Uncategorized

Shahrazad Complete Novel

 

 [4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: *GODIYA* 

Godiya ta tabbata ga Allah (s.w.A) daya bani ikon fara wannan littafin  , tsira da amincin Allah su kara tabbata ga manxonshi annabi Muhammadu ( S.A.W) da iyalan gidan sa da kuma sahabban sa.

     *Tukuici* *GA* 

Sameera aliyu da anas dina Allah ya rayashi ya albarkace shi. Ameen.

 

   *GAISUWA* *GA* 

Dukkan dukkan marubuta littafan Hausa.

  *KYAUTARWA* *GA* 

     Shahrazad dina wannan novel nakine halak malak.

 *TUKUICI* *GA*

Dukkan makarantana na ko INA ciki da wajen kasarmu, ban cire kowa ba.

  *JINJINA*

Ga shahrazad my shona pyar zindagi

*JAN* *KUNNE*

A dinga kokarin aje littafinmu a lokutan sallah da aikin gida, da makaranta.

     Na gode.

❣ *SHAHRAZAD*❣

(Labarin sharrin zuciya)

*By* *NUSNIM*

 

              1&5

Ke kam fatima kina wanka kamar mai canxa fata dallah mallama kiyi Sauri, in ba haka ba wallahi mutafi mubarki , ni’imah CE ke wannan mitar .

Khausar ta amshe maganar da cewa aikuwa dai don na kosa mu isa gidan aunty shahrazad don a kage nake danaji labarin ta, kun San tace muxo da wuri don labarin da tsayi.

Nusaiba dake gefe tana karanta wani story book, ta dago ido ta kalle su race haba sisters kubar fatima tayi wankanta mana. Duk kunbi kun cikata da mit__ __ kafin tagama rude bakinta sai ga fatima tana cewa, rabu dash daughter.

Ni’imah ta harareta saboda haushi race munkusa muyi gaba wallahi Mara “m” 

Fatima ta kallesu a kaikaice , cikin wasa tace  ” Ku don’t kun saba yin jika jika ni ban saba ba ” amma banda daughter nusaiba

Khausar tayi dariya tayi tafi tace .

” lallai ma wannan yarinyar yar rainin hankali CE, an gaya miki mu kaza mai ne? Kalle mu fa ki gani”

Tayi Dan murmushi , tace “ai najima da sanin Ku !!

Ni’imah ta harareta cikin wasa ” kefa baki da mutunci , duk uban zaman nan da mukayi muna jiranki babu abundant zaki saka mana dashi sai cin mutunci? Mun gode  amma ki sani zamu rama” 

   Tayi dariya tace sai dai Ku rame wallahi”,

Nusaiba tace kunga Ku rufe wannan chapter din naku muyi abunda ke gaban mu , mummy fati sorry yi sauri kishirya , toh baby nuscy.

Su nim da khausar suka ce hmmm wayaga uwa da ya, fatima tagama shirinta suka fito haraban gidan su.

Yan mata be su hudu masu ji da Kansu , fadimatul zara’u ni’imah , nusaiba Kausar, tafiya suke cikin kasaita kowacce idan ka ganta said ka rantse babu mai damuwa cikin su.

Alhalin ba haka bane kowaccen su ta dandana bakin ciki biyu daga cikin su suna da aure.

Fatima tana da sure yayinda akayi mata auren dole alhalin tana da Wanda takeso amma shi bai San tanayj ba, iyayen ta sunyi fama da ta fitar da miji amma bata fitar ba , sai dai kullum tacewa iyayenta sukara mata lokaci . mahaifin fatima ya gaji da jiranta akan da ta fidda miji.

Shine ya yanke shawaran hadata aure da Dan abokin sa mai suna abubakar , fatima tayi kuka sosai akan hukuncin da abbanta y yanke mata, ba yadda zata iya haka ta hakura ta karbi auren abubakar.

Amma zuciyar ta tana wajen najibullah , Gangar jikinta ne ke wajen abubakar.

Watan Fatima biyar agidan mijinta ts gudu saboda baza ta iya rayuwar aure da mutumin da bata so .

Tashigo motan zuwa Kaduna dama ita yar kano ce acikin mota ne suka hadu da ni’imah.

 

*kubiyoni* *agaba* *don’* *jin* *wacece* *ni’imah* 

TAKU UMMU RUMAN ( *nusnim*)

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

  (Labarin Sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

         5&10

Acikin mota ne suka hadu da ni’imah itama sakamakon guduwan datayi Daga gidan aurenta, ita mijinta muxguna mata yakeyi bai bata abinci sai dai ita taje ta nema.

Da hakan ta kai karanshi gdan iyayen ta amma sai suka ki su yarda da ita ” saboda su a tunanin su sharri take masa ” tunda dama tun asali bata son auren akayi.

Daga karshe dai tarasa ya zata yi shine ta yenke hukuncin data gudu , tunda anki sauraronta.

Wannan shine takaitaccen labarin auren ni’imah da fatima.

Fatima tana zaune kusa da Ni’ima a cikin mota” tayiwa ni’imah sallah tare da mika mata hannu , ni’imah ta amsa mata tare da mika mata itama hannu.

Fatima tace baiwar Allah idan bazaki damu ba ina da tambaya? Ni’ima tacs bismillah Allah yasa na sani?

Fatima tace nagode da kika bani dama.

Dama zan tambaye kine kema Kaduna zaki ? Ni’imah tacd mata eh Kaduna zani.

Fatima tace yauwa Ashe waje daya zamu je ” ni’imah tayi murmushi , fatima taci gaba da cewa don Allah wani unguwa ne agarin Kaduna Wanda kasuwanci yake da saukin yi aciki Wanda komin kankar tarshi zaka samu abunda kake nema?

Ni’imah tayi nadan wani lokaci sannan race eh to dayake nima yau nafara zuwa Kaduna ba lallai bane na sani, amma inba zan manta ba agarinmu suleja akwai wata makociyar my tana cewa   , kasuwanci a u/rimi yafi dadi don tayi zaman wajen gasu da girmama mutane da sanin kimar mutane,” shiyasa Nima nake son na sauka a u/rimi.

Fatima ta numfasa tace inna fahimce ki, kema bakuwa ce again zuwanki na farko kenan?

Ni’imah tace eh , fatima tace Ashe tafiyar mu daya dake nima bakuwa ce kuma ma idan munje Kaduna bansan inda zan sauka ba , banda kowa agarin.

Sai ga hawaye na zuba a idanun fatima , Ni’ima tayi saurin cewa yar’uwa lafiya naga kina hawaye? Meyasa ki kabar garinku ? Bayan baki San kowa anan Kaduna ba?

Fatima tayi murmushi takaici, tace yar’uwa cewa zakiyi meyasamuka bar garin my bayan ba mu San inda zamu ba?

Sai ga hawaye a idon ni’imah , Ni’ima taci ni ina da kwakkwaran dalilin barina mahaifata wato suleja.

Ni’imah taci gaba dacewa da farko dai yaka mata mugaba tarwa da kanmu junan mu” fatima tace hakane.

Fatima tace ni sunana fatima Muhammad kuma ni yar garin kano ce.

Ni’imah tace ni sunana ni’imah haruna ni yar garin suleja ce , daga suleja nazo kano sannan kuma na Hau motan Kaduna.

Nan fatima da ni’imah suka ba mawa junayen su labarin kan su , duk sun tausaya ma Kansu , kuma sun kills kawance kamar  yan uwan juna, fatima tace mubar ma Allah komai “sannan mune ma taimakon sa akan bukatun mu, sannan kuma ya ganar da iyayen mu akan kuskuran su da suka aikata.

Ya Allah ka bamu ikon yiwa ya’ya’yen mu adalci kuma kabamu ikon yiwa iyayen mu biyayya ameen.

Da haka suka sauka garin Kaduna mai train albarka garin gwamna (center of Learning) Suns kara sowa kawo wani sanyin dadi sukaji y ziyarce zuciyan su.

Bayan sun sauka daganan suka Hau napep da zuwa u/rimi ” mai napep din ne ya tambaye su dai dai ins zasu sauka a u/rimi sukayi Dan shiru na wani lokaci sannan fatima tace dai dai wajen makarantar nan me Suns Kaduna (state university Kasu)yace to.

Ni’imah ta kalli fatima tace fatima me zamuyi amakaranta bayan bamu da kudin Shiva kuma wajen ai, ba wajen Sana’a bane wajen karatu ne.

Fatima tace hakane amma inaji ajikina kamar zamu samu irin su photo copy’s tunda nasan Baxa arasa acikin school din ba ko kuma shagon provision hakane kam.

Sun karaso dai dai gate din Kasu, suka sauka tare da biyan mai napep kudinsa.

 Sun tsaya cirko cirko abakin Kasu Suns tunanin ta INA zasu fara, su saka wannsn su kulla wancan.

Da haka Suna wannan tunanin ne suka hango wata yar budurwan yarinya waccd baza ta wuce shekaru 23 ba tana tafiya cikin nutsuwa da alamun zata shiga cikin (Kasu) din ne .

Fatima race ni’imah anya bazamu yiwa wannan yarinyar magana ba ko ma samu hanyar shiga cikin Kasu?

Ni’imah tace aikuwa kuma da alama tana da saukin kai suna cikin magana ne sukaji ta musu sallama tare da wucewa suka amsa sallamar ta.

Had ta gota su fatima tayi saurin cewa baiwar Allah Dan tsaya cak ta tsaya.

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* ( *NUSNIM*) 

 

Pls duk me novels dina ya taimaka y turon

Adalilin sonta

Hanta da jini

Kuncin rayuwa

Kutausaya min

Labarin ni’imah

Aljana CE ko mutum

08064481931

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin Sharrin zuciya)

    *BY* *NUSNIM*

              10 & 15

Fatima tayi saurin cewa baiwar Allah Dan tsaya cak ta tsaya tare da juyowa fuskarta dauke da murmushi, fatima da Ni’ima suka karaso inda take , suma fuskar su dauke da murmushi suka gaisa.

Fatima da Ni’ima suka fada mata sunan su tace wood mai sunan mamana fatimah ” sannun Ku ni kuma sunana nusaiba sulaiman ” ni’imah Suna mai dadi.

Fatima tace nusaiba Dan Allah inbaza ki damu ba taimako muke nema , mu baki ne agarin nan, mun fito Neman aikinyi ne don mu rufa mawa kan mu asiri , koda iron aikin photo copy’s ne tunda munyi karatu Daga secondry har diploma na ( computer school).

Nan dai suka mata bayanin Daga inda suke !!! Amma basu fada mata dalilin fitowar su Daga garin su ba.

Nusaiba ta danyi shiru na Dan wani lokaci kadan yayin da fatima da ni’imah sai addu’a sukeyi azuciyan su, Allah yasa su sami abunda sukazo nema.

Nusaiba ta dago idonta Tamara kallon su da kyau , sannan tace ba damuwa in Allah ya yarda zan taimaka muku iya gwargwado nah!!! Don kaima bakasan nan gaba wazai taimake ka ba.

