years ”

tsananin mamaki ne ya kamasu jin yace pad da panties, amma basu ce komai ba saboda baya a tsarin aikinsu fira ko tambaye tambaye da ɗan masu gida,

“Sojan yace shikenan, ka koma ciki nan da 15 minutes sakonka zai iso,

Amsa yayi da cewa “thank you i will be waiting,”

Sannan yaja motar a hankali yayi baya da ita ya karya kwana ya koma ciki,

A bangaren sehrish kuwa tagama galabaita, ta jigata sosai tarasa uwar ubanta , sai faman zarya take tsakanin toilet da bedroom , daga taji ya zubo sai taje ta wanke ta dawo ciki yana ƙara zubowa sai ta koma da gudu tana kuka 😖

 

Junaid sai faman zagaye zagaye yake yi acikin babban falon yana jiran dawowar sojan da ya aika, sai faman zullumi yake yi gudun kada yarinyar ta halakar da kanta da damuwa saboda ya lura ta tsorata sosai,

Knocking yaji da sauri ya ƙarasa bakin kofan shiga falon , sojan ne ya dawo hannunsa ɗauke da kwalin pads tare dozen na pant kamar yadda ya umarta , hannu junaid yasa ya karba yana zabga masa godiya,

Sergiant ɗin yace “ga sauran chanjin ” ko dubu biyar bai kashe ba a siyayyar junaid yace ” bana buƙata”

Yana faɗin hakan ya kama hanyar da ɗakin sehrish yake,

murmushi sojan yayi tare da cewa a cikin zuciyarsa “lallaine yaro! iyayenka sun tara ma kana daga zaune kana shan iskar A.C,’

yana faɗan hakan ya juya ya fi ce,

Cikin sanɗa yake tafiya time ɗin da ya isa kofan ɗakin tsawa yayi jikin door ɗin yana sauraren kukanta tana cewa ” Ya Allah kadauki raina na huta, narasa me zanyi bansan menene ke faruwa da ni ba, jini ko ina ya ilahi.

 

 

 

lumshe idonsa yayi tare da buɗe su lokaci guda, hannunsa na rungume da kwalin pads ɗin ga panties ɗin dake cikin leda asaman kwalin ya haɗa ya rungume a ƙirjinsa,

“Junaid ynx taya za’ae ka kai mata wannan ? Shin zata ji daɗi kuwa idan ta gane cewa ka gane cewa ita maca ce ba namiji ba? mezai faru idan tagane cewa ka ganta acikin wannan yanayin zata ji daɗi kuwa !?

Natsuwa yayi yana sauraran abunda zuciyarsa ke sanar dashi , rufe idonsa yayi tare da cizon red lips ɗinsa yana mai jin takaici gaza shiga yakai mata taimakon gaggawa, ga kukanta da yake ji ba ƙaramin hurting ɗinsa yake yi ba, tausayinta yake ji saboda bata da kowa anan da zai taimaka mata in bashi ba dayasan halin da yake ciki, Allah sarki daɗin uwa kenan da ƴan uwa da ace tana da ɗaya daga cikinsu a kusa da ita da abun yazo mata da sauƙi,

 

Jin alamar ta shiga cikin toilet yasa shi yin saurin kutsa kai a hankali ya shiga, ya ajiye mata kwalin pads ɗin a saman gadonta abunda bai sani ba sehrish bata da masaniya akan wannan abun daya ajiye mata,

Jin alamar tana ƙoƙarin fitowa yasa shi yin wuff ya fice, a kofar ɗakin ya tsaya yana sauke ajiyar zuciya natsuwa yayi yana sauraran ta taciki,

Sai faman wiping tears take yi, tayi jaga jaga tafita out of sense ɗinsa, har wata ƴar rama tayi ga azabar menstruation ga tashin hankalin blood din dake bleeding a in between legs ɗinta,

dakyar tasamu ta ɗaura wannan mayafin fari mai sharara ajikinta, tsayawa tayi agaban mirror tana lalube lalaube ita kanta batasan me take nema ba kawai burinta tasamu abunda zata cusa a vagina ɗinta ko tasamu yadaina zuba tana cikin laluben nan ,

Karaf idonta ya hango mata kwalin nan da junaid ya ajiye mata a saman bed, ta cikin madubi ta hangosu,

A firgice ta juya tana kallonsu, cikin tsananin tsoro take takawa a hankali tana tunkararsa har ta isa gabansu,

Tsayawa tayi cak tana kallonsu , ledar sama tabi da kallo dayake ta kana iya hangen set na panties ɗin da ke ciki, tabbas tagane cewa pant ne amma tarasa gane wannan madai-daicin kwalin na menene 😥

Karanta jikinsa tayi tare da furta “Dry love” sunan pads ɗin da tagani ajikinsa kwalin kenan,

tunani take wanene ya ajiye mata wannan? anya ba al’janu bane ba? waiwaye ta shiga yi tana kallon gefe da gefenta taga ba kowa sai ita,

Kamar wata sullu6uyo haka ta koma, hannu takai cikin tsoro ta ɗauki ledar panties ɗin ta zaro su tana kallo,

Ba ƙaramin kyau su kayi mata ba, amma bata jin zata iya anfani dasu saboda batasan waya ajiye mata ba,

Ajiyesu tayi sannan takai hannu tasha fa saman kwalin pads ɗin kafin ta janye hannun cikin wani irin yanayi furta ” Ya allah ka tsare ni daga sharrin aljanu, ni dama nasan wannan blood ɗin da nake gani bana lafiya bane, ashe sune suka shafe ni,”

Nan tashiga jera wani kukan, duk a kunnan junaid ganin cewa zasu kwana ido a buɗe ga dare yayi sosai kusan ƙarfe 1:00 ynx ,

Cikin kuka ya sake jiyo ta tana cewa “Dan Allah koma wane aljani ne yake hukunta ni akan ƙaryar da nayi na shigar mace a matsayin namiji don Allah ayi haƙuri a haife mun wlh nima ba da son raina nayi ba..” kuka ne yaci ƙarfinta

Jin cewa yarinyar tayi amanna da cewa aljanune suka kawo mata kayan nan kuma sune suke horar da ita yasa junaid gyara muryarsa cikin wata irin amsa kuwa yace “Ke ! Yarinya ! mune nan ke hukunta ki bisa zunubin da kika aikata ! ,” .

