Uncategorized

Wace Ce Ita Chapter 8 Complete Novel

    WACECE ITA⁉️ (WHO IS SHE⁉️)

~Unique Barakancy~

   EIGHT📍

           Jin shiru ne yasa fatima zainab kwashewa da dariya,ko a haka aka tsaya tasan kwalliya ta biya kudin sabulu,ita kanta tasan ko a haka ta gigita rayuwarsa,ta razanashi,ta dimautashi,gobe inya isa ya kara….. Tuno yanda khaleel yake kuka yana bata hakuri yasa ta kara tintsirewa da wata muguwar dariya (ni ko unique barakancy nace wai danma bakisan harda fitsari ya saki a wando ba😹)…. Zuciyarta fess ta fita daga dakin,dayan dakin tashiga inda ta sauka,toilet ta shiga tayi wanka sosai,sannan ta dauro alwala ta fito,dogon hijabi kawai ta zira ganin lokacin sallahr isha yayi ta tada sallah a nitse,ta daura da shafi’i da wutiri…… Shiryawa tayi sannan ta dauko regular dinta tasha,saida ta jita very high,sannan wani dauyayyan bacci ya kwasheta…….

          Awan khaleel biyu a toilet sannan Allah ya bashi ikon farkawa daga suman daya yi,kalle kalle ya shiga yi tsabar rudewa sai yaga kamar ita yake hangowa ta gurin windown toilet,wani ihu ya rusa yana cewa “Wayyo Allah,azo a taimakamin,dan Allah kiyi hakuri na tuba,bazan sake ba wallahi kimin rai sharrin shedan ne,ki tausayamin ki rabu dani”……. Sai kuma yaga ya daina ganinta kamar wacce ta bace,ai saiya kara fashewa da kuka….. Kamar ance ya kalli gefenshi,sai yaga kamar ita,ihu ya sake zawo na zubo mishi ya kuma sumewa (nan ko duk hallucination ne tsabar yanda yasa abun arai,amma bata gurin,ita tana chan tana shan baccinta)……….

After one hour khaleel ya sake farkawa daga suman wucin gadin da yayi,sai a lokacin ya fara karanto addu’oi,nan da nan ko yaji wani nitsuwa ya saukar masa,sai a lokacin yaga wautarshi na mantawa da Allah tintini………. 

Mikewa yayi da niyar kunna shower,gabadaya yaga jikinshi ya baci da zawo da fitsari,he couldn’t believe wai shi classic khaleel ne a haka…. Girgiza kai kawai yayi ya sakarma kansa ruwan sanyi,sannan yayi wanka…… A hankali yake leka dakin sadap sadap dan ganin ko tana cikin dakin haryanzu,ajiyar zuciya ya sauke ganin bata dakin,fitowa yayi ya nufi kofar dakin ya rufe da sauri sannan ya shirya………

           2am dot kamar an tabata ta farka,alwala ta dauro,tazo ta tada sallah,sosai take hawaye tana tsawaita dukkan sujjadanta,nafilfili ta cigaba dayi har saida taji kafafuwanta sun fara mata nauyi sannan ta haqura ta dau qur’ani ta fara karantawa,saida taji alarm din dake dakin yayi ringing alamun sallahr asuba tayi sannan ta hakura ta tada sallah,tana idarwa ta daura da azkar……… Mikewa tayi ta sake yin wanka,drugs ta kuma sha,wani baccin ya sake kwasheta………

             Karfe goma na safe khaleel ya fito parlour,dube dube ya shigayi yana nemanta,a tsorace ya kalli dakin dake gefen nasa,yasani indai tana sama to tabbas tana ciki…. Da sanda ya sauka kasa,har wani hamdala ya sauke ganin bata kasa,kwasar takalmansa yayi a hannu ya fita daga parlourn a guje😹………..

