Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 12 Book 1 Complete Hausa Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

………Sehrish………………

gaba ɗayansu sun hallara, kowannan su ya sami gurbi a dining chairs ɗin, azmee ce ke ta faman ɗawainiya yin saving ɗinsu, saboda sehrish na can cikin yanayi

_kowannan su ya hallara a saman dining chairs ɗin, kwansu da kwarkwatarsu,

Yau suna gida ba fita aiki, a bisa umarnin Babban yayansu, 

_Duk sunyi dress cikin Jallabiya, dama yana ɗaya daga cikin favourite dress ɗin su, basu cika son kaya masu nauyi ba_

_azmee ce ke saving ɗinsu, kowa tana zuba masa abunda yake so_

_duk sun natsu suna ci, hannu ayan yasa acikin aljihun jallabiyarsa ya zaro wayarsa dialing ɗinta ya shiga yi Jahan ya tura wa saƙo kamar haka_ 

_”ya maganar hotel room ɗin? Kayi mana booking?_

Jin ƙara shigowar message a wayarsa dake ajiye gefen plate ɗin abincinsa yasa shi duba ya karanta, ɗan murmushi yayi kafin ya bashi amsa da cewa  _”Eh yaushe zamu fara zuwa don a matse nake wlh_

Download>>> Yaro Ne Complete Document

duba wa Ayaan yayi ya basa reply shima,

_”ko yau ka ce am ready to do it, am so horny dear kamar nayi hauka_😖

duba wa jahan yayi wit smile on his face ya tura masa reply shima, _” u must be horny dear, 2 days ba testing ɗin *Ak47* dole Mu shiga yana yi_

Before Ayaan ya bashi amsa muryar fawan ta katse su da cewa 

*Ga Babban yaya nan kowa ya shiga taitayinsa*

Cikin sauri kowannan su ya mayar da wayarsa cikin aljihunsa, don ya hana ana cin abinci ana danna waya,

 Atare da junaid suke saukowa ɗga stairs ɗin, farar shirt ce ajkinsa ta ɗame sa, mai dogon hannu , daga ƙasa kuwa shorts ne launin ash, gaba ɗya surar jikinsa a bayyane take sboda duk yadda Sgr zai sa sutura sai halittun jikinsa sun fito muraran,ba abunda ke 6oyewa nadaga kyakkyawar surarsu, hakan ba ƙaramin tayar musu da hankali yake ba especially abbansu yayi fama dashi saboda bakin mutane tun da dai abu tubarkalla, Bai jin kunyar shiga ko wata iri ce da zata nuna tsiricinsa, bai sa suturar kirki sai in takama yafi son yasa sexy underwears sune best dres nasa, hada ƙarin hakan yasa ake kai masa farmaki,

tun da azmee ta ɗago so ɗaya batasake ɗagowa ta kalle sa, sbd tshn hankali, wannan kallonsa ma a wurin mace zai iya zama haramun,

Kujera ya ja ya zauna yana facing kowannansu, shima junaid ya zauna yana ta faman zabga murmushi, 

cikin sauri azmee takai hannu zata zari plate ta zuba masa abun sawa abaki , amma abun mamaki sai fawan ya riga ta kai hannu ya ɗau plate ɗin jiki na rawa, ya buɗe warmer ɗin dake ɗauke da farfesun naman shanu, yasa saving spoon ya shake masa plate ya ajiye masa a gabansa, sanna ya haɗa masa da kakkauran tea a gefe,

Ƙiris ya rage azmee ta fashe da dariya, wannan fadancin na fawan ya bata mamaki, 

Bin su ya ke da kallo ɗaya bayan ɗaya, bayan sun gaishe shi, kowannansu ya shiga taitayinsa, don sun sani sarai bayason hayani ko kɗan, hakan yasa suka rage ƙarar spoon ɗin da hannunsa daga wannan sautin kwas kwas da ya ke yi,

Hannun sa ya miƙa acinkin wani empty bowl, azmee tasanya masa ruwa ya wanke, kafin ya tsoma hanun acikin naman, tsoka ya ɗauke ya jefa a bakinsa, a hankali yake taunarta, yana ci yana binsu da kallo One by one,

Ƙasa ƙsa da murya irfan yayi shi dake kusa da jabir yce “wannan kallon da babban yaya yake yi, bana lpy bane, duk ƴan ciki na sun kaɗa , jabir ya ɗauki cup of tea ɗin dake front ɗinsa ya kare fuskarsa dashi kamr zaisha, sannan yace “kai kenan ma, wlh jiki na kamar na mai zazza6i don fargabansa,’

Khadeel dake sauraronsu ya ce”jikin wasu na ƙaiƙayi da alama,’ 

Sun gane me ya kenufi cikin sauri suka ja baki su kayi shiru, 

Kowa tsit kamar mutuwa ta gifta, sautin ƙarar cokulan da hannunsu twins yake yi ne (kwas kwas) ya cika masa kunne, ɗagowa yyi ya aza eye balls ɗinsa akansu, zo ka ga tashin hankali, bakomai ya haddasa hakan ba, face kermar da jikinsu ke yi, 

mirya na rawa ayaan ya ce “mun shiga uku, idon babban yaya akan mu jahan,’

“menene” ya tambaya a ɗan firgice suka ɗago suna  Kallansa, ya sake cewa “are u not feeling well ? ganin yadda jikinsu ya ke rawa,

Ido luhu luhu Jahan yace” Ba mu jin daɗi ne, ni da ayaan, “

ɗgowa yusif yyi yana kallansu, jin zasu ja masa bala’e, tun Kan big bro yace wani abu, yusif yayi hnzarin cewa “but why u didnt tel me about ur sick ? ya tambya yana kallansu, 

cikin sauri ayan yace “dama tun jiya da dare ne, 

“Atlease u should inform me abt ursick, ko ƙarfe nawa ne zan duba ku ae,? shiru su kayi shi dae Rafayet binsu da kallo kawai ya ke yi kafin ya dakatarsu da cewa “its ok, after we finish the breakfast, yusif makes sure that u check them well,’ 

  “.Insha Allah babban ya ya” zuru su kayi jin za’a duba su, Bayan sun san cewa lfyarsu lou, 

Mayar da idonsa yayi kan Junaid wanda ke ta faman murmushi, kamar zautacce, ada sun yi tuanin cewa yaron ta6in hankali gare sa, amma da aka bincika sa sai aka tabbatar da cewa haka Allah ya haliccesa wit smiling face,

ɗagowa junaid yayi suka haɗa ido da babban yayan, cikin sauri ya sunnar dakai yana ci gaba da murmushi, Shifa kallon dollar $ ya ke ma yayan nasu, shiyasa murnarsa ta ƙaru in ya kallesa $ kawai ya ke gani a fuskarsa, ya riga da ya kammala lissafin nawa zai amsa da nawa zai kashe wa sehrish ɗinsa 😥

……………..SEHRISH……………………

A 6angaren sehrish kuwa, zarce wa tayi da bacci, na ɗan mintina ta farka tana sauke ajiyar zuciya, sunan shi ne kawai zuciyarta ke ta faman ambato, idonta takai kan agogon bangon dake manne, ƙarfe 12:30am, ynx sun isa kammala breakfast ɗin, 

Download>>> Kwarata Complete Document

tashi tayi ta kimtsa, ta fita taga me ke wakana, basa nan ciki duk sun fita, wayam kuma azmee ta gyara ko’ina yayi fess, a kitchen ta same ta, tana wanke dishes ɗin da su kayi amdani dashi,

“Aunty azmee sannu da aiki,” da fara’a a face ɗinta tace “Yawwa Sehrish ina fata kin washe yanzu,” 

Murmushi sehrish tayi tare da cewa “eh Alhamdulillah da wani aiki da zanyi yanzu?. ta tambaya tana kallonta,

Azmee tace “a’a yau fa hutu ki ke hajiya sehrish, na ma kammala komai sai zuwa anjima zamu shirya dinner atare amma pls karki maimaita shiriritar ɗazun,”

Ƴar dariya sehrish tayi kafin tace”Insha Allah” ta ɗan yi shiru tana so ta zuba abinci, taci amma ƙunya take ji saboda 6arnar da tayi na zubawa farfesu abun wanki,” 

“Ke bakya jin yunwa ne wai? kullum sai na ce ki zuba abinci ki ci, ko saina fara sa miki bulala ne?

