Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 9 Complete Hausa Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

*💋romantic love story btwn Sehrish & Surgeon General Rafayet💋*

    _Heart touching story abt a Triplet_😢

mamaki ya ke ganin taƙi ɗauke eyes ɗinta akansa, kuma bata da niyar daina kallonsa, hannunta har rawa yake yi wurin ajiye spoon ɗin da ta ɗauko,

Lumshe idanunsa yayi a hankali yana ƙare mata kallo acikin zuciyarsa yana cewa “Ya Allah ka mallakamin wannan baiwar ta ka,’ 

A yayin da sehrish ke cewa” 

_tsarki ya tabbata ga ubangijin daya halicci wannan kyakkyawar surar Junaid duniya ne_💋

_shigowar azmee ne ya dawo dasu daga wannan tunanin na ƙurawa juna ido kowa ya waske_

cikin fara’a azmee tace” junaid me ka ke bukata ne na kawo maka? naga baka ci komai ba,

A cikin zuciyarsa yace”kallon ta danake koshi nake Aunty azmee”

A fili kuma yace” nima cornflakes ɗin zan sha, a haɗo mun da fresh fruits’

“Junaid ba ka son cin abinci ko? Kafi son ƴan lashe lashe kamar Tukur”?

Wani irin murmushi ya saki jin abunda azmee tace har time ɗin idonsa nakan sehrish wadda ta mayar da idonta kan cheese burger ɗin dake gabanta so take ta ɗauka taci amma zuwan junaid yasa duk ta dabarbarce sai ƴan kame-kame take 

“Aunty azmee ae we are the same ni da shi,’ 

Azmee tace “gsky saina haɗa maka da farfesu mai zafi zaka ji daɗinsa,’ 

Junaid yace “its ok am waiting,

zuciyarta sai faman ɗar ɗar take yi mata, kamar mara gsky koda yake ba gaskiyar ae,

Shi kam ya zuba mata ido yana kallonta, yarinyar ta kwanta masa a heart ɗinsa, just he is affected 💘 

Azmee ce ta ƙaraso hannunta ɗauke da plate wanda ta zuba masa farfesun ganda aciki, ajiye wa tayi a gabansa, sannan ta koma ta Kawo masa fresh fruits ɗin daya bukata acikin wani haɗaɗɗen round tray, 

sannan ta koma ta kammala haɗa masa corn flakes ta kawo masa, 

A hankali ya furta “shukran aunty azmee’

azmee ta juya ta fice tana ɗan murmushi bata ta6a sanin cewa junaid Romeo bane na gaske sai da ya gane cewa reeshi maca ce ba namiji ba, ❣️

Ƙamshin farfesun gaban junaid ne ke ta faman kai mata hari, ɗagowa tayi tana satar kallonsa, 

A hankali yake sa hannu yana ɗaukar gandar ta dahu tayi tubus taji kayan haɗi na kamshi, irin wadda daga kasa a baki zata dagargaje😋

A hankali yake turawa abakinsa yana tauna, ganin bai kara ɗagowa ba yasa tayi saurin wawurar burger ɗin tana turawa a baki, 

Muryarsa ce ta katse ta “Ki ci a hankali,” ya furta yana ɗan smiling ashe ya ɗago bata sani ba

kaɗan ta gutsara ta maida ta ta ajiye, hot dog ɗin ta dauka tana ci, 

a yayin da shi kuma ya ɗauki spoon yana shan cornflakes ɗin da azmee ta kawo masa, 

Wani tunani ne ya faɗo masa aransa a lokacin da yake kallon sehrish wadda take ta faman ƴan kame kame, 

Bin ta da kallo yayi aransa yace ” Wani abu na ban mamaki nikam, ko ya aikai take matse boobs ɗinta, suyi flat tamkar babu, dama Allah yasa su 6ace muga yarda zata yi……..

Shi kansa baisan dariya ta kubuce masa ba, har ya fetsar da cornflakes ɗin dake bakinsa, zuba mishi ido sehrish tayi gaban ta na faɗuwa tsoranta kada ace wani abu junaid ya ganu wanda zaisa ya gane cewa ita maca ce,😳

Sai faman tiƙar dariya ya ke yi ba kakkautawa, sam ya gaza stopping kansa, 

Tamkar tv haka ta ƙura wa junaid ido yana dariya, fararen hakoransa jere rass take kallo ga ƴar wushiryarsa siriri ya, 

ganin ya kasa controlling kansa ya sa ya miƙe ya kama hanyar fita yana ci gaba da dariyar,  

Abun ya bata mamaki, ganin ya tashi yana ta dariya gashi baici abun kirki ba, anya junaid yana da lafia kuwa? Ko dai yana da psycriatric disorder ne? 

