Uncategorized

Wace Ce Ita Chapter 16 Complete Novel

WACE CE ITA⁉️ (WHO IS SHE⁉️)

Unique Barakancy

    SIXTEEN📍

      Shigowar daddy yayi daidai da faduwar khaleel… Kokarin taroshi yayi saidai ina yariga ya kai kasa,cikin tashin hankali daddy ya karasa inda khaleel yake zuciyarsa kamar zatayi tsalle ta fito tsabar tashin hankali,kowa na gidan yasan khaleel ne weak point din daddy,irin son da daddy yake nuna masa abin har tsoro yake bawa yan gidan…….

Ruwa ya shiga yayyafa masa amma abu kamar wasa khaleel yaki farkawa,hakannne yasa sukayi rushing dinsa zuwa asibiti… Ita kanta momma ba karamin rudani tashiga ba, ace daga magana?,wani irin abu ke shirin faruwa da khaleel ne? Gashi akan yarinyar data tsana? Kai inaaaa!!!…

Emergency aka nufa da khaleel while momma da daddy na reception suna jira,gabadaya sun kasa nitsuwa,ko zama sun kasayi sai kai da kawowa sukeyi……

Chan daddy ya kalli momma yace 

    “Meya samesa da har ya samu attack? Kuma yaushe ya dawo?….

     “Shigowarsa part dina kenan,ko gaisawa bamu gamayi ba naga ya fadi,bansan yaushe ya dawo ba”

Momma ta fada tana marairaicewa…..

      “Are you sure ba abinda aka masa? Dan nasan baya samun attack saida dalili”…

     “Ba abinda aka masa”….

Shiru ne ya biyo baya a tsakaninsu sai kaikawon da suka cigaba dayi kowa da abinda yake yawo a ransa…

Ba karamin wahala likitoci sukasha ba kafin su samu bugun zuciyar khaleel ya daidaita,a hakanma zata iya birkicewa any time……..

Suna cikin wannan halin Doctor ya fito da sauri daga emergency ward din,da sauri suma suka nufesa, sai ya musu nuni da su biyoshi ciki kawai…..

Rige rigen karasawa gurin khaleel sukayi,karshe dai daddy ne ya fara zuwa,kama hannunsa daddy yayi yana masa sannu…….

      “Dan Allah momma ki fadamin inda take plssss”

Suka tsinto khaleel yana fadin haka cikin muryar marasa lafiya…. 

Wani mugun kallo daddy yayiwa momma jin khaleel nata sambatu da alama kuma momma tasan komai duk da bai wani gane me yake nufi ba…. 

Sake ruko hannun khaleel yayi yace…..

     “Son, it’s me your daddy, tell me what you want, I promise to get it a ko ina yake a duniyarnan, so tell me?”…..

Dan kallonshi khaleel yayi kamar me neman tantance waye… Chan kuma sai ya ruko hannun daddy sosai yana fadin….

      “That pretty girl, meyin shara da daddare, inaso in ganta, momma tace bazan kara ganinta ba, daddy pls help me”…… 

Cikin rudani daddy ya kalli momma da alamar tambaya, a iya saninsa shi baisan wacce take shara cikin dare a gidanba, toh kodai gamo khaleel yayi ne?…..

Ganin kallon da daddy yake mata ya sata saurin cewa…

      “Nima haka ya dinga damuna wai yanaso ya ganta, gashi ni bansan wa yake nufi ba,Allah yasa dai ba aljanu bane suka shafesa dan babu meyin shara cikin dare…….

Gyada kai daddy yayi dan shima yafi tinanin hakan, inko aljanune suka shafi khaleel to tabbas sun shiga uku, abun tashin hankalin kuma abun na taba ciwonsa wanda tashin ciwonsa kuma barazana ne ga rayuwarsa, su yanzu ta ina zasu fara toh?……. 

Maganar khaleel ce ta dawo da daddy daga dan gajeran tinanin daya shiga….

       “Ba aljana bace, mutum ce, momma tasanta kuma, kawai bataso ta fada ne kuma…….