Azmee ce tayi maganar cikin zolaya, dariya sehrish tayi da cewa “dama ynx nake so na zuba ne,” 

ƙara sawa tayi ta ɗauko tray, 

Bin ta da kallo azmee tayi ganin ta jera pancakes, ga sandwich ta kuma haɗa da scrambled eggs, duk a ciki a haka bai ishe ta ba sai da ta hada da fried chicken, taje ta ajiye  ta kuma dawo ta haɗa cornflakes a cup ta zazzaga uwar madara, ta tsula sugar, 

   Zama tayi asaman dining chairs ɗin na kitchen tana kallonsu, tunani take da me zata fara, muryar azmee ce ta katse ta da cewa “Sunyi miki haka? Ko zaki ƙara da wani abu ne? 😒

  sunnar da kai sehrish tayi cikin jin kunya tace “sun isa haka,” Wato su sehrish banza ta samu, dama talaka bai iya samun wuri ba, ni bama wannan ba, Soyayyar babban yaya tasa ta manta da halin da su Hosana ke ciki, ada in zata sa abu mai daɗi a bakinta sai ta tuna dasu  tayi kuka  sosai, amma ynx ba wannan mgnr, *BABBAN YAYA* kawai 😥

      Sandwich ɗin tafara ɗauka tana ci, tunanin ta nakan *RAFAYET* azmee na lura da ita duk wani motsi da sehrish zatayi murmushi take yi, hankalin azmee bai kwanta da irin wannan zauce war da Sehrish tayi ba akan Babban yaya, tabbas soyayyace mai ƙarfin gaske take masa, tunkan tasa shi ma a idonta, da jin sunansa kawai ta faɗa tarko, balle ynx da tasa shi a ido? hakika jikin azmee yayi mugun sanyi tunawa da Junaid, bawan Allah wanda kullum burinsa ya ga yarinyar cikin farin ciki, 

Babu wanda yasan da zaryar da junaid ya ke yi izuwa ɗakin azmee, kullum roƙonta ya keyi akan dan Allah taba sehrish kulawa ta musamman, komai sehrish take buƙata, tagaya masa zaiyi mata, 

Junaid ba ƙaramin so ya ke mata ba,  😿

(Tabbas akwai tashin hankali, ni babban damuwa ta, waɗannan zuciyoyin guda biyu ❗‼⁉

Wane hali zuciyar sehrish zata shiga ita da ta kwallafa rai akan mutun da ya kasance misoganist ! ya ƙi jinin mata, baya sha’awarsu basa gabansa, balle ma maganar aure, shin wane hali zuciyar junaid zata shiga ❓shi da bashi da ƙoshin lafiya, ga soyayyar wadda bashi ke gabanta ba, yayansa take so ❗  wane hali hosanna da Jahad zasu shiga in suka amince da bukatar Inspector Eesha!? shin za’a yanke musu hukuncin kisa ne, ko zasuyi zaman gidan yari ne ⁉  😭😭😭

 Me zai faru idan su Aunty Babba Suka ziyarci Bokan nan na dajin enugu wato baba Iblis wanda muddin yayi asiri sai ya ci mutun jazamun, in ba wani iko na ubangiji ba 😿 dole fa ku gyara zama domin yanzu cakwakiyar ta soma 🔥🔥🔥

Download>>> Ana Dara Ga… Complete Document

“Idan kin kammala cin abinci, inaso mu zagaye gidan nan tare dake ki ƙara ganin haduwarsa sosai,” murmushi sehrish tayi wadda tuni cikinta ya fara birkice mata dakyar ta iya cewa “tom aunty azmee, amma sai na fara shiga toilet shaf shaf,’ 

Azmew tace “dama nasan wannan jazamin ne ae, zuba miki ido kawai nayi Allah, ni zan shiga ciki, in kin kammala ki same ni a bedroom ɗina, kyau ma mu fara sallar azhar naga time yayi,” 

Sehrish ta amsa da toh, cikin sauri ta kammala, sbd dama a ƙagare take ta zagaye gidan, ta gaji da zama wuri ɗaya, daga bedroom sai kitchen, shaf shaf ta wanke kayan da ta 6ata, sannan ta wuce ɗakinta toilet ta shiga, bayan ta fito da alwalarta tayi sallah, sai wurin addu’a ta tuno da su hosana, tayi musu addu’a sosai, kafin ta cire hijab ɗin ta tura a wardrobe, dama already dress ɗinta na maza ne ajikinta, gashin baki kawai ta aza, tagyara sumar kanta, ta naɗe ta cikin hularnan tashi da kwakwa, daga sama ta bi da mayafi ta yi kamar turban, ta saki jelar mayafin gefe, 

A tare da azmee su ka zagaya, sehrish tasha mamaki, ganin haɗuwar katafaren gidan, ko’ina take bi da kallo kamar wuyanta zai 6alle, muryar azmee ce ta katshe ta da cewa “kin ga nan, wurin motsa jiki ne wato gym, bi da kallo sehrish tayi an kawata abun wurin da komai na motsa jiki, kamar ta shiga ta jaraba itama haka taji, amma taci alwashin watarana sai ta shiga ciki tayi gym itama, 

gaba su kayi suka sake zuwa wani room ɗin, “nan kuma ɗakin bincike kenan ,” jinjina kai sehrish tayi ganin wasu matsiyatan Computers gava ɗaya na’urori ne a ɗakin ke sarrafa komai, wurare daban daban ta nuna mata Hada weapon’s room ( ɗakin ajiye makamai) , hada haɗaɗɗen parlor wanda suka ware domin yin kallo acikinsa, an ƙawata shi da faskekiyar plasma tv, ga speakers na sauti, ga ƙawatattun kujeru aciki da sauransu,

daga nan suka fita can harabar wajen, sehrish tasha kallo sai taga kamar tabar 9ja ne, saboda cikin gidan duniya ne, bakomai ya ƙara burgeta ba face swimming pool ɗin da tagani, mai faɗin gaske ruwan ciki yayi blue sky, daga gefe a hada kujerun shakatawa da table, bata ga komai ba sai da su ka shiga garden Aljannar duniya, juyawa tayi ta kalli azmee tare da cewa “har yanzu muna cikin nigeria”? dariya azmee tasaki tare da cewa “of course,” jin jina kai tayi wasu komai na cikinsa kore ne 🌲, sai aka ƙawata shi da Red & yellow flowers 🌹🌻, ga wani tsaftataccen ruwa dake guda na (waterfalls) yana gangarowa daga jikin dutsi zuwa ƙasa ya taru acikin pool yyi kamar lakes, Bakomai ya burge sehrish ba face agwagin dake ciki suna yawa farare, 

“Aunty azmee gaskiya gidannan ina kokwanto anya ba hotel bane, girmansa da haɗuwarsa yayi yawa,”  tayi maganar tana kara bin ko’ina da kallo, azmee tace “haryanzu fa akwai sauran wuraren da baki gani ba, ynx dai na gaji mu zauna mana,

Wuri suka samu asamn  garden chairs ɗin suka zauna auna facing juna, bin ta da kallo azmee tayi ganin tana ta faman murmushi, wato bakomai sehrish ke tunani ba fa ce ranar da zasu fara magana da baban yaya harsu shaku ssae su rinka zuwa garden ɗinnan atare suna kewaya wa, lumshe idonta tayi sbd wata iska da ta ratsa ta, aranta tana cewa “Ya Allah ka nunamin wannan ranar da raina da lafiya ta, ni da shi atare muna strolling Cikin farin ciki,” 😥

“Me ki ke tunani ne”? Firgit sehrish ta yi jin maganar azmee a dodon kunnanta , cikin sauri tace “bakomai kawai ina mamakin haɗuwar gidan nan kamar a mafarki,” 

  Murmushi azmee tayi sbd sarai ranta ya bata cewa, tunanin ta na babban yaya ne,’ 

    “Estate za’a mai dashi” cikin mamaki sehrish ta ce “dagaske aunty azmee? Amma zai fi kyau wlh girman yayi yawa,” 

Azmee ta ce “eh naji da jima wa abbansu ya faɗi cewa za’a ƙara wasu part ɗin, yana so zai ware ma kowannansu nasa saboda baison in sunyi aure suyi nesa dashi, yace duk wanda yayi aure zai dawo ciki da matarsa, duk da sun mallaki gidajensu nakansu, amma shi yafi son hakan,” 

Wani daɗi ne ya rufe sehrish, kamar anyi mata albishirin cewa itama zata kasance ɗaya daga cikin surukansa da zasu zauna agidan, 😒

 Bayan sun ɗanyi shiru na wani lokaci azmee tace “i have something to discuss wit u,’

   “Menene aunty azmee” sehrish ta tambaya da ɗan mamaki a fuskarta,

“Ko kinsan cewa a cikin sojojin gidan nan akwai wanda yasan cewa ke maca ce ba namiji ba !!”