Zaro ido sehrish tayi jin wannan  muryar mai ban tsoro tabbas wannan muryar aljanin ce ta faɗa a ranta, nan take zufa ta soma sintiri a fuskarta dukkan ilahirin jikinta kuma ya soma makekketa, ta ƙanƙame jikinta a tsorace tace “dan Allah kuyi hakuri bazan ƙara ba i promised u kuskure ne ku yafe mun wayyo Allah na nashiga ukuna,”

murmushi junaid ya saki dama yayi tunanin hakan yadda take a firgice tsaf muryarsa zata koma mata ta aljanu,

don haka ya ƙara gyara muryarsa ya ɗaga ta sosai ya ce “Munjiiiiiii ! Zamu iya yafe miki amma bisa wasu sharruɗɗa in kuma kika kuskure zamu raba sassan jikinki mu kaisu bayan duniya hhhhhhhhh,”

 

Download>>> Yaro Ne Complete Document

 

ya ƙare da wata irin dariya mai razanarwa, nan take fitsari ya kubce mata ta tsorata matuka kuma ta ƙara tabbatarwa kanta da cewa aljanun ne ke maganar saboda ita dai bata ga kowa ba acikin ɗakin,

cikin kuka tace “Na amince komai kuke so zanyi,” .

lumshe ido junaid yayi shi kaɗai yasan yadda yake jin daɗin wannan yanayin,

Hannu yasa tare da gyara makoshinsa yace “Sharuɗi na farko ! Zaki runtse idanunki kada ki buɗe har sai munce ki buɗe in ba haka ba hhhhhhhhhhhhhhh zamu tsoma ki jikin rijiya gaba dubu,”

la66anta har rawa suke yi wurin faɗin “Na amince na amince zann ..zann nama rufe yanzu haka wlh banzan buɗe ba don Allah kada ku sani acikin rijiyar nan banso zan bi umarninku,” ta ƙarasa maganar tare da runtse idanunta cikin tsananin tsoro,

“Kin rufe !!! taji aljanin ya ambata cikin sauri tace “eh na rufe, .

dariya cike fal a bakinsa dakyar yake gumtse ta, a hankali ya tura kofan ɗakin yasa kai ya shiga,

Bin ta da kallo yayi bil’hakki ta damtse idonta garam, kawar da kansa yayi daga kallonta saboda hakan na isa yasa shi cikin yanayi saboda mayafin da ta ɗaura shara shara yake,

Cikin sanɗa ya ƙarasa gaban kwalin pads ɗin yasa hannu ya buɗe sa, zaro dami ɗaya yayi ya ajiye saman gadon, 6an6are sa yayi cikin gaggawa wa ya curo guda ɗaya, sannan ya ɗauko pant guda ɗaya ya shimfiɗa a saman katifar gadon, ya buɗe sa sannan ya ɗauko pads ɗin ya cire ledar jikinsa mai gam, ya manna a tsakiyar pant ɗin ya sanya mata shi da kyau sannan ya ajiye, ɗagowa yayi ya sake kallon fuskarta ba ƙaramin tausayi ta bashi ba ganin yadda eye lid ɗinta ta kumbura, hancinta yayi jawur saboda yasha matsa ga lips ɗinta sun kumbura sosai,

Sai da yasanya mata pads ɗin ajikin panties kusan guda biyar, duk ya jera mata su, sannan ya lallla6a ya fice ya tsaya jikin kofar, yana sauke ajiyar zuciya kafin yayi gyaran murya ya ce “muna baki umarni da ki buɗe idonki yanzu,”

A hankali ta buɗe idonta basu sauka akan ko’ina ba sai kan abunda ya haɗa mata, binsu tayi da kallo gasu nan ajere gwanin kyau, muryar aljanun ce ta sake katse ta ” Sharaɗi na biyu kina sauraron mu da kyau ,”?.

Cikin natsuwa tace Eh ina sauraronku,

Murmushi jubaud yayi tare da ɗaga muryarsa da ƙarfi yaci gaba da cewa ” muna baki umarni da ki ɗauki ɗaya daga cikin panties ɗin nan ki sanya shi in kika kuskure zamu ɗauki gangarar jikinki mu kaita ƙasa ta bakwai,”

Jiki na rawa tasanya hannu ta ɗauki pant ɗaya ta zura a jikinta, nan take taji wani sanyi a ranta, cike da biyayya tace “Aljani na sanya,”

gaza jure dariyar dake cinsa yayi don haka ya kwashe da dariya cikin wani irin salo kamar Aljanun ne ke dariya yace “Hhhhhhhhhh yarinya kinyi kyan kai, don haka ! daga ynx in kina so ki tsira daga faɗawa daga tarkon bakin aljani dole ki rinƙa sanya wannan abun da muka aje maki in ba haka ba zaki fuskanci matsala …..hhhhhhhh,’

Cikin sauri tace ” zan….zanyi komai kuka ce,”

sannan ya ce”Sharaɗi na ƙarshe ! Hhhhhhh yanzu ki hau saman gado ki kwanta da safe zamu kawo miki saƙo hhhhhhh,”

Cikin gaggawa ta haye saman gadon, har ta kai hannu zata ɗauki bedsheet ɗinta ta tuna cewa ya 6ace don haka dole ta hakura, ta ƙudundune kanta, tayi lamo tana jiran bacci yazo ya ɗauke ta,

