Uncategorized

Wace Ce Ita Chapter 23 Complete Novel

WACE CE ITA⁉️ (WHO IS SHE⁉️)

Unique Barakancy

                         TWENTY-THREE📍
            Tasowa mai gadin gidan yayi da sauri ya leka ta karamin gate dan yaga su waye…… 
Sameer ganin mai gadi ya leko ya sasa fitowa daga mota yazo ya samesa yana tambayarsa ko mai gidan na nan….. 
       “Eh yana nan”…
Mai gadin ya basa ansa…
     “Toh ko zaka iya mana sallama dashi?”….
   “Toh shikenan bari in sanar masa, amma wa zaa ce?”…
        “Kace masa sameer ne”…
       “Toh ina zuwa”…
Gyada kai Sameer yayi yayinda mai gadin ya shiga ciki dan neman izinin Deen….
 Dai dai kofar main parlour sukayi kicibus da Deen daya fito jin karar horn sosai…..
Gaishesa mai gadin ya karayi kamar ba dazun suka gaisa ba, be amsa ba yace masa;
      “Ya akayi”
   “Sallama akeyi da kai yallabai”….
   “Waye?”…..
    “Yace ace sameer”….
Dan jim Deen yayi yana tinanin su mami dake ciki, baze so sameer ya hadu da mami yanzu ba dan yasan haduwarsu bazatayi kyau ba, sannan bayasan sameer yaga yarinyar, so yake kawai ya maida ita gidansu batareda sameer ya biya bukatarsa ba, sai kuma yasa masa ido karya kuma kai mata hari…….
       “Kace masa ina zuwa”…….
Deen ya fada yana komawa ciki…….
Juyawa mai gadi yayi dan ya isar da sakon…….
Sameer na hango fitowar Deen ya kalli mutumin dake gefensa yace;
    “Gashi ya fito, muje!”,,,
Kallon Deen yayi ya girgiza kai yace;
     “Bana fadamaka yana nan tareda yarinyar ba? Yanzu ka yarda dani?”…..
     “Sosai, muje mu samesa”…
“No basai naje ba, duk abinda zece maka karka yarda  dan tana cikin gidannan”……
     “Toh nagode”….
Fita daga motar Sameer yayi ya karasa inda Deen yake a tsaye a bakin gate…… 
Mika masa hannu Deen yayi suka gaisa sannan yace;
    “Ashe kana tafe”…
“Ka fadi haka mana, wallahi Deen ka bani mamaki, ashe kaima sonta kake shine kake raina min hankali tuntini?”……
Cewar sameer rai a hade….. 
    “You’re very stupid for saying this! An gayamaka kowa shashasha ne irin ku da zaka zo kana gayamin maganar banza daga taimako, kai yanzu kana tinanin zan iya san yarinyar da kuke hauka akai? Toh ka bude kunnuwanka da kyau kaji I can never stoop so low and love the fucking girl you’re talking about, now get out of my sight”…..
Deen ya fada cikin zafin rai kamar ze mari sameer, dama yana neman wanda ze saukema bacin ran dayake fama dashi sai ga sameer yazo masa da maganar banza……
Ganin yanda Deen ya fusata yasa sameer kama kansa, dama ba wani yarda yayi da zancen ba, amma kuma abinda yake daure mishi kai ya akayi yaga Deen a gidan kamar yanda wancan ya fada?….. 
Dafa kafadar Deen yayi yana fadin;
      “Calm down man, abin be kai haka ba, I guess i misunderstood, honestly ba laifina bane wani ne ya fadamin haka”…
Nan ya kwashe duka yanda sukayi da wanchan ya fadawa Deen….
Jinjina kai Deen yayi yace;
     “Ya yake”….
Describing dinsa yayi kamar yanda Deen yayi expecting, ya kuma fadamasa tare sukazo, yana cikin mota ma……
         “Muje na gansa”….
Karasawa gurin motar sukayi, sameer ya zagaya ta inda mutumin yake zaune ya bude kofa yana mishi magana ya fito…… 
Shiru yaji baa amsa ba…. 
