Hausa novels

Gargadar So Chapter 15 By M Shakur

Tunda tai wanka tadawo daki tai salla batabar kan dadduma ba haka bacci yayi awon gaba da ita.**Around 4 cikin bacci ta shiga juyi agado tanadan kankame filon dake gadon saikuma chan afirgice ta tashi zaune cikin muryan da baya fita da kyau sabida bacci tace “hasbunallahu wa ni’imal wakeel” wayanta ta shiga tattaba gadon tana nema chan ta juyoshi da sauri ta dauka ta kunna flash dakin yayi haske ta ijiye wayan akan gadon sannan takama cikinta tarike tana kankame idanu, kusan 3minutes tayi ahaka sannan ta dago filo ta dauka ta daura kan cikinta tarike saikuma ta kwanta da kyar tana kallon silin dakin chan kuma saita mirgina tahau kan filon tana kulle idanunta tana sauke ijiyan zuciya saikuma takara tashi zaune da rarrafe ta sauka daga kan gadon ta duka tana kife kanta akan gado chan tasake tashi tana layi tashiga tafiya atsakar dakin kafin tasake dawowa tahau gadon ta kwanta akan filo ta mika hannunta tadauki wayanta kiran Samsung S20 Ultra tabude number datai saving da best ta shiga kira wayan na gab da katsewa aka daga cikin muryan bacci Ni’ima tace “Best” ahankali cikin muryan da baya fita sosai Hawwa tace “Best na shiga uku, yauma yadawomin abin ke kadaine?” Da sauri Ni’ima ta kalli Aliyu dake bacci a gefenta saita tashi da sauri tawuce tafita daga dakin tana maida kofa tarufe tawuce falo ta zauna batare data kunna wuta ba tace “gani nan nashigo falo, don’t worry Baban Yaseer na bacci, Best this week alone this is the 2nd time da sha’awa ke tadaki daga bacci, ina maganin dana baki”? Kaman zatai kuka tai wahalallen tsuki tace “na shanye” ahankali har wani fiffizgewa jikin Hawwa keyi tsigan jikinta na tashi tace “mezanyi yadena Best? Cikina har ciwo yakemin” dasauri Ni’ima tace “sannu kinji Best shan kanwa is not good for mata dasu lemon tsami, just ki daure kije ki watsa ruwa mai sanyi sosai zaki warware kinji, Allah yakawo miki miji duk ki huta da wahalan nan, jeki watsa ruwan sanyi” ahankali Hawwa tace “okay” ta katse wayan, zare wayan Ni’ima tayi daga kunne daidai nan ana kunna wutan falon da sauri tajuyo hada idanu tayi da Aliyu dagashi sai gajeren wando yana kallonta cikin idanu da dan damuwa kan fuskanshi yace “what is wrong with Hawwa?” Dan kallon mijin nata Ni’ima tayi saikuma ta tashi daga kan kujeran ahankali ta taho wajen dayake da dan sanyin jiki tace “just girls problem ne Husby sorry na tadaka daga bacci muje mu kwanta” tai maganan zata wuceshi ta shiga bedroom nasu taji ya damki hannun bata ankara ba taji ya fizgota da karfi zuwa gabanshi har saida wayanta yafadi akasa ya daka mata tsawan gaske kaman ba Baban Yaseer ba yace “tell me meke damun Hawwa?” Ayanda Ni’ima ta firgita batasan sanda bakinta yace “sha……..sh….sha’awa ne Husby, Uhmm daman ina bata magani so yakare shine yau take wahala” dan lumshe idanu Baban Yaseer yayi yadan sauke ijiyan zuciya, adan rude Ni’ima tace “what’s wrong Baby ko bakada lafiya ne?” Takai hannunta zata taba wuyanshi hannunta yakama batare daya bari ta tabashi ba kawai ya jata ciki zuwa gado rikice mata yayi saida aka fara kiran salla ya barta ya sauka yawuce bayi