Ajiyar zuciya junaid ya saki don shima ya gaji ga bacci dake damunsa shida ya saba bacci da wuri,

Jin shirunta ko shesshekar nan ta kuka ta daina yi hakan ya tabbatar masa cewa she’s sleeping , don haka ya lallaba ya tura ƙofar ya zuwa hannu jikin bangon ya kashe mata hasken ɗakin sannan ya tafi,

Tabbas taji ƙarar kashe mata ƙwan ɗaki da akayi amma bata kawo komai aranta ba, don haka tace acikin zuciyarta “daga gani waɗannan aljanun masu imani ne basu cutar dani ba, sun taimake ni, Ya Allah na gode maka

Da wannan tunanin bacci yayi awon gaba da ita,

A bangaren junaid kuwa hmmm ina sam bacci ya ƙauracewa idonsa daga ya runtse ido fuskar Yarinyar yake gani, sam ya gaza sukuni sai fama juyi yake yana rungume fillow a ƙirjinsa ya gaza mantawa da wannan beautiful face ɗin mai cike da annuri ga sanyin kyau launin fatarta ba ƙaramin burgesa tayi ba ya jima baiga mace me qualities irin na yarinyar ba,

(to dama ai macen novel ce 😂)

 

Asubar fari kowannensu ya farka domin shirin tafiya gabatar da sallar asba banda wasu daga cikinsu,

Kamar junaid wanda bai samu bacci ba Daren jiy, ya ƙudundune cikin lallausan blanket ɗinsa kamar wani jinjiri ga fillow ya yi hugging ɗinsa tightly a chest ɗinsa,

Fawan ne ya shiga bubbuga kopan ɗakin nasa ƙwan! Ƙwan !! shiru ba alamar zai zo ya buɗe, ƙara knocking yayi bai taso ya buɗe kofan ba,

Tsayawa bakin kofan yayi yana kiransa “Junaid ! Junaiiiid !!! Wake up bro its time to pray oh shirt ! am tired pls open the door,” ya ƙasa maganar cike da ƙagara,

jabeer, irfan ,khaleed da kanal yusif suna ata down stairs suna jiran su, saboda atare suke tafiya sai sun harhaɗu duka sannan,

tsoki yusif ya saki tare da cewa “ni fa bana son wasting time, nauyin baccin nan nasu junaid da twins abun yayi yawa don haka daga ynx ƙarfe 9 kowa zai rinƙa bacci wannan umarni na ne,’

Amsa wa sukayi da “toh insha Allah zamu kiyaye hakan,

Khaleed ya ce “bari naje na tada su twins , yana faɗan hakan ya kama hanyar ɗakinsu, time ɗin daya isa ya tsaya a bakin kofan yana knocking da ƙarfin gaske,

Suna cikin manne da juna kamar chew gum, sautin bugun ƙopan da khaleed ke yi musu ne yasa jahan farka wa, fuska a kumbure alamar anyi disturbing ɗinsa cikin ƙuƙuni yace” who is that pls,”

Khaleed dake waje ya ce “ubanka ne in hakan bai ishe ka ba ka fito ka gane wa Idonka stupid,’

turo baki yayi kamar yana gabansa, hannu yasa yasha fa sumar Ayaan tare da kai bakinsa saitin kunnan sa ya ce “wake up honey its time to pray !

Shiru bai motsa ba zubawa fuskansa ido jahan yayi yarasa dalilin dayasa a duk time ɗin daya kalli ayaan sai yaji ya koma mesa mace sak, kodan yana da kyau sosai ne oho,

hannu yasa tare da jan dogon hancinsa cikin zolaya ya ce”ko dai kafarka ko kuma in sa ma cool water a face ɗinka,”

Murmushi ayaan ya saki dama yana jinsa shiru kawai yayi, cikin muryar shagwa6a ya ce” i know u can do that cos u love me so much u dont wanna hurts me,”

murmushi jahan yayi “now its ok ga yaya khaleed can yana buga ƙopa, time ɗin sallah yayi ka tashi muje toilet mu tsarkake jjikinsu saboda jiya mun 6ata shi da sperm,’

ƙasa ƙasa su ke magana saboda sun son khaleed na tsaye a kofan door ɗin yana jiransu,

“Ni bazan iya tashi ba sweetheart kasala nake ji, jiya duk ka kashe mun jikina… Cikin shagwa6a ayaan ya faɗi hakan,

Ba ƙaramin yanayi yasa jahan ba ganin yadda ya ke magana cikin kwarkwasa,

Sauka daga gadon jahan yayi ya zuƙunna at d egde of the bed ɗin ya juya masa bayansa ya ce ” ina fatan hakan yayi maka,’

yar dariya Ayaan yayi tare da janye bargon jikinsa ya sauko ya haye bayan jahan tare da ƙanƙame sa, a haka suka shiga cikin toilet ɗin

Shaf shaf suka sakarwa kansu shower suka ɗauro Alwala, suka fito cikin sauri kowa ya cire kimono robe ɗin dake jikinsa suka sanye jallabiya don tsabagen yaudara hada riƙe cazbaha a hannunsu kamar wasu larabawa haka suka fito hmmmm

Fawan kuwa har ya gaji da buga kofan junaid ƙarshe yasa ƙafarsa da ƙarfi ya harba kopan ta buɗe, sakin baki yayi ganin sa ya faɗo daga saman bed ɗin bargon lulluban yayi gefe ga fillow daya ƙanƙame a ƙirjinsa,

to fah fawan ya faɗa tare da ƙarasa wa inda yake baje , samun fuskarnan tasa yayi ɗauke da wani irin matashin murmushi dimples ɗinsa sunyi matuƙar lotsa wa kai kace ba bacci yake ba,

russinawa yayi tare da kai hannunsa ya cafki fillow dake ƙirjinsa yana ƙoƙarin ciresa, nan fa junaid ya damƙe fillow gam cikin magagin bacci yake faɗin “kyakkyawa ce ! ita ta musamman ce meyasa bazata bayyana min komai ba ,