Lekawa ciki yayi yana tinanin ko ya chanja guri ne, sai yaga wayam, sama da kasa kuma ya nemesa ya rasa a motar…. A birkice ya shiga duba ko ina a motar Deen na tsaye yana binshi da kallon banza….
Ba karamin tsorata sameer yayi ba da ganin baiga mutumin a ciki ba, if he can recall ya fita ya barsa a ciki kuma shida Deen na facing inda motar take so bayanda zaayi ya fita be sani ba, abu kamar magic?…
Dage kafada Deen yayi yace;
     “How can you even believe a stranger? Dan iskan ai da yasani ya tsaya danaci ubansa a gurinnan, Well zan baka shawara karka kara bawa shedaninchan face if not kai zaka kwan ciki, ruwanka kuma ka yarda dani ruwanka ka yarda dashi”…..
Cikin zaro ido dan harga Allah har lokacin a tsorace yake yace;
     “What do you mean by shedani?”……
  “You’ll see for yourself if you keep on believing him har kana zuwa kana min shouting, kaga bacewar nan dayayi? Kadanne daga cikin abinda zaka gani, just give him chance and see”…
     “Boss why’re you doing this to me? Kana nufin ba mutum bane, stop giving me uncompleted statement pls, bakaga yanda na tsorata ba wallahi”….
     “Bakaga komai ba! I’ve said enough!”… 
   “Yanzu gidan waye wannan toh?”..
   “Mami, ko zaka shiga ku gaisa? Dama nemanka take!”…. 
      “Ni? Haba? Inaa.. Bazan shiga ba, yauwa why are you here? Tagane ka gudu ne?”…
Sameer ya fada a rikice kamar ze zura a guje, be gama fita daga wanchan rudanin ba ga wani kuma, shiko ina zesa ransa?….
   “Yes ta kuma gane dasa hannunka, she traced me even before I get to your house, Allah ne ya rufa maka asiri dan har base taje nemanka baka nan, I’ll advice you ka rufawa kanka asiri ka bar garinnan because she’s taking this thing beyond your imagination!”……..
      “Innalillahi kace muna ruwa, yanzu haka tana ciki kace?”….
    “You can go in and see for yourself, duk abinda ya faru kuma don’t blame be”…,
     “Naji naji let me start leaving, but what about the girl? Naje base banganta ba, thought kai ka tafi da ita a daura auren”….
    “Wani irin nina tafi da ita? Ina fadamaka ko base banje ba mami tayi attacking dina, kaje dai ka duba inda ka ajyeta, da zaka rufawa kanka asiri daka rabu da yarinyar nan cuz wahala kawai zaka sha a gurin wanchan dan iskan”…..
Cikin kwarin gwiwa sameer yace;
     “Wani irin wahala, I’ll know how to handle everything too, bari dai na tafi yanzu inje in kara duba yarinyar”….
    “Ok, don’t forget to leave abuja today! If not kasan sauran!”…..
     “Yes I’ll, yanzu zanje in duba yarinyar, I’m very sure tana gidan, kawai saina koma US da ita”….
Daga kafada Deen yayi yace;
    “As you wish”…..
Sannan ya juya ya shige batareda yajira amsar sameer ba…..
Harya shiga mota wani dan shakku ya shiga ransa akan maganar da Deen ya fadamasa, idan har mami ta kamasa da gaske kamar yanda ya fada zata barshi ya fito kuwa? Sannan dayace a masa sallama da mai gidan meyasa Deen ya fito inba gidansa bane?…. Sai kuma wata zuciyar tace masa Deen baze maka karya ba, musamman bacewar da mutumin chan yayi yasasa karyata abinda ya fada masa, ya dauki maganganin Deen ya yarda dasu…..
Sai kawai ya tada motar yayi ya bar layin…..
Driving yake da sauri yana tsara yanda ya kamata yabar kasar da yarinyar, kamar ance juyo kawai yaga mutum a zaune a bayan mota yana masa murmushi….