tabishi da kallo kaman akwai abinda ke damun Aliyu har yau takasa ganewa, tashi tayi tana kallon wayanta dayake kasa chan sai gashi yafito wayan nata ya kalla dake kasa karasawa wajen yayi yaduka yasa hannu yadauki wayan yaduba ganin wayan is fine yasa yamike yataho wajen gadon datake tsaye yamika mata wayan tareda mata murmushi yace “tashi kije kiyi wanka kiyi salla, anjima sai muje mu gaidata ko tareda su Yaseer”? Gyadamai kai tayi asanyayye tasa hannu ta karba wayan, hannunshi yakai yashafa kumatunta ahankali yace “Ni’ima”kallonshi tayi asanyaye daukanta yayi yay gaban bayi da ita ya sauketa yace “go and shower” shikuma yajuya ya shirya yasa jallabiya yafice.Hawwa na fitowa daga bayi taci karo dawata wata mata da tadan manyanta rike da buta a hannu ga asuwaki a bakinta tsaye dab da bayin tana mata wani kalan kallo dasauri Hawwa ta dauke kanta cikeda dan kunya dajin nauyi danta daura towel akanta tace “ina kwana Umma” mugun kallo Umma ta watsamata ta juya ta tofar da ruwan asuwakin bakinta a wajen tace “anje anyi abinda aka sabayi tohh Allah kyauta tir da wannan hali” dudda Hawwa tajita bata bata amsaba tawuce dakinta ta shiga da basket din sabulunta da soso dakin ta ijiye taje gaban mirror taja dan stool ta zauna tana kallon kanta dake daure da dankwali da duk ya jike zare dankwalin tayi ta ijiye gashin kanta ya zubo sannan tadauki abubuwan face nata tafara shafawa kafin ta shafa cream ajikinta ta feffesa turare sannan tawuce tabude sip tadauki wani simple gown tasaka lokacin an fara kiraye kirayen salla, shanya zanin da towel data cire tayi a kofa sannan tasa hijabi tahau kan dadduma.Tana kan dadduman nan har gari yawaye sannan ta tashi tazauna tana duba hannunta da har yasoma warkewa tai shiru she’s just happy yau bazata aiki ba DIG yabasu off taga message din a group dinsu na watsapp, kwanciya tayi agadon tadauki wayanta ta danna tana kallon hoton dake jikin screen dinta da wata yarinya ce dake kama da ita ahankali tace “I miss you Mims” tashi tayi tafara gyara dakinta da babu datti tafito da sharan waje sannan tafara share tsakar gidan lekowa daga kitchen Umma tayi ganin itane yasa taja tsaki takoma cikin kitchen din abinta.Tana cikin sharan Baba yashigo gidan da sallama using crutches dinshi dukawa tayi gabanshi tace “ina kwana Baba” binta yayi da kallo kaman mai nazarin wani abu sai chan yace “kin tashi lafiya, yau babu aikin naki ne”? Kanta na kasa tace “ance muhuta yau sabida operation damukayi” shiru yasakeyi kawai kallonta yake chan yace “muga hannun” ahankali ta dago kanta for the first time ta kalleshi da dan masifa Baba yace “kina kallona Baban Yaseer ya sanar dani kinji ciwo a hannu wajen aiki, tashi ki nunamin in gani” ahankali ta mike tsaye daidai lokacin Umma na lekowa daga cikin kitchen tahaderai, dan jan hannun dogon riganta tayi tanunamai ciwon wanda yake small cut, matse crutches nasa Baba yayi a hammata yakai hannunshi ahankali yakamata hannunta dan boyayyen ijiyan zuciya Hawwa ta sauke rabon da Baba yarike hannunta tun tana secondary school, kallon fuskanshi take, cikeda so dan damuwa Baba yace “bakince ke a office ko a mota kike