Halysaah Page 28 By Khaleesat Haydar
HALYSAH 28…Khaleesat ta kwala wani karan da ya gigita Ummanta da Mama Salame, Umma ta mike da sauri tana kallonta a kidime, haka ma Mama Salame da tace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, menene haka Khaleesah?” kishiyoyin Umma duk suka yo dakin a guje su ma don Khaleesat bata fasa ihun da take kwalawa ba cikin tashin hankali take cewa “Wallahi bana son shi bazan iya zaman aure da shi ba, na shiga uku na lalace, don Allah Umma ku min rai ku rufa min asiri, wallahi bana son sa” Umma dai sake baki tayi tana kallon Khaleesat tashin hankali karara a fuskarta gashi ta kasa cewa komai, daya daga kishiyoyin Umma da ake kira Mama Shatu tana gyara zaninta da ya kusa kwancewa saboda gudun da suka yi tace “Ji wani gulma da kinibibi? Shi Abdul din ne da ya daukeki ya kai ki kasan turai karatu yayi ta kashe kudadensa ne baki so yau? A ajiye batun ubanki a gefe, ke abinda ya kashe maki yau ko kaf kasar da uwarki ta baro za a siyar za a iya biyansa aka ce maki?” Ita ma daya Co-wive din da suke kira Mama Zubaida tace “A’a rainin wayo mana Shatu, gwara ai a rena mana hankali, don uwarta kasuwa ne nan da zata cika mana gida da ƙuwa, wannan ai iskanci ne da walakanci” Khaleesat bata fasa kuka da ihun da take a dakin Ummanta ba tana surutai ita kanta bata san takamaiman abinda take cewa ba tsabar tashin hankali, Kanninta Noor da Islam kuwa har sun fara kuka su ma a dakin, kan kace me har makota sun fara tururuwan shigowa gidan, aka tsaya cirko cirko bakin kofar dakin Ummanta ana salallami, Mahaifinta ne Malam Ali ya shigo gidan yana zazzare ido, shi ma ya karaso da sauri yana tambayar abinda ke faruwa a gidan, Mama Shatu ta tabe baki tace “Wai er da ta fi kowa ce ta sauka yau daga Amurka shine uwar ke sanar mata ai an daura aurensu da shi wanda ya kai ta waje karatu har ta dena ganin kowa da gashi, shine fa ta cika anguwa da ihu da koke koke wai ita bata son auren bazata zauna da shi ba, ga jama’a na ta shigowa an zata gobara muke, wannan ai tsabar sangarci da iya shege ne” Juyawa Malam Ali yayi ya nufi gun da ake ajiye itacen girki da sauri ya suri daya ya dawo ya nufo dakin Umma yana cewa “Ina take…” Matan makota dake tsakar gidan suka hau basa hakuri suna don Allah ya kyaleta, yaki sauraron kowa yana zazzare ido, Khaleesat na hangosa ta tafi bayan Ummanta da gudu tana kuka ta rungumeta, kanninta ma suka yi bayan Umma gaba daya suna kuka, Mama Salame ta tsaya tayi bake bake gabansa tace “Haba haba, haba Malam Ali, meye haka kake kokarin yi?” Yace “Salame ki bar ni dai inci malfar ubanta a wajen, mu zata tona ma asiri? Ni zata ja ma sabon bala’i da fitinan da ya girmeni?” Mama Salame tace “A’a wallahi baza ka doketa da wannan rafkeken icen ba ita ba jaka ba, mu je waje Malam Ali” Ita dai Umma kanta na kasa bata ce komai ba, haka Mama Salame ta samu ta tasa keyarsa ya fita daga dakin tana biye da shi, Mama Zubaida ta rike haɓa tace “Ikon Allah, mu muke ganin kinibibi iri iri a gidan nan, to in aka bibiya wani ta kyallara ido ta gani a Amurkan shine zata tona ma uban asirinsa da ke rufe, da can menene yasa ta hakura zata aurensa? Sai ranan da aka daura aure ta nemi tara mana mutan anguwa tace bata san zance ba? Yau ni nake ganin iskanci, to ta tsotsi nonon buzuwa ba dole ta iya makirci da kissa ba” Ita dai Khaleesat kuka kawai take a jikin Ummanta siblings dinta na kusa da ita suna taya ta, Mama Salame ta sake labulen dakin Umma duk don matan dake tsaye bakin kofar su kama gabansu, Umma ta juya tana kallon Khaleesat gaba daya ta kasa cewa komai, zamewa kasa Khaleesat tayi ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita tana cewa “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, na shiga uku na lalace” a sanyaye Umma ta tafi gefen katifar dakin ta zauna ta kasa cewa komai. Karfe biyun dare Umma na zaune kan darduma da carbi a hannunta, Khaleesat ta tsallake kanninta ta fito daga cikin net din da take kwance bayan ta tuna ko isha’i bata yi ba, tunda Mama Salame ta daura mata net tace ta shiga ta kwanta wajen karfe sha daya take kwance duk da ba bacci take ba, don ko bacci barawo bata gani ba, amma tayi shiru cikin net din tunani iri iri na yawo a kanta, gaba daya ta ji kamar hawayenta ma ya kafe, har a lkcn babu maganar da ya hadata da Ummanta, tana jin jiri da zazzabi ta nufi kofa zata fita ta dauro alwala, Umma dai ta bi ta da kallo, bayan ta dauro alwalan ta dawo ta saka hijab dinta ta tada sallah, bayan ta idar tayi nafila raka’a biyu, tana zaune kan darduman ta jingina da bango tayi nisa tunanin da take, gani take kamar a mafarki ake sanar mata an daura mata aure da Abdul amma ta ki farkawa daga mummunan baccin nan har yanzu, muryar Ummanta yaji ta kirata a hankali, Khaleesat ta juya ta kalleta amma ta kasa amsawa, Umma ta mike ta koma kusa da ita ta zauna tana kallonta, cikin sanyin murya tace “Me ya faru kuma tsakaninki da Abdul din Khaleesat? Wani abun ya kara maki? Me yasa kika ce baki son auren?” Khaleesat ta fashe da kuka a hankali tace “Umma wallahi bana son sa, bazan iya zama da shi ba, in aka ce za a kai ni gidansa zan iya mutuwa wallahi, don Allah Umma ku taimakeni ku yi min rai” Umma ta kasa ce mata komai hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da hijab dinta, Khaleesat ta daura kanta kan kafadar Ummanta tana kuka me tsuma zuciya tace “Don Allah ku taimakeni Umma, bazan iya ba wallahi” Umma ta rungumeta tana patting bayanta ita ma hawayen na sauka idonta amma bata iya ta ce mata komai ba, they sat there for almost 40 mins, jin tana sauke numfashi a hankali Umma ta gane bacci tayi, a haka Umma ta zauna wajen Khaleesat na jikinta don bata son tashinta har kusan lokacin sallahn asuba. Da safe wajen karfe tara Umma ta shigo dakinta rike da cup din kunu da kosai a roba, ta karasa kusa da Khaleesat dake kwance gefen katifarta ta ajiye mata sannan ta zauna cikin kwantar da murya tace “Ta so ki ci ko kadan ne Khaleesat” Khaleesat dai kallon cup din kunun kawai take, lkci daya hawaye ya cika idonta, Umma dai ta sunkuyar da kai, Islam ce ta shigo dakin rike da paracetamol da Umma ta aiketa ta siyo ma yayar tata, ta zauna kusa da Umma tace “Umma ga maganin na siyo ma Aunty” Umma ta amsa ta ajiye a gefenta tace “Tashi ki je ki karasa min aikin da na sa ki” Islam dake kallon Khaleesat ta mike a hankali ta fita daga dakin, Umma ta maida dubanta kan Khaleesat tace “So kike ki sa ma kanki wani ciwon ne Khaleesat nima ki sa min damuwa? Ki tashi ko kunun ne ki sha” Khaleesat ta girgiza mata kai cikin rawan murya tace “Ni bazan iya sha ba Umma” a sanyaye Umma tace “Toh ya kike son in maki Khaleesat?” Umma ta kasa ci gaba hawaye ya fara sauka idonta ta dafe kanta, kuka kawai Khaleesat take tana kallon Ummanta, Umma ta dake tana share idonta tace “Ko wajen Nenne zaki sai ki gaya mata ki ji abinda zata ce, ni kin san babu abinda zan iya yi akan lamarin nan Khaleesat” Ita dai Khaleesat bata ce komai ba, Umma ta mike a sanyaye ta fita daga dakin don juye mata ruwan wankan da ta dora mata a kan wuta yana ta tafasa, a haka ta ta dawo ta samu ta lallabata ta ɗan sha kunun sannan ta tafi waje yin wanka, kafin ta fito har Umma ta fiddo mata kayan da zata sa tayi tagumi tana