 

Download>>> Kwarata Complete Document

 

Tsananin mamaki ne ya kama fawan , ganin zai bata masu lokaci yasa Shi sa ƙarfi wurin cire filon aikuwa junaid ya haɗa dashi duka ya rungumo a jikinsa ya ƙanƙame yana faɗin “naji daɗin kasance wa tare da ke a daren jiya zanso na sake ganin wannan kyakkyawar surar,’

Tsananin haushi ne yasa fawan ya gartsa masa cizo a kunnansa,

A firgice ya farka tare da sakin fawan da filon ya tashi zaune idonsa sunyi ja alamar bai samu enough sleep ba,  cike da ƙululu yake kallon fawan “dama nasan kaine bakin mugu laifin me na maka ka cizar mun Kunne na saboda rashin tsoron Allah,’

Ya faɗa yana kallon fawan wanda ke zabga masa harara “dan Allah malam tashi kaje ka ɗauro Alwala kai kaɗai muke jira,’

rai abace junaid ya tashi yana faɗin “dole sai munje tare ne, kuyi gaba sai na biyo ku abaya,’

 

Ya idasa faɗan hakan yana turo kopan toilet ya shige yana ci gaba da ƙuƙuni,

Sun kammala harhaɗuwa don haka suka kama hanya  domin zuwa gabatar da sallah.

SEHRISH ❤

 

baiwar Allah tana ƙudundune gwanin ban tausayi ta farka da wani irin matsanancin ciwon kai, ga zazza6i ga ciwon ciki duk ita kaɗai ga fuska a kum6ure saboda kukan da tasha,

Ko kakkwaran motsi ta gaza yi tarasa yaya zatayi da rayuwarta, jikinta sai kerma yake hatta haƙoranta game wa suke da juna suna bada wani sauti kaf kaf, tayi matuƙar galabaita tana so taje ta sanarwa azmi amma tagaza ko tashi sai faman nuƙurƙusa take yi,

……hmmmm ina matuƙar tausayawa waɗanda basu da uwa atare dasu basu da wani nasu a kusa da zai kasance tare dasu aduk lokacin suga shiga hali irin wannan Allah sarki much love to our mothers & sisters and so on ,

Addu’o’e kawai take jero wa daga bakinta tana neman sauƙi a wurin Allah, raɗaɗi iri iri ga matsananciyar damuwar dake damuwanta, wa zata kaiwa kukan ta in ba Allah ba ?

A wannan halin wani baccin ya qara ɗaukanta,

tun da suka dawo daga masallaci kowa ya koma bedroom ɗinsa wasu suka koma bacci wasu kuma suka kama karatun ƙur’ani kowa da kiwon daya kar6e sa,

gaza samun natsuwa yayi tunda ya dawo tunaninsa wane hali yarinyar take ciki? ga kuma promise ɗin da yayi mata nacewa da safe zata ga sako a matsayinsa na bakin aljani,

Cikin sauri ya buɗe closet ɗinsa jerin kaya ne iri iri masu tsadar gaske, gidan ƙasa ya duba jerin sababbin barguna ne da zanin gado, hannu yasa ya zaro blanket ɗaya da bedsheet ɗaya sababbi fal masu kyau da tsada, ajiye su yayi a saman bed ɗinsa,

gaban dressing mirror ɗinsa ya koma a cikin drawer ɗin dake haɗe da madubin ya janyo gida na farko,

Katan katan ne na kwalin sabulu masu kyamshin gaske, dozen ɗaya ya ɗauko tare da wani haɗadden soson wanka acikin ledarsa,

a saman blanket ɗin ya ajiye su,

Zuba musu ido yayi yana kallo yama rasa me zai yi gani yake kamar sunyi mata kaɗan, sam bayaso ta gane cewa shi ba aljani bane ,

fita yayi ya wuce ɗakin da suke ajiyar magunguna iri iri da allurar da sauransu tamkar patient room haka yake , saboda suna da military doctor & nurse hakan yasa suka buɗe ɗakin don ko mutun bai lafiya za’aya iya duba sa acikin gidan,

yasan cewa dole ta tashi da ciwon kai saboda kukan da tayi kuma dole ta tashi da ciwon ciki, don haka ya ɗauko mata magungunan da yasan zata samu relief, ya zura cikin aljuhun rigarsa,

Duk hakan bai ishe shi ba, yana ji aransa cewa dole ta buƙaci abinci akwai yunwa a tattare da ita,

Komawa ɗakinsa yayi cikin sauri ya rungumo kayan da ya ajiye a saman gadonsa ya fito dasu,

Ya ci sa’a ba kowa har yanzu gari bai idasa washewa ba suna can suna sharar bacci,

Lalla6awa yayi a hankali ya wuce bedroom ɗinta tsayawa yayi a kopan ɗakin saboda baiso ace idonta biyu, kasa kunnansa yayi yaji shiru ba motsin komai ɗan tura kopan yayi ya leƙa yana kallonta,

Kwance take idonta rufe alamun bacci take amma jikinta sai rawar sanyi yake a haka ta kwana tun jiya dama da bedsheets ɗinta take lullu6a kuma ta 6ata sa, ga tsoron baƙin aljanin daya ziyarce ta daren jiya duk shi ya firgita ta tarasa kwakkwaran motsi balle ta ɗauko wani abu tayi covering jikinta da shi,

Ajiyar zuciya ya saki, cikin sanɗa ya kutsa kai ya shiga yana takawa a hankali a gefenta ya ajiye mata kayan, sannan ya zaro lallausan blanket ɗin ya rufa mata a jiki a hankali, har cikin ranta taji shi gaba ɗaya har kanta ya haɗa ya lullu6e mata, sai gata tsulum acikin bargon kamar wata new born baby,

smilling yayi alokacin da yaga ya kammala sa mata batare da ansamu matsala ba,

Yana fita ya wuce ɗakin azmi tsayawa yayi bakin kofa yayi mata knocking,

“Shigo ciki”