A firgice sehrish ta mike hannu dafe da kirji tace “Who”? fuskarta da tsananin tsoro,

Dariya azmee tayi kafin tace ” zan faɗa miki but firstly ina so ki mun alƙawarin cewa u will calm urself,” 

Jiki a sanyaye ta koma ta zauna zuciyarta na bugu, tsoranta kar ace cikin jarababbun ne wato Fawan ko Twins,

      “Aunty azmee wanene dan Allah.. ..” tayi maganar tana haɗiye yawu,

Murmushi azmee tayi kafin tace “king of smile” 

“Wanene haka azmee”? Ta tamvaya da mamaki, 

“Oh baki gane ba tom nabaki satar amsa kije ki gano waya dace da sunan,’ 

duk iya tunanin sehrish bata gano wa azmee take nufi da *King of smile* ba, takasa samun natsuwa ta gano sa, sun jima suna fira bfr su koma ciki donyin sallar La’asar,

……….SEHRISH………………………

bayan ta kammala sallar la’asar, kimtsawa tayi kafin ta fito ta wuce kitchen tayi mamakin jin shiru alamun duk sun fita ne, tunanin ta ko’ina Babban yaya ya ke, ta lura baya fita sai dai azo a same shi in da ya ke, tun kafin azmee ta iso, sehrish ta fara ɗauko abubuwan da zasu yi amfani dashi, doya ta fara ferewa tasan suna yawan amfani da ita, tana aiki tana ɗan murmushi, sa6anin da tana aiki cikin damuwa saboda tunanin halin dasu Hosana da Jahad su ke ciki, zuwan big bro ya canzawa sehrish rayuwa gaba ɗaya, 

Download>>> Matar Hariji Complete Document

Sam bata ji shigowar azmee ba, sai dae muryarta taji “Sannu da ƙoƙari rishi hakan ya burgeni,” 

murmushi sehrish tasaki tare da cewa “Yawwa aunty azmee ina wurina,” 

“Lafiya lou ta faɗi tare da shige wa ciki domin fara gudanar da aiki, cikin lokaci ƙankani kitchen ɗin ya fara kamshin abinci, 

“Wani kalar abinci ki ka fi so”? Azmee ce ta jefa mata wannan tambayar yayin da ta ke zuba kayan ƙamshi acikin sauce ɗin da ɗaura, sehrish tace “farar shinkafa da jar miya ina son abincin nan sosai aduk lokacin da akayi mana shi a gida zumuɗi muke yi kamar hauka saboda muna jimawa bamu ci ba, shine abinci mafi daɗi a wurin mu,”  ta karasa maganar muryarta a sanyaye ba don komai ba sai don tuna wa da hosana, a lokacin da su ke tare da mahaifiyarsu duk in akayi musu tuwo tafi kowa mita ta rinƙa sababi tana cewa “oumma wai mu kullum tuwo kullum tuwo, da rana ayi tuwo, da daddare ma tuwo, in safe tayi ma ɗumamen tuwo, ni wlh nagaji zanje gidan makwabciya in ciyo shinkafa da jar miya hada ma wasilla zata samun, ” 

Hawaye ne suka soma koƙarin zubowa a fuskar sehrish tunawa da rayuwarsu ta baya, 

“Ni kuma nafison Tuwo arayuwata miyar ku6ewa da busasshen kifi wayyo daɗi in inaji kunne na har motsi ya keyi, musamman in ya kasance ɗumame ne,” 

Azmee sai zuba ta keyi sam bata lura da sehrish ba wadda, take matsalar kwalla, jin shesshekar kukanta yasa azmee saurin ƙarasowa inda take tana faɗin “subhanallahi sehrish meke faruwa ne ? Cikin sauri sehrish ta dai dai ta natsuwarta, 

Murya na rawa tace “ba komai aunty azmee, zafin albasar da nake yankawa ne, ya shiga ido na,’ 

     “Eyyah sannu barshi na ƙarasa kawai,” 

   “A’a aunty azmee aikin zaiyi miki yawa, zan idasa,’ 

    “Sehrish akwai ayyuka dayawa ba dole sai wannan ba, kibarmun yankar albasar ki kula da miyar dana ɗaura,” 

     “Shikenan aunty azmee amma kafin nan, ayimun uziri zan shiga toilet,” 

   “Shikenan ba damuwa kije kawai,”

Cikin sauri sehrish ta fice, saboda tana so tasamu space ta matse hawayen dake son zubo mata, tana shiga bedroom ɗinta, ta fashe da matsanancin kuka, a gefen gado tazauna tana matse hawaye,

   Cikin murya kuka tace “Ya’ Allah ka karemun ƴan uwana, aduk inda su ke, ka sauƙaƙawa rayuwarsa, Hosana da jahad kowane yanayi zan shiga na rayuwa duk mun  daɗinsa I will neva forget about you, i will keep praying for u till d rest of my life 😭

    haka ta dinga addu’o’i akansu, sai daga baya ta tuna da azmee wadda ta baro a kitchen tana aiki, cikin sauri ta shiga toilet, agaban wash basin ta tsaya, ta kunna fanfo ta wanke face ɗinta sannan ta fito,  

ƙarar shigowar motoci taji, a lkcn da take ƙoƙarin barin ɗakin, nata cikin sauri tadawo ta tsaya agaban window ɗin da tasaba leƙe, janyen labulen tayi ta zuge glass ɗin tana kallonsu, 

  Motocinsu ne a jere, bayan sunyi parking wani Soja black american gabjejan gaske, ya fito ta gaba tare da buɗe mashi mota, a hankali ya zuro kafarsa dake sanye cikin slippers ɗin *Gucci* sun hau ƙafarsa raɗau ba ƙaramin kyau su kayi masa ba, idasa fitowa ya yi zuba mishi ido sehrish tayi sam batasan time ɗin daya fita ba, ashe baya gidan,

    Sanye ya ke da V-neck shirt light green color, sai dogon wando Army trouser, surar nan fa tafito raɗau bai matuƙar jan hankali, sumar kansa mai tsayin nan tasha gyara na musamman ta zubo masa abaynsa ya ɗaureta, 

  Ba shi kaɗai bane tare da abbansu su ke, da Kanal yusif, 

   gaba ɗaya jikin Sehrish ya gama mutuwa, zuciyarta ta gama narkewa, tafiyarsa ma kawai abun kallo ce, ta majiya ƙarfi *Rafayet* tamkar Zaki ya ke, wanda ke mulkar namun dawa a ƙarƙashinsa, 

    Zuge glass ɗin window tayi, tare da cije le6enta, sam bata gajiya da kallonsa, cikin sauri ta fito ta wuce kitchen saboda tasamu damar ƙare masa kallo in sun shigo,’ 

    “Sannu da dawowa ya idon nake”? Azmee ce tayi mata wannan tambayar, 

    “Alhamdulillah ae sun dawo dai dai aunty azmee,” sai faman murmushi take tana ƴan kame-kame,

 Shigowa su kayi atare suna ɗan ta6a fira, anan main palor ɗin suka samu wuri suka zauna, abbansu na facing ɗinsu yayin da shi da Kanal yusif suke zaune a 3 seater, 

Murmushi abbansu ya ke ta faman saki ba don komai ba sai don jin daɗin zuwan Babban yayan, musamman yau da suka yawata atare, duk da kin sakin fuskarsa da kuma ƙarancin maganarsa, _muryarsa tsada gare ta, saboda daɗinta shiyasa wata’kil ya ke rowarta_ (nace ba, da zai faɗi farashinta dana ƙulkula nasiya😂)

Hannunsa na riƙe da wayarsa, yana daddanawa, bazan faɗi ƙirar wani company bace, sbd wata irin haɗaɗɗiyar waya ce, very expensive wadda takasance mallakinsa, kuma sunan sane ajikinta wato (SGR) ba mai iya controlling ɗinta sai shi duk bala’in mutun, saboda sometimes da Voice ɗinsa take amfani, daga ya faɗi abu zata nuno masa, 😔

Download>>> Ingarman Namiji Complete Document

gyaran murya abbansu ya yi tare da cewa “Ina magana,” a hankali ya ɗago da sexy blue eyes ɗinsa ya aza akan abban nasu tare da cewa “Am all ears,” 

     Abba yace “Ina so kayi mun promise ɗin cewa har ka bar nigeria, bazaka ta6a kowa ba kayi shiru da bakin ka salin alin ka tafi cikin salama dan Allah,’ 

    wani irin kallo babban yayan ya ke wa abban nasu jin abunda yace, hannu ya kai tare da ajiye phone ɗinsa saman table ɗin da ke front ɗinsa, ya jingina bayansa jikin royal sofa ɗin, tare da aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya, duk abban nasu na kallonsa burin sa ya ji amsar da zai basa, 

    murmushi kawai kanal yusif ya ke yi wanda ke ta faman danna wayarsa, amma kunnansa nakan maganar da suke yi, 

      ɗan ta6e small lips ɗinsa ya yi kafin yace “*IMPOSSIBLE*” atakaice,

    Sauke ajiyar zuciya abban yayi dama yasan amsar kenan,

    Cikin takaici yace “Oh sai kayi kenan”?

