Uncategorized

Macijine Shi Page 11-12 Hausa Novel

Na mammy kabeer

(Anty mammy)

Elegant online writers📚📚

Free book 

Page 11/12

Ta ƙabbalallahu Minna waninkum.

Slm, Æ´an uwa masoyan littafin MACIJINE, ina  miÆ™o gaisuwa tare da Barka da Sallah ,Allah ya maimaita mana,yasa munyi karÉ“aÉ“É“iyar

Ibada.

________________Kai tsaye su baffa suka nufi gurin lamiÉ—o,hannunsa riÆ™e da na fattu ,wacce ke tafiya ahankali cikin azabar raÉ—aÉ—in  da hannunta keyi,dakuma ciwon jiki.yayinda su arÉ—o ke mara musu baya burinsu kawai suga wane irin hukunci lamiÉ—o zai É—auka akansu fattu ,cikin zuciyarsa arÉ—o yake fatan inama lamiÉ—o ya kori su fattu daga rugar ,inyaso su bisu hanya  suyiwa fattun fyaÉ—e,dan su kashe Æ™ishirwarta dake cin ransu.

Shikuwa mai gari tun daga nesa ya hango su fattu,gaba ɗaya nutsuwarsa ta bar jikinsa,ƙureta yayi da ido guri!!yana haɗiyar yawu da lasar leɓe kamar tsohon maye.

Kallonta yake yana ji kamar yaje ya kamota yayi É—aka da ita.

haba malam ,yarinya bul-bul  da ita kamar nunannen tumatur,lallai yau zai sha shagali.lamiÉ—o ya faÉ—a cikin ransa yana mai kallon fattun.

Baffa kuwa suna ƙarasowa gaban mai gari ya nemi guri ya zauna tare da zaunar da fattu kusa dashi,wacce gaba ɗaya arikice take ,tsorone ƙarara shinfiɗe akan fuskarta.tayi luƙus ajikin baffanta jikinta sai rawa yake, ta kasa ɗaga kanta ta kalli kowa ,sai hawaye take sharewa.

Kowa yanemi guri ya zauna ,masu tsayuwa suka tsaya , da Æ™yar lamiÉ—o ya iya saita kansa ya aro nutsuwa ya  yaÉ“a  akansa, tare da É“ata ransa ya kalli  baffa yace “malam bukar kana sane da irin abinda Æ´arka take aikatawa awannan garin ?lamiÉ—o ya faÉ—a cikin kakkausar murya .

Ahankali baffa ya gyara zama kafin yace ,naji anata  wai wai  agari cewar Æ´ata tayiwa su jauro turen maciji ,amma sam ban yarda da wannan magana ba,dan kuwa Æ´ata ba mai kashe mutane bace ,sannan ba mayya bace kamar yadda ake faÉ—a”baffa ya faÉ—a cikin É—aure fuska .

 Cike da É“aci rai lamiÉ—o ya fara magana.

“To wllh malam bukar bazan É—auki wannan abun agarina ba,yanzu ace abun nata ya wuce kan kowa sai kan É—ana  ?sannan kuma kace wai baka 

yarda da zancen ba ?kana nufin nayi maka Æ™arya ne?to bari kaji dole ne saina É—auki mataki mai Æ™arfi akanka da Æ´ar taka ,dan ka nuna rashin É—a’a a gaban fada.bayan kuma kowa yaga abinda Æ´arka tayiwa yaranmu,

Dan haka  bazan yanke hukunci yanzuba sai zuwa gobe ,idan yaranmu  sun sami lafiya,dan haka yanzu za’a shiga da ita cikin gida anan zata zauna cikin wancan bukkar da ake ajiye masu laifi .

Dan haka kowa ya watse sai zuwa gobe da la’asar adawo nan dan jin hukuncin da zan yanke”mai gari yana gama faÉ—in haka ya jingina da jikin kujerar da yake zaune akai. 

gaba É—ayan mutanen dake  gurin sunyi na’am da wannan hukuncin nacewar fattu   ta zauna a gidan mai gari ,dan karta gudu.

Kuka sosai fattu ta sanya tana riÆ™e hannun baffa “wayyo Allah na baffa ka taimakeni,dan Allah karka bari akulleni adakin hukunci ,wllh bani nayi musu haka ba ,kuma sunzone da nufin keta min haddi baffa ka kalli Yadda ya famamin targaÉ—e na  wllh ba laifi na bane” fattu ta faÉ—a cikin matsanancin kuka kamar zata shiÉ—e.