jiranta, karfin hali kawai Khaleesat take amma ji take kamar zata iya collapse at anytime, bayan ta shirya Umma tace “Amma bana son yan gidan nan su san inda zaki, kar su gaya ma Malam” Khaleesat ta jinginar da kanta da bango, a hankali tace “Umma bazan iya zuwa ni kadai ba don Allah ki rakani” Umma tayi shiru, can tace “To zan fita in shiga gidansu Er Lami in jira ki a can, bana son su ga mun fita tare, bayan na fita da minti goma kema sai ki fito” Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Umma ta mike ta dau hijab dinta ta saka sannan ta dora nikab ta fita daga dakin, Su Mama Shatu da Mama Zubaida suna ta girka abincin siyarwansu da yaransu za su fita talla da shi, tace masu zata shiga makota sannan ta fita, duk suka bi ta da kallo sun tabe baki, Mama Shatu tace “Ma ji ma gani dai, a sanda ake mana fafa an tura ‘ya kasar waje ga namu yaran a zube ai babu bakin cikin da ba a kuntsa mana ba” Mama Zubaida tace “Sun gana tattatse ɗan mutane rana daya su fito su ce basu san zance ba, ke ina kika taɓa ganin anyi haka? Ai na so Malam ya rarrade shegiya jiya da daddare, to dai ba kanta kadai zata ja ma babban magana ba, har shi Malam din” Duk Khaleesat na jin su, ita dai tana zaune ta jinginar da kanta da bango tana sauke numfashi a hankali, bayan minti goma da fitar Ummanta ta tashi da kyar ta fiddo gogaggen Hijab dinta ta saka sannan ta dora Nikab ta fita daga dakin, tunda ta fito suke kallonta, a haka ta nufi hanyar fita daga tsakar gidan tana ji kamar iska zai kadata ta fadi. Gidan da Ummanta tace zata jirata ta nufa, ta samu Ummanta a tsakar gida tana jiranta yan gidan ma duk basa nan, Umma ta taso suka fita daga gidan, tafiyar kusan minti sha biyar ne zuwa gidan Nenne daga gidansu, Nenne ta ajiye tsintsiyar hannunta tace “Dawowa yayi da ita daga inda take karatun don an daura aure?” Umma ta zauna kan tabarman tsakar gidan ta cire Nikab din fuskarta ta gaida Nenne, Khaleesat ta zauna gefen Ummanta, Nenne ta amsa tace “Ai dama nace ko da ta dawo sai ta huta an kintsa ta kafin ayi maganar wata tarewa tunda yace baya bukatar taron komai, amma baza mu dau yarinya haka kawai ace an je kai ta ba” Umma dai tayi shiru bata ce komai ba, a hankali Khaleesat ta cire Nikab din fuskarta ta ajiye, Nenne ta ɗan duka tana kallonta tace “Lapiya naga idanuwanta sun kumbura haka, me ke faruwa?” Umma ta sauke ajiyar zuciya ta kasa cewa komai, A fusace Nenne tace “Magana nake ku ka min shiru fa? Meye haka aka shigo min da ita da kumburarrun ido” Cikin rawan murya Khaleesat tace “Nenne ni bana son sa, bana son auren…” Nenne ta saki baki tace “Baki son auren kuma?” Khaleesat ta gyada mata kai hawaye wasu na bin wasu a kuncinta, Nenne ta nemi waje ta zauna tace “Atoh dai, ni dama shegen bai taɓa kwanta min ba, amma abun dubawa a nan shine na isa da Alin? Ashe ma ba er banza bace ni a gunsa kenan” Nenne ta mike ta shiga dakinta ba a dau lokaci ba ta fito ta dire wani babban ledan hannunta sannan ta bude tace “Kun dai ga duk wata shegiyar kyautarsa da yake kawo min ban taɓa amfani da ko daya ba duk na tara masa kayansa waje daya, ga atamfofinsa nan da turarurruka da tarkace, ba ruwana ban yi amfani da su ba, ke ma Zahra’u inda abunsa da kika san ya taɓa baki ki tattaro su waje daya, shi Ali ina ma yayi amfani da nasa shi ya sani, sai ya shiga kasuwa da wuri wuri” Ita dai Umma tayi shiru bata ce komai ba, Khaleesat kuwa kuka take a hankali, Cikin sanyin murya Umma tace “Kin mance abinda ke kasa ne Nenne, ai yanzu ba maganar wai abinda ya bamu bane damuwar” Nenne tace “Yo ina ruwana da abinda ke ƙasa, ko ina ruwan yarinya da abinda