Taka burki yayi da sauri yana fadin;
      “Na shiga uku, dama Deen saida kace zanga abinda yafi wanchan”…..
    
      Yanda ya barsu haka ya tarar dasu suna dan hirarsu sama sama idon Umm kur akan fatima zainab…..
      “Ba nisa nayi ba, wani ne yayi mistaking gidannan da wani gida shine naje na nuna masa gidan dayake nema”….
Deen ya fada ganin mami na bashi wani questioning look….
     “Kaga na tambayeka ne? You can get your mouth shut!”……
Shiru yayi be kara cewa komai ba sai ma juyawa dayayi yana taya Umm kallon fatima zainab dake bacci hankalin kwance…. Ya dade bega wanda yakejin lamarinsa sosai kamarta ba, ya rasa what’s so special about her that he’s feeling that way?, yanzu babban damuwarsa yanda ze taimaka mata as a Doctor ta samu lafiya sannan ya maida ita gurin iyayenta……
Suna cikin wannan hali sukaji ta kwalla wani irin ihu sannan ta tashi a birgice…….
Rige rigen zuwan gurinta sukayi ko tsoron karta musu wani abu basaji….
Umm datafi kusa da itane ta rungumeta tanajin kamar ta mata kuka, it’s so sad ace as young as she is tana battling da mental illness dan harga Allah sun yarda tanada problem a kwakwalwarta kamar yanda Deen ya fada…..
Kamar magic ta nutsu tana jinta a jikin Umm sai kuma ta fashe da wani mugun kuka me taba zuciya, shafa bayanta Umm ta hauyi tana fadin;
      “Shhhhhh! Relax baby girl, stop crying okay?”…
Ta kuwa nitsu sosai dan har cikin zuciyarta takejin wani sanyi tinda matar ta rungumeta dukda batasan wacece ba, amma hakan besa tadaina kukan ba……
Mami na tsaye tana binta da kallon tausayi dan itama imagining kawai take as young as she’s tana fama da matsalar brain?….
Hankalin Umm ne ya kara tashi ganin sai rarrashinta take taki dena kukan, dagota tayi tana kallon cute face dinta ta shiga goge mata hawayen tana fadin;
     “Waya fadamiki pretty ladies na kuka? Yanzu fadamin waya saki kuka in rama miki, kodai Saif ne?”……
Tsaida kukan tayi ta kalli gefe daidai inda Deen yake, batasan sunansa ba amma haka kawai taji alamun shi ake nufi”…..
Suna hada ido tayi yunkurin mikewa tana fadin;
     “Yes shine, wallahi saina kasheka”…… 
Ta fada cikin muryarta me mugun sanyi da dadi….
Mami data fara suspecting ko dai akwai abina Deen ya mata ta riketa tana fadin;
     “Meya miki dear fadamin, I promise you zan tayaki hukuntashi!”…
     “Kasheshi zanyi yanzu, I will kill you”…. 
Fatima zainab ta fada tana kokarin kwace kanta….
Shiko Deen tuni ya dade da tafiya wata duniyar akan muryarta, shi baya ma jin maganar zata kashesa da takeyi, all he hear is her melodious voice that is ringing in his brain, kana kallonshi kaga wanda is so lost in thought, sam besan wainar da ake toyawa ba…
Nufota ya shigayi cikin rashin sanin abinda yake fada yace;
     “Dan Allah recite Quran again for me kamar wanchan ranar, you have no idea how it has been giving me sleepless night, it’s worth listening”….
Mami ce ta daka masa tsawa me rai da lafiya ganin kamar shima ya fara samun mental problem din yazo yana musu sambatun da basu gane ba bayan suna fama da yarinya tana dagewa akan saita kasheshi shikuma dake wawa ne yana nufota, tace;
      “Get out!!!”….
  “She’s not okay, I need to treat her”…..
Ya kuma fada absentmindedly….
     “My friend get out of this room now!!!”…..
Fita yayi da sauri jin tsawar har kansa, sai kuma ya jingina a jikin kofar yana sauraran maganganunsu….
