Uncategorized

Wace Ce ita Chapter 20 Complete Novel

 

WACE CE ITA⁉️ (WHO IS SHE⁉️)

Unique Barakancy

   TWENTY-ONE📍

             Cikin bacci me nauyin daya dauketa takejin wani bakon al’amari da bata gane kansa ba, sam ta kasa tantance wani yanayi take ciki hasalima bata gane meke faruwa ba, kamar dai lips dinta ake tabawa tadai rasa me takeji gashi ta kasa motsawa, haka ta daure tanaji tana gani aka cigaba da mata abinda akaga dama akan lips, jin kamar an shaketa dan har lokacin bata gane abunda yake faruwa ba yasa ta kasa jurewa ta fara mutsu mutsu tana kokarin farkawa amma kuma saita kasa…… 

Jin motsinta ne yasa Deen janyewa da sauri yana ayyana irin karfin jininta, wannan abun da sameer ya shaka mata sai mutum yayi 24hrs be farkaba inba allura aka masa ba shine ita take motsi within few hours? It’s surprising!, sai a lokacin kuma yagane aika aikan dayayi,  meya hadashi da kissing yar mutane? Shida yakeso ya taimaketa ya fitar da ita daga gidan kafin wanchan dan iskan ya dawo shine ze bada kansa? dauke idonsa daga kan fuskarta yayi yana istigfari a ransa….. 

Shafa lips dinsa daya jike yayi yanaji kamar har lokacin yana cikin bakinta, sai a lokacin yayi realizing ashe babu mask a fuskarsa, dube dube ya shigayi har ya gano mask din a kasan gado, mamaki ne ya kamasa dan ko zaa kashesa besan sanda ya cire mask din ba, he was lost indeed, shima kenan da ba ruwansa da mata couldn’t control himself, toh inaga in sameer ne mayan mata? Kai anya ma be tabata ba? Wani mugun bacin rai ne yazo masa dan haka kawai yaki yarda sameer betaba yarinyar ba, koma dai menene yayiwa kansa alkawari ba wanda ze kara tabata, inta farfado kuma ze tambayeta WACECE ITA? Sannan ya sadata da iyayenta ya kuma basu shawara su mata aure kar a lalata musu yarinya, dan sameer ba kyaleta zeyi ba inba gani yayi tayi aure ba, ze kuma gaya musu karsu bawa khaleel dan duk basu dace da yarinyar ba, gwara su nemi wani nitsattse su ba……

Zagaye dakin ya shigayi yana tinanin mafita dan gaskiya bayaso sameer yazo ya samesa be fitar da yarinyar daga gidan ba, toh amma ina ze kaita? “Ka kaita gidanka mana” wata zuciyar ta fada masa haka, gyada kai yayi kamar yana magana da wani, ya yarda da shawarar kaita gidansa dari bisa dari dan it’s the best solution for him tinda ba wanda yasan gidan a friends dinsa, wata zuciyar ce ta kuma ce masa “to amma mami ta sani ai, what if she come looking for you?”….. Girgiza kai yayi yana fadin “no zan fitar da ita daga gidan kafin mami tayi tinanin ina chan”…. 

Wani lissafi ya kumayi yaga alamun komai ze tafi masa daidai , abinda zeyi shine ya kai yarinyar gidansa ya ajye sai ya dawo ya renawa sameer hankali yace shi dayazo bega kowa ba…. “Yes” ya fada yana kokarin daukarta…..

Daukarta yayi kamar wata yar baby a zuciyarsa yana fadin gata dai a haka kamar a cike amma she’s weightless,  kodai batacin abinci sosai ne?, tsaki yaja yana tamabayar  kansa ina ruwansa?….

Carefully yake rike da ita gudin having body contact da ita amma duk da haka be tsiraba dan yanajin dumin jikinta sosai kamar wanda yake rungume da ita, haka ya daure ya karasa bakin mota da ita….

Bude gaban motar yayi ya zaunar da ita still tana nan a sumen da take, sannan ya kwantar mata da sit din sosai yanda zataji dadin kwanciyar ya kuma gyara mata zaman hijabinta…..

Bude gate yayi kasancewar babu me gadi a gidan tinda ba wani zama suke ba, ya fita da motar waje sannan ya kara dawowa ya rufe gate da gidan gabadaya ya nufi mota…..