daga bisa ni ta ta6e bakinta alamar i dont care taci gaba da shan abunta, 

Bedroom ɗin abbansu ya wuce directly, a hankali ya tura kopan ya shiga, samun shi yayi a tsakiyar gadon ya baje abunsa, ya warware, 

Murmushi ya saki ganin abban nasa, har cikin ransa yaji daɗi ganinsa ya dawo cikin ƙoshin lafia,…

“Lallai abba abu yayi kyau, shine an dawo ko a neme ni, aiko yanzu baccin nan naka zai ƙare,’ 

Ja da baya yayi sannan ya watsa a guje ya faɗa saman gadon sai ajikin abban nasu a firgice cikin magagin bacci abban ya rinƙa faɗin “a miko bindiga 6aro ya shigo ‘ 

fashe wa da dariya junaid ya yi, yana kallon abban nasu wanda idonsa ke a rufe yana ta faman sambatu,’ 

tabbas yaji nauyin mutun akansa, amma sam ya gaza buɗe eyes ɗinsa sbd a gajiye ya ke, 

Cikin rashin imani junaid yasa hannunsa yana gwale masa idanu, sunyi ɗan ja, biji-biji yake ganin junaid sai faman zabga murmushi yake,

Cikin nishaɗi ya ce “Abba its me your heart beat, i came here to disturb u,  🤣

a hankali abban ya idasa buɗe idanunsa, a firgice ya yunkura ya janye junaid gefe ɗaya, ba ƙaramin tsorata yayi ba, saboda idonsa wani farin aljani nuna masa sai da ga baya gane cewa she junaid ne, 

“Yanzu ka kyauta ? dama ina ji an hau saman jikina nasan cewa kaine, duk duniya babu maiyi mun haja sai kai,’ 

“Cikin shagwa6a junaid yace “ka dawo baka neme ni ba abba,’ ya ƙare maganar yana zumbura masa baki, 

yatsina fuska abban yayi yana kallonsa aransa yana cewa ” ynx fa sai yace zaiyi mun kuka shi ala dole gabu auta, bari na jaraba shi nagani ya canza ko hanyarzu yana nan yadda na barsa, 

ɗaure fuska yayi tare da nuna ma junaid hanyar fit yace “kai tashi ka fice mun bana son takura jarababbe,’ 

cikin yanayin mamaki junaid ya ce” abba Ni kake ce ma jarababbe? Kadawo baka neme ni ba kuma shine kake korata ? 

Abba yace “ka ga tashi ga fice mun tunkan nawaje suji mu,’ ya faɗi yana kara tamke fuska, 

.ganin cewa dagske abban nasu yake yasa ahi tashi jiki a sanyaye ya sauka daga saman bed ɗin ya isa bakin kopa, bai bude kofan ba tsayawa yayi yana jiran abban ya bashi hakuri,

ɗan juyawa  yayi da kansa ya saci kallin abban nasu wanda ke zaune tsakiyar gadon, haɗa ido sukayi lokaci guda 👀

narai narai da ido junaid yayi alamar zai yi kuka, shi kam Abban abun ɗaure masa kai ya ke yi, har wani sa in tunani ya ke anya Junaid namiji ne ba mace ba? Ace har yau mutun jin kansa ya ke kamar jinjiri, ko don ba nonon fatima yasha ba ? Don tabbas yasan cewa da ace fatima ta shayar dashi da guyababbe zai zama ba susu ba, amma duk da hakan ƙara son yaron nasa ya ke fiye da sauran, zuba mishi ido ya ci gaba da yi, 

Junaid dake tsaye yana sum6ura baki, biji biji ya soma gani a idanunsa, lokaci guda ya soma sakin tari, hannu yasa tare da dafe saitin zuciyarsa, yana ambaton kalmatussha hada, 

Hankalin abban nasu a tashe a wani irin firgice, shi kansa baisan lkcn da ya wuntsilo daga saman gadon ba, sai wurin junaid wanda kafin isowar abban nasu ya zube ƙasa 😨

Cikin wani irin tashin hankali, abban ya dire guiwarsa a gaban junaid inda ya ke kwance ba numfashi,

Muryarsa har rawa rawa take yi wurin furta “Innalallahi wa’inna ilaihirraji’un junaid !! Junaid!!! meke faru wane ! Ka tashi dan Allah nifa wasa nake ma, 

hannunsa yasa yana bubbuga ƙirjinsa, tuni idon abban nasu ya cicciko da kwalla “kai ka tashi bana son wasa ! ya kake so nayi da rayuwata in na rasa ka, 

Junaid bai buɗe ido ba sai da yaji dirar hawayen abban nasu a fuskarsa sannan ya buɗe su yana dariya,