Su fatima sunji dadi sosai sai godiya suke ta mata, nusaiba tace nima aiki nake acikin (Kasu) din fannin photocopys din, nida kawata”” amma yanxu bara na kaiku gidan mu Ku huta tunda kunsha gajiyan hanya, kafin zuwa anjima muga yadda zamu bulluwa al’amarin.

Suka ce to mun gode nusaiba.

Nusaiba ta tsare musu napep ya kaisu dagel (1) banisa Daga Kasu duk area din u/rimi ne, bayan sun sauka tabiyashi kudin sa.

Nusaiba nagaba, su fatima nabinta abaya har suka Shiva cikin gate din, babban gida ne mai flat dayawa aciki akalla zasu kai flat 20 sannan kuma ga mai 1 bedroom with toilet aciki.

Wannan mai 1 bedroom with toilet yan makaranta sunfi kamashi sabanin mai flat shi kuma irin masu iyalan nan ne.

Su nusaiba suka Shiga bangaren mai 1 bedroom tabude wani daki tace bismillanku daki ne Dan ma dai dai ci da toilet aciki sai gado da akwatina , sai (TV) said kuma kujera guda daya dake gefe , kayan dakin basu cika yawa ba komai dai dai .

Fatima da Ni’ima suka zauna bakin gado , nusaiba tace  musu tana zuwa , bayan fitar ta da yan mintina, ta dawo dauke da kulan abinci sai ruwa da drinks ta ijye musu agaban  su.

Ga abinci kuci in kungama ga toilet can koda  zakuyi wanna ko wani abun, ni zan koma wajan aiki ne, saboda akwai abunda zanyi amma bazan Dade ba zamu tashi Daga wajen aikin ba.

Ni’ima tace OK badamuwa nusaiba sai kin dawo mungode , tace laa bakomai” duk anxama daya Allah ubangiji dai yamana jagora a dukkan al’amuran mu allahumma ameen.

Su fatima sunci abinci sungama har suka watsa ruwa , tare da gabatar da sallolin su , bayan sun idar sukaci gaba da tattaunawa akan al’amuran su.

Nusaiba ta isa wajen aikinta wata yar matashiyar budurwa wacce baza ta wuce sa’ar nusaiba ba, tace haba nusaiba tun dazu fa nake jiranki, mu karasa aikin nan  kin San yau za suzo karba ko, duk ta marairaice fuska kamar zatayi kuka .

Nusaiba tace sorry my lovelly sisto wallahi wani abune ya tare ni, nan nusaiba ta labar ta mata abunda ke faruwa , tace Allah sarki har sun bani tausayi.

Yanxu abunda yadace muyi don mutaimaka masu shine muyiwa oganmu magana dama muna Neman Karin ma’aikata, sannan kuma sai muyiwa hajiya magana akan makwancinsu , sai aka ma musu dakunanan dake kusa da da kunan mu tunda bakowa acikin su.

Sai tabamu hayan daki daya , Daga baya idan sun fara samun kudi sai su kama dayan dakin !! Kinga munzama mu hudu kenan dakunan mu a Jere batare da takura ba.

Nusaiba tace yauwa sister gaskiya kin kawo idea mai kyau dama ina tunanin tayaya zamu bulluwa Lamarin, sai ko gashi cikin sauki kin kawo mana bayani.

Nusaiba sunyiwa ogansu magana kuma ya amince , sannan kuma sunyiwa hajiya magana akan sun son daki daya, Daga baya zasu bata kudin dayake ta yarda dasu kuma suna bin dokokin hayar gidanta, shiyasa batajin shakkan ta hanasu daki ba.

Duk sai da suka gamawa su Fatima komai kafin su shiga gida , bayan sun shigo cikin (compound) din gidan su , nusaiba tace sister bani key din dakin ki in dauko wayata dana jona chaji daxu OK.

Bayan ta dauko suka shiga dakin nusaiba sallama sukayi tare da tura kofan , yayin da Ni’ima ke kishingide tace Waalaikumus salam !! Fatima tace a’a nusaiba har kun tashi ? Tace eh wallahi sannunku da hutawa” yauwa.

Fatima ta kalli abokiyar tafiyar nusaiba .

Tace nusaiba wannan itace kawar taki wadda kikace kuna aiki tare ? Tace eh itace nan dai aka kara gaggaisawa.

Nusaiba tace wannan itace kawata khausar ita yar adaamawa ce na yankin (MUBI) ni kuma yar Hadeja ce.

Fatima tace allah sarki anan garin kuka hadu kenan? Nusaiba tace eh dukkan mu mun baro gdan iyayen mune saka makon auren dole daza amana , alhalin dukkan mu munada wayanda mukeso .

Amma iyayen mu sunki bama damar fidda mijin da muke so , ganin ana shirin yimana auren mukabi shawaran zuciyar mu mukabar garin mu.

*kubiyoni* *agaba* *don* *muji* *shin* ya *rayuwa* *yan* *matannan* *zai* *kasance*  *star* *dinsu* *tanan* *tafe*  *cikon* *tabiyar* *din*  

 

Ina Neman novels dina please

Adalilin sonta

Hanta da jini

Kuncin rayuwa

Kutausaya min

Labarin Ni’ima

Aljana CE ko mutum 

08064481931

*TAKU*  *UMMU* *RUMAN* (NUSNIM)

08064481931

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

 (Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

          15 & 20

Shine mukabi shawaran zuciyan mu mukabar garin mu .

Ni’imah tace Allah sarki Ashe duk matsalar mu daya ” sai dai mu anriga da ammana auren. Don da auren mu muka bar garin my , khausar tace kai garin yaya hakan ta faru?

Nan’ ni’imah ta labarta masu komai har zuwan su Kaduna ” kowaccen su saida ta share kwalla , nan dai suka bamawa junayen su shawara , nusaiba tabayyana musu zancen aikinsu da dakin kwanan su , sunji dadi sosai suka kara yi musu godiya.

Rayuwar su shar shar komai ya dai dai ta musu, sai dai Dan damuwan da baza arasa ba wacce bata wuce na kewar gida ba, suna aikin su kuma suna samu da haka har suka kama dayen dakin .

Kowaccen tana da dakinta , suna sana’oi da dama shiyasa basu zama ” saboda suna da zumar cigaba da karatu.

Akwana atashi bawuya wajen Allah har sun samu shiga *Kasu*  fatima da nusaiba depertment dinsu daya  suna karantar ( biochemistry) yayinda ni’imah da khausar suke karantar (microbiology).

Ayanxu haka suna matakin 200 level, rayuwar su shar, anan Kasu suka hadu da aunty shahrazad wajen cin abinci, lokacin itama take lunch” tabayan kujeran da take zaune ne taji su ni’imah suna tattaunawa akan rayuwar su sai taji tana son su kulla kawan ce” ko don  ta basu shawara akan biyewa sharrin zuciyar su da sukayi.

Duk da ta dan girmemu su , sannan ita matar aure ce kuma tan 300 level itama (biochemistry) take karanta.

Shahrazad ta tashi Daga kujeran da take tazo wajen su khausar tare da cewa assalamu alaikum .

Suka amsa mata da wa’alaikumus salam, tace sannun Ku fa cikin fara’a ” suma suka maida mata da martani tare da bata wajen zama” taji dadin karban da suka mata.

Tace ni sunana shahrazad abdulmaleek ina karatu acikin Kasu inda nake karantar biochem. Sannan kuma inada aure da yaro daya me suna *umar* *farouq* .

Nusaiba tace woow suna mai dadi khausar tace aunty shahrazad ina son yaronki  duk da banganshi ba , amma naji ina sonshi” shahrazad tayi murmushi tace nagode.

Tace gaba da cewa dafatan zaku karbeni amatsayin kawar Ku in badamuwa , Fatima tace why not , insha Allah munxama kawaye , amma fa kinzama auntyn mu , tace haba dai kawar Ku nazama.

Ni’imah race auntynmu kika zama” tunda kin girme mu gaki da aure harda baby boy !! Kinsan shi aure yana jawowa mutum girma da Kima a idon mutane . shahrazad tace  hakane nagode da wannsn girman da aka bani.

Shahrazad tace saura Ku ‘ Ku sanar min da kanku ” sun gabatar mata da Kansu kuma ta gamsu.

Kawance mai karfi ya kullu tsakanin shahrazad dasu nusaiba ” har suna zuwa gdan ta su wuni dayake mijin shahrazad matafiyi ne ” gidanta yana nan a malali a halliru Dan turo cresent.

Su fatimah suna jin dadin tarayya da shahrazad , saboda macece mai kirki da Sanin ya kamata ” ga hidimomi datake yawan yi musu ” alheri kala kala ba wacce basu gani Daga wajen shahrazad ” hakan yasa sukayi mugun shakuwa da ‘ita , kuma takan basu shawara akan abunda yashige mu su duhu, saboda yadda da sukayi da ita yasa basu boye mata sirrin su ba.

Lokacin da shahrazad taji asalin labarin su ” ta tausaya musu ” sannan kuma taga wawtarsu akan biyewa Sharrin zuciya har suka bar mahai fansu, wannan ba karamin kuskure suka tafka ba.

 

Shiyasa tace musu da suxo ranar weekend don tabasu labarinta da irin hakurin da tayi” ta mikawa Allah lamarinta .

*wannan* *shine* *takaitaccen* *labarin* *wayannan* *gwanayen* *matan*

Bayan fatima tagama shirinta su ka fito haraban gdan su, suna tafiya nusaiba tace oh rayuwa kenan gashi wai yanxu har muna 200 level muna tsaka da shiga 300 level kamar ba yau muka fara ba , fatima tace hakane daughter nusy.

Wato shi lamarin rayuwa yanxu sai da hakuri da addu’a kafallamawa Allah komai lamarinka ” sai kaga yamaka jagora a rayuwarka mu tsarkake zukatan mu ” muriqe gaskiya da amana aduk inda muke.

Ni’imah tace tabbas kuwa yanxu kufa kalla yaushe muka fara wannan business din takalman da atamfofin nan ” sai ganin cigaba mukeyi kuma Dan danan ya kare ankawo wani.

Khausar tace lallai kam alhamdulillah ” babu abun bautasa da gaskiya sai Allah, Allah mun gode maka.

Sun fito bakin gate din daidai hajiya mairo ta fito da mota zata fita sukaci karo da ita”suka gaisheta cikin girmamawa” tace a’a daughters dina sai INA zuwa , suka ce malali zamuje gidan kawar mu.

Tace hanyar mu daya kuxo muje inkaiku , ni zani f.j.c ne makarantar su salim ” OK hajiya mun gode, tace bakomai har kofar gidan shahrazad ta sauke su , sukayi mata godiya ta tafi.