Kamar a mafarki yaga mutum ya bude masa gaban mota harda zira hannu yana kokarin zaro ta…….

Saida jijiyoyin wuyarsa suka fito tsabar bacin rai, toh shikuma wannan dan rainin hankalin daga ina?….

Fincikosa yayi da karfi sannan ya hankadasa chan gefe, cikin bacin rai da takaici Deen yace;

       “Who the hell are you da kake kokarin zaro min mata daga mota? You must be very stupid”….

Tasowa yayi da sauri yana kakkabe jikinsa, cikin jin haushi shima yace;

       “Kai ya kamata in tambaya ina zaka kaimin mata, dagayin tafiyar kwana biyu shikenan saiku sata a gaba?, bame tabamin ita ya zauna lafiya wallahi!!!”….

     “Ji wani shashasha mahaukaci, a masallacin ubanwa aka daura muku auren da zakace matarka ce, kai dalla ware dan wallahi ka bari na fusata sai na zubar maka da hakoran gaba duka, ba kunya ba tsoron Allah kazo kuna claiming matar mutane!”….

Deen ya fada yanajin kamar ya daddalla masa mari, saidai bata wannan yake ba, burinsa kawai ya gudu da yarinyar kafin sameer ya dawo, gashi wani dan iska yazo ze rena masa hankali ya bata masa lokaci …..

       “Idan kana san rayuwarka ka bani matata mu tafi”…..

Deen besan sanda ya zabga masa wani wawan mari tsabar bacin rai jin ya kara maimaita kalmar matarsa ce, ko a gidan ubanwa aka daura musu aure oh……..

Wata muguwar dariya ya fashe dashi yace….

     “Ni ka mara? Hhhhh karshen ka yazo yaro”…

Wani marin ya kara masa dan ba karamin haushin dariyar yaji ba, sannan cikin masifa yace;

     “An kara maka wani, do your worst karamin dan iska kawai, now bani hanya!”….

Yana fadin haka ya shige mota yasa lock, kokarin tada motar yayi mota tace to tadani kagani, babu kalan dabarun da beyiba amma shiru mota taki tashi, jin yana juyo dariyar dan iskan chan ne yasasa whining glass dan yaga meyake yiwa dariya….

Yana bude glass din ko yajuyo shi yana fadin;

        “Hhhhhh kai ka dauka zaka mareni har so biyu kaci bulus? Inaaa, ai in fadamaka kome zakayi motarnan bazata tashi ba, bama motar ba babu inda zaka iya motsawa daga nan inba bani matata kayi na tafi ba”…..

Wani agogon sameer me tsada da yake cikin motar Deen ya dauka ya cilla masa a goshi, a take goshin ya fara zubar da jini, murmushi Deen yayi yace;

        “Ka kara kiranta matarka a gurin nan wallahi saina kasheka, na kuma kashe banza a banza! Wato kai shedani ko? Toh ko bude idonka da kyau kaga yanda zan bar gurinnan da ita akan idanunka, duk shaidancin da kakeji dashi na fika wallahi”……..

Sai kuma ya kalli fatima zainab ya harareta yana fadin;

     “Ashe a cikin kwashe kwashen naki harda shaidani? Ba dole kita abu kamar mara hankali ba, zamu gamu ne in kika farka, saina saitaki da kyau kafin in kaiki gun iyayenki!”..

Sai ya maza ya zuge glass dan bayason jin abinda wanchan wawan zece, wani cassette din Quran yasaka  ya kunna suratul baqarah yayi bismillah ya sake tashin motar, cikin ikon Allah ko motar ta tashi, figarta yayi a guje ya bar wanchan da sakekken baki……….

         Kuka yakeyi sosai cike da nadama, tsugunawa yayi har kasa yana basu hakuri akan su taimakeshi su rufawa masa asiri….. 

Mami kuwa har lokacin bata gama dawowa daga shock din data shiga ba, she always know Deen as a stubborn person amma bata dauka rashin jinsa ya kai haka ba, wani kalan hatsabibin yaro ne Allah ya bata haka? Like how could he even think of this? To ina ya tafi haka…..

Dawowa daga tinanin tayi jin Umm na fadin;

      “Idan zaka fadamin gaskiyar abinda ya faru na kumayi bincike na tabbatar gaskiya ne, I’m assuring you that abinda ze sameka”…

Da sauri cikin kuka yace;

      “Wallahi zan fadamiki, bazan yi karya ba”…

     “Good, now tell me how you got here, in full details!”…..