    “Eh” ya bashi amsa ba wasa, 

 Jinjina kansa yayi tare da cewa “ni narasa gane tsakanin kai da Momynka Alexandra waya fi wani taurin kai, kafiya da ji da izza,’ 

   da buɗen bakin babban yaya sai cewa ya yi “Ita,” 

    Fashewa da dariya yusif yayi, tare da sa wayarsa a saitin mouth ɗinsa yana karewa, saboda gudun kar babban yayan yakai masa naushi, 

    “Yi mai Isarka,” Babban yayan ya faɗi yana shafa damtsen hannunsa da right hand ɗinsa alamar zaiyi bugu,

    yusif yace “Ai ni na wuce bugu ko Abba,” ya faɗi yana kallon abban nasu wanda shima dariyar ya keyi,

   Da ƙarfin gaske babban yaya ya yunƙura zai kaiwa Yusif punch a face ɗinsa, jiki na rawa abbansu ya taso yayi saurin rikosa, duk da yasan wasa ya ke ba bugun nasa zaiyi na, yusif ihu yayi yana faɗin “Abba dont let him punch me,”  

Dole yusif ya tsorata, shifa Babban yaya a ƙa’ida ya naushi mutun a cheeks ɗinsa, sai haƙori ya fita 😳

  In kuwa yakai ma zazzafan naushi a saitin zuciyarka, sai dae uwar mutun ta haifi wani, bugu ɗaya sai lahira 😳😳😳

   Murmushi kawai sehrish ke saki domin komai ke faruwa a idonta, duk da akwai tazara sosai amma tana hangensu ta cikin kitchen ɗin, bakomai ya burgeta ba, fa ce yanayin yadda Sgr ya ƴunƙura ya dunkule hannu zai kaiwa yusif naushi, sumar kansa da ta yarfo ta gefen forehead ɗinsa ba kamin tafiya yayi da ita ba, 

“Bari na shirya miki abunsha ki kai musu,” muryar azmee ce ta katse ta daga kallon nasu, 

     ɗan zaro ido tayi jin ance zata kai masu abunsha, ga tsoran tunkararsa ga kwaɗayin son ganinsa da take yi, 

  A tray ta shirya mata cups masu ɗauke da coffee, ta miƙa mata jiki na kerma, sehrish tasa hannu ta kar6a, a hankali take tafiya zuciyarta cike da fargabarsa,

 Da sallama ta isa inda su ke, duk suka amsa, miƙa wa abbansu tafara yi, da fara’a fuskarsa yasa hannu ya ɗauki cup ɗin tare da cewa “Yawwa madallah sannu da ƙoƙari,” murmushi ɗanyi tare da juyawa wurinsu heart ɗinta na beating, tsoro yasa tafara miƙa wa yusif cikin sauri yusif yayi mata alama da hannunsa tafara miƙawa babban yayan, Saboda ba’ayi masa haka sam, wato afara mika wa nakasa dashi abu kafin a bashi, hakan laifi ne a wurinsa, 

  Ita kanta batasan tana da irin wannan natsuwar ba, sai da taje gabansa, ji ka ke tsit hatta zuciyarta sai da ta lafa da bugawa cikin sauri,  daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya gauraye hancinta, zuba mishi ido tayi tana kallonsa, 

     Idonsa nakan screen ɗin wayarsa, jin alamar mutun ƙiƙam akansa yasa shi ɗan dagowa, tray ɗin hannunta yaci karo dashi,

      cire hannu yayi yasa a hankali ya ɗauki cup ɗin, bin hannusa tayi da kallo, wasu irin zira-ziran yatsun hannu, dogaye farare ƙal, ga fatar nan sai ɗaukar idon tsiya, mutun kamar ya lashe, agogon hannunsa tabi da kallo tazauna masa raɗau sai kyalli take,

      Mayar da idonta tayi akan sumar kansa mai ɗan bala,in kyau sam sehrish tagaza matsawa daga tsayen da take akansa, batasan bayason Kallo ba, a hankali yake kur6arsa a mouth ɗinsa, 

    Abun ya daurewa abbansu da kanal yusif kai, ganin yadda mai aikin nasu Ya tsayawa Babban yayan akai kamar sai lashe sa, duk da sun cewa shi abun kallo ne, dole akallesa, 

     “Miƙo mun mana,’ kanal yusif ne yayi maganar don yayi saurin dakatar da mai aikin nasu daga kallon ƙurullan dayake wa Babban yayan nasu, kafin ya fusata, 

    Lokacin da mgnr kanal yusif ta dira a ears ɗinta, jiki na rawa tadawo hayyacin ta, tare da matsawa ta miƙa masa shima ya ɗauka sannan jiki a matse ta koma kitchen, har ta shiga cikin ƙamshin turarensa ne ke ɗawainiya da ita, 

    Sam tarasa sukuni, sai faman sauke ajiyar zuciya ta ke, kamar wadda tasha gudu, 

   Muryar azmee ce ta katseta da cewa “tun da mun kammala, mu bari sai after magrib ayi arranging ɗinsu a dining,” 

      Sehrish ta amsa da “Toh aunty azmee,” 

       tana ganin lokacin da suka kammala firar tasu, su ka kuma fita atare,  

……..*Junaid*…………………….

Da tunanin sehrish ya yini, kasancewar ya fita gidan wani friend ɗinsa daya jima shima bai lpy, yaje duba sa, a can ya yini yana ta jansa da fira, hakan yasa ya jima, bashi ya dawo gida ba sai wuraren magrib ya shigo da motarsa, zuciyarsa cike da son ganin sehrish ɗinsa, da murmushi ya shiga ciki, bakowa duk sun je sallah da alama, 

Bedroom ɗinsa ya wuce, cikin sauri ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito,  shirt yasanya tare da dogon wando, kullum ya kalli kansa a mirror sai ya furta wannan kalmar wato “Mallakin sehrish,” 

(Sai naji dama ni yakewa tanadin kansa da ban bari yasha wahala ba, dama ƙopa a buɗe take musamman ga irinsu Junaid masu kyawun hali) 😅

Download>>> Maciji Ne Complete Document

Jin takon takalminsa yasa sehrish ɗagowa, wadda ke tsaye tana ta faman jera abincin a dining, ita ta riga azmee fitowa bayan sun gudanar da sallar la’asar, zuba mishi ido tayi atlease tayi kewarsa sosai don tun safe rabon da tasa shi a idonta, 

Shima farin ciki ne ya dabaibayesa ganin muradin ransa, ƙarasawa yayi yaja kujera ya zauna yana kallonta,

Cikin sauri tace “me zan zuba maka,” 

 “duk abunda yayi miki,” kai tsaya ya faɗa,

Jim sehrish tayi shiru ta tsaya da jeran da take yi, maimaita maganar da yayi yanzu acikin zuciyarta tayi wato daya ce “duk abunda yayi miki amaimakon yace duk abunda yayi maka tunda amatsayin namiji take,” 

ɗan ɗagowa tayi ta saci kallansa, har ynx idonsa na akanta fuskarnan ɗauke da murmushi, 

Jiki a sanyaye ta zaro plate haɗaɗɗiyar jallop din taliya ta zuba masa, tare da haɗa masa da Cokali aciki ta miƙa masa, 