*kutara* *tara* *agaba* *don* *jin* *wainar* *daza* *atoya* *agdan* *shahrazad*

TAKU UMMU RUMAN( *NUSNIM*)

08064481931

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

  (Labarin sharrin zuciya)

   *BY* *NUSNIM*

          20 & 25

Sukayi mata godiya ta tafi su kuma suka shiga cikin gidan da sallama, lokacin shahrazad tana kallon TV taji sallamar su , ta tashi cikin murna don tarban su.

Oyoyo sisters dina aiko yan xunnan nagama tadinku axuciyata” Ashe dai kuna tafe khausar tace aikuwa dai.

Shahrazad tace bismillah kuxauna” suka zauna fatima tace wash nagaji ” ni’imah tace aikin me kikayi daza kice kin gaji, ke da ba’akafa kika taho ba , bantala ace gajiyan tafiya ce.

Fatima ke raguwa ce Allah ” nusaiba tace kai ni’imah Dan Allah kibar min mummy nah ta sarara mana”  tun kafin muxo gidan aunty shahrazad kuke ta damunta keda khausar.

Shahrazad tayi dariya tace Ku dai Baku rabuwa da tsokana ” gaskiya ni’imah da khausar zamu sa kafan wando da Ku akan abunda kukewa fatima duk cikin raha suke magana.

Khausar tace kai kai aunty shahrazad abun ma yanxu saniyar ware ake mana” wato kin shigar mawa fatima da nusaiba  ko?

To gaskiya da sake bazamu yarda ba ” shahrazad tace kaina bisa wuya kanwata khausar amin afuwa”” bazan karaba su duka sukayi dariya kasan cewa yadda shahrazad ta marairai ce fuska kamar zatayi kuka.

 

Tace bara na kawo muku  ruwa da lemo, ni’imah tace aunty shahrazad zauna abunki bara naje na dauko bana so ki wahala dayawa, ki kasa bamu labari.

Shahrazad tayi dariya kai ni’imah ke kam kina son labari haka” bayan sunsha drinks din su da cake.

Sai shahrazad tace to sisters dina yanxu zakuji labarina Wanda nafada cikin ukuban rayuwa aciki saka makon kishiyar mamana.

Kamar yadda kuka sani ni sunana shahrazad abdulmaleek ” mahaifina Dan garin kano ne a unguwan fage haka mahaifiyata ma yar garin kano ce amms it’s suna hoto road ne.

Sunan mahaifiyata lubabatu , amms anfi kiranta da hajiya , hajiya lubnah tana yawan shigowa fagge kawo dinki kasan cewa yan fage sun shahara a iya dinki.

Anan shagon telanta me suna muntari suka hadu da babana abdulmaleek har suka kulla soyayya mai karfi Wanda ya kaisu gayin aure.

Alokacin babana yana aiki a Kaduna ” yana da gida a u/kudu anan yake xaune ” bayan auren su da wata daya ya dawo da mamata garin Kaduna acikin gdan sa dake u/kudu.

Anan suka ci gaba da rayuwar su” har Allah ya albarka cesu da haihuwan da na miji mai suna aminu.

Aminu yana da shekara biyar aduniya hajiyata ta sake haihuanwan diya mace , alokacin mahaifina ya ba mawa hajiyata  zabin sunan daza asamun.

Hajiyata tace tana son asamin shahrazad don ta Dade da son sunan tun kafin tayi aure.

Ni shahrazad na tashi cikin so da kulawa ” inada shekaru 7 aduniya mahaifina yasake aure ” inda ya auri yar’uwarsa  me suna indo, Daga azare aka kawota Kaduna.

Indo iriin masifaffun matan nan ne” gashi tana nuna mawa hajiyata tafita matsayi agun banana ” gata da kishin jaraba ga Neman fada, amma ita hajiyata bata kulata don bata son tashin hankali.

Indo tasa min ido bidi bidi tasani aiki Sam bata kaunar taga na zauna lafiya ” ga yaranta da ta taho dasu Daga azare, daman ta taba aure acan azaren , auren ya mutu ne shine ta kyalla ido tags banana ta like mai mahaifiyarta da mahaifiyar banana uwa daya uba daya suke” dalilin dayasa kakata taso auren kenan don akara kulla zumunci” nan kuwa basu San wacece indo ba . da sun Santa da basuyi kokarin hada auren ba.

Anan Layin mu akwai wani gida daya ke kallon gidan mu ” wato gidan tanko soba matarsa daya me suna aunty hauwa , babban Santa sunan sa Khalid said ta biyu amina ana ce mata amingi sannan na ukun shine umar sai auta me suna bilal.

Muna mutunci da yan gdan ” nakanje gidan don intaya aunty hauwa aiki in amingi batanan matar tana sons.

Inada shekara 12 aduniya na shiga secondry school wato j.s.s1 a makarantar government girls scondry school u/rimi , tun ina karamata Khalid ke tsokanana da matarsa ni kuma inajin kunya.

TAKU UMMU 

*nusnim*

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

 (Labarin sharrin zuciya)

 *BY* *NUSNIM*

          30 & 35

Allah sarki hajiya allah ya jikanki da rahma suka ce amin ” shahrazad taci gaba da cewa bayan rasuwan hajiyata da wata daya indo ta fara takura min , ta maidani baiwa ga hantara da duka da zagi kullum sai inxauna inta kuka, abinci sai taga daman bani.

Wataran sai dai in je gidan su yaya Khalid inci acan , duk nabi na lalace inda nagodewa allah bata hanani zuwa makaranta” ina cika shekara sha biyar da haihuwa  samari suka min caa , nikuma duk bani son ko daya, alokacin ne yaya Khalid y  danno kai, ranar alhamis ina zaune a kofar dakina , yayi sallama yashigo , lokacin indo batanan ” na amsa sallamar sa cikin murmushi sannu da zuwa yaya Khalid.

Yauwa matas  tayi murmushi tace ya aunty hauwa kwana biyu ban leka na gaishe taba, yace to mayyasa? wallahi karatu ne yasani agaba dayake mun kusa fara exam ayya Allah ubangiji ya taimaka amin.

Yaya Khalid yace shahrazad wai yanxu waye saurayin naki  ne? tayi murmushi tace ka kosa kaga mijin dazan aura ne” yayi dariya eyye har kin San wani miji”  tace kai yaya Khalid wai kana nufin ban girma bane ? Nifa inajin kaina on top  fa!! Ya kara kyalkyalewa da dariya woow my shazee anxama big girls haka nake so!! Tace hmmm wai shin kai baza kayi aure bane sai kara tsufa kake” ko ka rasa budurwa ne”” ko dayake baka da kyan da mace zata soka  cikin tsokana take wannan maganar.

Khalid yace lallai yarinyar nan kece dai baki da kyau tunda gashi kin rasa mashinshine” shiyasa nake son intaimaka maki karki kara tsufa acikin gda duk cikin zolaya yake wannan maganar .

Tazaro ido waje tace wa tabdijam akai kasuwa bana so ” kai nifa ingaya maka ni irin matan nan ne masu wuyan samu, shazee cute lady

Shazee Queen of star 

Shazee yar kwalisan yan mata 

Duk Wanda ya ganni sai ya kyasa ” kamar kai da kazo yan xunnan nasan kaima Neman shiga kake takarasa maganar cikin yi mishi gwalo .

Aiko bata Ankara ba sai taji rankwashi ta marairai ce fuska kamar zatayi kuka” kai yaya khalid da zafi fa Allah sai na rama!! Yace  sai dai ki rame ” ta juya mashi baya alamun tayi fushi” yace to sorry my kanwa kaina bisa wuya , tace to nayafe maka, yauwa yace shahrazad nazo ne muyi wata magana  mai muhimmanci” tace to yayana.

Dama ba komai bane illa nazo ne insanar dake son da nake miki Wanda tun kina karamar ki na kamu da   sonki, pls shahrazad kibani zuciyar ki , zan zame miki farin ciki arayuwar ki zan zame miki uwa da uba inasha allahu .

Please shahrazad karki ce baki sona kamar zaiyi kuka , tunda yafara maganar nan take kallon sa tare da zubda hawaye , saboda taga tsantsan sonta a kwayar idanunshi, kuma tana da tabbacin shi zai riketa amana ya rike maraicinta.

Tashare kwallanta tace yaya khalid karka damu na amsa soyayyarka Allah ubangiji yazaba mana mafi alkhairi arayuwar mu baki daya” wani irin sanyi farin ciki ya ziyar ce zuciyar sa ” yace wooow am so happy today tanx a lot dear shahrazad ana hubbik tartir ” itama tace me too I so much love you khalid.

Tun daga wannan lokacin soyayya mai karfi ta kullu tsakanina da yaya khalid Wanda aranar sai mu hadu sau biyar muke iyayin bacci.

Nusaiba tace lallai aunty shazee soyayyar Ku ta birgeni “

Shahrazad tayi murmushi tace kadan ma kikaji.

Ni’ima tace aunty shazee baki fada mana kamannin yaya khalid din ba?

Shazee tace eh to yaya khalid baki ne mai irin kyallin nan gashi da dogan hanci da manyan idanuwa sannan kuma shi bawani dogo bane can , kuma ba gajere ba dai dai dai, sannan kuma yanada sajen sa mai kyau fuskarsa dogo ma’abociyar murmushi.

Khausar tace woow gsky yaya khalid ya hadu gaskiya ina son inganshi, fatima tace dallah dagajin kyakkyawan mutumi har kina so ki ganshi , yarinya ki maida maitar ki khalid na shahrazad ne, dukan su suka kwashe da dariya .

Nusaiba tace gaskya zaku haifo yaya masu kyau ke gaki yar fara mai hanci da beauty point. shi kuma  black beauty dashi woow abun yayi , shahrazad dai tana jinsu sai dai tayi murmushi.

Taci gaba da cewa lokacin muna tsaka da soyayya yarinyar indo mai suna nafisa ta dawo gidan mu da zama , wulakanci ba Wanda bangani ba wajenta haka indo zata tula min wankin nafisa tace nawanke shi tsaf kuma nafisan bata wuce sa’ata ba , idan na fada mawa babana abunda ake mun sai dai yace mun shahrazad kiyi hakuri kiyi koyi da hajiyarki shikenan abunda yake cemun.

Akwai watarana ranar jumma’ah munyi waya da yaya khalid yace mun gashinan zuwa zaiga kwalliyar jumma’ata, aiko natsara kwalliyata mai kyan gaske yazo nafito kofar dakina ina gyara Maya fina ” naji nafisa nacewa kayan aro anyima saurayi kwalliya dashi ko kyau bakiyi ba ko kulata banyi ba nafita abuna.

Muna cikin hirarmu ta soyayya sai ga nafisa ta fito zata unguwa , har ta wuce mu ta dawo tare da kurawa khalid ido taji aduniyar nan ba Wanda take so sai khalid ” shiko kallon ya bashi haushi yace mallama lafiya , tayi saurin zabura tace yi hakuri sannan ta wuce tana tadin zuciya , tabbas nasamu Wanda nake so, tayaya zan sameshi da alama danji da Kaine taja dogon tsaki mtsssssssw , kai ya kamata ingaya mawa mama indo don gaskiya da sake wallihi.