Sai numfashinsa ya fara seizing,nan da nan likitoci suka rufu akansa,oxygen sukasa masa sannan suka masa allura….. Fashewa da kuka momma tayi tanajin kamar ta fadi gsky dan abin khaleel ya fara bata tsoro,daddy ko girgiza kai kawai yake ya rasa tinanin mai zaiyi, shidai yafi yadda da khaleel gamo yayi har yake tinanin momma tasanta…… 

Doctor ne ya umarcesu da su biyoshi office sannan anaso abar khaleel shikadai…….

Zama sukayi suna jiran abinda Doctor zaice….

Gyaran murya Doctor yayi ya fara musu bayani…

      “Maganar gsky danku is in a critical condition because heart rate dinshi is very high,it’s more than 130 beats per minute which is very dangerous,normal rate should range from 60-100 beats,kunga ko akwai matsala sosai, kuyi kokari a masa abinda yakeso tin kafin heart dinsa yayi blowing!”…….

Kallon juna momma da daddy sukayi suna zaro ido,suka daure dai suka amsawa likitan sannan suka fita…. 

Suna fita daddy ya kalli momma yace……

    “Kinji dai abinda Doctor yace, tin wuri in kinsan wacce yake magana akai gwara ki fada tin kafin ya mutu”…… 

Dagewa momma tayi akan gamo khaleel yayi ita batada masaniya akai, yes tasan ciwon khaleel na matukar damunta but that doesn’t mean ta barsa yayi settling for less, zata kuma dage da addu’a Allah ya yayemasa wannan abu daya dorawa kansa, amma kome za’ayi bazata nuna tasan wacce yake nufi ba…… 

Sai bayan azahar khaleel ya farka,yana farkawa ya birkice musu sai an kaishi gida,shiyasan tananan kuma ze ganta inyaje….

Ba yadda momma da daddy da Doctors basuyiba akan khaleel ya zauna ya kara samun lafiya,amma ya nuna sam baze zauna ba..  Sunaji suna gani suka rankaya suka tafi gida…..

Ko gama parking daddy beyiba khaleel ya fita daga motar,direct part din mama ya shiga,luckily ya kuma ganin Imaan da Husnah a zaune a parlour,baice musu komai ba ya kamo hannayensu ya fita daga part din,sudai binsa kawai sukayi da ido….. 

Part din momma yayi dasu, ya tarar da momma da daddy suna tattaunawa…. Kallon su imaan yayi yace

     “Kunce min a part dinnan take, toh ku fito min da ita!”…..

Zuba mishi ido sukayi duka banda daddy da ransa ya baci ganin kamar dagaske ba gamo khaleel yayi ba momma kuma bataso ta fadi gaskiya,su husnah ko rasa abinda zasu ce sukayi….

Daddy ne ya hada rai cikin tsawa yana nuni dasu husnah yace….

    “Oh ashe kuma kunsan wacce yake magana akai?”sannan a tsawace yace…..

        “who is that?”….

  A tsorace husna da imaan sukace…

       “Kamar fatima zainab yake nufi daddy”…..

A take gaban daddy da momma yayi wani mugun faduwa,ita momma saboda asirinta karya tonu na karyar da tayi, shi kuma daddy saboda wani dalili nasa daban….. 

  Da sanyin muryar daddy yace…..

    “Ina fatima zainab din take?”  Ya fada yana kallon momma…..

   A firgice momma tace bansan inda take ba kuma ba ita yake nufi ba!”….

      “Ita nake nufi daddy”… cewar khaleel batareda da tabbacin ko ita din bace…..

     “Koma ba ita bace  a nemota duk inda take a gidannan yanzu!, Imaan ku tashi ku nemo min ita!”…

Tashi sukayi da sauri suka shiga dube duben inda zasu ganta……

Babu inda basu duba ba amma shiru kamar baayi halittarta ba…. 

Dawowa sukayi suka fadawa daddy basu ganta ba….

Jin haka khaleel ya tashi da sauri ya shiga nemanta shima,haka yagama dube dubensa bai ganta ba, sosai ya daga hankalinsa ganin sun nemeta sun rasa…. 

Hakanan hankalin daddy ya kasa kwanciya da momma,yaki yarda batasan inda yarinyar take ba duk da bazaiso ita khaleel yake nema ba,saidai khaleel kamar rayuwarsa yake  babu abinda baze iya  masa ba…..

      “Koki fito da yarinyarnan ko a bakin aurenki wallahi!!”….