Aikuwa abban ya rufesa da duka, ta ko’ina, tashi ya yi ya watsa a guje suka shiga zagaye ɗakin suna yar guje guje

“wlh junaid baka da mutunci, ko tausayina baka ji, ka rasa irin wasan da zakamin sai wannan, kasa shugan sojoji zubda hawaye, ‘ 

Yana biye dashi  yana magana, haye wa saman gadon junaid yayi abban ya bisa,

A tare suka kwanta sama suna facing ceilling, junaida yace “abba na gaji wlh” 

“nima na gaji junaid, dan Allah kada ka sake min irin wannan joke ɗin bana so, baka ji yadda hankali na ya tashi ba,’ abba yayi maganar yana haɗiye yawu,

Junaid ya ce “dama haka kake so na abba, tab dole na tsula tsiyata son raina, wlh abba ka ban mamaki hada yar hawaye,’ 🤣

dariya abban yayi tare da cewa “ba dole ba, hmmm baka son yarda nake jin ka bane shiyasa, ynx dai tell me da bana nan waya ta6amin kai ? muɗaura ɗamarar yaƙi, ? 🤨

tashi zaune junaid yyi saman bedmattress ɗin yace “zan faɗa maka daddy but firstly tell me ka yi mun tsarabar da nace ?

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Abba yace “ya za’ae na manta babyna, ba traditional dress ka ce kana so ba ,na ƴan china? Ae na siyomaka abubuwa da dama ma, suna nan,’

Wani irin murmushin jin daɗi junaid ya saki tare da cewa “abba kayima kanka ƙiyamul laili da ace baka siyamun ba ko, hmmm da kaga rigima, 

dariya abban yayi yana kallonsa har time ɗin yana daga kwance, junaid yaci gaba da cewa “amma abba baka haɗu da wata zazzafar ƴar budurwa haka ba acen? Nasan ka da farin jini  , 

Cikin zolaya junaid yayi maganar, ɗan zaro ido abban nasu yayi tare da cewa “tab ! ae na gama wlh, Wa ? ni hussein la la la laa, waɗannan fararen basu da guarantee, yadda momynku ta gasa mun aya a hannu, wannan gasuwar ta ishe ni haka, na ɗauki darasi, 

Ae ko zan ƙara aure iya nan ne, bazan wuce hausa fulani ba, mata masu kunya, ga riƙo da al’ada ga girmama muji Allah sarki maryam 😢 

dariyar junaid yayi tare da cewa “su Abba anji jiki, dama ance jiki magayi ne, ynx kaji jiki ko? sai yanzu ka gane cewa matan mu suna girmama muji ko amma ka  tashi ka auro mana  ….’ 

bai bari ya idasa maganar ba ya yunkura ya janyosa jikinsa yana yi masa dundu a baya, yana cewa “junaid wai tsaran wasanka ka maida ni ko ? na ta6a cire kaya agabanka ne ? Shiyasa ka raini ko,?

dariya junaid ke ta faman 6a66akawa, shima abban dariyar ya yake yi, haka suke in suka haɗu suyi ta shiririta kai kace ba uba da ɗa bane, 💓

………….Sehrish…………………

ta koma cikin ɗaki kasancewar babu wani aiki da zatayi, su aunty azmee da chef ummu da momina duk suke gyara komai, 

zarya take ta faman yi a room ɗin nata, zuciyarta husanna da jahad kawai take Calling, aranta tana cewa “meyasa duk cikin abunda bature ya ƙirƙira baiyo wings ba ? fika fiki, a shiriritar ta , da ace tana da fiffike da tuni tayi sama ba tare da sanin kowa ba ta ware sai wurinsu husanna 😢

ita ce har wurin sallar magriba tana tunanin abu ɗaya, 

Acan ciki kuwa abba , yasamu ya fito shida baby junaid, bayan sun gudanar da sallah kowa ya hallara a main palour ɗin mazan kawai suka zauna, suna kara gaisawa da abban su.

general ishaq na zaune a 3 seater shi da Captain najeeb da talal, 

Abuhaisam na tare da Abbas da kanal yusif atare suma a mazauni ɗaya, 

Fawan da khaleed da jabeer da irfan suma duk suna a tare, 

Yayin da abba ke zaune tare da junaid a side ɗinsa sai twins, 

gyran murya abban nasu yayi sannan yace ” ina kara godiya ga Allah dayasa na dawo na same ku cikin ƙoshin lafiya, naji daɗin hakan sosai, naga wasu sunyi ƙiba, wasu sunyi haske wasu kuma fara ajiye tumbi 🤣

gaba daya suka fashe dariya, dama indai zolaya ce abban nasu ya saba, 

general ishaq yace “wannan dai dani ake, maganar masu ajiye tumbi, kuma na gode, 

murmushi abba yayi tare da cewa ” Sorry first born ni na isa na sa dakai, kai fa na fara gani kafin sauran,’