Ta faɗa daga ciki kutsa kai yayi ya shiga, zaune ya same ta saman sallaya da ƙur’ani a hannunta alamar karatunsa take yi,

murmushi tasaki ganinsa tare da cewa “junaid yau kaine a ɗakina i forgt when last ka shigo min,’

bai bata amsa ba sai da ya Samu wuri ya zauna agabanta ya lankwashe kafa sannan yace “barka da safiya dafatan kun tashi lafiya,’

“Lafiya lou Alhamdulillah ince ko lafiya,’ ? ta tambaya tana kallonsa don tasan dalili kawai ke kawo su wurinta,

Cikin natsuwa ya ce “meya faru jiya baki fito ba wurin dinner ɗin mu,’

“Bani da lafiya ne dama na faɗawa tukur meyasa ka tambaya,?

ta faɗa tana kallonsa, murmushi junaid yayi yana kallon azmi ya ce “nasan komai fa ynx!”

Ji tayi gabanta ya faɗi duk da batasan me yake nufi ba cikin nuna rashin fahimta tace” me kake nufi da kasan komai junaid?

“Ina nufin na gane cewa tukur ba namiji bane maca ce kuma nasan kinsan da haka azmi,”

shiru azmi tayi tare da yin jigum tana kallonsa ƙarya ta ƙare amma sanin cewa junaid ne yasa bata tashi hankalinta ba saboda sauƙin kansa,

“taya akai ka gane hakan”? ta jefa masa tambaya,

“Jiya bayan fawan ya bata punishment sakamakon kuskuren 6arawa Ayaan ruwan zafi a hannunsa,’

Nan junaid ya kwashe duk abunda ya faru daren jiya ya sanarwa azmi, hankalin azmi ba ƙaramin tashi yayi saboda ita batasan duk wannan budurin da akayi ba da ace tana kusa da bazata bari fawan ya hukunta sehrish ba, a wani 6angaren kuwa taci dariya sosai jin shiriritar da tayi daren jiya don junaid bai 6oye mata komai ba,

dakyar ta tsagaita dariyar da take tace masa “ynx me ka yanke akan yarinyar zaka sanarwa yan uwanka cewa maca ce ita ?.

girgiza kai junaid yayi tare da cewa “a’a korarta zasu yi nasani koda zasu sani ba yanxu ba sai sun saba da ita sosai, ni ma kuma bazan bari tasan na sani ba insha Allah,’

azmi taji daɗin hakan dama tasan hakance zata faru domin junaid yaron kirki ne duk cikin yan uwansa tafi sonsa ji take kamar ita ta haifesa saboda yadda yake respecting ɗinta,

“Ya sunanta’?

Ya tambaya yana kallonta azmi tace” sunanta SEHRISH”

 

Download>>> Ingarman Namiji Complete Document

 

short smile ya ɗan saki kafin yace” ynx azmi pls ki taimake ita, nayi mamaki jiya alamu sun nuna cewa bama tasan menene menstruation ba, tasha wahala sosai akwai kayan da nakai mata pls kice ke ce kika kaimata, sannan ga magani nan ki bata ta sha amma kafin nan ki sama mata abunda zata ji saboda akwai yunwa atattare da ita,” ya ƙarasa maganar yana sa hannu cikin front pocket ɗinsa ya zaro maganin ya miƙa mata, ajiye kur’anin tayi akan sallayar kafin tasa hannu ta kar6a tana cewa “kada ka damu insha Allah komai zai tafi dai dai nima ina ji araina tabbas akwai damuwa a tattare da yarinyar, a yanayin da kafaɗa min abunda ya faru jiya ya tabbatarmun da cewa tarasa wani 6angare na ilmi arayuwarta sakamakon wani dalilin,’

Har cikin ransa ya ƙara ganin girman azmi a idonsa, itama taga farin ciki a fuskan junaid wannan ya tabbatar mata da cewa akwai wata a ƙasa, Murmushi tasaki kawai

Yunƙurawa yayi ya mike ya kama hanyar fita har yakai bakin kopa ya sake jiyowa ya kalli azmi yace”pls & pls take care of her,’

Dariya azmi tayi ganin yadda ya susuce aranta tace tun ynx daga daren jiya kawai,

Shima fice wa yayi yana murmushi yanzu ya samu natsuwa don haka ya koma bedroom ɗinsa ya kwanta yana jiran safiya ta idasa yi koya samu yaga wannan kyakkyawar yarinyar,

Sehrish

Motsin mutun da taji a kusa da ita ne yasa ta farkawa tayi mamakin ganinta cikin bargo sai tayi tunanin cewa ko mutuwa tayi ne aka rufe ta don ita tasan ba komai ta kwanta,

Hannu azmi tasa ta zame mata bargon ta yane shi gefe ɗaya,

Ta tsorata da ganin yadda sehrish ta koma fuska tayi sumtun ido jawur ko magana bata iya yi,

“Subhanallahi meyasa sameki haka sehrish”? Azmi ta faɗi hakan cikin yanayin tashin hankali a matsayin batasan meke faruwa ba,

wani sabon kuka ne yazo ma sehrish cikin kukan take cewa “jiya baki nan fawan yasani tsallen kwaɗi saboda na 6arawa ayaan ruwan coffee mai zafi bansani ba, nasha wahala sosai aunty azmi har ciwo naji sosai tun jiya nake faman bleeding bansan me ya kawo hakan ba,”

ta ƙarasa maganan tare da sa ƙarfi cikin rashin jin kwarin jiki ta mike zaune,

Cike da damuwa azmi tace ” am sorry for that, I was not feeling well I ave told u about my headache it really pained me yesterday night tunda bacci ya dauke ni I no longer knew where my head was, now am listening to you tell me what happen to u ?

nan sehrish ta shiga jero mata abunda ya faru hada labarin aljanin daren nan da kuma maganar jini da taga yana bleeding daga under ɗinta,

bayan ta kammala bayanin ta shiga Nuna mata kayan da aljanin ya kawo mata sannan tace “Aunty azmi dama akwai aljani me mutunci irin haka ?