“Thanks” ya furta tare da soma cin abincin, ganin yana ɗiba da zafinta yasa tace “ka bi a hankali kana ka ƙone,” 

ɗagowa yayi ya kalle ta da buɗen bakinsa sai cewa yayi “kada ki damu zan kula”

daram taji gabanta ya ƙara faɗuwa, yau junaid yasaki layi sai kiranta ya ke da sunan macen ta, 

Jin ƙarar dirar motoci ya tabbatar mata da cewa sun dawo, nan da nan taji zuciyarta ta bada wani sound, saboda tasan hada mutumin ta aciki, 

Shigowa su kayi atare suna ta faman fira, kamar ba’a tare suke ba, 

 fawan da khaleed ne suka fara shigo wa tare da su Irfan da jabeer banda su twins, 

tayi tunanin shima zai shigo ne amma babu shi, haka abbansu ma, da kanal yusif, 

kai tsaye suma suka wuce izuwa dining ɗin suka ja kujera kowa ya zauna, 

“Sannun ku da dawowa” acewar junaid, 

Su ka amsa su duka, cikin sauri sehrish ta shiga yin saving ɗinsu, 

“Ina yaya Ayaan da Jahan su ke, banganku atare ba? Su basu dawo ba ne?

Junaid ne yayi wannan tambayar, 

  Fawan ne ya basu amsa da cewa “taya muma zamu sani? mun jima da rabuwa dasu, su sukansan inda suka je”

Jabeer yace “ko tsoro basa ji, babban yaya ya neme su, su basusan su kame kansu ba, kamar yadda mukayi,” 

“Ka rabu da shaggun jiki magayi,” acewar irfan,

    

   

Download>>> Nida Yaya Habeeb Complete Document

“Ka rabu da shaggun jiki magayi,” acewar irfan,

haka su kayi ta fira suna zuba abinci acikinsu,

Bayan sun kammala sehrish ta kakkwashe dishes ɗin da sauransu duka tayi kitchen dasu, har time ɗin azmee bata fito ba har sai da ta kammala wanke komai da su kayi amfani  dashi sannan tashigo agajiye tana faɗin”kin ji shiru ko wlh bacci ne yayi awon gaba dani shiyasa ban fito ba, 

    “Babu komai aunty azmee kwarama da kika huta sbd kina aikatuwa ssae,” 

    

   Azmee tace” hmmmm nasaba ne, bana gajiya da aiki, 

shiru su ka ɗayin kafin rishi ta kuma cewa “Su babban yaya basu shigo ba, shi a part ɗinsa za’a kai masa abincinsa ko anan down ?

murmushi azmee tayi tace ” a can ake kai masa amma in yakasance dinner ne, wani time ɗin kuwa anan su ke haɗuwa suci gaba ɗaya, ke zaki kaimasa ?

“Eh zan kai masa,’ cikin zumuɗi sehrish ta bata amsa, 

“Shikenan amma akwai wani abu da zan faɗa miki u ave to know it,” 

Sehrish ta ɗan yi jim kafin tace “menene shi”?.

“Babban yaya fa, baya son kallo sai fa kin kiyaye, because in ana kallonsa yana ji ajikinsa, sannan in ya tambayi abu ko menene kawai ki ce akwai, karki kuskura ya ce yana buƙatar wani abu akawo masa ki ce bamu dashi, ya tsani wannan ki kiyaye ! Sannan baisan kwaratsi ko kaɗan, sannan shi mutun ne mai tsaftar gaske, ko da gigin wasa kada ki kuskura ki bar abun ƙazanta a part ɗinsa ko min ƙanƙantarsa ko da ajikin ki ne, ke ma ki ƙara tsaftarki abisa wadda ki ke yi don daga yanzu ke ce zaki rinƙa kula da part ɗinsa,” 

Wani irin daɗi ne ya rufe sehrish, jin cewa itace zata rinƙa kula da part ɗinsa, koba komai zasu samu kusanci da juna, 😇

Azmee ta ci gaba cewa “and then he doesnt repeat words in yayi magana, dole yayi magana aji farat ɗaya, sannan in yana bacci ba’a tashin shi, don naushi ya ke kaiwa bana wasa ba……’

Katse ta sehrish tayi da cewa “In time ɗin sallah ne fa? Shima ba’a tashin sa? ta tambaya tana kallon azmeen wadda ke daga tsaye, 

Azmee tace “Abun ajinin sa ya ke ! muddin lokacin sallah yayi dakansa ya ke farkawa, sometimes kuma alarm ke tashinsa,

Jinjina kai sehrish tayi aranta tace”akwai matsala, Anya kuwa zan iya ? ta tambayi kanta,

Muryar azmee ce ta dawo da ita “zaki iya mana, matukar ki kasa natsuwa,”

Wata tambayar sehrish ta ƙara jefa mata, 

“Aunty azmee wai babban yaya ɗan wrestling ne? 

“Meyasa ki ka tambaya”?

sehrish tace “naga yanayin kirar jikinsa ne, wlh irin ta tasu ce,” 

Hmmm azmee tace “shi da ya ke soja, sojan ma bana wasa ba, wanda ya amsa sunansa ae fiye da wresting ma yana yi,” 

Murmushi sehrish tasaki Aranta tace “a shirye nake dana zama tamkar baiwarsa wurin yi masa biyayya sau da ƙafa, zan yi komai zan yi iya ƙware wata don naga yasan da zamana acikin gidan nan, 

    tayi maganar atime ɗin da take jera dishes din da takammala wanke wa, a cikin shelves , 

Atare da azmee suka idasa gyara kitchen ɗin su kai mopping da komai,” daga bisa azmee ta wuce ɗakinta bayan ta sanarwa sehrish cewa idan sun dawo ta tabbatar da ta kai musu dinner ɗinsu,

  Kasa bacci tayi burin ta, taji shigowar Babban yaya, domin takai masa dinner ɗinsa, 

Murmushi kawai ya ke saki ynx ya yanke shawarar zai sanar wa sehrish da cewa yasan ita mace ce ba namiji, rungume ya ke da pillow a ƙirjinsa, night dress ne ajikinsa riga ce ta wuce guiwa, ya baje a saman gadon abban nasu yana jiran dawowarsa, 

   Ƴunkurawa yayi ya ɗan tashi zaune, yana tunanin taya zai sanar mata batare da ta tsorata ba, gyara murya yayi kamar yana agabanta ya ce “Sehrish na riga da nagane cewa ke maca ce, don haka ki kwantar da hankalinki, ni mai sauƙin kai ne bazan bari kowa yasani ba, i promise u, ni burina ki ɗauke ni tamkar ɗan uwanki na jininki, nima zan ɗauke ki amatsayin sister ɗita……..’ 

 dariya ya saki bayan yagama tsara wannan maganar, ajiyar zuciya ya saki tare da cewa haka yafi dacewa na tunkare ta, na sanar mata, Allah yasa kada ta razana, ko taƙi accepting ɗinsa as her brother,

Koma yayi tare da kwantawa idonsa na facing ceiling, fuskarnan da murmushi, har cikin ransa yarinyar ta kwanta masa luf~~~~~~~

Har bacci ya soma ɗaukarta, taji dirar motocinsi, cikin hanzari ta buɗe idonta, murmushin farin ciki tasaki, tashi tayi zaune tana jira su kammala shigowa kafin takai masu dinner ɗinsu, zuru tayi tana jiran shigowarsu, tana jiyo muryar abbansu da kanal yusif suna magana, amma bata jiyo tasa ba, tamasan baza taji tashi ba, saboda wata irin Voice ce dashi bata da sauti sosae, wata’ƙil sai ransa ya 6aci sannan Za’aji tsiwarsa,

Sai da ba da kusan 30 mins, sannan ta tashi cikin sauri ta gyara kanta, kafin ta wuce kitchen, sai da tafara kaiwa kanal yusif nashi a room ɗinsa, sannan ta wuce kaiwa Abbansu nashi shima, 

  Da sallama tashiga,atare da junaid suka amsa mata, cikin natsuwa ta shiga da tray ɗin mai ɗauke da food warmer tare da plates da spoon, sai jug da cup, 