aiki ba meyakai har kikaji ciwo haka iyye? Idan wani abu yasameki fa iyye Hawwa”? Baba yayi maganan yana dago kanshi yana kallon fuskanta, maida kanta kasa tayi batai magana ba, ahankali yasa hannunshi yadawo da hannun riganta yarufe yace “ai shikenan, Allah baki lafiya, zansaka Auwallu ya karbo mini maganan hausa saiki shafa awajen kinji ko”? Ahankali tace “to Baba nagode” sakin hannunta yayi yace “gama sharan kizo falo muyi kari tare” ahankali tace “toh” yawuce ciki itakuma Umma takoma kitchen rai abace ahankali ta duka ta cigaba da sharan shikuma Baba yashiga katon falonsu ya daga labule ya daura a kofa ya zauna yana kallo Hawwan dake shara yanason diyarsa wani zubin haushi da bakincikinta ke mamayemai zuciya yayita zuba masifa, hango Umma tafito daga kitchen rikeda flask, Hawwa tace “ina kwana” ko kallon inda take batayiba tawuce ta tazo ta shiga daki ta ijiye abubuwan data dauko tasake ficewa takwaso sauran abubuwa tadawo ta ijiye komi ta shiga budewa zata zubamai ya juyo ya kalleta yace “zuba dana Hawwa” dagokai tayi ta kalleshi rai abace tace “kadaisan bana abincina da yarka ko? Bakuma yau yarka tasaba ciyar da kanta ba” hade giran sama da kasa Baba yayi yace “yo da bata kawo kayan abincin ba da a ina zaki sami wanda zakici eh mara kunya” kallon Baba tayi baki sake saichan tace “wannan kuma tsakaninku har gobe ni kaine ke ciyar dani ba wata ba dan kai nake aure kuma kaike bani kayan bacci, banda haka naga ai nima nawa yaran na kawomin kayan abinci” dan dariya kadan yayi yace “Zainabu kenan yau banso nafara rigima dake dan nasan ba cikakken mutunci gareki ba, to meya hanaki cin abincin yaran naki? Bari kiji idan ni nayi fushi da diyata wannan ni mahaifinta ne, bakida ikon fushi da ita, ke har kinada bakin magana dabadan Hawwa ba da tayaya zamu aurar da yammatanki hudu mu musu kayan daki ni da bani aikin komi, wayasa Aminu a university? Wayakai Maryama boarding yake biyan kudin makarantan ta?” Magana Umma zatayi ya nunata da hannu yace “kul, karki batamin rai da safen nan zubamata kari nace” hadiye abu Umma tayi daya tsayamata a wuya tashiga zubawa Baba yajuya ganin tagama shara tana wanke hannu yasa yace “zo kiyi karin kumallo Hawwa” Gyadama Baba kai tayi ta wanke hannu ta taho ta shigo dakin Umma ta tashi ta shige ciki ko ajikin Baba yace “yi kari maza” dumamen tuwo ne da shayi dayaji kayan kamshi hannu tasa tafara ci Baba yace “yaushe ne ziyaran Maryama a school”? Ahankali tace “nan da kwana bakwai ne Baba next week” ahankali yace “Toh Allah kaimu” saikuma yayi shiru yakai kofi baki ya kurbi shayi chan ya kalleta yace “Hawwa inaso nai magana dake!”Dan rage murya Baba yayi dudda haka babu wanda zai shigo gidan bazaijisa ba yace “Hawwa baki tunanin aikin nan naki nasa maza na tsoron tunkaran ki? Kin taba zama kinyi tunanin ko dalilin haka yasa suke guduwa? Ta iya yuwa kuma iyayensu na nuna bazasu dansu ya auro musu yar sanda ba iyye? Hawwa!” Baba yadan rage murya yasake kiranta kaman zaiyi kuka yace “gashi baki murmushi kullum fuskan nan taki ahade kaman kinga yan ta’adda” Baba yadan sauke ijiyan zuciya yace “nasan aikin nan ke ciyar damu, sune kudin