 

Cikin tashin hankali baffa ya riÆ™e hannun Fattu ,ji yake kamar ya fasa ihu,aduniya ba abinda ya tsana irin  yaga Fattu cikin damuwa,”kiyi haÆ™uri fattu ba abinda zai sameki,in Sha Allahu Allah zai saka mana dan wannan mugunta ce ake son yi mana ,kuma Allah yana bayan mai gaskiya”yana gama faÉ—in haka ya juya gurin mai gari yace “lamiÉ—o ina neman alfarmar abarmin fattu mu tafi gida ,zamu dawo da ita zuwa goben,dan bata da lafiya kuma barinta ita kaÉ—ai akwai matsala” ya faÉ—a cikin damuwa da alhinin wannan rashin adalci da ake Æ™oÆ™arin aiwatar musu.

Cike da mugunta lamiÉ—o yace “kai bukar ina ganin girmanka karkasa in daina gani ka iya bakinka a faÉ—a kake,kasan idan na riga yanke hukunci ba mai ja dani ,dan haka ka tashi ka bani guri tun kafin raina ya gama É“aci kuma yanzu zansa aje anemomin macijin duk inda ya shiga daga nan zuwa safiya ,”lamiÉ—o ya faÉ—a  yana mai kiran wasu matasa yace su shigar da fattu cikin bukkar.

Kuka fattu keyi tana faÉ—in”wayyo baffana wayyo Allah ka taimakamin zasu tafi dani wayyo Baffa na karka bari su nemo shi zasu kasheshi. “amma haka suka tura  Æ™eyarta suka tafi da ita É—akin hukunci.baffa yana ji yana gani ,hawayene masu zafi suka silalo daga idon bawan Allah ,zuciyarsa kamar ta faso Æ™irjinsa yakeji, ashe ma Æ™oÆ™arin keta masa haddin Æ´a akayi?amma saboda rashin imani  da adalci aka É—ora mata sharri,ba komai Allah zai saka musu.

Juyawa yayi ya nufi gida ransa amatukar jagule,yanzu idan wani abun ya sami yarinyar fa?idan wasu suka Æ™ara yunÆ™urin cutar da rayuwarta fa?”ya Allah ka karemin yarinyar nan Allah ka duba matsalolin dake kanta da wanda suke shirin samunta.ya Allah ka sauÆ™aÆ™a mata Æ™alubalen dake gabanta.haka  yayi ta mata addu’a harya Æ™arasa gida kwata kwata hankalinsa baya jikinsa.

Yana shiga gidan  gwogwgo hansai ta sanya dariya cike da mugunta harda riÆ™e ciki tana nuna baffa da hannu.”wllh malam Gara ka cire wannan yarinyar daga zuciyarka,  inba haka ba kana tsaye zaka yanke jiki ka faÉ—i ka mutu.ba ruwa  na bani da asara, ai wllh banso lamiÉ—o ya kyaleta wai har sai gobe ba,daya sani yasa anyanke mata kai yau -yau É—in nan ,da mun huta da nauyinta akanmu” ta faÉ—a tana turo wani baÆ™in É—an kwalinta mai shegen datti zuwa gaban goshinta.

Kallon ta kawai baffa keyi ,cikin zuciyarsa yake kissima iri saɓawa gwogwgo da zaiyi dan yau zai nuna mata matsayin fattu azuciyarsa ,sai dai yana yunƙurowa da nufin maida mata martani,kawai yaji bakinsa yayi nauyi,wani irin shayinta da tsoro ya mamaye zuciyarsa.kai kawai ya girgiza ya wuce ɗakinsa ,wato itama gidan mai garin taje kenan?ba komai akwai Allah.

Fattu kuwa tunda aka turata cikin É—akin nan banda kuka ba abinda takeyi, ita damuwarta ma yanzu bai wuce na rashin ganin macijinta ba,duk wannan abunda ke faruwa baizo ba.anya kuwa lafiya?kodai wani abu ya sameshi ne?

“Ya Allah ka kare wannan bawan naka ,ka bashi kariya daga sharrin mugayen mutane .

Shikuwa maciji adaidai wannan lokacin yana gidansu fattu yaje nemanta bai ganta ba yayi ta zagaye aÉ—akinta amma bata nan,tun lokacin datayi masa karatun nan daya fita yaje can jeji ya kwanta ,sam bayajin daÉ—in jikinsa sosai yake jin ciwo ta ko’ina ajikinsa,sai da lokaci yaja sannan ya nufi gidansu fattu ,ahankali yake tafiya cikin ciyawa da jikin katanga, harya Æ™arasa gidansu fattu.