       “Ya isa dearie, kinga yariga ya fita, I promise you bazai dawo ba badai shine bakisan gani ba?”….
Cewar mami tana zaunar da fatima zainab kusada Umm, sai suka sata a tsakiya….
Daga kai tayi tace;
     “Idan na kuma ganinshi saina kasheshi, why will he kidnap me, yasan wacece ni kuwa, wallahi I’ll deal with him!”….
Kallon juna Umm da mami sukayi suna jinjina alamarin, mami ta daure tace;
     “Be kyauta ba gaskiya, amma ba gashi munzo ba, ki kwantar da hankalinki”….
Shiru tayi batace komai ba amma haka kawai takejin zuciyarta ta aminta dasu….
       “What’s your name?”…..
Cewar Umm tana shafa bayanta…..
      “Fatima zainab! You?”…
Haka kawai ta samu kanta da jin dadin conversation dasu itada maganar arziki bata hadata da mutane….
     “My name is jamila, you can call me Umm, but dear your name sounds complicated, ya akayi kike bearing two real names?”….
        “Bansani ba!”…
Ta fada da iyakar gaskiyarta……
Shiru taga sunyi sai kuma taji wani iri tana tinanin kodai basujin dadin abinda tace bane, a karo na farko kenan a rayuwarta data farajin wani iri akan yiwa babba rashin kunya, cikin rashin sanin abinda zatace dan harga Allah she’s mannerless tace;
      “Kunji haushi ne?, so kuke na muku karya?”…
Dariya Umm tayi tana jan kumatunta tace;
     “Not at all dear ai nasan baki sani bane, kawai I thought you need some rest shiyasa nayi shiru”…
     “Okay, ita wannan ya sunanta?”…
Ta fada tana nuna mami da take binta da kallon ikon Allah ganin yanda take magana anyhow……
      “I don’t know if to call her your namesake or what tinda suna biyu gare ki, anyway she’s anty fatima, you can call her mami”…..
Dan jim tayi tanajin wani iri a ranta because she feels like this is the first time da take having conversation da wanda bata yiwa rashin kunya ba, hakanan taji kuma bataso maganar tasu ta tsaya”….
      “Toh shikuma wancen dan iskan waye?”…..
Ta fada ko a jikinta…….
Rasa wanda zeyi magana a cikinsu akai dan maganar ta dakesu, gashi su basusan meya faru a tsakaninsu ba bare su kareshi….
Murmushi me kayatarwa Deen dake bakin kofa yayi yana jin duk abinda suke cewa, honestly he never thought she can be this sweet dukda yasan babu manner da respect a yanayin maganarta amma wannan ce magana me dadi daya farajin tayi da wani dukda bashida tabbacin haka take magana…. Kada kai yayi yana murmushi at the same time a ransa yana fadin ‘wannan melodious voice bata dace da masifaffiya irinta ba!”…….. 
      “Ya kukayi shiru, ko baku gane wanda nake nufi bane, wanchan kidnapper din fa, ina magana kunamin shiru ko, wallahi idan nayi zuciya I’ll never talk to you people again forever!”…..
Ya sake tsinto muryarta tana fadin hakan, dariya yayi sosai ganin zata nuna musu halin tin baaje ko ina ba….
Ruko hannunta Umm tayi tana murmushi dan ita ma harta fara fahimtar yarinyar nada issue medically and it has to do with ego ko kuma she’s a spoilt brat irin yarannan masu ji da kansu da iyayansu suka lalatasu, shafa face dinta tayi tana fadin;
     “Ba kin kulaki mukayi ba, bamu gane wa kike nufi bane, and I guessed you misunderstood him, he’s not a bad person”….. 
Janyewa tayi tana bata fuska cikin wani irin murya tace;
      “Zan wuce, ana jirana”….
       “Wa yake jiranki?”….
     “Mijina”…
Da sauri Deen ya banko dakin yana fadin;
    “This is not her voice, wallahi ba ita bace!!”….
~Unique barakancy~

Back to top button