Abbas yace “ƙwarai mu aka fara gani kafin sauran, ƴan shisshigi da kutsu, ‘ yayi maganar yana kallon junaid wanda ya kwantar dakansa ajikin abbansu, 

“Ya fi kowa iyayi abba, kamar shi kaɗaine auta nima fa autan ne,’ acewar talal, 

fawan yace ” ae wani aikin ma sai in BABBAN YAYA ya dawo nan zaku ga shagwa6a da narkewa da yake mutuminsa ne, 

Abba yace “oh wai harynx kuna yiwa junaid irin wannan taron dangin, narasa me ya tsole maku, to bari kuji nan gani nan bari dukiyar uban wani ehe, ya faɗi yana kara janyosa ajikinsa, 

dariya su kayi abuhaisam yace “Abba kana sane kuwa da zuwan Lion da tiger? 

ɗan zaro ido abba yayi tare da cewa “kai haba ? Badai wannan uban ƴan ji dakan ba, ɗan wurin Alexandra kke cewa ba? Ka ce na tattara kayana na gudu ,” 

Yayi mgnr ne cikin zolaya sai kace ba akan ɗansa ake magana ba, 

“Abba kana kiran sunan momynmu kai tsaye ko sakayawa baka yi, ina laifin kace ɗan wurin fatima a musulunce dai,” 

Ayaan ne yayi maganar yana hura hanci, 

dakuwa Abbas yayi masa tare da maimaita sunan ance “alexandara ba sunan ta bane ? ita da kanta tace ko ƴa’ƴanta bataso su kira ta da mommy tafison sunanta Alexandra ko ƙarya nayi? 

Kanal yusif yace “aɗan sakaya dai yayanmu, saboda ƙannenmu,” 

Abba yace “ynx don rashin kunya, abbas agaban idona kake faɗin sunan masoyiyata kai tsaye? gaban kuma shalelena ?

Junaid ya ƙara rakwabe fuska, dariya su kayi  cikin nishaɗi suke firar kowa na ɗan tsoma bakinsa, 

Azmi ce ta kawo musu abunsha kowa ya kar6a, dama ka’ida ne duk bayan ƴan minti na sai ansha tea ko coffee 😌

tura kopan ɗakin tayi ta shiga tana faɗin “Amani baki ga text ɗina bane nace ki same ni a ɗaki”? 

aunty babba ce ta shigo ɗakin da amani ta sauka tana mata magana, 

Amani dake kwance saman bed hannunta rike da waya tana daddanawa, jin muryar auntyn tata yasa ta tashi zaune, bakar jallabiya ce a jikinta, kanta ba ɗan kwali sai doguwar sumar kanta data zuba a shoulder ɗinta, 

“Sorry aunty na ban ankara ba, na dai ji shigowar message ban duba ba,’ 

Ƙarasa wa tayi kusa da ita ta zauna a side bed din suna facing juna tace “hmmm amani kenan, wato tunda nayi miki hanyar arziƙi, ki kayi kyau kika ƙara haske, kwanciyar hankali ya samu ki ka daina tako wa kizo inda nake ko? Ko phone calls babu ? A whatsapp ma ina ganin ki online ba magana,  wato naira ta zauna ko? 

Yar dariya amani tayi “haba aunty na, pls stop saying that, ke fa ce silar shigata wannan daular taya zan share ki ? Ae kullum ƙara gode miki nake, sbd ynx ko a mate ɗin mu ba wadda takama kafa ta wurin arziƙi, ynx fa takai ga ko taro za’a yi na class mate ɗinmu indai ban halacci taron ba to fasa shi akeyi, kowa burinsa na zo ba don komai ba sai don aga wanka leshin da zan ɗauka da zinaran da zan sanya,’ 

jinjina kai Aunty babba tayi tana ƴar dariya “haka nake son ji my sister, nafi so naga kuna wuta ana binku da fetur, ku zama on top kai kuzama ma topic ɗin gaba ɗaya, inji kawai ana zancen ku a ko’ina, 

ta ƙarashe maganar da cewa “ina fata dai baki raga masa ko? Kina tatsarsa sosai kina matso sa sbd kinsan fa abunda ya kawo mu family ɗin nan dukiya muka zo mallaka domin mu raya namu family ɗin,’ 

Zuru Amani ta ɗanyi tana kallon auntyn tata, cikin sanyin murya tace “Mallakar dukiya kuma aunty? banda kuɗaɗen da muke samu a hannun mazajen mu har wata dukiya zamu mallaka ? 