Nan ya shiga basu labarin yanda wani ya hadasa da sameer, da irin matsalolin rayuwar da suke ciki, da rashin lafiyar mahaifiyarsa wanda shine main abunda yayi pushing dinsa ya karbi offer din, da irin alkawarikan da sameer ya masa idan ya gama aikin, har zuwa yanda aka barsu sukazo inda Deen yake, sukashi anan su kuma suka fita…… 

Kamar hadin baki Umm da Mami suka sauke numfashi dan harga Allah sunji tausayinsa saida as an interrogator bazaka gane hakan ba akan fuskar Umm……. 

       “For how long sukace zakayi replacing dinsa”

Umm ta fada with a serious look…

       “For two days sunce maximum three”…

  “Ohk ina suka ce zasuje?”.

“Basu fadamin ba wallahi”…

    “Da kuka shigo bakaji sunyi wani magana ba kafin su fita?”…

     “Akan wata naji suna magana, kamar gurinta suka tafi”…

    “Wata?!”….. 

Mami tayi interrupting tsabar mamaki…

     “Didn’t you over heard their conversation akan location din wacce zasuje”…

Umm ta cigaba da tambaya

 Cikin rawar baki da tsoron da har lokacin be fita ransa ba yace;

     “Banji ba gaskiya, kamar dai budurwan dayan ce, wanda yake gurin nan kamar rakasa yayi”….

Tafi kai Umm tayi tana kallon mami tace;

     “Shit! Kinsan Allah yaya haka kawai naji hankalina be kwanta da visiting din da kikace abokinsa ya kawo masa ba, see the way they fooled us dan Allah!”…..

      “They fooled us absolutely, amma karki damu we’ll get them soon, sai sun gane shayi ruwane, I’ll make sure I deal with them mercilessly! Sameer ya bani mamaki, ina masa kallan nittsatse kamar yafi Saifuddeen hankali ashe duk kanwar jace?”….

Mami ta fada cike da takaici…. 

       “Ai ko ni this time around bazan ragawa Saif ba, he’ll see the very other side of me!!”…

Umm ta fada tana daukan mask din data fuzge a fuskarsa, mika masa tayi tace;

       “Wear dan in wani ya ganka a haka you’re in big trouble! Wait kasan nature of crime dinsa ma kuwa?”….

Girgiza kai yayi alamun be sani ba

       “Ah lallai your dumbness isn’t in this world, how could jump into a job like this without asking for the person’s crime? Imagine a hada baki da yan gurin nan azo a kashesa anan inda kake do you think they’ll give you the chance to claim yourself”….

Cikin kuka ya shiga kada kai dan ba karamin ahigarsa maganarta tayi ba….

      “Toh an kashe banza dan shi bashi da asara and I’m very sure ko addu’a bazena maka ba dan mantawa zeyi da kai, hankali kwance ya cigaba da rayuwarsa, so don’t ever try this stupid act okay?”..

       “Bazan kara ba, nagode nagode mama”…..

Ya fada yana cigaba da kuka

        “Give me your parent address da address din hospital din da mamanka take”…

Da sauri ya fada mata komai…..

     “Ok, I’m assure ya baka tips din da mutanen gurin bazasu gane ba, so keep on with it kafin mudawo, karka damu we’ll get you out of here soon!”…..

Bata jira amsarsa ba taja hannun mami suka fita dakin…. 

Cikin siyasa suka tamabayi masu gurin yau karfe nawa aka ba Deen waya domin sugane koya tafi dashi ne, bayani suka musu sosai har time din da aka karbo wayar, godiya suka musu suka tafi dan sun riga sun gane abinda suke san ganewa……….

Suna fita mami ta kalli Umm tace;

     “Nasan inda zamu samesa, muje!!!”…..

            Saida yayi nisa sosai sannan ya rage gudun daya keyi, tuki yakeyi cikin nitsuwa  minti minti yana dagowa ya kalleta yana examining dinta, har lokacin karatun qur’ani na tashi a motar…… 

Daidai wani katon mansion ya tsaya, horn yayi akazo aka bude masa ya shiga da sauri…… 

Fadan irin kyawun gidan bata lokaci, duk yanda zaa siffanta gidan baze fadu ba, ba karamin achievement bane ace at his young age yanada mansion kamar haka dako government house albarka, wani in aka fadamasa gidan mallakin Deen ne baze yarda ba….