 

nan sehrish ta shiga jero mata abunda ya faru hada labarin aljanin daren nan da kuma maganar jini da taga yana bleeding daga under ɗinta,

bayan ta kammala bayanin ta shiga Nuna mata kayan da aljanin ya kawo mata sannan tace “Aunty azmi dama akwai aljani me mutunci irin haka ?

data shoulder dinta azmo tayi tare da cewa ” dukkan abun da kika gani jiya ba gaskiya bane ! you’re just dreaming cos you were scared but am the one that brought all these stuffs to u, kuma ni ce na kawo ki dakin ki, bansan dai mai ya faru ba amma nafito around 10 na ganki while u were fainted on the floor

sai nayi deciding na dauko ki na kawo ki bedroom dinki shine naga blood na zuba a jikin ki, dama already Ina da pad da panties shine na kawo miki wannan shine gaskiyan abunda ya faru,’

Azmi ta karasa maganar tana kallon sehrish wadda tasaki baki galala don mamaki gashi azmi ta rikita ta ta canza mata tunanin ta,

Azmi ta lura da yanayin da sehrish ta shiga sai taji tsoran karfa yarinyar ta rikice don haka ta kara da cewa “Nima na taba yin irin wannan mafarki just like u did, ba wani Abu bane, then maganar menstruation wato blood din da kika gani ba na cuta bane ko ciwo sakamakon punishing dinki da fawan yayi , wannan Jini ne na al’ada Wanda ko wace mace take yi shin baki taba sani ba kuma dama baki taba yi ba am just doubt abt it,

Ta ƙare maganan tana kallon ,

ɗan shiru tayi tana nazari ita dai tasan kamar ta ta6a ji game dashi sai ynx take ɗan tuna wani abin husanna da jahad sun riga ta farawa tasan game dashi rashin kwanciyar hankali da rashin natsuwa yasa ta gaza fahimtar cewa na al’ada ne tabbas tsohuwa ta ta6a koya musu wannan ,

” nasani mantawa nayi amma aunty azmi wai dagske ba wani aljanin da yazo min ? kina nufi is not true amma fa har abu aka samin a pant na sanya kuma ni banga kowa nd i didnt see u a time ɗin ,’

ganin ta fara ƙoƙarin gane ƙarya take mata ne yasa ta ce “pls forget about the past ! we’ll talk about It later ,

Daganan azmi ta ƙara wayar mata da kai game da yadda zata tsarkake jikinta da sauran muhimman abubuwan,

Duk ranar batayi aiki ba azmi ce tayi komai kuma har room ɗinta takai mata breakfast lafiyaye hada kayan marmari , sannan ta tunatar da ita akan tasha maganin da ta bata,

Junaid yayi kewar ganin ta, ya kasa fita ko ball ya buga saboda tunanin ta , sai faman sintiri yake yi yaga ko zata fito amma shiru babu ita ji yake kamar yaje bedroom ɗin nata yayi mata magana,

Gaza jurewa yayi cikin sauri ya sauko down jikinsa sanye da jeans da tshirt

A kopar ɗakin ya tsaya tare da yin knocking ,

lokacin har tayi wanka ta shirya tsaf shigar da ta saba yi ta maza, ta canza kuma pad ɗin data sa,

har ynx batayi tunanin wasu abubuwan ba  kamar hankicif da taga an naɗe mata gashin bakinta da na jagirar ta duk ba tayi tunanin wani abu ba, sai ta sawa aranta cewa duk azmi ce tayi wannan,

ta gyara komai daƙar tayi fixing ɗin gashin bakin saboda gam ɗinsa ya ɗan saki saboda jikinsa yayi wetting sakamakon kukan da tasha,

Jin knockinga yasa ta yin gaggawar idasa kifa hular akanta, sannan ta ƙarasa gaban kofan ta buɗe,

Lokacin da ya yi arba da kyakkyawar fuskar nan tata sai yaji natsuwa da kwanciyar hankali sun zo masa

“am tukur dama nazo naji meke faruwa ne yau banganka ba,’;

ɗan murmushi tayi jin yadda ya damu da ita tace” Zazza6i nayi amma ynx da sauƙi Alhmdllh,’

ta ƙarasa maganar tana sunnar da kai, aransa ya ce “mai ƙarya ɗan wuta, amma a zahiri sai ya ce “Allah ƙaro sauƙi,

“Ameen ngde” ta faɗa tana ƙara gyara tsayuwanta,

Shiru su kayi na ɗan wani lokaci wani irin kallo yake binta dashi confidence ɗinta na bashi mamaki 🤔

 

Download>>> Ana Dara Ga… Complete Document

 

Shiru su kayi na ɗan wani lokaci wani irin kallo yake binta dashi confidence ɗinta na basa mamaki ita ala dole namiji ce,

“Can u make a choculate cake for me,’?