dariya aunty babba tayi tare da dafa kafaɗar Amani tace “ke fa matsala ta dake wani lokacin baki da lissafi, bakya gane wa, ae ynx kowa ta kansa ya ke yi, kuɗi kawai dole mu nemi kuɗi kamar hauka, saboda ynx mun shigo wani zamani da in baka dasu ba’ayi dakai, ka zama tamkar non living thing, masu kudi sune living thing, masu rai kenan,’ 

Ta ƙare mgnr tana kallon Amani wadda ta ɗan dabarbarce sbd auntyn tata ta fara bata tsoro, 

Aunty babba taci gaba da cewa “Oh wai ke da soyayya kika zo kisha wurin ABBAS? Ae ni ban haɗa auranki da abbas ba don soyayya kawai, face don ki rinƙa tatsar mana shi, sannan naga haryanzu babu ciki a jikin ki, uban me kika tsaya jira !?

Hankalin Amani fa ya tashi ganin yadda lokaci guda auntynta ta, ta bayyana mata mummunan ƙudirinta akan family ɗin Abban Sojoji,

Ajiyar zuciya tasaki kafin tace “aunty ra’ayinmu ne yazo ɗaya, shima bayason haihuwa da wuri munyi planing sai nan da 5yrs, ynx soyayya kawai muke sha……. “

Katse ta auntyn tayi da cewa “ko ba soyayya ba? Nabi soyayyar da gudu, ashe head fish gare ki sam bakya gane wa, to bari kiji in faɗa miki, ki aje wannan planing ɗin, ki ɗauki ciki kawai ! mun samu mai cin gado, nima nan da kike gani na, ba don lalurar da ta same ni ba,  da tuni na jima da sauke wani,

Jinjina kai Amani tayi tana kallonta cikin mamaki, 

ƙasa ƙasa da murya tayi kafin tace “ke nifa wani target gare ni akan wasu cikin family ɗin nan, kuma ina mai tabbatar miki da cewa it will work,’ 

Amani tace “me ke nan aunty”?

wani shu’umin Murmushi aunty babba ta saki kafin tace “BABBAN YAYAN su ! da MARSHAL OMER, ” 

zaro ido amani tayi tare da dafe kirji tace ” aunty me kike nufi dan Allah, fahimtar dani, kaina ya ɗaure,’

ƴar dariya Aunty babba tayi sannan tace “So nake na sama ma, ƙannan mu gurbi acikin gidan nan ! Kuma waɗannan shahararrun su nake hari ! ta ƙarfi ta tsiya 😳

cikin tsananin tashin hankali Amani tace ” Aunty anya ba giya kika sha ba ? kinsan suwa ki ke magana akai kuwa ? Babban yaya fa da marshal omer ? 

Cikin jaddadawa Aunty babba tace “ƙwarai kuwa ! Su nake nufi kuma a shirye nake da nayi koma mai zanyi don na asirce su naja ra’ayinsu akan Hayaam da Abrah,” 

Zuba wa juna ido su kayi suna kallon kallon, har ynx Amani ji take tamkar mafarki take yi ba gske ba, ƙarfin hali irin na auntynsu ya bata mamaki tarasa wa zata ce sai Rafayet da Omar ? Anya kuwa aunty bata sha wani abu ba? 

Katse mata tunanin ta tayi da cewa “na lura har ynx bakisan me nake hari ba, bari nayi miki dalla dalla, 

Rafayet da ki ke gani duk family ɗin Abban sojoji ba wanda yakama  ƙafarsa wurin tarin dukiya, gashi matashi ga kyau, a binciken da nayi Rafayet ya mallaki  billions of dollars nasa na kansa, bayan tarin gidajen dake gare sa a us da sauran countries ɗin da yake yawan zuwa, sannan kuma ya mallaki privet jet nasa nakansa, ga tsadaddun motoci dake gare sa ƙirar bugatti, ƙirar mercedes benz, ƙirar pagani da ferrari da sauransu, ke duk wani abu da kike sani mai tsada rafayet ya mallake sa, shi kanshi tsadar gare sa, ke nifa farko dana fara ganin shi wlh, sai da nayi danasanin auren ishaq, hmmm ke fa bakisan shi ba ko, ae zai zo ne,

Amani ta gama rikice wa da jin irin dukiyar Babban yaya, cike da mamaki tace “wai dagaske kike auntyna ?

