Uncategorized

Shin Da Gaske Sheikh Dahiru Bauchi yace Gobe sallah?

 

A nan ake yada labarin cewa sheikh Dahiru Bauchi yace gobe Lahadi sallah kamar yadda labarin yake yawo a yanzu sada zumunta kamar haka.

Fitacciyar ‘yar gwagwarmaya daga Tamil Nadu, Sabarimala ta Musulunta

 “YANZU-YANZU: Gobe Lahadi Take Sallah, Cewar Sheik Dahiru Bauchi

 Bayan shafawa da hotunan mai kariya Maulanmu Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya tabbatar da an ga jaririn watan Shawwal a jihohin kamar jaka Birnin Tarayya Abuja, jihar Nasarawa da kuma Kurgwi dake jihar Filato.

Karshe dai Maulana Sheikh ya bada umarni a sha ruwa gobe Lahadi babu Azumi Insha Allahu, domin Azumin bana ya zo karshe..

 Maganan Sallan Idi kuwa Shehu ya ce tunda nafila ce a dakata sai ranar da za a yi na gari gaba daya sai a yi tare.

Lallai na yadda Annabi Muhammadu Shine fiyayyen Halitta-cewar Rani Mukherji sananniyar Jarumar fina-finan Indiya.

 Daga Abubakar Ibrahim”

 Amma a bisa haka Hausaloaded sunyi musu sun gano cewa karya ne duba da shafin shehin malamin ya nuna yana Saudiyya wajen umrah kuma ya wallafa cewa za’a yi sallah a ranar Litinin.

Back to top button