Daddy  Ya fada a hassaale..…..

Zaro ido momma tayi tace…..

     “Alhaji wani irin magana ne haka a gaban yara?, nifa bansan inda yarinyarnan take ba”…..

    “Kindai ji abinda na fada miki,na baki 10mins kuma!”…..

Ba karamin rudani momma tashiga ba,wannan wani kalan masifa ne?, itafa matsalarta daya da daddy abu kadan sai yace a bakin auranka, Itako da wannan aure ya mutu ai gwara ta fito da ita kawai inyaso daga baya sai tasan yanda zatayi……

Haka akayi kuwa cikin borin kunya ta dauko makullin dakin ta mikawa khaleel,sannan ta nuna masa dakin…… 

Khaleel baice komai ba ya nufi dakin,hannu na rawa ya bude ya shiga da sauri….. 

And there he saw her lying helplessly, ko numfashi batayi alamun dai ta suma,he couldn’t help it but held her tight,from that moment, that very moment he knows every single breath of his depend on her…..

   “This is all I know about Fatima zainab”….. Khaleel ya fada yana sauke numfashi kamar wanda yayi tsere…….. 

Sameer daya zama speechless ya kurawa khaleel ido batareda yace komai ba……. 

         Tuki suke da dan sauri motar mami na tsakiyar ta police dake biye dasu kasancewar Deen motarta aka barshi ya shiga saboda matsayinta na ‘Chief Justice’…….

Driving mami take cike da damuwar abinda Deen ya dauko musu, Allah yasani Deen is her beautiful distraction, of course beautiful tinda hannunka baze rube ka dauka ka yarba…..

Shiko gogon hankalinsa kwance kamar ba station suka nufa ba,shi damuwarsa daya yanda ya tafi ya barta batareda ta farka ya tambayeta ‘WACECE ITA’ ba, gashi yanzu duk ta hargitsa masa lissafi,daya rufe ido ita kawai yake gani da beautiful face dinta that is treacherous,sai yaji dama bai kalleta ba da kila yana cikin peace yanzu….. 

     “Nace what crime have you committed again?”…….

Ya jiyo muryar mami na fadin haka,sai a lokacin ya dawo daga duniyar tinanin daya lula…..

Cikin rashin sanin abinda zai fada yace….

      “Bangane ba mami?”……

Hade fuska tayi sosai tace…..

     “Zaka gane idan ka tsinceka a cikin cell suna jibgarka”……

     “Tabdi jam! Wa zaa jibga? Ni? Allah ya kiyaye, wallahi sai na zubarwa duk wanda yayi gigin tabani hakora!”……..

      “You see your issue ko? Stubbornness! Bansan a ina ka kwaso wannan mugun halin ba! Well baze wuce ubanka ba!”…….

Shafa gemunsa yayi yana smirking yace….

     “Kunfi kusa(haka yake fada duk sanda kowannensu ya zagi daya a gabansa danshi ya kasa gane meya hadasu da suke rashin jituwa haka), but seriously mami banyi komai ba, I don’t know even know what they’re accusing me of”..

     “What ever it is zamuji in munje, Idan kuma kasa naji abinda yasa zuciyata ta buga na fadi na mutu, sai ka zuba ruwa a kasa kasha tinda haka kakeso dama!”…. 

Wani iri Deen yaji a ransa musamman datace haka kakeso dama sai yaji wani guilty feeling ya kamasa,marairaicewa yayi kamar wanda ake forcing dinsa yayi magana yace….

     “I’m sorry”…..

Bata kulashi ba duk da irin mamakin data shiga akan hakurin daya bata dan tasha masa fada yayi tafiyarsa ya barta a gurin ko a jikinsa…… 

Shigowarsu station din yayi daidai da shigowar Dad da securities dinsa….  

Kallon mami Dad yayi yana mamakin ya akayi tazo? Kodai Deen yana gurinta a abuja dama,tabbas biri yayi kama da mutum inba hakaba meya hada Deen da zaman abuja, wato itace ta janyeshi duk neman da yake masa da tsare likitocin da basuji ba basu ganiba na watanni akan sai yaga danshi ze sakesu, ashe dan yana gurin uwarsa…. A take zuciyarsa ta hau ta zauna akan lallai Deen yana gurinta duk wannan neman dayake masa…… 

     Yan sandan basu bawa kowa damar magana ba suka fara bayanin abinda ya faru….. 