Ni nusnim nace tabdi jam , kutara agaba.

TAKU UMMU RUMAN

( *NUSNIM* l

08064481931

[4/15, 10:02 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD*❣

 (Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

       25 & 30

Tun ina  karama Khalid ke tsokana na da matarsa ” ni kuma nakanji kunyarasa yakan shigo gidan mu suyi hira da hajiyata ” kamar abokanai suke da hajiyata.

Akwai lokacin suna hira da hajiyata atsakar gida yake cewa hajiyan mu niko idan shahrazad ta kara girma zaki aura min ita ? Hajiya tayi dariya tace kai Khalid kace wasa dayawa” yace Allah hajiya da gaske nake ina son shahrazad” Ina son ta kasance matata in Allah ya yarda.

Hajiya ta kura mai ido da kyau taga dagaske yake maganar sa. Ta numfasa tace Khalid  inaso ace Kaine ka kasance mijin shahrazad ” zanyi alfahari da hakan saboda nasan kai waye ne” idan shahrazad itace mafi alkhairi agareka Allah ubangiji ya mallaka maka ita” in ba ita bace Allah ubangiji ya zaba maka mafi alkhairi ” Khalid yace allahumma amin.

Tudaga lokacin Khalid ya dingajin kunyar hajiyan shahrazad.

Akwana atashe ba wuya awajen Allah Allah yayiwa mahaifiyata rasuwa  , mutuwan da ta girgizani da sauran mutane, don adaren ranar da hajiyata zata rasu tace shahrazad zoki zauna muyi hira, nace to hajiyata.

Na zauna kusa da mahaifiyata ” tace shahrazad ina son nan gaba ki zama abun alfahari agun al’umma , ina son kiyi karatu mai zurfi don watarana zai taimakeki ” kuma inso da ki rike addu’oi don shine takobin mumini.

Idan kin kai munxulin aure ina rokan Allah daya zaba miki miji nagari , Wanda zai iya rikeki ” banda ruwan ido irin na sauran  mata , nayi  saurin rufe ido nace kai hajiya ta ” menene kuma na batun aure , nifa ban isa aure ba.

Hajiya tayi dariya tace shahrazad kina girma ammah baki San kin girma ba , tace da akauye ne   ai da kin dade dayin aure tunda shekarunki sha uku fa , kefa budurwa ce yanxu .

Amma bana so kiyi aure yanxu har sai kin gama secondry school dinki in San samu ne , kifara karatu a jami’ah , don yanxu rayuwar ce tazama abunda tazama.

Baza ki gane abunda nake nufi ba sai nan gaba , duk randa Allah y daukaka ki Ina son kidinga  taimakon Mara su karfi , ki Kasan ce mace mai yawan ibadah da sadaka .

Ki rike yayanki sosai shi kadai gare ki , ki rike indo amatsayin mahaifiyar ki , duk abundant zata miki ki dinga hakuri , ko ba komai kun hada jini da’ita.

Mahaifin ki ma ki kasan ce mai yi masa biyayya , duk da nasan kinayi ki kara akan Wanda ki keyi .

Shahrazad tace hajiyata meyasa yau kike tamin irin wayannan na sihar ? Wlh duk jikina yayi sanyi sai ga kwalla sun fito Daga idanunta.

Hajiya tace haba shahrazad menene kuma na kuka , taja hannuna  ta daura kan cinyarta ta rungume ni tare da  shafa min bayana kamar wata yar yarinya har sai da nayi ajiyar zuciya.

Tace my shazee tashi kije ki kwanta Allah y miki albarka, y kare ki Daga sharrin mugayen mutane da aljan, Allah y albarkaci rayuwar ki da zuri’a dayyiba (amin) na kai bakin kofa  na juyo na kalli hajiyata tayi min murmushi, nima nayi mata murmushi, Ashe haduwar mu na karshe kenan .

Kallon mu nakarshe kenan , maganar mu na karshe kenan. 

Hajiyata tace ga garinku nayi kukan da bantaba yi ba hakama Dan’uwana da babana .

Nan shahrazad ta fashe da kuka su fatima kuwa duk fuskar su ta jike  da hawaye , nusaiba tace kiyi hakuri aunty shahrazad Allah yafiki son kayan shi, shiyasa ya dauka ni’imah tace hakane.

Allah sarki hajiya allah ya jikanki da rahmah.

*kuyi* *hakuri* da *wannan* *page* *din* 

TAKU UMMU RUMAN

( *nusnim*)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

    35 & 40

Bayan wuce wan nafisa, Khalid yace my shazee wannan mahaukaciyar daga ina?  Hmmm yarinyar mama indo ce mai suna nafisa!! Ta dawo wajen mamanta daza. Khalid yace tabdijam Allah ubangiji yasa karkarta takura miki, afili Shahrazad tace ameen, amma acikin xuciyarta tace na yaushe kuma.

Cikin alamar rawan murya Nusaiba tace aunty Shahrazad ina fatan nafisa ba kwace miki yaya Khalid xatayi ba? 

Shahrazad yayi murmushi tace Nusaiba kenan kedai kici ba da bina cikin labarin nan zakiji komai.

Shahrazad tace bayan kwana biyu da haduwata da yaya Khalid , ina zaune ina cin abinci sai naga mutum atsaye akaina, daga kaina nayi inga ko wayene nafisa ce ta rike kwankwaso sai girgije girgije takeyi .

Nace nafisa lafiya kika tsaya mun akaina , budan bakinta tace ba lafiya ba, dama Nazo ne in miki kashedi akan ki rabu da Khalid ” don shi ba tsaranki bane dani yafi dacewa, in kuma kinki jikinki zai gaya miki , don ba karamin aiki na bane inmiki rashin mutunci eheeen .

Haka nabita da kallo daga sama har kasa, cikin zafin nama nace wlh baki isa ki rabani da yaya Khalid ba, kuma inkince zaki shiga tsakanin mu, to wallahi zamu raba abun kunya.

Nafisa tace oh haka kika ce? Eh haka nace  bismillah shege ka fasa,, haka nafisa take kallona cikin mamaki don bata taba zaton haka nake ba, afusace tabar daki.

Sai jin ihunta nayi atsakar gida tana cewa wayyo Allah mama indo Shahrazad ta kwada min tabarya akai, sakamakon jin abunda take fada sai naji gabana ya fadi 

Don nasan yau kashina yabushe awajen mama indo.

Indo ne ta fito da gudu tana nafisa lafiya , nan nafisa ta kora mata karya da gsky, habawa kamar jira takeyi, tafa zunduma ashar tana kwala min kira Shahrazad Shahrazad Shahrazad Shahrazad Dan ubanki kina ina?  Yar iskan yarinya mayya kawai.

Cikin sauri nakara so inda take har ina tuntube, ban Ankara ba , nafara jin duka ta ko’ina,  mama indo da nafisa suka rufeni da duka,  gajimun shegiyar yarinya zata kashe mun yata don bakin ciki , haka kawai ki dauki tabarya ki kwala mata akai.

 

To kema bara kiji inda dadi, nafisa miko min tabaryan in kwala mata taji Inda dadi, ihu nake ina magiya ina basu hakuri amma ina ba Wanda ya tankani, saida suka min lilis sannan suka kyaleni, dakyar nake iya numfashi.

Fatima ta fashe da kuka tace wannan wasu irin mugayene haka za suyi kisan kai , amma sai Allah yasaka miki aunty shazee, dukkan su suka goge hawaye, Shahrazad tace Fatima kadan daga cikin muguntan da su mama indo suka min.

Tacigaba da cewa.

Da kyar na rarrafa nashiga dakina inata kuka ina wayyo Allah na wayyo hajiyata wayyo Khalid dina, yayin da hannuna a kumbure da kyar nake dagashi sakamakon bugamun tabaryan dasu kayi, ina cikin kuka ne baba nah ya dawo yana kirana amma nakasa amsawa”” saboda kukan da ya sarke wuyata, .

Dayaji shiru shine  ya biyo ni daki, yadaga labulan dakina yana ke Shahrazad lfy kike kuka? Waya tabaki da kyar ta iya fada mashi, ranshi ya bace amma bayadda zaiyi, yace tashi muje agyara miki hannun da alamun targade ne , tace to baba , ya taimaka mata suka fita abakin kofan GDA suka ci karo da Khalid ya fito amota.

Ganin masoyiyar shine cikin wani hali yayi saurin kara sowa da gudu duk arude yake , yana baba lafiya.

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (nusnim

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     40 & 45

Yana baba lafiya mai yasa meta haka? baban yace rauni taji  shine zan kaita aduba mata hannun nata don kar yayi tsami, Khalid yace baba koma gida kawai zamu kaita nida ameena, wato kanwarsa.

 

Baba yace to ba damuwa, Khalid ya bude ma Shahrazad mota tashiga, ya dauki wayarsa ya kira amingi , itama cikin sauri tafito, abunka da makwafta banisa tsakanin su!!! Tana kara sowa tashiga mota kusa da Shahrazad, “” cikin damuwa amingi tace shazee waya dake ki haka, Shahrazad ta sunkuyar da kanta kasa tana hawaye.

Khalid yana kallon ta , ta madubi yayin da zuciyarshi ke suya , amingi ganin shazee na kuka tayi saurin rungumeta tana lallashinta, sorry my sister stop crying , kukan Shahrazad yakara tsananta.

Hankalin Khalid yagama tashi bai San lokacin daya ja burkiba ya tsaya !! Tare da juyo kansa baya , cikin muryanshi mai dadin sauraro, yace Shahrazad Dan Allah waya  dake ki? don wannan ba faduwa kikayi ba, alamun  duka ne. Na daga rinannun idanuwa ta na kalleshi, zanyi magana, yayi saurin cewa please my d karki boye mun komai kifada mun?

Na kura mashi ido ina kallonshi, azuciyata ina fadin shin in fada mashi gaskiya ko kuma sabanin hakan !!!   Wata zuciyan tace gara kawai ki fada mashi gaskiya don baki da kamarsa “” daga abbanki sai shi.

Amingi tace muna jinki shazee, nan na labarta musu komai , innalillahi    yanxu bala’in da nafisa ta kunno dashi kenan, Allah natuba me zanyi da ita, amma ko sai nayi maganinta, sai tasan ta ta baki,””  amma mama indo bata kyauta ba, yana magana yana goge yar kwallan sa.

Amingi tayi kwafa tace ba komai Allah na  nan shi kadai zaiyi maganin su , kici gaba da hakuri Shahrazad, kuma ki cigaba da mika mawa Allah lamarinki , insha Allah wannan wuyan na Dan wani lokaci ne.