Koda yaje yaga bata nan saiya yi ta zagaye É—akin yana nemanta ,amma bata nan. Kwanciya yayi akan É—aurin kayanta yayi lamo kamar ya mutu.saidai hawayene ke zuba cikin idanunsa .

Can kuwa gidan mai gari ,da misalin ƙarfe bakwai na dare sosai hadari ya haɗu agarin, dan haka kowa ya shige cikin gida dan gudun zubowar ruwan,da akowane lokaci yana iya sauƙa.

Daidai wannan lokacin kuma fattu na duÆ™unÆ™une cikin É—akin  hukunci sai kuka take zuciyarta tayi mata Æ™unci ga yunwa dake addabar ta rabo ta da abinci tun madarar da baffa ya bata da safe.hannunta sai zagi yake mata.

Ahankali taji ana turo kofar É—akin hukuncin,da alama shigowa za’ayi,ga duhu aÉ—akin.

Zabura tayi cikin sauri ta miÆ™e tsaye jikinta na karkarwa,kar dai ace su jaurone suka dawo ?wayyo  Allah na ” ta faÉ—a tana dafe Æ™irjinta ,zuciyarta kamar zata fito dan tsoro da firgici.

Cikin rawar murya tace “wa…w….ayee.”

Ahankali cikin murya mai kama da raÉ—a,yace “ke kwantar da hankalinki,nine nan lamiÉ—o”

Ya faÉ—a yana mai haska tocilan É—insa  .

Cikin zubar da hawaye tace “dan Allah lamiÉ—o ka fitar dani daga gurin nan ,wllh ban aikata komai ba,bani na kashe jauro ba”ta faÉ—a cikin kuka.

“Kinga ki nutsu jauro bai mutu ba yana raye ,kuma idan kika bani haÉ—in kai muka yi komai  cikin sirri ,to zan kyale ki ki tafi gida abinki”lamiÉ—o ya faÉ—a yana matsowa gareta.

Ja tayi da baya cikin sauri tace “me kake so nayi maka ?dan Allah ka gyaleni na tafi gida ,an fara ruwa”ta faÉ—a cikin kuka,dan ta gano manufarsa ,irin tasu jauro ce ,wato fyaÉ—e yake son yi mata.

Matsowa lamiÉ—o yayi tare da ruÆ™o hannunta yana mai cewa”Ayya fattu yarinya mai kyau da kyan jiki ki yarda dani mana duka -duka minti nawa ne ba dayawa zanyi ba kinji ki taimaka min”ya faÉ—a yana mai janyota jikinsa sosai .

“Wayyo Allah na baffa kazo ka taimakeni,dan Allah lamiÉ—o kayi haÆ™uri wllh ba kyau kaji tsoron Allah ka tausaya min na roÆ™eka”fattu ta faÉ—a cikin rawar jiki da matsanancin kuka,tana mai tureshi daga jikinta,banda warin tsufa ba abinda yake yi.

“Ke dan ubanki ki tsaya ko saina miki ta Æ™arfine?Shegiyar yarinya haka zamu zuba miki ido muna kallonki kin cika kinyi tunjum dake amma ba mai morarki,ki tsaya dan ubanki”lamiÉ—o ya faÉ—a yana mai É—auke fattu da wani gigitaccen mari Wanda saida ji da ganinta suka tsaya na wucin gadi.kusan minti biyu kafin kwakwalwar ta ta dawo aiki,kuka ta sake fashewa dashi mai tsananin gaske lokacin da lamiÉ—on ya Kaita Æ™asa yana Æ™oÆ™arin dage yar ficiciyar rigar dake jikinta ,wacce jiÆ™aƙƙiyar Æ™asar nan ta gama bushewa .

“Innalillahi wa inna ilaihir raji’un wayyo Allah na baffa wayyo mai taimako kana ina?kazo gareni,ina buÆ™atar taimako ka ahhhhhhhh “fattu ta kwalla wani irin Æ™ara mai Æ™arfi lokacin da lamiÉ—o yayi………

Tofa masu karatu me lamiÉ—o yayiwa fattu ne ?

Muje zuwa kuci gaba  da bin alÆ™alamin anty mammy.

Mrs babi 💘💘

Share and comment fisabilillah

More comment 

More typing.

Back to top button