           Zaune take a katafaren parlourn nasu,hannunta dauke da remote,idonta kur akan tv,idan ka kalleta a haka zaka dauka tabawa kallon dukkan hankalinta,saidai sam hankalinta baya kan tv’n,ta nitse a kogin tinanin da tasan baze Fissheta ba,anfi sati kenan da bata ganta ba,tin bayan ta hankadeta ta fita bata sake dawowa hostel ba ,ita kuma tinda tayi tozali da hannayenta taji tanasan sanin WACECE ITA?,babban abinda yake damun eesha shine meyasa ta hankadeta bayan nufin taimakonta da tayi?….. Tin bayan wannan rana bata kara samun nitsuwa ba,burinta kawai taga ta dawo ta samu ta tambayeta meta mata ranar data ture ta sannan ta bata hakuri,amma shiru kamar wanda taje kai bawa garinsu,bata kara dawowa hostel ba,ita kuma eesha sai tasa a ranta itace silar rashin dawowarta hostel,shiyasa abun ke damunta sosai…….

“Aisha,Aisha!”…… Firgit ta dawo daga duniyar tinanin data fada,karasowa wacce ke kiranta tayi ta zauna kusa da ita,dafa kafadarta tayi tace “tinanin me kikeyi haka?,sai magana nake bakyaji,what’s wrong with you?”…….. Sallamar mahaifiyar eesha ce ta katsesu,karasowa tayi tace “ah toh tayani tambayarta dan ni dai nayi iya yina taki fada,maybe ke ta fadamiki”………… Murmushi kyakkyawar matar dake late 50s dinta da tsabar gyara da hutu sai kayi tinanin batafi 38 ba a duniya,ta dubi eesha tace “look daughter,you know I’m a good listener plus I won’t judge you,ki fadamin damuwarki karkiji komai,okay?”………. Mamaki ne ya kamasu ganin eesha ta fara hawaye,nan tashiga basu labarin little she knows about fatimah zainab dako sunanta bata sani ba,har zuwa ranar data hankadeta,da neman da take mata amma taki dawowa har yau……….

Gabadaya sai suka zama speechless suka cigaba da bin eesha da kallo……. Chan aminyar mahaifiyar eesha tace “As a judge,the girl is suspicious!”…… “Yes she is!” Mahaifiyar eesha data kasance itama judge ta kara da cewa…. Murmushi aminiyar ta sakeyi tace “amma ga wani tactics,nasan Insha Allah in kikabi a sannu zaki san WACECE ITA,just keep me updated,I’m interested too!”….. Gyada kai eesha tayi tace”Take you mom”…..

              Deen bai farkaba sai washegari da safe around 9am,bude ido yayi ba kowa a dakin lokacin,bin dakin yayi da kallo,anan ya tabbatar da a hospital yake,sai a lokacin incident din daya faru ya dawo mishi,yanda accident din ya kasance da komai,fincike drip din da aka dauramasa yayi ya daki karfen gadon yace “It was intentional,yes it looks like a set up!,and I’m sure it’s from that demon,I must get her,dole ma insan ko WACECE ITA?,Today!”…….. 

Tashi yayi da sauri ya fito daga amenity ward din,kasancewar mutane nata kai kawo a harabar asibitin yasa ba wanda ya kula dashi,gashi kuma ya maze kamar ba mara lafiya ba,fita yayi daga ospital din gabadaya……. Sai kuma ya fara tinanin ina zeyi tinda ba mota,gashi yaji ba wallet dinshi a jikinshi,infact ba komai ma a jikinshi,luckily ya hango wani branch din bank dinsa,da sauri ya nufi bank din,in ka kallesa bazaka taba tinanin bashida lfy ba dan shi haka Allah ya yishi,mutum ne me mugun dauriya,haka yake jarumi ne a komai nasa,kana kallonsa kaga kakkarfan namiji kuma,gashi ba abinda ya tsana irin zaman asibiti shiyasa kawai ya gudu inyaso ya cigaba da treating kansa,shi bama wannan bane a gabanshi,babban treatment din da yake bukata a yanzu shine sanin WACECE ITA?,tabbas ya yadda ta dalilinta wannan accident din ya sameshi,amma ba gudu ba ja da baya harsai yasan wacece ita,he’ll just get prepared for the worse,yasa a ransa ko ze rasa ransa sai yasan WACECE ITA?……..