makarantan Aminu da Maryam, amman ni wlh banki naji yunwa inhar hakan zaisa kisami mijiba, nagaji da zuba miki ido” yayi shiru yace “maganan danakeso nayi dake itace nama Malam Sama’ila magana ya sanar a masallaci ina nemamiki miji tun satın daya gabata, ya sanar ina nema miki miji” ahankali Hawwa tadago kai takalli Baba zuciyanta yamata badadi sosai Baba yace “dazu da asuba yasanar dani zai kawo wani anjima, kowaye yafito yace yana sonki zan bada ke banson ki kara wata biyu agidan nan, banso ki cikashe talatin agidan nan Hawwa, naga alamu idan nacigaba da linke hannu ina kallonki Maryama dake shakara sha hudu zatazo tagama sakandire tasami miji tai aure ke baki auren ba, lamarinki naga alamu saina shiga ciki nai dumudumu sannan zakisan da gaske nake kinajina ko”? Kasa magana Hawwa tayi sabida ji datayi tuwon dake bakinta ya makale mata a wuya, Baba yacigaba. “Idan akai nasara Malam Sama’ila wanda ya samo yanada dan abinyi ko cikin dalibansane zan badake” dasauri Hawwa takalli Baba tace “amman kisani saikinbar aikin nan gaskiya zakibar aikin” dasauri Hawwa ta kalli Baba, Baba shima kallonta yake yace “kwarai, me ake da aiki? Aure shine rabin addinin diya mace, aure bautan Allah, aure ibada ne kuma sunna ne, dan Allah idan mijin kwarai yafito yanuna baison aiki zaki barsa duk shirme ne aiki da yawon banza, inada yan gonaye saina saida mu dinga cin abinci, Hawwa idan bakibar aikin nan ba bazaki auru ba kowa zaita guduwa kinajina ko”? Sauke kanta Hawwa tayi kasa batare datai magana ba, daidai nan wani yaro yabugo sallama yana shigowa tsakar gidan yace “wai Malam Sama’ila yace nayi sallama da mai gidan” annuri ne ya fadada a fuskan Baba yashiga kokarin tashi yana daukan crutches dinsa yace “Ya Allah, Ya Allah kasa Malam ya samawa Hawwa na miji zanyi azumi tasami miji” da sauri yafita Hawwa tabi Baba da kallo kafin ta sa hannu ta dauki cup da ruwa ke ciki zata sha ko abin wuyanta zai sauka takai baki Umma tafito ranta abace tasami waje tazauna tace “ai alhakina bazai taba bari kisami miji ba duk wahalan banza mahaifinki yake” ijiye cup din Hawwa tayi ta kalli Umma still abincin na wuyanta, Umma tai murmushi tace “ni da mahaifinku tun muna yara aka mana alkawarin aure, muntaso tiryan tiryan munason juna rana daya ya hadu da mahaifiyarki marigayiyi ta kwacemin shi yajuya yace sam bayasona mahaifiyarki tasa saida aka sami matsala adanginmu, kuka ne, roko ne babu wanda banmai ba amman yace baya sona haka ya auri uwarki nakasa wani auren, sai bayan shekaru goma da sukai hatsari ta mutu shi kafafunshi suka koma haka sannan yazo ya aureni yadauramin wahalanki akai lokacin kina yar shekara shidda, tamoreshi ni na sameshi a gurgu ai bazaki taba ganin daidai ba” dan murmushi kadan Hawwa tayi kaman bazatace komiba saikuma tasa hannu tadauki cup tasha ruwan tass ta ijiye ta kalli Umma tace “Umma kenan ai ko azaban dakika azabtar dani yabiya koma wani kalan laifi Mamana tamiki, kibar tunanin dakikeyi, lokaci kawai baiyi bane, duk sanda lokaci yayi zanyi aure Umma, bakece dalilin ba” tayi maganan tana mikewa Umma tace “sai ayi mugani, mara kunya kwantai kawai”.

Back to top button