Ya tambaya yana kallonta

ɗan zaro ido tayi hakan ba ƙaramin kyau tayi masa ba,

Cikin en ina tace” choculate cake kuma ranka shi daɗe banda lafiya,’ ta faɗi hakan tana ɗan dafe waist ɗinta alamar akwai ciwo wurin,.

yar dariya yayi kafin ya ce “naso ace zaka iya haɗamin da nayi ko browsing ne a wayata sai na baka ka ga yarda akeyi saboda ina buƙatar cin…..’

tun kan ya idasa ta katsesa “zan iya tsaf in ka ban wayr zan ga yadda ake yi sai nayi….

abun yaso yasa shi darawa dama dagangan yayi mata haka saboda ya gane cewa ita ce ke satar masa waya tana kiran yan uwanta, yayi hakan ne don ya haɗa ta da ƴan uwanta dake nemanta,

tayi tunanin ita ce tayi masa wayau batasan cewa shine yayi mata wayau ba domin yasa recording da za’rar ta fara wayar recording ɗin zai soma yana so ya ji meke damun ƴan uwan nata,

Bayan ya bata wayar ya fi ce daga gidan, jikinta har rawa yake yi ta samu nama,6oyewa tayi a wani corner ta danna wa su husanna kira,

A lokacin jahad bata kusa sun fita amsar wani tallafi da ake rarrabawa a gidan wani ɗan majalissa ita da tsohuwa sun bar wayr a gida,

wayau su kayi ma husanna don ta zauna suka bata wayar tayi game sannan suka datse ta a ɗaki da key gudun kar ta fita kar kuma wani ya shigo ya cutar da ita tun da ba kofa a gidan buhu ne kamar labule,

da tagama buga game ɗin taji shiru gidan ba kowa ta kwakkwala masu kira kawai sai ta kama rera kuka tayi mai isarta ta koma ta kama bacci,

Ringing ɗin wayar ne ya tayar da ita har sai da ta tsorata saboda ta ajiye wayar a saitin kunnan ta,

Cikin sauri  tasa hannu ta ɗaga wayar tana sauraran jin muryar wanene,

Sehrish ta gyara murya tare da cewa”assalamu alaikum yar uwa ni ce pls kiyi mgna da sauri ya jikin naku ya husanna taji sauƙi ko har ynx da haukan nan akanta ?

ta tambaya tana jiran amsa

Sautin kuka taji tunda taji hakan ya tabbatar mata da cewa husanna ce ta ɗauki wayr saboda ta tsani ace mata tana hauka ita bata yarda ba har yau !

“Subhanallahi kash ! husanna ke ce..? ta tambaya kamar tana a gabanta,

Cikin muryar kuka tace “ni ce! shine kika tafi ki ka barmu ko ? cikin wahala da bakin talauci kullum ba abinci sai mu jera kwana 5 muna cin ɗumamen tuwa….’

Jin wannan maganar yasa kwalla ta taru a idon sehrish ci gaba da sauraronta tayi

“ni nagaji dan Allah ki dawo ko kizo ki dauke ni wlh bana jin daɗi, ko isasshen bacci bana samu ga sauro ga yunwa ko kayan sawa babu kullum wasu tsummo karai tsohuwa take bamu muna sawa ni nagaji gsky,’

Sehrish batasan lokacin da kuka ya 6arke mata ba, sam tagaza magana tuni jikinta ya soma jijjiga kamar wadda sanyi ya buga

“Kinyi shiru baki ce komai ba ? kin manta oumman mu tace duk runtsi duk wuya karmu rabu da juna amma kika tafi ko ? baki sona ko ? So kike na mutu ko, to shikenan zan je na kashe kai….’

tsawa sehrish ta daka mata wanda hakan ya dakatar da ita daga magana ” ya isa ! Ya isa! ya kike so nayi? saboda ku nake zaune a nan husanna, bashi ne na dubu ɗari tara akaina how can i pay it ? i dont ave anything dole na tsaya nayi musu aiki na tsawon shekara ɗaya da rabi,saboda ku !

daker ta ƙarasa maganar tana share kwalla,

Jin yadda sehrish ke faman shesshekar kuka yasa jikin husanna yin sanyi ta ce “kiyi hakuri in na 6ata miki rai bansan ran ki zai 6ace ba,’

dakyar sehrish ta tsaida hawayen ta gyara wayar a kunnanta tace” rai na be baci ba ina kuka ne saboda ku halin da kuke ciki, amma karki damu kinji ƙanwa ta in na samu kuɗi zan tura muku insha Allah ki tayani da addu’a,’

cikin sanyin murya husanna tace” ina miki addu’a kullum bana mantawa,’

Murmushi sehrish tasaki kamar suna kusa da juna tace”I love u so much shashasha,’

tana jiyo muryar husanna ta cikin wayar tana tiƙar dariyar saboda ta tuna mata da wani abu,

daga nan sehrish tace “zan ajiye waya send my regards to jahad & tsohuwa,’

husanna tace”insha Allah zasu ji”

daga nan ta katse wayar ranta fal saboda taji muryar husanna, cikin koshin lafiya,

nan fa ta soma tunanin yadda zata haɗa masa chocolate cake ita hasalima a suna kawai tasan cake ɗin,

Wuri ta samu saman ta zuƙunna ta shiga lalubar masa waya instead taje tayi aikin daya sata,

Gallery ɗinsa ta shiga madaddalar hotuna, na fa ta fara ganin haɗaɗɗunan pictures ɗin samarin familƴ ɗinsu hada waɗanda su kayi a ƙasashen waje,

A nan ne taga hotonan wannan haɗaɗɗen matashin saurayin mai shegen kyan nan, shi da junaid su kayi hoton a cikin jirgi da alama privet jet ne mallakinsu saboda su biyu ne acikinsa, sunyi hugging ɗin junansu fuskarsu ɗauke da murmushi,

wuce wa gaba tayi next picture nan fa ta ƙara ganin hotonsa cikin dandazon sojoji suna sara masa,