Kuma insha Allah ba Wanda ya isa ya rabaki da yaya Khalid, naki ne ke kadai, kinji yar kanwata, nayi murmushi nakalle ta”” nace ba komai aunty amingi ,rayuwace kowa da tashi kaddaran, yauwa yar kanwata shiyasa nake sonki.  Allah yabar mu tare amin.

Bayan munje wajen mai gyara ta duba hannun tace targade ne , ta gyara mun, amma fa nasha azaba,”” ni’ima tace sannu aunty shazee Allah y saka maki duk Kansu suka ce ameen.

Babana yasamu indo yayi mata fada akan abunda tamin , amma indo ta musanta “” sai cewa ma da tayi wai rashin kunya na mata,  ba yanda babana zayyi kawai karkade kai kawai yayi, tare da cewa Allah ya shiryeki ya ganar dake gaskiya tace amin.

Nafeesa ce zaune  shiru tana tunani, tayaya Khalid zai zama mallakin ta “abun duniya duk ya isheta, mama indo ce ta karaso wajenta tana lafiya nafeesa? Kin wani fada kogon tunanin.

Budan bakin nafeesan tace ba dole infada tunani ba mama indo,  xuciyata tana kokarin fashewa idan ban samu abunda nake soba  , mama indo tayi saurin cewa lafiya mekike so haka? Kika kasa sanar dani, fada min yata?

 

Ko menene sai na mallaka miki shi,komin wuyanshi ,  nan nafeesa ta washe hakora alamun jin dad.

Mama dama ba komai bane illa ina son in mallaki yaya Khalid amatsayin mijina, sai da gaban mama indo ya fadi, tace turkashi, ke nafeesa ki rasa Wanda zakice kina so sai wancan yaron mai taurin rai !!! Kuma kinsan alhaji yasan komai tsakanin Khalid da Shahrazad , don har manya sunshiga magana.

Nafeesa ta hade fuska tace ni gaskiya mama sai na aureshi wallahi don inajin idan na rasashi sai zuciyata ta fashe in mutu, mama kawai kice baza ki taimaka mun ba, nan tafashe da kuka.

Maman indo ta jawuta jikinta tana lallashi kiyi hakuri na miki alkhawari sai kin auri Khalid kwanan nan, sai dai inba na raye.

Shahrazad ta goge hawayenta.

Khausar tace lallaima matan nan , yanxu fisabilillahi tsakanin masoya zata Shiga , ko dayake, aibata fada in Allah ya yarda ba, kuma insha allahu baza su sami nasara ba.

Ni’ ima tace aunty shazee nakosa inji karshen labarin nan, bana so ki rasa Khalid,  Shahrazad tace karku damu nakusa.

Taci gaba dacewa bayan nadawo gida daga gyaran targade na, na kwanta adakina ina ta tunani , sai ga mama indo ta shigo dakina afusace kamar wacce aka hankado.

Nace sannu da gida mama, ta watsa min harara , cikin daga murya tace Shahrazad dama nazo ne inja kunnanki akan yanxu lokacine da yayi zaki rabu da Khalid , gabana ne yayi mummunan faduwa,!!! Taci gaba da cewa, don nafeesa nake son in aura mashi, saboda haka sai ki he gun babanki kice mashi kinfasa auren khalid  umurni nabaki ba shawara ba .

Cikin kuka Shahrazad tace haba mama indo karkiyi mun haka, kin San kalan soyayyar mu da yaya Khalid tun ina Yar karamata, kuma hajiyata kafin ta rasu , tabashi ni”” wallahi bazan iya rayuwa inbashi ba.

To ki mutu mana ni ina ruwana, aini ada dinane ai inkin mutun , tayi ficewar ta, kuka nake ba kakkautawa kozan samu zuciyata tayi sanyi amma ina  sai ma zafi danaji tana min.

Wayyo Allah, Allah karka bari arabani da yaya Khalid dina.

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* *NUSNIM*

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

    45 & 50

Allah karka Bari arabani da yaya Khalid, natashi na dauro alwala don gabatar da sallah,  nayi addu’oina masu yawa , sannan nashafa na kwanta abuna.

Cikin bacci ne naji wayata tana ringing  , dauka nayi ganin sunan danayi ajikin wayan , yasa nayi murmushi my D wato yaya Khalid,  nasa wayan akunne na tare dafadin  

Assalamu alaikum

Adayan bangaren aka ansa min 

Wa’alaikumus salam , gimbiyar kamshi dafatan kina lafiya , ya karfin jiki?

Lafiya lau full option!! Dafatan kamai kananan lafiya?

Ina lafiya kamar yadda kike lafiya, amma inba kya lafiya to nima bana lafiya.

Haba dai yaya nah  ka kwantar da hankalin ka, lafiyata kalau, sai dai kawai zuciyata tana cike da begenka da soyayyar ka!!  Fatana mukasan ce a inuwa daya  in Allah ya yarda, ina tsoron watarana in rasaka my D.

Shahrazad insha allahu zamu kasan ce a inuwa daya tare da farin ciki mai daurewa , fatana ki rike mun alkhawari !!!! Ina sonki Shahrazad ina kaunar ki Shahrazad “” in ina tare dake inajin wani shauqi,  Shahrazad kina Jan ragamar soyayyata.

Kai yaya nah dadina dakai ka iya lafuzza masu sanyaya zuciya.

 Shahrazad ikon Allah, karki tabaji a ranki wai shazee ba abin  kaunar Khalid bace.

Khalid na son shazee 4rever & ever, Khalid naki ne, shazee dukiya ce Dan  ko kinfi kudi, gida mota da komai ma,  Khalid yace Shahrazad rayuwa CE, taka a sannu taka shazee ga shazee  Yar Fulani.

Woow yayana duk wannan kalaman ni kadai gaskiya kasani farin cikin Mara misultuwa ina sonka yayana, nima ina sonki babynah, dukun mu muka kwashe da dariya.

Nusaiba tace woow aunty shazee gaskiya kuna wuta fa, Fatima tace sai kace masoyan cikin littafin (kutausaya min)na nusnim wato rumana da king laisu.

Gaskiya kun burgemu,, Shahrazad sai dariya take, kurufa min asiri ni na’isa mu iya irin soyayyan *rumana* da *king* *laisu*,  khausar tace kai aunty kunmafi haka.

Shahrazad tayi murmushi kudai kuci gaba da .

Washe gari da safe ina zaune adaki sai ga mama indo ta fada dakina, tare da cewa Shahrazad ya maganar da mukayi dake jiya? Kifa ganin ina binki ta ruwan sanyi don ba fin karfi ne kikayi ba, “” don idan naga dama ayau zan iya daura mawa nafeesa aure da Khalid kuma ya zaunu.

Kin fada mawa baban Baku abunda na fada maki jiya? Na sunkuyar da kaina kasa nace a’a, to me kike jira? Ba komai, mama kiyi hakuri wlh bazan iya tunkaran baba da wannan zancen ba.

Aiko ban Ankara mama indo ta kai  mun  duka abayana, ja’irin yarinyar insaki Abu kice mun baza ki iya ba to wlh ba a haifi Wanda zaimun haka !! Ke har kin isa , tashi kifi ta kimun aikina.

Mama kiyi hakuri don Allah , hakurin ubanki , har tsakar gida ta biyoni tana duka da hauri , tana cikin dukana sai ga kawar ta me suna ma’u, tashigo cikin sallama, tana indo lafiya kike ta masifa? Tundaga waje nake jiyo muryar ki .

 

Hmm ma’u ba lafiya ba, wai harni zansa Shahrazad Abu tace mun baza ta’iya ba,!! Ma’u tace  shin me kika sata  ? Nan indo ta labarta mata komai.

Ma’u tace ashsha indo Ashe baki da wayau ban sani ba, akwai hanya mafi sauki daza ki raba yaran nan, batare da kinsha wahala ba.

Nayi saurin dago kai don inji wani hanya ne ma’u take son fada mawa indo.

Indo tace ma’u bangane me kike nufi ba?

Ma’u tayi gyaran murya tace kixo muje wajen wani malami dake saman tudu, ya iya aiki sosai shan yanxu maganin yanxu, batare da kanki yayi ciwo ba.

Ai ban San lokacin Dana saki wani uban ihu ba ganin za arabani da masoyina, nayi saurin kama kafafun mama indo ina mama ki tainakeni ki mun rai, karki rabani dashi Dan Allah , komai kika ce in miki zan miki amma karki rabani dashi .

Indo ta hanka data gefe Dalla mallama yi mun shiru!! Wallahi kinji na rantse sai na ba mawa yata abunda take so , saboda haka kisa ka aranki, sai dai inba indo ba, kuma ki wuce ki karasa min aikina.

Jikina ba kwari ga zazzabi dake addabata ga yunwa, nake jibgan aiki ko su tausayamin !! Amma ina , ina aiki INA waswasi  , shin ingaya mawa babana da yaya Khalid abunda ke faruwa , ko kuma infada mawa Khalid kawai mugudu muyi auren mu awani wajen, wani bangare na zuciyata ke fada mun haka, !! Gyangyadi ne naji tana diba na!! Har na jingina kusa da bangon kicin dinmu nafara yin bacci.

Cikin bacci na naga hajiyata tazo min tana cewa Shahrazad karki biye, mawa *Sharrin* *zuciya* ki aikata abunda zaki dawo kina da kin sani , mafita kawai kici gaba da addu’a, ina cikin hakane naji an watsa min ruwa”” mama indo ce , eyye wato in saki aiki kixo kina bacci, toh na baki nanda minti talatin kingama, muryata na rawa nace to mama.

 Da daddare ina zaune Khalid ya kirani awaya yace mun yana kofar gdan mu, nace mishi to gani nan zuwa.

Mintina kadan na fita wajen shi, nayi sallama ya amsa min, Khalid yace shazee ya naganki wani iri , alamun kina cikin damuwa , nayi saurin kakalo murmushi, tace yaya nah mugaisa tukun na , inayi ni, yasu aunty Hauwa da amingi, yace lafiyan su kalau sunce agaishe ki da jiki.

Ina amsawa.

 Tace yaya Khalid Dan Allah mugudu muje muyi aure awani wajen , Khalid yayi saurin cewa lafiya kike kuwa shazee? haba  tayaya zaki ce mugudu bayan iyayen mu sunsan  muna son junan mu, kuma zasu aurar damu.

To menene kuma na guduwa, nace Khalid baza ka gane bane, nan nafayya ce mishi komai.

Khalid yace innalillahi wa’inna ilaihiraji’un, Allah kayi mana tsari da wayan nan mutanan, ta Allah ba tasu ba, !! Shahrazad mu dukufa wajen Neman kariya amma baza mu biyewa sharrin zuciya mugudu ba.

Koda mun gudu, idan Allah yayi asiri zai kamamu to tabbas sai ya kamamu ,koda birnin sin mukaje, kinga ko guduwa baida amfani,, !!! Addu’a itace maganin.

 

Na sauke wani nannauyan numfashi nace hakane, amma ina tsora fa my D,!!! Karkiji tsoro baby nah, to yayana.