Murmushi Aunty babba tayi “ƙwarai ma kuwa, Rafayet he’s among the most richest men in the world, youngest billionaire ne, Kuma yana ɗaya daga cikin most handsome men  saboda kyansa da structure ɗin jikinsa, 

    Jin jina kai kawai Amani take yi ta jin jinawa lamarin, 

Murmushi aunty babba tayi kafin taci gaba da cewa “Bayan Babban yaya kuwa a wurin arziƙi cikin family ɗin nan sai Hajiya azeema, wannan matar da ki ke ganinta ƙuruwa ce wurin arziki,business ɗin golds take yi da diamonds, ina wannan agogon ta hannunta ? Kin ganta ae ko ?

  ta faɗi cikin son fahimtar da Amani,

“Eh aunty na ganta mai kyau kamar na sace wlh,’ 

   “Hmmmm to wannan da ki ke gani ƙirar graff diamonds ce, $40 millions a us dollars, a naira kuwa sun kai 24 billions,’ 

   dafe ƙirji Amani tayi gaba ɗaya tabi ta susuce, jin abun take tamkar a mafarki, sakin baki kawai tayi galala jin wannan daular,

   Aunty babba taci gaba da cewa “daga ita kuwa sai marshal Omer wurin arziƙi, shima billionare ne duk wani abu da Babban yayansu ya mallaka shima ya mallaka, don dai ya wuce shi da wasu abubuwan, sune kawai nayi bincike akansu, sauran kuwa kowa attajirin kansa ne, ya ki ke  gani idan Hayaam ta samu shiga Wurin Rafayet ita kuma Abrah muka kutsa ta wurin Omar ?

  Washe baki Amani tayi tare da cewa “ae shikenan kawai ba sauran magana, mun gama kwaɗaice wa,” 

  dariya su kayi gaba ɗayansu a dai dai lokacin Azmee tayi knocking kopan ɗakin, cikin sauri suka gyara natsuwarsu,

Amani tace “Shigo ciki” tura kopan azmee tayi ta shigo da fara’a a fuskanta tace “dama an kammala dinner ne, naji shiru baku fito ba shine nace bari nazo na sanar daku,”

*Me zaku ce game da Aunty babba da Amani dake shirin mallake dukiyar da ba ubansu ya tara ba ?*

Yinin ranar jin jikinta take yi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa, shi dai gayanan wata ni’ima ni’ima , ga wata irin kasala da ta mamaye ta, sai wani lalaci da take ji, saukin ma aunty Azmee ta sanar da ita cewa bata da aiki ta zauna ta huta kawai, yau ranar hutun ta ce , yini tayi tana safa da marwa frm wall to wall, zullumi iri iri agame da su HUSANNA da JAHAD, ga kuma wani irin bugu da zuciyarta take yi mata, ita dai tunkan ta sa wannan Babban yayan nasu a ido take jin feelings agame dashi  (kina ruwa 😂)

Har cikin bedroom dinta azmee ta shigo mata da dinner dinta, ba karamin dadi taji ba, kaunar azmi na kara shiga cikin zuciyarta, sbd tana kula da ita kamar yar cikinta, ta damu da ita sosai, Allah sarki, 

Zuba wa meatballs din dake shake cikin plate din dake ajiye saman bedside drawer dinta tayi, ga fresh milk acikin glash cup, shiru tayi tana kallonsu, jikinta a mace yake, ga kamshinsa ya cika ta, amma a kullum ji take kamar batayi wa yan uwanta adalci ba, tana cin irin wannan dadin yayin da suke ciki mawuyacin hali, 

Zugudum tayi a yayin da take zaune a saman gadon daga baki baki, ta lankwashe kafanta a sama, 

Azmi ce ta sake turo kopan ta shigo hannunta dauke da fresh fruit acikin dan plate, 

“Ya akai har yanzu baki fara ci ba? me kike jira ?

ajiyar zuciya sehrish tasaki tare da cewa “Aunty azmee zuciyata bata mun dadi in na tuna da yan uwana, sai naji bana son cin komai, 

Cikin nuna damuwa azmi takarasa ta ajiye mata plate din a hannunta, sannan ta zauna gefenta cikin natsuwa tace ” kin yi imani da Allah!?

daga kai sehrish tayi tare da cewa”Eh” 

   “Ina so aduk lokacin da zakiyi addu’a ki kasance mai cike da imani, kiyi imanin cewa addu’ar nan da kika yi Allah ya karbeta, don’t doubt about it sbd karancin imanin kesa muna rasa wani abun,  amma muddun ki kayi masu addu’a kina me cike da imanin cewa Allah ya karbeta, ba tare da kinsawa ranki kokwanton cewa Anya Allah ya karbi addu’ a ta kuwa? Ko kuma kinji shiru har ynx ba ki ga sakamako ba, duk ba’a son wannan, kawai kisa ma ranki cewa duk in kikayi addu’ a Allah ya amsa kuma tom insha Allah zaki ga sakamako mai kyau, kuma zakiji natsuwa acikin zuciyarki,” 

Jinjina kai sehrsh tayi tare da cewa “ngde aunty azmee kuma insha Allah zanyi kamar yadda ki kace”