Blocking wanchan card din yayi sannan yayi requesting sabo,within 15mins ko aka gama aka bashi,withdrawing enough cash yayi sannan ya fita daga bank din…… Bolt yayi ordering ya nufi inda ake siyar da motoci direct,wata mota kirar’Rolls Royce’ ya siya,duk da tarin motocinsa haka kawai yaji bazai iya jira har akawo masa mota abuja ba,clearance akayi da komai sannan aka bashi car key ya shiga ya ja….. Transcorp ya nufa straight hoping ko ze ganta achan….. Yafi 30mins a parking lot yana kalle kalle ko Allah zesa ya ganta,koda ze ganta ta bace shidai kawai ya ganta,amma ina ko alamunta be gani ba,gabadaya sai yaji ya damu,ranshi ya baci,shi haka yake in dai be samu abinda yake so ba sai ransa ya baci,yayi zuciya ya hakura,amma a kanta kamar wanda akayiwa baki ya kasa hakura ya dena bibiyarta,ko yayi zuciya yanzu anjima ze fara tambayar kansa toh WACECE ITA?,shiyasa kawai ya dauki hakan a matsayin kaddararsa……… Ya kuma chanja mata suna from ‘Demon’ to ‘My Fate’…….

Hakura da zama cikin motar yayi ya shiga cikin hotel din… 

Wanka yayi ya shiga rama sallolin da ake binsa,yana godewa Allah sanin cewa dad is not aware,dan da sun sani sai dai kawai ya tashi ya gansu a hospital din,kuma yasan straight gida zasu wuce dashi,sai kuma yaji kamar fa yaga mom da dad jiya,girgiza kai yayi yace “No,hallucination ne amma basu nagani ba,in sune ina tashi yau zan gansu,nasan ma basu sani ba,and I’m glad”……….. Fitowa yayi ya fara lissafin ta ina ze fara nemanta………

           Sai karfe daya ta farka,shima jin azahar tayi ne,sallah kawai tayi ta sake kwanciya,sai la’asar ta kuma tashi,sai a sannan ta jita garau…… Wanka tayi,tayi sallah,shiryawa cikin wata free abaya tayi,hangloves da socks ta saka as usual,sai nose mask da shades kamar yanda tayi sanda zata zo………

Ko bi takan khaleel batayi ba ta sauka kasa,ta nufi hanyar fita da niyar taje ta ci abinci sannan,tinani ta shigayi to ina ma zata fara,sai kawai ta yanke shawarar duba kitchen din khaleel ko zata samu abinda zataci,tana shiga ko ta tarar da abubuwa dayawa saidai duk basu mata ba,kawai saita fita daga kitchen din…….

Bude kofarta kenan shi kuma yana kokarin knocking…… Karo sukayi shades dinta ya fita daga idonta ya fadi kasa,kallon kallo suka shigayi a tsakaninsu kafin a hankali yace “Fata barakallahu ahsanil khaliqeen” saboda arba dayayi da kyawawan lumsassun idanuwanta,da gashin gefen kunnenta daya kwanta kamar dasasa akayi a gurin,gashi sai sheki yake,kafin ya gama tantance yanayin da yake ciki yaji ta hankadasa,amma ko gezau kamar baa tabashi ba,saima kokarin cire nose mask dinta da yake domin yaga fuskarta da lokaci daya ya kwadaitu da san gani……..

     

Duk naga taaziyarku,kuma Nagode sosai,Allah ya bar zumunci lovelies❤️

~Unique Barakancy~

Back to top button