Parking yayi ya fito da ita a hankali yana dagawa me gadi hannun alamun ya dakata basai ya karaso sun gaisa ba…….. 

A kan three sitter ya kwantar da ita yana kallonta, so yake ya koma base gudun kar sameer yazo be gansa ba, sai ya masa karya yace be ganta ba toh amma gaskiya yana tsoron barinta ita kadai musamman idan ya  tina encounter dinsu da wanchan mahaukacin, wannan wani kalan dilemma ne? Yanzu wanne zeyi a ciki?….

Ya dade yana sakawa da kwancewa be zabi wanda ya kamata yayi ba, karshe dai yaga gwara ya zauna da ita kar wani abu ya sameta kafin ya dawo ko wanchan dan iskan yazo ya dauketa, inyaso daga baya komai zasuyi da sameer saidai suyi……

            Motar Deen na barin gurin sameer ya karaso, taba gate din gidan yayi ya jishi a rufe, mamaki ne ya kamasa amma be damuba da yake yanada extra key a hannu, be kawo komai ba ya bude gidan ya shiga…. Be bi takan neman Deen ba ya tafi dakin daya ajyeta straight, wayam yaga ba kowa, still be karaya ba ya shiga duba sauran dakunan gidan ko yamanta ya chanja mata daki saidai ko alamunta begani ba…

Ba karamin shiga tashin hankali yayi ba na rashin ganinta, gashi bega Deen ba, toh kodai Deen ya tafi da ita wajan daurin auren ne? Wai ko surprise ze masa ya dawo masa da ita a matsayin matarsa, tinanin hakan ne yasa hankalinsa ya kwanta sosai, duk wata damuwar dayazo da ita gidan yaji ta kau, ya kara samun kwarin gwiwar bijirewa mahaifinsa akan abinda yazo masa dashi, sam beji dadin haduwarsu ba dukda bawai yanajin dadin haduwarsu bane dama saidai wannan is worse, tinda yaje yake masa masifa ta inda yake shiga batanan yake fita ba, karshe kuma ya basa umarnin yin wani aiki me wahala da yake ganin ko duniya zasu taru akansa baze iyaba, Hakadai ya amsa masa zeyi badan zeyin ba……

 Wayarsa ya fito da ita da niyar kiran Deen sai ya tina Deen be fito da waya ba, kishingida ya danyi yana jiran dawowar Deen da good news dan yasan ba shakka shiya tafi da yarinyar…….

 

          Haka Deen ya zauna yana kallonta kamar wanda aka bawa ajiyarta, har lokacin mamaki yake wai shine haka akan mace, macen ma irin wannan da sai a hankali? Yanzu idan wani yaji ai sai y masa mummunan fahimta ya dauka sonta yake, shi ko me zeyi da wannan da daga gani zata basa ciwon kai, bama wannan ba meya hadashi da yarinyar da wa’yanchan mahaukatan ke hauka akanta tsabar rashin class, shi in soyayyar zeyi ai sai ya nemo yarinyar da shine ze zama first and last love dinta, bayasan mace me tarkacen masoya, sannan kuma bayasan reni so gwara ya dauko mace age mate dinsa atleast ta kai 30 ba irin wannan ba da daga gani she’s still a teenager (haba mallam deeni yada jumping into conclusion🙄) tazo tana basa wahala….

Ganin lokacin sallah yayi ya sasa tashi ya dauro alwala, a nan parlourn ya tada sallah a nitse…..

Samun kansa yayi dayi mata addu’a duk sujjadarsa kamar wanda aka bawa kwangilar mata addu’a, abun dariya kuma addu’a biyu yake maimaitawa, Allah ya shiryeta da Allah ya bata miji nagari yaketa fadi harya idar da sallah. Still be hakura ba ya cigaba da mata addu’ar ko bayan ya idar da sallah……

Yana cikin wannan hali yaji ‘tasssss tassss tasssss’ alamun fashewar abu me glass, mikewa yayi da sauri ganin ta dau center table ta buga akan tv, a take tv’n ya fashe kuwa, rasa abunyi yayi ya tsaya yana kallon ikon Allah, wurgi take da duk abinda ta samu a parlourn kamar mahaukaciya sabon kamu, tsabar shock ya kasa motsi bare ya hanata, toh yaushe ma ta farka? Wannan wace kalan yarinya ce haka?….