Murmushi azmee tayi tare da cewa “yawwa rishi na, ko kefe yanzu dai ayimun wannan murmushin kashe zuciyar nagani” ta fadi cikin zolaya tana kallonta,

Sunnar da kai sehrish tayi tana murmushi, itama azmeen murmushi take yi, hannu azmee tasa ta dauki yankakkiyar abarbar dake cikin plate din dake ajiye a saman hannun sehrish,

  A baki takai mata tare da cewa “Ha bakin nasa miki’ 

 Bude baki sehrish tayi tana yar dariya, zura mata abarbar tayi, sehrish ta taune, nan take zakin abarbar ya cika mata baki, takama lasar labba, 

   Azmee tace “yawwa ko ke fa ynx naji magana, bari na baki meatballs din abaki,” 

  Cikin sauri sehrish tace “a’a aunty azmee zanci ynx, kunsha aiki kun gaji, gashi ban tayaku ba,’ 

  “Kada ki damu sehrish, ae ni nace ki zauna tun da gasu Chef ummu aiki na tafiya yadda ya dace, ina fata dai bakiyi tunanin BABBAN YAYA ba yau ?”

 Ta karasa maganar tana kallonta, cikin zolaya,

 Sunnar dakai tayi tana murmushi jin an ambaci sunan da ke mata kaikayi a cikin zuciyarta, 

  “Bani da amsa kenan, tam ni zan tafi ynx kada ki manta, a daren yau kiyi sallolin nafila, kiyi addu’o’i wa yan uwanku da kuma sauran al’ummar musulmai,” 

    “Insha Allah aunty Azmee ngde sosai” 

Tashi Azmee tayi ta fice 👋

Hakika sehrish ta samu natsuwa a ranta, azmee ta iya kalami masu dadi masu sanyi da ratsa zuciya,

zama tayi ta dinga cusa fruits din dake agabanta cikin bakinta, cikin dadi take shan su, 

     bayan ta gama dasu ta ajiye plate din ta dauko na meatballs din ta shiga dauka tana jefawa a baki, kunnanta har motsi yake, yayi dadi sosai, yaji kayan kamshi,  lokaci zuwa lokaci ta kan hada da cool milk din dake acikin cup, tana kurba 😋

Kwance suke rungume da juna, daga su sai dan towel a waist dinsu, da alama daga bathroom suka fito duba da ruwan dake a jikinsu,

“Ayaan ba karamin dadi naji ba wlh’ 

“game da me kenan ? Jahan ya tambaya yana kara shafa sumar kan ayaaan,

  “game da zuwan babban yaya, i felt so happy da junaid ya sanar damu cewa ba date ba time na zuwansu,’ 

    murmushin takaici Jahan ya saki tare da cewa “hmmm da alama bakasan wannan mutumin ba, ni nayi imanin cewa daker babban yaya zai wuce gobe baizo nigeria ba !!!! Ina ji araina !

    dan dagowa Ayaan yayi daga jikin jahan yakasance yana kallon face dinsa, cikin kwarkwasa yace “pls stop thinking about that, kawai musa wa ran mu cewa ba nan kusa zai dawo ba, hakan zai bamu courage din ci gaba da jin dadin junan mu,,” 

      murmushi Jahan ya saki yana kallon cikin kwayar idon Ayaan wadda takasance ash colour ce, mai ruwan toka, mai kyan gaske , shima kallonsa yake yi cikin tsananin sha’awar junansu, zuciyoyinsu na kara azalzalansu akan su kara second round, hannu jahan yasa ya janyo ayaan bakinsu ya hade dana juna ya zura harshensa acikin nasa, nan suka shiga misayar saliva a tsakaninsu, 

………………….AUNTY BABBA…………………

zaune take agefen amani sbd dama basu tafi ba, suna jiran zuwansu babban yaya, duk da ita amani acikin garin take , amma abbas ya bata iznin ta zauna ta kwana tunda auntyn ta na nan itama , Inyaso zuwa gobe sai ta dawo gida,

Dukansu suna sanye cikin sleeping dress, riga da wando, masu kyan gaske, kowa ta zubo gashin kanta dayake Allah yabasu,

  “Ina sauraronki aunty na” amani tayi mgnr tana kallon auntyn tata dake gefenta saman gado,

“Shiri na musamman ya kamata muyi wa lamarin domin cin nasara akan wadannan zafafan guda biyu, shawo kansu ba abu mai wuya bane, dole sai an hada da shahararrun bokaye, kamar wannan bokon na kurmin dajin nan dake a enugu, ” 

   Xaro ido Amani tayi tare dacewa “Aunty enugu fa kikace ? gsky da kamar wuya wlh,’ 

   Dariya aunty babba tayi tare da cewa “a wurinki ba, ae ni akan na cimma buri na wlh ba abunda bazan iya yi ba, hmmm ke dai kawai abar kaza cikin gashin ta har ynx bakisan wacece yayarki Laila ba, ‘ 

      zugun Amani tayi tana kallonta hankali a tashe, lamarin ya fara bata tsoro “yanzu aunty yaushe zaki enugun? 