          Kwance suke atare shigowarta yasa su tasowa zaune, cikin girmamawa tagaishe da abbansu, da sakin fuska ya amsa mata, 

  umarni ya bata da ta ajiye mashi anan ƙasa, ajiyewa tayi a hankali kafin ta tashi, suka haɗa ido da junaid ya kashe mata ido,

    gabanta ne taji ya faɗi, sai ta ga abun kamar a dream, tafiya take zata bar room ɗin nasu, tasake juyawa tare da kallonsa, again ya sake kashe mata idon,

   Cikin sauri ta fice tana mamakin wannan abun, amma tariga tasawa ranta cewa “Junaid yana da ta6in hankali,” wasu ɗabi’un nasa yayi mata kama da na masu psychiatric disorder 😂

A ɗan kayataccen tray ta shirya mashi nasa, gabanta na faɗuwa ta tunkari upstairs apartment ɗinsa,

 A buɗe tasamu kopan parlor ɗinsa, haske everywhere, bata gajiya da kallon hadaɗɗen parlor dinsa, sallama tayi taji shiru idasa shiga ciki tayi, asaman table ta ajiye masa shi, tsayawa tayi tana tunanin ya za’ae yasan ta an Kawo masa dinner ɗinsa, ran ta ne ya bata cewa ta shiga cikin bedroom ɗin nasa tayi informing nasa, 

   zuciyarta na ɗar ɗar ta tunkari cikin bedroom ɗin nasa, a hankali ta ɗanyi knocking door ɗinta, gabanta na faɗuwa,

     shiru tayi tana jira abata umarning shiga, sexy Voice ɗinsa ce ta ratsa kunnanta da cewa “Come In”

Ajiyar zuciya sehrish tayi, tare da lumshe idonta, wani irin sanyi ne ni’imataccen gaske tare da ƙamshi su ka ziyarci hancin ta, a hankali ta idasa shiga ciki tana wurwur ga eyes ɗinsa can ta hangosa, daram taji wani irin bugu azuciyarta, 

     daga shi sai ɗan pant na maza ajikinta, yana tsaye at the front of the mirror Allah yaso ya juya mata baya, ba ita ya ke fuskanta ba, da taga tashin hankali, 

Zuba wa surar jikin shi ido tayi cikin tsananin tsoro, dogo ne bana wasa ba, ga wannan ƙirar karfin tasa, idonta ta saukar akan zanen tattoo ɗinsa mai tsananin kyan gaske A farar fatarsa, bata ta6a lura dashi ba sai yau, 

   sam tarasa buɗe baki ta faɗi abunda ya kawota sbd kallon Kyakkyawar surar Babban yayanmu, 💞 

hannayensa na cikin sumar kansa, yana shasshafa mata mai, sai salƙi take kafin ya ɗaure ta yasa ke ta izuwa bayansa, mayar da hannunsa yayi acikin jerin tsadaddun turarukansa dake agaban mirror  ya ɗauko kwalbar turaren (Imperial Majesty) haɗaɗɗen turare mai wani irin fragrance mai ratsa sassan jiki, sai wane da wane ke mallakar irinsa, 

Download>>> Abban Sojoji Part 1 Complete Document

    Feshe jikinsa ya yi dashi ta ko’ina kafin ya mayar ya ajiye, 

 Ya jima yana mamakin wanene ya shigo masa bedroom ɗinsa haka, ya ba da permission ɗin a shigo amma shiru ba aƙara magana ba, 

    gyaran murya yayi alamar son jin bayani daga wurin wanda ya shigo masa ɗaki, 

     gyaran muryar da yayi ne ya dawo da ita cikin hayyacin ta, cikin sauri murya na rawa tace “am…dama…dinner….ne ….na kawo……yana a parlor, 

    “Its okay, wait 4 me there, am coming now,” ya faɗi yana kai hannunsa saman bedmatress ɗinsa inda ya ajiye sleeping dress ɗinsa da zai sanya, 

   Jiki a mace sehrish ta fice, tana cizon lips ɗinta, haƙiƙa tagama narkuwa cikin tsananin ƙaunarsa 💘

A parlor dinsa ta tsaya tana jiransa kamar yadda ya umarta, hannunta na a chest ɗinta dafe da saitin Zuciyarta, surarsa kawai idonta ke tariyo mata, Murmushi kawai take saki *Big bro* ya gama tafiya da ita, 😍

   Sam bata ji fitowarsa ba, sai da ya ƙaraso ya zagayo inda royal sofa ɗin suke sannan ta ankara, 

   Wani sabon kallon tabi shi dashi, sleeping dress ɗinsa sunyi matuƙar yi masa kyau, koda ya ke shine yayi musu kyau, irinsu Babban yaya sune suke wa kaya kyau, wato masu sa kyau tayo kyau ko bata da kyau 😇

Riga da wando ne ƴan ƙasar indonesia masu laushin gaske, irin wanda ko mutun baijin bacci yasa su dole yaji shi, maroon colour masu zanen flowers milk colour ajikinsu, daga sama rigar bata rufe ƙirjinsa ba, dama shi bai cika sa kaya waɗanda ke covering chest ɗinsa ba, bai sanya links na rigar ba, 

      Cikin natsuwa ya zauna saman 3 seater, sam sehrish tagaza janye idonta akansa balle tafara saving ɗinsa har sai da taji voice ɗinsa a ears ɗinta yace “Ni zanyi saving kaina ne!? ya tambaya fuska a ɗaure, 

    Cikin sauri sehrish ta ɗauke ɗan bowl tare da buɗe warmer ɗin dake ɗauke da Chicken pepper soup, tasanya saving spoon ta Shaƙe masa shi, wani irin  aroma ne ke tashi daddaɗan gaske, ajiye masa tayi sannan ta zuba masa white rice acikin plate, bayan nan ta haɗa masa da drink mai sanyi,

    Natsuwa tayi bayan ta kammala zuba mashi duk abinda ya dace, ta ɗan ja baya zata juya ta fice sbd tuna mgnr azmee na cewa Bayason kallo, muryarsa tasake ji ya ce “In na kammala wazai kai kayan kitchen!”? tsananin mamaki sehrish kawae take yi, ashe yana magana har haka, acewarta, muryarsa ba ƙaramin daɗi take mata ba, tayi mamakin yadda yake furta yaren hausa duk da kana ji kasan bai saba da ita ba, in ka gansa bazaka ta6a tunanin cewa zai iya magana da hausa ba, saboda yanayinsa,

    Cikin hanzari tace “Ni” jinjina kansa yayi, ya ci gaba da cin kazar dake gabansa, murmushi ta ɗan saki tasamu wuri ta tsaya, da tazara tsakaninsu, amma komai yakai hannu zai ɗauko cikin sauri sehrish ke ɗauka ta zuba masa in na zubawa ne, in kuma nasha ne ta tsaiyaya masa, har ya kammala sam babban yaya baya wasa da cikinsa, yana basa haƙƙinsa yadda ya dace, 

        Sehrish ta tsaiyaya masa ruwa ya wanke hannunsa acikin wani bowl, sannan ta ciri tissue ta miƙa masa ya goge mouth ɗinsa dashi, 

   Haka tabi shi da ido harya tashi ya wuce cikin bedroom ɗinsa, ta lura bacci yake ji yadda taga yana lumshe idonsa, 

   Sai daga bisani ta tattare kayan ta fice tana mai jin kewarsa atare da ita, kafin zuwa gobe ta kuma sashi a idonta, cikin kitchen tamayar da kayan sai da ta wawwanke dishes ɗin acikin daren sannan ta wuce nata room ɗin tana mai cike da shauƙinsa, 

Ta jima ba tayi bacci ba, su twins basu dawo cikin gidan nan ba sai around shabiyu na dare, Time ɗin ma kowa yayi bacci, cikin sanɗa su ka wuce room ɗinsu, 

a cikin ƴan kwanakin nan rayuwar sehrish ta canza sosai, wani irin azababben so take mashi, wanda har ya kai ga ko sallah take yi da tunaninsa aranta, daker take samu ta dai daita natsuwarta wani sa’in, 

Junaid kuwa sam ya gaza gaya mata abunda ya shirya zai sanar mata, ƙarshe azmee tace yabarta ita da kanta zata sanarwa sehrish ɗin, a yayin da sehrish ke wannan haukan sam Rafayet har yau bai ta6a ɗagowa da idonsa ba, yasa cikin nata, bae masan wanene ba ko wacece ba ke famar ɗawainiyar kai masa abinci da gyara masa part ɗinsa ba, abunda yasani shine yana samu kyakkyawar kula agurin  kowanene ma  💋

*Hafsat Bature*…………………………………………………………

………….._Katsina state_…………….