 

To danyi dariya mana, nayi murmushi, yauwa ko kefa  .

Shahrazad rayuwa ta koya mana cewa so ba qunshe  yake da kallon juna ba amma muna kallon bangare daya atare  lokaci guda,  ina sonki shazee , me too yayana.

TAKU *UMMU* *RUMAN* (nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     50 & 55

Nagode shazee kici gaba da addu’a, to yayana, to ya kamata ki wuce gida dare nayi kar baba yayi fada toh, yayana sai da safe!!! Yauwa yan matana sai da safe.

Washe  gari ma’u,takamo hanyar zuwa wajen  indo akan  maganar da sukayi nazuwa wajen mallam nakan tudu, nafeesa na zaune kusa da indo tana bata labarin kalan soyayyar da takewa Khalid!!! Indo tace karki damu  yanxu zamuje gun mallam.

Kai amma naji dadi mama indo shiyasa nake sonki, sallamar ma’u ce Takatse musu hirar su !!! Indo tace a’a ma’u har kin karaso ? Eh wlh nakara so, dafatan dai ashirye kike, ashirye naki.

To tashi maza muje , sun fito kenan suka ci karo da ni, saida gabana ya fadi tuni nafara karanto addu’a, indo ce tace ke lafiyar ki kike kallon mu?

Shin me ma ya kawo ki kofar daki dana  , cikin rawar murya nake magana dama omon wanke wanke  nazo ki bani, indo tace nafeesa ki ba mawa wannan yarinyar omo, to mama, sannan suka fita.

Nafeesa ta jehon omon ajikina tare da cewa mai house girl gashi, karki kara cemun house girl don ni ba sa’ar ki bace!!! Mtsssw ke kika sani , Khalid dai yau sai yazama nawa, sai dai a hadiye zuciya bakin , karya kike ya rinya sai dai ke ki mutu ba niba,”” kuma duk abunda kuka shuka sai kun girba, ta Allah ba taku ba, mtssw nayi wucewa na ina Dan kwalla.

Su ma’u sunje gun mallam, mallam yace me kuke so ayiwa yarinyar , so kuke  akasheta, Ko kuma so kuke a haukatata, ko amata kurciya tabar gida, ko kuma arabata da yaron yace yafasa aurenta?

Mama indo tace so nake yaron da kanshi yace yafasa aurenta, yadda abun zaifi mata ciwo ta hadiye zuciya ta mutu.

Ni’ima tace kaji muguwa azzaluma kawai, wato idan yaya Khalid ya furta miki bai sonki abun zai fi miki ciwo , sai kiji gara ki hadiye zuciya ki mutu, Nusaiba tace kin San irin wannan yafi  bakin cikin, saboda masoyin da kake so tsakani da Allah kabashi yarda da amana , sannan daga baya yazo yace maka baya Sonka kuma baki da baki, ai sai kinji kamar ki hadiye zuciya ki mutu”” shiyasa mama indo tazabar mawa aunty shazee haka.

Kai Allah ya wadaran naka ya lalace khausar tace haka ameen dai.

Aunty shazee muna jinki ci gaba toh.

 Hmm ingaya muka mallam ya ba mawa mama indo magani ta zoba azauren gdan mu inda yaya Khalid ke zama, ki tabbatar kinsa  to mallam mun gode, cikin murna indo ta dawo gda , nafeesa ta tare ta da sannu da zuwa mama dafatan andmashi 

Mama indo ta fadada murmushi eh andace, yanzu kece zaki ka rasa sauran aikin, toh mama  ni me zanyi cikin zaro idanu, ke dallah ba wani Abu bane duk kikabi kika tsorata, kinga wannan garin maganin zakije zaure ne, ki barbada a inda Khalid ke zama shikenan”” sannan nafeesa ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa yanxu naji hankalina ya kwanta .

Da nayi zaton wani abune tunda wannan ne ai Abu mai sauki ne, aiko anjima kadan zanje in xuba mashi, shikenan nakusan mallakar. Khalid , duk Kansu sukayi shewa.

Zaune nake  adakina na idar da sallah azahar , na dauki alqur’anina ina karanta wa, bani nagama  karutun ba sai da aka kira sallah la’asar , sannan nayi sallah na, nacigaba da addu’oina.

Da yamma nafeesa ce ta fito cikin sanda alamun kar a ganta , har ta isa zauren , tana zuwa ta rufe kofan zauren ta barbada maganin yadda baza agane ba , bayan ta gama ta fito,””.

Ina cikin addu’a wayata tayi kara na dauka nayi sallama yayana y kake ya gajiyan aiki, yace lafiya lau,  anjima kadan ina nan zuwa to angona sai kazu , please ka Dan ta homin da lemon tsami, kedai baza ki bar shan lemon tsamin nan ba, kin fi son kina tafiya akayi iska ya gudun  min dake ko, haba dai yaya Khalid tayaya iska zai tafi dani? 

Aiko to inbaki rage shan lemun tsamin nan ba wataran iska zai tafi dake,  bakisan yanasa rama ba ko, “” to zanrage my”” dukkan mu mukai dariya, yanxu sai nazo , to Allah ya kawo mun kai lafiya ameen.

TAKU UMMU RUMAN (nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

      55 & 60 

Natashi naje zan debi ruwa arijiya inyi wanka sai ga mama indo, tace a’a Shahrazad me zakiyi da ruwan sanyi yanxu da yamman nan, wlh wanka zanyi, to ga Dan ruwan zafi can atukunya sai ki kashe sanyi dashi, don kin San garin akwai sanyi”” baki nasake cikin mama ki nake kallonta tare da cewa to mama sannan ta wuce.

A zuciyata ko sai tunani naka anya wannan mama indo ce  ” daya bangaren cikin zuciyata yace itace, watakila ta canxa haline? Kawai nakada kaina naje na diba ruwan nayi wanka na.

Bayan nafito na daura alwalan magrib nashige dakina, nayi shafe shafe na”” na tsantsara kwalliya ta mai kyau na dauko duguwar rigata kalan blue ba kara min kyau tamun ba Dan kwalina ban daura ba” saboda hijabi zansa nayi sallah yanxu!!! Bayan na idar da sallah ta na karanto addu’oi na Dana saba, nazauna gaban madubi don in daura Dan kwalina.

Ta jikin madubi na “” nake hango gaban kofan daki na sai naga kamar ana lekena , nayi sauri na tashi don duba waye ne, bude labulan dazanyi sai naga nafeesa ce,” ganina duk tabi ta daburce, alamun Mara gaskiya , don bataji karan tahowa taba da ta gudu, nace nafeesa lafiya me kike nema?

Cikin muryan marasa gaskiya tafara cewa dama nazo ne in Dan ara silifas dinki zanshiga bayi ne banga nawa bane, cikin rashin yarda da ita nace mata ta dauka!!!   Sannan najuya  baciga ba da daurina kamar wata amarya, ni kaina nasan nayi kyau ina kuma ga sahibin nawa idan ya gani!!! Nakara sakin murmushi  .

Nafeesa kuwa bayan barinta dakina ta wuce sashen su, mama indo na ganin ta , tace nafeesa ya me Shahrazad takeyi ,  tana daki tana shiryawa da alamu Khalid yana hanyar zuwa, yauwa autana!! Farin cikin ki ya kusan cika, aikuwa mama wayyo dadi kasheni.

Bayan nagama daurin dankwalina nafeshe jikina da turare , ina cikin hakane naji karan text yashigo wayata dubawan dazanyi, naga yaya Khalid ne”” ya rubata min,

Babynah kiyi hakuri bazan samu zuwa ba, nayi bakine , tuni naji raina ya bace” kamar zanyi kuka, cikin gungunai nafara magana di kai!! Yanxu fisabilillahi yaya Khalid saida  natsara kwalliya mai kyau saboda, sai kace mun baza kazoba, ni wlh nayi fushi ma””” 

Fatima tace kash meyasa yaya Khalid zai miki haka duk wannan kwalliya da kika tsara don shi, yaci aci ace ko lekowa ne yayi agurguje.

Nusaiba tace ai rashin zuwan nashi shine mafi alkhairi , kun mata ansaka mashi magani awajen zaman sa, kunga ko idan yazo yazauna awajen , shikenan aunty shazee tayi bankwana dashi, dukkan su suka ce eh kuma hakane fa, Shahrazad dai nata kallon su, batace komai ba”” sukace muna jinki aunty shazee.

Murya can kasa sai naji ance karkiyi fushi my D wasa nake miki gani a kofar gdan Ku, tuni na zabura nafara dube  dube don inji ta ina nake jin muryan ya Khalid , Ashe nadan na kiranshi ban lura ba , yaji lokacin dana ke magana, yace Ashe ma bakisan kin kirani ba saboda masifa, na kalli wayar dake hannuna!!! Nace haba habibi tunda kamin haka, to nima bazan fito ba, nakashe wayata.

Yana ta kirana naki dauka sai dariyar mugunta nake, can kuma naji karan shigowan tex ya Khalid ne yaturo min tare da cewa

Allah sarki shazee!!! Kukanki na samun damuwa “” damuwar ki tana bani takaici”” faran cikin ki shi nake so””” shazee tafi kudi, gida, mota, “”” Shahrazad duniya ce  , I love you.

Cikin jin dadi na rungume wayata akirjina ina murmushi, na dauki gyalena na fita banganshi azauran mu ba, nafita waje jikin motarshi naganshi ya kwantar da kanshi Asama.

Cikin sallama na karasa yayi saurin waiwayo wa yana ganina  na sakar mashi wani irin murmushi tare da kanne ido daya, shima ya maida min da martani.

Nakara masa da gwalo tare da cewa nima na rama ai, yace aikuwa kin rama, ido ya Bini dashi kamar zai hadiye ne, nace wannan kallon fa ai saka sa infadi kasa, yasaki murmushi”” kinga kuwa sai intaro ki, nasan zamu bada ma’ana, “” na fashe da dariya tace kai yayana ai sai kajira ranar auren ba yanxu  “” sai kasa mutane su mana fassara kuma hakane fa.

Shahrazad gaskiya kinyi masifar kyau , uhmn nida banda zolaya , Allah ba zolaya bane da gaske kinyi kyau, kai Allah ka mallaka min wannan Yar babyn nawa amatsayin matata, inhakan tafaru , inaga nafi kowani namiji sa’a aduniya,!! Nace ko yace allah.

Na kalleshi nace kaima ya Khalid duk macen da ta sameka tagama morewa ado daukan wanka iya magana , kula da mace , duk kai kadai, nima nayi sa’a yayana, na’am shazee nah

You have touched my heart and filled my world with so much love , honey I love u more and more with each passing day.

Thank you my D I so much love u, dukkan mu mukayi murmushi, nafeesa dake lekan mu sai tsaki take sakewa alamun bata ji dadin tsaya warmu anan ba .