   Cike da kwarin guiwa aunty babba tace “Ni bana aiki cikin gaggawa,  a sannu zamu cimma nasara, amma kafin nan muna Bukatar kudade dayawa, don tunkarar wannan bokan ba abu bane mai sauki, dole mu hada karfi da karfe ki tatsar mana wurin abbas nima na tatso wurin Ishaq, daga bisa ni mayi mgnr zuwa can,’ 

    shiru amani tayi ita dai haryanzu akwai karaya atare da ita, cike da kasala tace ” aunty nifa ina tsoro wlh,” 

    Mtswww aunty babba taja tsoki “ke dallah wane tsoro, aje wannan ma gefe, ke bakisan abunda nake hango mana ba, muddin muka ci nasara akan Babban yayansu da marshal omar to ina mai tabbatar maki da cewa gabadaya zamu rinka juya kowa na family dinnan, sai yadda muka so za’ayi” 

    ta idasa magabar tana kallon Amani, wadda tayi tsuru tsuru, 

   ajiyar zuciyata tasaki har zatayi magana wayarta dake saman saman pillow ta soma ringing, da sauri takai hannu ta duba sunan “Babyna” ya bayyana 

  Aunty babba tace “halan Abbas ne ? Amani tace “eh shine,’ 

   “Yawwa maza ki daga, ki rinka kashe masa murya kina masa ladabi ko mun ci nasara akan kudin da muke bukata,’ 

     amani ta amsa da to, tare da picking call din ta kara a kunne tare fadin ” baby na y kke? nayi kewarka sosae,” 

    Saurara wa tayi tana sauraran muryar abbas dake cewa “nagaza bacci ne, na fito daga wanka ne, naji ba abunda nake son ji face muryarki,” 

Murmushi Amani tasaki tana kallon aunty babba data kura mata ido, cikin sanyin murya tace “nima haka babyna, ynx haka maganarka nake ma,’ 

     “Are u serious ? Zamu yi video call ne inaso naganki cikin sleeping dress din nan naki, ‘ 

    Kallon aunty babba tayi taji me zatace saboda wayar a handsfree take, da ido tayi mata alamar tace masa eh, 

            “Eh babyna a shirye nake , nima a kagare nake dana ganga, ” 

     Murmushi aunty babba, tayi tare da mike wa ta fita daga dakin tana ji  aranta cewa burinta zai cika,

Dare yayi sosai Junaid na dakin abbansu , ya addabe shi ya hana shi sakat, shi ala dole ga auta, suna kwance atare saman king size bed dinsa, junaid ya aza masa kafarsa a saman jikin abbannasu, zallar rigima yake ji,

    “Junaid dan Allah ka barni na huta, ka tafi bedroom dinka ka kwanta mana, ko kaje Wurin yayyen ka kwana mana,” abban nasu ne yayi maganar cikin jin bacci,’  

       cikin shagawaba yace “nafi jin dadin kwanciya ajikin ka abba,  In kuma kana so nadaina zuwa kwana nan, tam ka je ka dawo da mommyn mu, ” 

   rai a dan bace abban nasu yace ” kada na sake ji ka kira min sunanta Allah,” 

    Cikin zolaya junaid yace “kaifa kace kana so Abba, ba wanda yayi maka dole, saboda dadin soyayya ko su Ammi basu sani ba kaje har us ka aurota, wato kaga kyakkyawa, doguwa fara mai dogon gashi ko ? 

  Yunkura wa abban yayi tare da fadin “bismillah” ya janyo pillow, ya shiga bugun junaid dashi, dama sun saba ya maida shi tamkar tsaransa, kuma Abban ba karamin dadin hakan yake ji ba, cikin kukan wasa junaid kecewa ” Abba dan Allah kadaina ae gsky na fada, wlh momyn mu akwai kyau, shi ya rudaka ma, 

    Cikin mamaki abban yace “wai junaid ko dan muna kwana shimfida dayane yasa ka raina ni? 

    dariya suke gaba dayansu, duk yadda yaso junaid ya rufe bakinsa ya daina masa maganar Alexandra (Alekzandra)  amma yakiya, dakyar bacci ya kwashe su, su duka,


Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Insha Allah za’a samu Lunch ko dinner, in Allah ya yarda amma ✨

*💋💋SURGEON GENERAL RAFAYET & MARSHAL OMAR💋💋*

Back to top button