Zaune take ta haƙimce a saman 3 seater, ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, hannun ta na riƙe da remote, ta ƙura ido tana kallon faskekiyar plasman dake manne jikin bango tana facing ɗinta,  

Ko kyaftawa batasan yi, dayake shirin ta ake yi, wato shirin daɗin kowa na Arewa 24, maimaici ne take kallo, sai faman washe baki take yi tana fadin “Oh koya za’a kaya tsakanin mlm na tala’a da hajiya fatima akwai bada ƙala a wurin nan,’ ta faɗi tana jinjina kai, ita kadai abunta, acikin matsakaicin parlor ya hadu iya haduwarsa ba hayaniya, ga komai cike da tsafta kwal, 

Download>>> Kishin Bal-Bal Complete Document

Tsohuwa ce amma ba tukuf ɗin nan ba, tana da hasken fata, jikinta na sanye da riga da zani na atampa, ta coge ɗaurin dankwali, daga ganin ta kasan taji hutu ga kuma kwanciyar hankali da natsuwa, 

“Saude ! Saudee !! saudatu wai ina ki ka shiga ne? kin shanya ni ina ta faman jiran ki, da alama watan barin ki agidannan ya tsaya,” 😡

tsohuwarce ta fadi tana murguda baki kamar wata yarinya,

Cikin sauri wadda aka kira da sunan saude ta fito daga kitchen hannun ta ɗauke da plate wanda naman kaza ne acikinsa jar suya 

Karasowa tayi tana faɗin “dan Allah goggo ayimun afwa, wlh bata ida soyu ba ne shiyasa,’ 

hararar ta tayi tana yamutsa fuska tasa hannu ta kar6i plate din tana cewa “Last warning, in ki ka kara, zaki tattara kayanki ki koma can ƙauyenku aci gaba kiwon shanu baki ba ra6ar A.c ,” 

Shiru saudatu tayi tana tamke fuska, ta tsani taji ance za’a maida ta ƙauyansu, gashi kullum tsohuwar cikin yi mata mita take bata gajiya, 

hannu tasa ta ɗauki tsokar naman ta tusa abaki, tana tauna tana yamutsa fuska, 

“Anya kuwa saude kinsa farin magi aciki kuwa,” ta tambaya tana kallonta yayin da take lasar naki, 

A ƙule saude tace “bansanya ba, babban likita ya hana,!

dagowa tayi baki asake tana kallonta “saudatu ! Rashin kunya ko? Ki kalli tsabar idona ki ce babban likita ya hana ! shiya haife ni koni na haife sa dazai hanani jin daɗin rayuwa!?

Cikin ƙunkuni saudatu tace “Ke ki ka haifesa, amma ae don lafiyarki yayi hakan….’

tunkan ta idasa magana, goggon ta jefe ta da ƙashin ciyar kaza a fuska,’ 

Hannu saudatu tasa ta shafa wurin da ta jife ta, kafin ta kalle ta tana zumbura mata baki,

“Ke ki kiyaye ni Allah ! wato ya daure maki gindi kina iya shegen da kika ga dama ko ? Cikin sauri saude ta dafe kai cikin jin kunya tace “dan Allah goggo wannan maganar ba daɗin ji Allah, gatsar ba sakayawaa, 

Baki asake goggo tace “ba shakka, yau yarinya zatayi fiffike ta koma gidan ubanta,’ 

Kafin Saudatu ta bata amsa, sukaji dirar motoci a cikin gidan da jiniya,

Kallon juna su kayi atare, saudatu tace “goggo meke faruwa ne, ko kinyi da wani zai zo ne ? ni naji kamar jiniyar motar ƴan sanda,” 

Murmushi goggo tasaki tare da ajiye plate ɗin kazarta, kasa tana cewa 

“Kin manta muna da rundunar sojoji a family ɗin mu 😇  Shiyasa nake gargaɗinki kibi ni a hankali, kiyi mun biyayya ko kin gama da duniya lafiya, cikin zolaya tayi maganar, dariya saudatu tayi, 

adai~dai lokacin marshal omar ya shigo wanda dirarsa kenan, 

sanye yake cikin jeans da farar t shirt mai dogon hannu tabi shape din jikinsa, surar kirjinsa ta bayyana muraran, fuskarsa na sanye da face mask, ba karamin kyau yayi ba, koda yake dama jinin kyau ne su, 

tun da ya shigo baki asake saudatu ke kallonsa kamar ranar ta fara ganinsa, 

Cike da wannan tafiyar tasa ta nigogi majiya karfi yake tafiya,  

Tsananin farin ciki yasa goggon katsina harba plate ɗin kazarta ya watse ƙasan carpet ba tare da ta sani ba, kamar karamar yarinya haka ta watsa a guje ta rungumesa tana fadin “Wata sabon gani, mafarki nake ko gaske, Oh ni Omar, 

Sakin shi tayi tana ta faman zabga murmushin jin daɗi, a hankali yasa hannu ya ɗan zame facemask ɗinsa yana kallonsa fuskarsa da fara’a ya ce “Goggo na har ynz dama baki daina wannan tsalle tsallen ba sai kin 6alla ƙafa ? 

dariya tayi ta ruko hannusa tana fadin” wlh duk cikin farin ciki ne Omar, ji nake kamar in zuba ruwa a ƙasa in sha,

zama su kayi atare, sai lokacin saudatu ta samu damar gaishe shi ” sannu da zuwa ƴa’ƴa Omar,’ 

“yawwa” ya bata amsa without looking at her, idonsa na akan goggonsa wadda ke ta faman binsa da kallo, hannu tasa ta shafa fuskarsa tana faɗin “Oh ni Omar haka ka zama, tukunna ma dai yaushe ku kazo daga U.s ɗin? kuma ya naganka kai kaɗai ina sauran suke ? tare da matarka ku ka zo ? ta haihu yanzu ko ? 

Zuru yayi yana kallonta, aransa yace  mai hali bai ta6a canzawa in banda zafin ɗumi irin na goggon katsina Yaushe yayi budurwar balle akaiga maganar aure da ƴa’ƴa? 

Download>>> Burin Abbana Complete Document

ajiyar zuciya ya saki kafin yace “wacce amsa ki ke so na fara baki gaggona ?

Murmushi ta dan saki tare da cewa “ni ba wannan ba ma, Oh ni Omar wai kai ne ka zama haka !  kazama kamar dodo, Ka tara ƙirar karfi ba mata, kyau ace akwai inda za’a rinƙa sauke nauyin nan,…

Cikin jin kunya saudatu dake tsaye ta juya tayi cikin kitchen, domin kawo masa abun sha, 

dafe kansa yayi tare da cewa “Omg !! goggo shiyasa ba kowa ke son zuwa wurinki ba, sbd in ki ka fara zuba kamar radio mai jini,’ ya faɗi yana yamutsa fuska saboda baisan hayaniya arayuwarsa,

Hannu tasa tare da rufe bakinta tace “nayi shiru tom, ka da kace zaka daina zuwa wurina bari nayi shiru, 

dawowa saudatu tayi hannunta rike da tray da ta zuba masa snacks da abunsha a cup, ajiyewa tayi agabansa,

hannu yakai ya dauki lemun domin ya kur6a, muryar goggon ce ta katse sa da cewa “dole nayi magana Omar, Oh ni Jibi yadda ka tara nonuwa  a kirjinka sai kace dai za’a sa akwatin nono na mata a suturta……” 

ae baisan lkcn da ya ajiye cup din ba ya miƙe tare da cewa “Ni zan tafi, kunyartar ta isa haka,” 

saude dake a wurin tuni ta sulale ta gudu,sbd tayu matukar kunya ta, da sakin layin da goggon take masa,

Cikin lallami ta tashi itama tsayen tana cewa “haba ɗan shalelena, duk fa cikin murnar ganin ka ne,’ 

ta6e bakinsa yayi tare da cewa ” no goggo tafiya zanyi, dama bani kadai nazo ba akwai yara na dake a waje suna jira na,” 

Sam bataji daɗi ba, jin zai tafi tayi tunanin zai tsaya ya kwanar mata ne, itama tasan cewa surutunta ne ya ja mata, sarai tasan cewa bayason ɗumi haka,

Cikin sanyin murya goggo tace “toh baza ka tsaya ku gaisa da Babban likita ba ? kusan kullum sai yayi mgnr yaushe zaku zo daga America,

marshal Omar ya ce ” yana ina ne ? Ko yana on duty ne ? goggo tace “Eh tun da safe ya tafi asibiti aiki,’ 