Yayana mushiga zaure mana ko anan yau zamuyi tadin ne, aikuwa sai naji ban San karasawa ciki aiko dole mushiga”” bakaga mutane duk sun zubo mana ido ba,”” to mushiga ina gaba yana bina abaya.

Nafisa naganin zamu shigo taruga cikin gida da gudu tana murna.

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* nusnim

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     65 & 70

Bayan tafiyar yaya Khalid da kwana uku, mama indo ta kirani tace  Shahrazad nikam kwana biyu shiru bana ganin Khalid, ko lafiya?

Na danyi shiru na Dan wani lokaci ina tunanin wani kalan amsa zan fada mata, sai naji bangaren zuciyata tana cewa , kawai kice mata kema baki sani  kuma inkinkira wayarshi bata Shiga” ilai ko haka na fada mawa mama indo.

Cikin nuna alamun damuwa mama indo tace assha ,shine kuma kike zaune maimakon ki leka gdan su kiji ko lafiya, maza dauko Maya finki kishiga gdan”” nace to mama!! Na juya dakina ina tafiya ina sake sake da alama mama indo akwai abunda suke kullawa”” amma ta Allah ba tasu ba.

Nashiga dakina na dauko mayafina nafito nace mama na wuce, tace to ki gaida Hauwa””” to zasuji.

Nafito kofar GDA ina Dan murmushi na, nace kawai bara nashiga gdan su ummi kawata mudanyi hira”” cikin GDA kuwa su mama indo ne da nafeesa suna ta Hiran su najin dadi, nafeesa tace mama gsky aikinmu yayi,  kai nakusa zama amarya, aikuwa dai autana, yanxu dai bara mujira dawowanta” muji mai zata CE!!! Aikuwa.

Tunda nashiga gdan su ummi nakira yayana mukaita hira dashi, nafada mai abunda ke faruwa, yayi dariya”” yace shazee akwai abunda mutanan suke kullawa Wanda bamu sani ba,” kamar sunyi niyan raba mu ne, shine suke tunanin hakar su ta cimma, nanko basu San , kamar kara manna mu akayi ba, aikuwa dai habibi 

Yanxu dai inkin koma gida kiyi alamun kamar kinyi kuka kice kinje wajena na nuna ban sanki  ba ,” na Kore ki na hantare ki!! Muji kuma mai zasu ce “” kai yaya nah ka iya kawo idea.

To sai anjima in munyi waya to baby nah, bayan mungama waya ne sai nayiwa ummi sallama nace mata na wuce gida ,”” kafin infita daga gidan saida nashafa mawa idona ruwa alamun nayi kuka,””.

Da sallama nashiga zauren mu ina gunjin  mama indo ta tashi tana lafiya Shahrazad kike kuka me Khalid ya miki, nan nakwashe yadda mukayi da Khalid din na fada mata”” tace kai amma Dan Adam butulu ne, yanxu abunda zaisaka maki dashi kenan, amma ba komai , sai naje har gidan nasu inji dalili”” nayi saurin cewa a’a mama ba sai kinje ba, ki kyalesa da halinsa”” ni barsa da Allah .

Mama indo tace ba komai Allah zai saka maki , Shiga daki ki kwanta abinki”” nafeesa dake lekan mun kamar ta zura aguje don murna, bayan na shige daki na fada kan gadona ina dariya ba kakkautawa.

Yayin da mama indo da nafeesa anacan ana murna.

Lokaci sai tafiya yake  yau satin Khalid dina daya a abuja, ” mama indo taje ta samu kawarta ma’u tace,” ma’u aikin mallah na kan tudu yayi fa, nan ta fayyace mata komai , ma’u tace kinga ai na fada, yanxu kuma menene kuma agaba?

Yanxu abunda zanyi zansa nafeesa taje gdan su don tabishi” ko Allah zaisa akara  dacewa”to hakan ma yayi.

Bayan mama indo ta dawo gida take fada mawa nafeesa ga abunda zatayi, nan nafeesa aka hawan rawan jiki, taje tayi wanka aka tsantsara kwalliya, tace mama nayi kyau kuwa? Eh autana kinyi kyau, nagode mama sai na dawo , mama indo”” tace to sai kin dawo.

Duk abunda sukeyi a kunne na  , bayan fitan tane na kwashe da dariya, shirmen banxa “” iska na wahalar da mai kaya.

Nafeesa na zuwa kofar gidan su Khalid taci karo  da kanin Khalid , tace yauwa Umar Dan Allah kadan min magana da yaya Khalid mana” yace ai baya nan yayi tafiya amma ya kusan dawowa ,tace to nagode Allah ya dawo dashi lafiya”” amin.

Haka ta dawo gida duk ranta abace, maman ta na ganin ta tace nafeesa lafiya mama wai Ashe yayi tafiya, amma yakusan dawowa, !! To shine kika bi kika tada hankalin ki”” kika sani ko ya tafine don bai son ganin Shahrazad, sannan nafeesa ta saki ranta , yauwa kokefa, yanxu inxai dawo sai ki mashi girki mai dadi, kafin nan na koma gurin mallam na kan tudu na karbo miki maganin mallaka kamar yadda muka karbo  Wanda ya zauna  akai rannan, yauwa mamanah.

Karaf akunne na, hankali na ya tashi, na dawo dakina da gudu, na fashe da kuka”” nace dama abunda mama indo ta shirya min kenan, ai da gudu na tashi naje zauren mu wajen da muke zama!!! Ko zanga alamun maganin, Ina ta dubawa bangani ba kamar ance in waiwayau.

TAKU *Ummu* *Ruman* (nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

 *BY* *NUSNIM*

       70 & 75

Ai da gudu na tashi naje zauren mu wajen da muke zama ko zanga alaman magani , ina ta dubawa ban gani ba, kamar ance in juyo sai na hango wani takarda alungun wajen!! Na karasa nasa hannu tare da bismilla na dauka  magani ne, amma kadan ne aciki, da alamun shine maganin da aka zuba mawa yaya Khalid!!! Na kare fashe wa da kuka, ina kiran sunayen Allah da Neman tsari.

A haka har na koma dakina inata kuka, daga sama naji muryan mahaifini yana Shahrazad Shahrazad Shahrazad kina ina , nayi saurin goge hawayena tare da fitowa , nace baba gani, yauwa dama zan fada miki ne gobe dangin mahaifiyar  ki zasu zo, za akawo kayan sa ranar ki.

Don jiya Khalid yasanar mawa baban sa yana so kayi bikin Ku da wuri, saboda nanda wata biyar zai koma abuja da zama, saboda aikinsa.

Karaf akunnan mama indo cikin kaduwa tace alhaji me kace”” ya kara maimai ta  mata,,, tace alhaji ai wannan maganar banxa ne, bayan yaron nan yaciwa Shahrazad mutunci, yace baya sonta   baya kaunar ganin ta, nan yarinyan nan ta dawo tana kuka,, tace ta hakura dashi har abada.

Sannan kuma yanxu zaka zomana da wani  maganar da baida ma’ana, baba ne yace indo kinsan abunda kike fada kuwa, anya kina cikin hayyacinki kuwa?  Kwarai da gaske ina cikin hayyacina.

Ai ga Shahrazad din agaban ka, katambayeta kaji gaskiyar maganar “” tunda baka yarda da nawa ba,!!; baba ya juya ya kalle ni, alokacin fuskata duk tagama jikewa da hawaye.  Kuma raina abace jin maganganun mama indo.

Budan bakina nace abba nah  duk maganar da mama indo ta fada maka, duk shiri nane,  nayishi akan wani dalili.

Cikin zabura mama indo tace mun ke Shahrazad me kike nufi da shirin kine “” karki cemun , duk abunda Khalid ya miki karya ne, babane yace shin lafiyarku menene kuke haka Ku fahimtar dani yadda zangane.

Nace baba bara na maka bayani,  nan na kwashe komai na fada mashi, amma ban fada mashi mama indo taje gun mallami ba, na rufa mata asiri awannan”” haka baba yayi salati yayi sallallami yace!!! Yanxu indo abunda kikayi yadace kenan, saboda son zuciya da kuma sharrin zuciya zaki raba Shahrazad da Khalid “”” sannan kuma ki hada yarki nafeesa da Khalid din.

Fisabilillahi atunaninki kin kyauta kenan, amatsayin ki na uwa”” amma kin bani kunya ,, koba ke kika haifi Shahrazad ba ,amma jinin kice ita,”” abunda zaki so yarki dashi yakamata itama kiso ta dashi!!! Tun ba yau ba kike azabtar da marainiyar yarinyannan, inke akama yarki haka zakiji dadi,”” to ina jan  kunnan ki akan kishiga hankalinki ki nutsu”” inba haka kuma duk abunda ya biyo baya kekika sani,, ya juya abunsa ya tafi.

Bayan tafiyar sa cikin kunan rai mama indo tace wato ina miki kallon shiru shiru Ashe ke babbar muna fika CE”” to ki kwan da sani muddin in ina raye baza ki taba auren Khalid ba,, nafeesa ce zata aureshi , duk Wanda yaja dani kamar yaja da mutuwar sane, tana gama fadar haka, ta kama hanya ta wuce,, yayin da ni kuma azuciyata ta sai cewa nake, ta Allah ba taki ba.

Bayan kwana biyu

Yan’uwan mahaifiyata zun xo, yan gdan su yaya khalid sun kawo kayan sa rana, da kudin gaisuwa , inda suke neman alfarman bada kudin sadaki atare kawai,,  kuma sun amince anbada kudin sadaki dubu hamsin.

Cikin gida kuwa wata kanwar hajiyata tace niko Shahrazad , Ashe haka kike zama da wannan indon,, nace inna me kika gani, hmm daxu ne naje bayi ina dawowa  naci karo da indo, ta wani rike kugu sai girgiza takeyi, tana habaice habaice, har tana fadin ayi dai agama Khalid dai na yatace nafeesa, idan ba abar mana shi Dan Allah ba, za abashshi don wuya, shine abun ya daure mun kai, da alamun akwai Yar tsama ciki,, shiyasa nace bara na tambaye ki, don ko sai antashi tsaye da Neman kariya wajen ubangiji!! Hakane inna.

Nan na bayyanawa innatah, yadda muke da mama indo, haka itama ta dinga salati da sallallami,  wato Shahrazad shine baza ki kira waya ki fada mun ba, da sai ataimaka maki da wani Abu, don naga wannan matar bata da karki ko kadan don zata iyayin komai.

Muna cikin magana ne, autan  su hajiyata yashigo Wanda muke ce mashi kawu mamudu

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

       75 & 80

Shahrazad tace karku damu kuci gaba da bina.

A kwana atashi  ba wuya lokacin bikina  sai kara matsowa ya keyi, yan uwa sai shiri sukeyi .

Yayinda nafeesa kuma abun duniya duk ya dame ta, kamar zatayi hauka “” ta hana kanta fita ko ina tana daki in banda kuka ba abunda takeyi !!! Mahaifiyar tata tayi lallashi har ta gaji. 