Ƙasa tayi ta shiga videos nan fa ta gane wa kanta zahiri,

Videos ɗinsa tagani kamar hauka da alama junaid na yinsa sosai,

ran ta yana bata cewa wannan ba kowa bane face BABBAN YAYA wato surgeon general RAFAYET,

ta jinjina wa matsayinsa ganin kowane video zakaga dubban sojoji ne turawa kewaye da shi suna taka masa baya, ko suna sara masa ,

tana cikin wannan laluban wayar ta soma ringing bin hoton da ya bayyana a calling ɗin tayi ,

zaro ido waje tayi tare da buɗe baki alamar mamaki, mutumin da take bibiya ynx haka shine ke kiransa a waya,

tunani ta soma yi ta yi ɗaga ko kar ta ɗaga ? katse wa kiran yayi wani kuma ya sake antayo wa wayr ta ci gaba da ringing,

Cikin tsananin tsoro da jin fargaba ta ɗaga tare da karawa a kunnanta bata ce komai ba, tayi shiru tana sauraronsa

abun da ya ɗaure mata kai shima bai ce komai ba ! hasalima alamu sun nuna cewa ya manta daya danna kiran saboda tajiyo hayaniya mutane ta cikin wayar alamar tattauna wa ake,

katsewa kiran yayi, janye wayar tayi daga kunnan ta ta zuba ma number ido da sunan da aka a jiki “My everything”

ta jima wurin zugudun tana kallo kamar daga sama taji muryar junaid

“An kammala haɗa min cake ɗin”

A firgice ta tashi zaune tana kallonsa tayi wuri wuri da ido tana mazurai,

Murmushi ya saki tare da miƙa mata hannu ya ce “Gimme my phone,”

cikin rawar murya tace”am..umm..dama ynx nake am..:

hannu yasa yayi mata alamar tayi shiru kafin yace its ok ba damu zan sa a kawo min ne kawai,’

ya faɗi hakan tare karban wayar ya shige ciki binsa da kallo tabi shi har ya 6ace wa ganin ta,

A cikin waɗannan kwanakin wata irin shakuwace ta shiga tsakaninta da junaid tarasa dalilin dayasa yake kyautatamata sannan abunda ke ɗaure mata kai ynx baya bari ta shigo ɗakinsa musamman inda ga shi sai shorts (gajeran wando) a jikinsa, abunda bata sani ba shine ya gane cewa ita macece da cen abunda yasa yake sakin jiki bai kunyar yin komai a gabanta saboda a tunaninsa namiji ce, ga shi kullum sai ya bata aron wayarsa ya ce ta buga game, waɗannan abubuwan na matuƙar ɗaure mata head,

Ba ƙaramin daɗin hakan taji ba, kullum sai sunyi waya dasu jahad da husanna, kullum sai tayi mata complain akan ta turo musu kuɗi sun gaji da talauci, tai ta faman basu hakauri akan su bata lokaci,

bata samun matsala da kowa ynx, tana taka tsantsan akan duk wani abu da zai sa a kore ta daga gidan, Mutunci tsakanin ta da azmi sai ƙara habbaka yake abun ba’a magana ta maida ta kamar auntyn ta ita ma haka azmi ta maida ta kamar yar cikinta ko nace ƙanwarta komai na tafiya dai dai,

A 6angaren su husanna kuwa dake cikin mawuyacin halin kamar kansu farau talauci, suna buƙatar agajin gaggawa domin maganungunan da doctor ya ba ta sun ƙare dole sai an samu ƙuɗi an siya mata wani,

don haka jahad ta yanke shawarar turama sehrish saƙo, a lokacin da message ɗin ya shiga wayar na hannun junaid,

Karantawa yayi kamar haka” sister maganin husanna fa sun ƙare akwai matsala tazama wata zararriya ta hana mu sakat pls ki taimaka mana,”

Koda junaid ya karanta message ɗin sai ya tura masu da “Send me your account number,’

ganin wannan saƙon cikin zumuɗi jahad ta zari hijabi don tashiga gidan makwabtansu saboda yarinyar gidan nada account number su nan basu dashi,

kafin ta dawo husanna tafarka daga bacci saboda cikinta daya katsa, ta soma laluben waya saboda toilet ɗin akwai duhu irin na gargajiyar nan ne ginin ƙasa, nan ta samu yar nokia ɗin da jahad ta ajiye a saman jakar kayansu taɗauka  ta shiga da ita toilet ɗin, to ka’ida in ta kunna fitilar wayar ta zukunna sai ta fara buga game tana sukuni,

 

Tana cikin zuƙunno nan wani ƙaton kyankyaso mai fiffike yayi tsalle sai saman kanta, cikin firgici ta tashi a razane nan take wayar dake hannunta ta sulale daga hannunta ta faɗa cikin ramin masan Subhannallah,

Can ance a turo account number nan kuma wayar da suke da ita kwalli kwal ta faɗa cikin masai,

 

Zaro ido tayi tare da buɗe baki saboda tsoro, taji haushin kyankyasan nan har taji cewa bazata kyalesa ba dole ya mutu,

Nan suka shiga sintiri ita dashi shidai wings ke gare sa, ita kuma da ƙafa take binsa sai faman tashi sama yake yake yi tana binsa da gudu, hada ɗauko takalmi tana kokarin kwaɗesa,

Baki a washe jahad ta shigo ta samo account number ɗin yarinyar ta rubuta mata a farar paper,

ɗakinsu ta shiga tana neman waya, sama ko ƙasa babu ita ta shiga lalube ko’ina babu, tashiga mamakin ina aka kai wayar bayan babu,

tunawa tayi da cewa tabar husanna a kwance tana bacci tabbas tana wurinta , fita tayi cikin saurin tsakar gidan

Adai dai lokacin Husanna tafito tana sauke ajiyar zuciya tace”wash Allah da ace ban kashe shi ba dana binne kaina,’

“Husanna ina wayar nan take”?

jahad ta jefa mata tambaya ita bama ta lura da ita ba sai da tayi magana, nan fa tashiga wurga ido na mara gaskiya shiru tayi tana kallon ƙasa,

hakan ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali yayi ba, saboda akwai abunda ko ba’a faɗa maka ba zaka fahimta ne ta yanayin mutun,😿

 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

 

Back to top button