“Okey may be na leƙa masa bfr na wuce kaduna gobe da safe, ‘ 

“Yanzu omari tafiya zakayi daga zuwa,’ ?  tayi mgnr kamar zata yi kuka,

“Calm down your mind gaggo na, Captain adam da su mg Osman na nan zuwa, duk zagi gansu, nima zan dawo insha Allah, ynz akwai mahimmin aiki a gabana ne shiyasa,” 

Jin sunan waɗanda zasu zo dayawa yasa ta washe daga ɗaure fuskar da tayi,

“Aiko da naji daɗi, in suka zo, zan masa a ayi musu fura, in suka zo suyi ta sha,” 

Murmushi Omar yasaki ya fice yana faɗin “Zaki ga saƙona gaggo,” 

Download>>> Abdul Jalal Part 1 Complete Document

Cikin jin daɗi tace “ina jira ɗan Albarka, ta ɗaga murya tana ci gaba da cewa  “Allah ya haɗa ka  da kaddarar ka acikin garin nan,’ 

sarai yaji ta fita yayi yana ɗan murmushi, yarasa dalilin dayasa, tsofaffin nan suke disturbing ɗinsu akan aure aure 😏

tunkan ya ƙarasa inda motocinsu su   ke, da sauri wani sergeant ya buɗe masa mota ya shiga A jere motocinsu suka fita, 

    sai da ya tafi sannan saude ta fito tana cewa “wlh goggo sam bakya kyauta, shikenan daga tsufa ya fara kama mutun sai yaita ƴan sambatu yana sakin layi ynx abunda ki kayiwa ƴaƴa omar kin kyauta “?

  ta tambaya tana kallon goggon wadda ke zaune saman kujera, baki asake take kallon sauden,

Jinjina kai tayi tare da cewa “ba shakka raini ya shiga tsakanin mu, gobe goben nan zaki koma ƙyauyenku ni nagaji dama liƙamin ke akayi aka manna bin ba don naso ba,’ ta faɗi tana hararar ta,

Riƙe ƙugu saude tayi tare da cewa “to kisa ni ba inda zani je, koma tafiyar zanyi ƙafa ta ƙafar Babban likita ,’ 

  “Saboda ke ki ka haife shi”? goggon ta tambaya, 

Saude tace “bani na haifeshi ba, amma zaki ga yadda soyayya ke aiki……’ bata idasa ba goggo tabi ta aguje itama ta tashige ciki da sauri, dama sun saba, 

  

_Husannsa & Jahad_

A 6angaren husanna dake kwance rai hannun Allah magashiyan, ba’a son inda kanta ya ke ba, 

Likito ci sun gaza gane, menene matslarta, iya abunda suka sani tana da mental ilness sai asthma, bayan nan binciken su bai nuna masu komai ba, 

Rashin kwanciyar hankali ne ya hana, jahad ta yi masu bayanin cewa tana da Iska, sam ta manta da wannan sbd ba natsuwa kullum cikin kuka take asibitin, 

Atare suka shigo inda aka kwantar da ita, suna tattauna wa akan ciwonta, su biyu ne professional doctor ne wanda su ke kira da Babban likita (big doctor) tare da wani jami’in ɗan sanda, dr ɗin na koƙarin yi masa bayani akan yarinyar, 

Sam basu lura da husanna wadda ke kwance, magashiyan sai faman fisge fisge take tana nishi, hannu tasa ta cire roban oxygen ɗin da suka sa mata, tari wurgi da shi, tana wani irin huci kamar zakanya, idanunta sun juye sun canza launi,

A haukace ta ƴunkura da ƙwarin gaske takai hannu ta zare bingidar dake soke ƙugun police man ɗin da suke magana da big doctor ba tare da saninsa ba, 

sai da ta zare sannan likitan ya lura cikin tashin hankali yace “Innalallahi wa’inna ilahirrraji’un !!” 

A firgice ɗan sandan ya shafa waist ɗinsa yaji ba gun ɗinsa, gaba ɗaya hankalinsu ya tashi ganin tayi sai ta su da ita, kuma ta rike maɗalllin, nan fa ido ya raina fata, lallashin ta suka shiga yi don ta ajiye bindigar amma ina, sai ma ta fisgi hanya da gudun gaske tana harba bindigar a duk inda ta samu ji ka ke daram!! Daram !! , zo ka ga yanda mutane ke gudu ba likitocin ba, ba nurses ɗin ba hatta marasa lafiyan dake kwance magashiyan neman hanyar gudu wa su ke yi, a tunanin su, ƴan bindiga daɗi ne suka kawo masu ziyara ta musamman 😂🤣😂

Jama’a gawa na tsoran rami, 😂🤣

Husanna fa ta haukace, misbehaving take yi kamar ƴar mahaukaciya, 

Gashi dama ba hijabi ajikinta sun cire mata, da za’a kwantar da ita, 

Wannan mahaukacin gashin, nata mai yawan gaske da tsayi ya bazo mata ta ko’ina har gaban fuskanta, tana gudu yana kara rufe mata ido ko gabanta ma bata kallo, 

“Jama’a kowa ya watse, kowa ya gudu yayi takansa an samu matsala, mahaukaci ta gudo daga psychiatric hannunta riƙe da bindiga kowa yayi takansa,” 😆

Wani copral ne ke bada wannan annoucement ɗin,  don asamu kowa ya kare kansa, 

Bin ta police men ɗin suke da gudu suna rokon tabasu bindigar nan, amma ina Husanna tayi nisan da bata jin kira, 

Jahad ta gama rikicewa ganin bala’in da husanna ke ƙoƙarin ja, musu a guje itama take binta tana faɗin “Husanna dan Allah ki daina, kada ki kashe wani kija mana bala’i, dan Allah ki basu bindigarsu, innalallahi wa’inna ilaihirraji’un

Asibiti fa ya harmutse, kowa gudu yake yi , gashi ita husannar sai yawo take musu da hankali sai zagaye cikin asibitin suke, duk inda tabi mutane sai su watse, sai ihu ake ana zabga salati kai ka ce zombies ne suka bayyana,

Ƴan sandar sun fusata sosai ransu yayi mugun 6aci, kiris ya rage su harbe ta gudun kada tasa ayi asarar rayu ka, sbd ko’ina tasamu harbi take yi, 

Abunda basu sani ba wannan ihun da ake yi shi ke ƙara haukatar da ita, bata cika son ƙara ba, 

Sannan ita kanta husannar a tsorace take sbd police ɗin dake bin ta, 

Tana cikin gudun nan hankalin ta atashe , gudu take amma tana waiwayon su cike da tsoronsu, cikin rashin sani kwatsam taji ta faɗa ajikin mutun,

Gam ta faɗa a faffaɗan ƙirjinsa, ta ƙankamesa, ta rungumosa sosai, a tsananin tsorace,

Nan take komai ya dakata, ji ka ke tsit kamar mutuwa ta gifta, babu mai kwakkwaran motsi acikinsu, 

Gaba ɗaya duk suna tsaitsaye likitocin da nurses ɗin da wasu daga cikin marasa lpy masu ƙwarin jiki da ƴan dubiya, ga ƴan sanda , kowa dai 

Saukar ajiyar zuciya kowa yake saki, ita kam jahad ta tsorata, da ganin mutumin da Husanna ta faɗama wa, duk da yasa face mask a fuskanshi, amma ƙirar karfin nan tasa, dole tasa hankali tashi, 

Tsoranta karya ce zai hukunta Husanna da ta faɗa masa bagatatan, 

A tare zuciyoyinsu ke bugawa, bugu bana wasa ba, ta kwanta luf ajikinsa, wato wata irin ni’ima ce atattare dashi wadda tasanya husanna dawo wa cikin hayyacinta lokaci guda, sam tagaza tashi daga jikinsa, ƙamshin turarensa ya gama kashe mata dukkan wani ƙwari na jikinta, 😌

Sai faman ajiyar zuciya take saki, hannunta ta ƙarasawa ta zagaye waist ɗinsa so tightly, 

Ganin hakan yasa Soja  dake bayansa mai riƙe da mukamin major, yasa hannu ya zare gun ɗin dake hannunta , saboda ta zagayo da hannun nata a ƙugunsa ga bindigar a fili,

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Back to top button