ke kasa? Sai a ma jikata auren dole kike nufi kenan? Ni fa tun asali katon mutumin nan bai min ba sam, ayi mutum ba fara’a ya shigo maka sandan sandan ya fita gansan gansan? A duba fa wannan lamari, da kyar kaga murmushinsa kamar rikakken ɗan ta’adda da aka kusa yi ma preedom, yo wannan uban kudi na ubansa wa ma yasan ko ta’addancin suke da garkuwa da jama’a, hatta ruwan gidana gansamemen mutumin nan bai taɓa sha ba, yanda na ajiye masa haka yake barin min tsiyata bai san yarana mata ruwan gora suke siya min ba ya zata durawa nake, haka zai zauna maka kamar sarki yayi ta danna waya ga gidan er banza ya shigo, to ban isa da Ali ba kannensa mata ma basu isa da shi ba, shi kawai ta kansa yake a rayuwar nan baya duba makomar er da ya haifa a cikinsa, ko dan yaga yaran rakacaa an haifa masa ne ba kwantrol oho, gashi ba jin maganar yayyin uban nasa zai yi ba balle ince ku je ku samesu, in kuma muka ce mu tafi mu kai rahotu gidan yan sanda daga karshe mu za a kulle, to ni Ramatu ya zan yi? Amma dai ba komai zan aika a kira min Alin anjima, hatta batun daurin auren sai jiya da za a daura muke samun labari” A hankali Umma tace “Shi ma Malam din shekaranjiya da yamma suka kirasa suka sanar masa ga abinda suke so za ayi” Nenne tace “Tirrr, duk sun rainamu sun mayar da mu yan iska kawai, na tabbata shi kansa Alin bai taɓa rokon Awdul din naira biyar ba balle uban Awdul” Umma ta girgiza kai tace “Bai taɓa ba kam, jarabawa ce kawai Allah ya dora mana babu yanda mu ka iya” Nenne tace “A’a har da dai iskanci, ku baku da baki? ke da er taki baza ku iya kwatar en cin ku ba, ita kadai ce mace a gidan? Tun asali dama kin maida kanki gantalalliya a gidan” Umma dai tayi shiru, Nenne tace “Ko kuma kawai ku tafi gida zan daidaici lkcn da zai koma gida da magariba in taho gidan” Umma tace “Toh shikenan Nenne” a haka Khaleesat da Ummanta suka bar gidan bayan Nenne ta dama mata fura da nono ta tilastata ta sha. Khaleesat na kwance dakin Ummanta wajen karfe shidda na yamma, har zuwa sannan ta kasa cin komai tun bayan furan da ta sha gidan Nenne, tun da suka dawo gida take karatun qur’ani don ta rasa me ke mata dadi a duniyar kawai bata son tayi ta daga ma Ummanta hankali yasa ta hakura da kuka sai na zuci kawai da take yi, gaba daya taji duniyar yayi mata zafi, da ta tuna wai fa ita matar aure ce yanzu kuma matar Abdul, sai taji dama kawai Allah ya dau ranta ta huta, bayan taji she is exhausted da karatun qur’anin da take tayi shine ta kwanta gefen katifar Ummanta, tayi nisa tunanin da take jin hawaye na taruwa idonta ta mike zaune tana kallon Ummanta dake gyara kayan su Islam a dakin tace “Umma ina wayarki?” Umma ta kalleta tace “Ko sati ba ayi ba na nemeta na rasa an dauke a gidan nan” Khaleesat tayi shiru tana kallon Ummanta, sai kuma ta jawo handbag dinta a hankali ta bude ta ciro wayar da Jay ya bata duk da babu SIM card a ciki, she just want to do something that will keep distracting her from her worries, har zata shiga game sai kuma ta fasa ta shiga gallery din wayar, ta ɗan yi jim na few seconds kafin ta bude hotunan, a hankali take flipping tana kallon each and every image of him and AJ, sai a sannan ta lura da kaman da suke yi even though it’s not obvious, wani hotansu tare ta tsura ma ido ganinsu cikin shiga ta alfarma irin ta sarauta, ita dai tana ta kallon hoton babu ko kiftawa, sai kuma tayi flipping zuwa next image, haka ta dinga ganin ire iren hotunan, wani taga Jay shi kadai wani taga Ajay shi kadai, ko kuma ta gansu tare, with horses and so many things related to gidan sarauta, kashe wayar tayi a hankali ta mayar cikin