Ganin ta nufi dining ya daka mata wani mugun tsawa yace;

       “Ke wata irin mahaukaciya haka? Daga taimakonki shine zaki zo ki illatamin gida, maza ki jiwa kanki ciwo mahaukaciya kawai”………

Fasa zuwa gurin dining din tayi ta tawo inda yake da gudu, chakumeshi tayi cikin masifa tace;

       “Kaine babban mahaukaci for kidnapping me, akanme zaka sato ni ka kawoni nan, I’ll not spare you, saina kasheka!!!!”……

Dariya ya shigayi tsabar mamaki, wai ita wannan masifa takeyi a haka da bedroom voice, lallai ba kanta…….

Hannun data chakumeshi ya cire daga jikinsa yana bin hand gloves dinta da kallo…… 

Duka da naushi ta fara kai masa ta ko ina a jikinsa da karfi ko Allah zesa taji radadin da zuciyarta ke mata ya ragu dan tagama yarda mugune shi tinda harya saceta, ta kuma ci alwashin saita nuna masa he messed up with the wrong person…..

Ko gezau beyi ba saima gyara tsayuwarsa da yayi yanda zataji dadin dukansa da kyau, ya kuma gane ta dauka shiyayi kidnapping dinta ne….. 

Ganin dukan baya mata yasata zura a guje ta tafi kitchen ta dauko wuka da niyar chaka masa ta wuta dan haka kawai takeji kamar ana zugata ta kashesa…..

Harta dauki wukar taga gwara ta fara yiwa kitchen din lahani tukunna, nan tashiga masa banna sosai a kitchen din, babu wani abu me glass a kitchen din dabe fashe ba… 

Jin karar sabon fashe fashe ne ya kara tabbatar masa mahaukaciya ya dauko, bedroom dinsa ya shiga da sauri ya hado allurar barci me karfi ya zira a aljihu, gwara ya mata allura kawai ya huta da wannan masifa, haka kawai daga taimako ya kwasowa kansa masifa…..

Bayan ta gama da kitchen din ta fito hannunta rike da wukar tana nemansa a parlourn, ganin bata gansa bane yasata cigaba da fashe fashenta, har dining din daya hanata zuwa dazun saida ta masa lahani yanzu, saida ta tabbatar ta illata komai na parlourn sannan ta fara nemansa shima ta kasheshi ta wuce……..

Fitowarsa daga dakin yayi daidai da juyowarta daidai center dakin daya fito, kama haba yayi yana kallon millions din data masa asara kamar a kasa ake tsinto kudin….. Sai yaji batasu yake ba, he’s after her well-being karta jiwa kanta ciwo…..

Gadan gadan ta nufoshi da wuka boye a bayanta, tana zuwa ta chaka masa… 

Saurin kaucewa yayi wukar ta dan yankeshi a hannu take hannu ya fara zub da jini….. Rasa abinyi yayi kawai ya rungumeta yana kokarin zare wukar a hannunta….. 

Wani bakon lamari ne ya ziyarcesu duka kowa da abinda yakeji, ita ji tayi kamar an zare mata laka jikinta yayi sanyi sosai amma batadena mutsu mutsu ba, shikuma Deen laushin jikinta ne ya tafi da imaninsa dan Allah ya sani karfin hali yayi ya samu ya zare wukar daga hannunta, ya kankameta kam kamar wacce zaa kwaceta…..

Murya chan kasa kamar mejin bacci yace;

      “Ki nutsu dan Allah, karki jiwa kanki ciwo plssss”

Bata kulashi ba ta cigaba da fizge fizge burinta kawai ta kwace kanta daga wannan tight hug din dolen….

Tana cikin wannan hali taji an dage mata hijab, bata gama ganewa ba kuma taji kamar an chaka mata abu, kuka ta fashe dashi sosai dan a rayuwarta in akwai abinda ta tsana toh be wuce allura ba, bare wannan allurar batasan ta mecece…. 

Jin kukanta yake har cikin ransa saidai shine best solution daze taimaki situation dinta, patting back dinta ya shigayi sai bata hakuri yake ba tareda yasan abinda yake fada ba, suna cikin wannan yanayi yaji ana taba kofar parlourn !!!!!!…….

Unique Barakancy

Back to top button