     “He’s accused of criminal robbery , sannan ya kashe mutune uku mun  kuma tabbatar da haka ne ta dalilin thumbprint dinsa dake kan gun din dayayi kisan, minutes before he had an accident”….

     “What?!! This must be a joke!” 

Mami ta fada a zafaffe ….. 

Taran numfashinta dad yayi kamar wanda yake jira tayi magana yana fadin…..

     “Dole kice joke mana! Duk abinda yakeyi bake kika janyo ba? Yanzu ga abinda ya dauko nan ai saiki san yanda zakiyi dashi!”…..

     “Oh haka ma zakace? Ni banyi complain ba sai heartless person like you? Of course zansan yadda zanyi dashi because I’m not nonchalant like you!!”…..

      “Har me zaki iyayi akai bayan kingama lalatawa yaro rayuwa, yadena jin maganar kowa, kina nema ki mayar dashi mara mafadi kamarki, nonsense!!”….

     “Dakata mallam! Karka kuskura ka gayamin maganar banza, in zakayi magana ka dinga tina a gaban wa kake, wallahi yanzu sai insa a dauremin kai kuma banga ubanda ya isa ya fitar dakai ba duk abinda kake takama dashi kuwa!!”…..

Wata dariyar mugunta daddy ya sheka yace…

    “Lallai wuyarki ta isa yanka! Banida lokacinki yanzu amma ki rubuta ki ajye we’ll come back to this!” Yanzu ta da’na nake!”….

     “Kace danka mana tinda kai kayi naqudarsa ka haifesa! Kuma duk wani stubbornness na Deen ai a gurinka ya dauko kowa yasan wannan karatun kuma!!!……..

        “Dake kikayi naqudarsa wani tarbiya kika basa banda gurbataciyyar rayuwa da kikasashi? Wallahi nayi danasanin saninki a rayuwa Fatima!!”….

        “Ai nice da danasani da Allah ya hadani da munafuki azzalumi macuci irinka, above all maciyin amana wanda besan halacci ba,zakaga yanda zan wanke Deen tatas with the power of the law koda shi yayi kisan kuwa!” 

Mami na fadin haka ta samu guri ta zauna bata kara kula dad ba……….

          Driving yake zuciyarsa a dagule saboda tinda suka fito daga asibitin taki kulasa gashi ya rasa meya mata balle ya bata hakuri, maganar duniya yamata taki cewa komai…… 

Lumsassun idanunta ta bude kadan ta kallesa, so take ta tambayesa abubuwa dayawa amma ta kasa, ta dade a haka kafin tayi summoning courage tace….

    “Are you responsible for the incident?”….

Zaro ido yayi sosai ya marairaice kamar karamin yaro yace…..

      “Ni kuma love? How could you ever think zan iya cutar dake? Aiko wani ne ya tabaki sai inda karfina ya kare wallahi!”…..

      “Who knows! Aibani kadaice ba, Tinda kace bakai kayi causing komai ba toh ina wanda mukayi accident din tare? I can recall vividly bani kadaice a motar ba!”…..

Ta fada rai a hade…..

      “Sorry to say ya mutu, tin jiya aka binneshi”…..

      “Karya kake wallahi! He’s not dead!!”… 

Fatima zainab ta fada a zafaffe….

       “Ni kike cewa karya nake?”….

       “Angaya maka din, sai me? Just tell me where you take the damn guy to!”…….

        “Naga alama kina nema kifi karfina! Ni kikema tsawa haka akan wani banza?”…… 

Ya fada mamaki fal ransa, wai ita ke maida masa magana haka yau? Yasani sarai bata ganin kan kowa da gashi amma fa duk iskancinta banda shi! 

        “An maka tsawar! Kafi karfin a maka ne toh? Mallam where’s is the man I had accident with?!”….

Cikin bacin rai yace

        “Get out of my car!!”…. 

Itama cikin zafin rai tace……

         “Wallahi bazan fita ba!, Tell me where the damn man is kaga in ban fitar maka daga useless car dinka yanzu ba!!”…..

Back to top button