jakarta ta ajiye jin muryan Babanta ya shigo gidan, ya ɗaga labulen dakin Ummanta yana kallonta yace “Ki fita ga Abdul can ya zo yanxu” Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta dinga kallon Babanta bata ko kiftawa, Umma ta juya ta kallesa tace “Ta fita kuma Malam? Dama ana haka? Ai ina ga ba sai ya zo ba sai ya jira har zuwa sanda zata tare ko” Malam Ali da ya bude baki yana kallonta yace “Wato dai duk wani salon dauko min magana kun iya shi Zahra’u, in ya zo ta fita sai aka yi yaya? Addini ne ya haramta hakan ko kuwa shirmen ku? Kuma da kike batun tariya ko gobe yace yana bukatar ta tare mu muna da ja ne dama?” Umma tace “Ai ko muna da ja Malam, tunda baza mu dau yarinya haka kawai mu kai ta dakin miji ba, duka duka ma yaushe ta dawo kasar” Khaleesat ta fashe da matsanancin kuka tana jin kamar zuciyarta zai fashe ta huta, Babanta da ya bude baki yana kallonta yace “Ni kike neman tona ma asiri ko ko ya kike so inyi? Sabon magana za ku ja min ke da uwarki kenan? In ma ba yanzu za a tare ba tunda ya zo ai sai ki fita ku gaisa tunda ba haramun bane, in kun gaisa sai ki dawo cikin gida” Khaleesat taki cewa komai sai kuka take, Ya daka mata tsawa yace “Kar ki ga ina lallabaki don uwarki, zaki tashi ki fita ko sai na rarrade ki da icce” Khaleesat na kuka ta sauka daga kan gadon, Umma da hawaye ya cika idonta ta kauda kanta, Khaleesat ta dau Hijab dinta ta saka ta fita daga dakin tana kuka sosai, Kishiyoyin ummanta dake zaune tsakar gida duk suna sauraron abinda ke faruwa sai tabe baki suke, ganin Malam Ali ya bi bayan Khaleesat, Mama Shatu tace “To rakata wajen nasa zaka yi ne Malam?” Sai kuma ya juyo da sauri yace “Au to” Ya nufi ɗan karamin dakinsa dake tsakar gidan, Mama Zubaida ta tabe baki tace “Ma ji ma gani dai” Khaleesat na fita kofar gida hawaye na sauka idonta taga motarsa wanda ke dauke da tinted glass yayi parking dai dai inda su AJ suka tsaya jiya, ko saukowa bai yi daga cikin motar ba, hawaye na bin fuskarta ta tafi ta tsaya kusa da motar taki budewa kuma tasan yana kallonta, after almost 5 mins taga ya sauke glass din motar yace “Ni zan sauko in same ki?” Ita dai taki kallonsa, kuma taki cewa komai, after few seconds ta bude gaban motar a hankali ta shiga amma ta ki kulle motar, yace “Sauron unguwan ku zaki cika min a motata, are you in ur right senses?” A hankali ta ja motar har sannan taki yarda ta kallesa ta kulle, gabanta sai faduwa yake don jin muryarsa take kamar ana tsira mata allura a kunne, Lokaci daya ta juya da sauri tana zaro ido ganin ya zuge glass din ya tada motar ya kara volume din sautin da yake ji sannan ya ja motar, a rikice ta fara kokarin budewa motar taji a kulle gam, ta kwala wani azababben kara tace “Na shiga uku na lalace, don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ina zaka kai ni? Ka bude min in sauka….” Ko kallonta bai yi ba fuskarsa babu yabo babu fallasa yake driving dinsa idonsa na kan hanyar dake gabansa, ta rikosa da hannu biyu cikin gigicewa tana masa magiyan ya bude mata motar, bai yi wata wata ba ya sauke mata wani lafiyayyen back hand slap a fuska, sai da taji dumm na few seconds, lkci daya jin ta da ganinta ya dauke na ɗan lokaci, duk da haka bata sake sa daga rikon da tayi masa ba tana kururuwan ya bude mata motar, ya fincikota ya jefar kan kujeran motar cikin kaushin murya yace “Kika sake taɓa ni sai na wanka maki wani marin” Lokaci daya duk jikin Khaleesat ya mutu saboda shock, ta dinga sauke numfashi da kyar idonta na ganin dishi dishi daga marin da yayi mata tana kallonsa, shi dai driving dinsa kawai yake fuskarsa babu yabo babu fallasa……*