Mama indo ta kasa zama kullum sai aikin fitan nema mawa yarta farin ciki, amma ina ba sa’a.

Yau saura wata daya aurena,  innata tazo  daukana ta tafi  dani,, don za amin gyaran amare.

Da kyar babana  ya barni, ana gobe za mu tafi, Khalid yazo gidan mu da daddare, ya kirani awaya yace gashi nan awaje  nace to yayana.

Na Dan gyara fuskata   na fita, da sallama ta na isa wajen sa”” yaya nah y kake dafatan kana lafiya,, amaryata ina lafiya” ya shirye shiryen tafiya !! Gashi nan sai yinta muke .

To madallah yauwa ga kayan nan Wanda zaki bada dinkin fitan biki, yauwa kaga dasu ma zan tafi, dama kawu babayo yace inkawo zai dinka min, toh shikenan ma.

Khalid yace Shahrazad nace na’am yaya Khalid yanxu tafiya zakiyi ki barni !!! Kai yaya nah, bafa dadewa  zanyi ba, zafa agyara maka nine, baka son ranar bikin in kara kyau ne,, kai ina so mana,, aidanafi kowa murna ganin amaryata ta hadu,  nayi dariya “” to ai nasan sai kafini haduwa yaya nah,, hmm wlh Shahrazad kin iya zolaya,,, ni na isa ki hada kaina da ke!!! Kinsan nesa ba kusa ba, kin fini kyau ,, ke ingaya miki duk fadin unguwan rimin nan banga wacce tafiki kyauba.

Wayyo Allah yayana kadai na sa kaina ya kato   , eh mana gaskiya na fada my lady to godiya nake my prince.

Khalid yace ga 20,000 kudin dinkin ki, wannan kuma 30,000  ne kiyi tsaraba dashi sai dai ba yawa, kai yayana wannan kudin sunyi yawa gaskiya ka rage.

Haba shazee ina yawa anan ni awajena ma sunyi kadan wlh, don kinfi komai awajena, to yaya Khalid nagode Allah ubangiji ya kara budi ya dauka ka ka duniya da lahira ameen kanwata.

Allah ubangiji ya kaiku lfy ya dawo min dake  lafiya, ameen, toh bara nashiga ciki, OK Allah ya tashemu lafiya.

Washe  gari muka kama hanyar kano, ba karamin murna nayi ba da ganin yan’uwana , nashiga cikin dangi, duk inda nabi ace ai Yar gidan marigayi yace, sai da muka kara kokawa na rashin hajiyata,, nasha gyara ba kadan ba, har wani canxawa nayi.

Gida kuwa mama indo sun rasa ya zasuyi duk hankalin su ya tashi, gashi ta sa babana agaba wai sai dai a hada auren mu nida nafeesa,, baba yace indai tasamu miji  tsab kuwa zan hadasu aure ita da Shahrazad”” alhaji baka gane nufina ba?

Toh me kike nufi,, ina nufin a hadasu su biyun a aurawa Khalid din tunda ita nafeesan tana son sa, haka baba yasake baki yana kallon ta cikin mamaki.

Shin wai indo yaushe kika fara haka ne ban sani ba,, Khalid din ne yace miki yana son nafeesa ko kuwa sabagen iskanci ne kika zo min dashi yaja tsaki  mtssssw yayi wuce Warsa.

Indo kamar tasa hannu aka tace wayyo.

Ina kwance kan gadon kakana na dauki wayata nakira angona muna hiran soyayyar mu, yace shazee nah wai yaushe zaki dawo ne “” nayi missing dinki fa, kinga saura sati daya biki fa, kar ka damu my one jibi zamu dawo.

 

OK Allah ya kawo min ke lafiya amin,, my shazee kinfi kudi, mota , gida, ke rayuwace ,kina Jan ragamar soyayyata, nima haka my prince,, kagama mallakar zuciyar shazee,, shazee taka ce insha Allah da haka har mukayi sallama dashi na kwanta.

Yau litinin mun kamo hanyar zuwa Kaduna, tun a hanya nake kiran yayanah , yana ringing amma ba adauka ba” almost 20 misscall ba adauka ba!! Har muka isa Kaduna lafiya, muna shigowa cikin gida naci karo da nafeesa a zauna kan kujera tayi tagumi, tana ganina ta ballamin harara, nayi wuce wata  daki,  su innama suka karatso.

Dama baba yasa angyara dayan dakunan don saukan yan biki”” na diba ruwana naje na watsa tare da dauro alwala nayi sallah, naje dakin babana don gaisheshi amma baya nan.

Hmm

*ranar* *da* *bazan* *taba* *manta* *waba* *arayuwata*

Kuka ne ya kwacewa Shahrazad, su fitama da basu San menene ba suma suka fashe da kuka” cikin raunin murya Nusaiba tace aunty shazee mai ya faru pls ki fada mana.

Da kyar Shahrazad ta tsaida kukan ta, tace ina cikin dakina, naji nafeesa ta fasa wani uban ihu , maman ta sai lallashinta takeyi, tace kiyi hakuri nafeesa insha allahu Allah zai bayyana mana shi.

Nayi saurin kara sawa gaban mama indo, ina cewa mama lfy meke faruwa shiru mama tayi tana kallona, tare da Nuna alaman tausayawa, ta kasa magana.

Aunty amingi ne tashigo gidan mu da gudu ta rungumeni, ta baya tana shazee mun rasa yaya Kha___ kafin ta karasa na juyo afusace tare da girgixa ta, nace meye sa meshi karki ce mun ya mutu, don bazan iya jure rashin sa ba, pls kifadan gaskiya, duk nabi na kadu kamar mahaukaciya”” sai jin baba na nayi yana cewa sace Khalid akayi yau kwana biyu kenan babu shi babu alam____ ai kafin baba ya karasa na fadi sumammiya.

Khausar tace innalillahi wa’innailaihi raji’u sai tafashe da kuka, gabaki daya yan mata biyar din nan kuka suke.

Nima anan na ijye wayata don bazan iya ganin bayin Allah nan cikin wannan halin.

*TAKU* *Ummu* ( *nusnim*)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

        85 & 90

Allah ka kawo min sauki cikin rayuwata,, ni Shahrazad waye zan fitar amatsayin abokin rayuwana, Wanda zai rike ni da amana, ya kare mun mutuncina da maraicina, oh Allah anya kuwa zanyi auren nan,, don bana jin akwai wani namijin dazan iya kallonsa har muyi  soyayya sannan kuma ayi aure, kai banajin hakan zai taba yuwa,, Khalid kadai naba mawa matsayin nan,,,na kara fashewa da kuka nace babana  kayi hakuri tunda nake bantaba saba maka dokan  kaba “”” amma wannan karan bazan iyayin abunda kake so ba.

Hmm ni nusnim nace akwai aiki gaba, kucigaba da bina.

Shiri nakeyi don tafiya islamiya don na makara, nafito nakama hanyar zuwa misbahul”” ina tafiya ne na wuce wajan dondazon maza, sai naji suna cewa,, tunda masoyin ta ya bata haryanxu taki tayi aure”” gashi shekarunta sai  tafiya yake tana kara kwantai”” inbatayi wasa ba me mata uku ko biyu zata aura, don ba saurayin dazai auri wannan tsohuwar, suka kwashe da dariya .

Tuni nakara sauri sakamakon hawayen dake zuba da gudu gudu a fuskata, zuciyata kamar zata fashe saboda bakin cikin, nasa hannu na, don goge fuskata, sai naga anmiko min abunda zanshare fuskata, , tare da cewa karbi ki goge hawayen ki , kar mutane su gani.

Da sauri na karba ko kallon mutumin banyi ba, yace kiyi hakuri ki dunga addu’a kuma ki dinga saka murmushi afuskarki,, kar agano kina da damuwa, bayan na goge na mika masa abunsa amma ko kallon sa banyiba sai dai nace na gode  “” nawuce abuna ina zancen zuci ina Allah wadai da wasu mutanan!! Da haka har nakarasa islamiyan.

Shiko mutumin nan yace Allah sarki baiwar Allah, daga ganin ta kaga damuwa atattare da ita”” Allah ga baiwar kanan tana cikin damuwa ka yaye mata, ka kawo mata haske a rayuwarta ameen ya Allah.

Su Fatima suka ce aunty shazee amma  mutanan nan yan iskane wallahi, sai Allah yasaka makin” waya sani ma ko suna Neman shigane sunga ba fuska  shiyasa suka miki haka.

Nace sosai ma kuwa dayawa daga cikin su sunsha zuwa wajena da zancen soyayya sai dai nabasu hakuri”” shiyasa suka miki haka, Allah ya miki sauyi da mafi alkhairi ameen.

Da aka tashi islamiya na biyo hanyar gidan mu ,, zan shiga gida kenan  naji abaya ance assalamu alaikuma ya mu’allima ? Cak na tsaya batare da na juyo ba, na amsa nace wa’alaikumus salam batare da najuyo ba.

Yaci gaba da cewa ba mallama inba zaki damu ba ina son yin magana dake  ,, gaba nane ya fadi , nasan bazai wuce zancen soyayya ba,, nayi saurin ce mashi mallam ni matar aure ne inada miji” yayi saurin cewa subuhanallah, amatsayinki na mallama bakiyi kama da maiyin karya ba,”” gaba nane naji ya kara fadi.

Yaci gaba dacewa ni nasan ke ba matar aure bace, kuma nine mutumin da ya baki Abu daxu da safe kika goge hawayen ki,, cikin xuciyata nace ya ilahi”” me wannan mutumin yake nufi da nine? 

Yace kar ki damu ba komai nake nufi dake ba sai alkhairi,, na zaro ido waje tare da to she bakina wato yaji zancen zucin danayi.

Na bude bakina kenan zanyi magana sai ga babana yazo zai shiga gida, sai washe hakora yakeyi, alamun yana cikin farin cikin ganina na tsaya da saurayi.

Nace sannu da zuwa baba yauwa baba ya mika mawa mutumin nan hannu don musabaha,, amma sai ya noke hannun sa ya tsugunna kasa yana gaishar da baban!!! Baba yaji dadi sosai,, ni kuma ganin haka kamar in kwasa mawa mutumin nan mari”” tuni nayi shigewa ta gida, baba yace Dana ya sunan ka?

Kuma me ke tafe da kai?

Wannan saurayin yace baba ni sunana Muhammad sauban, ina zaune a unguwar malali”” to nakan shigo  unguwar rimi wajen abokina dake ramat close”” to garin wuce wa nane , nake ganin mallaman nan,, kuma duk sanda zanganta cikin damuwa take”” shine take bani tausayi, na tsinci kaina da son shiga cikin rayuwarta, na kulla alaka mai karfi tsakanin mu, wato ina son in aureta, tazama mata agareni in Allah ya yarda.

Baba har cikin zuciyarshi yaji dadi ya kuma yaba da hankalin Muhammad sauban, baba yace Muhammad, naji dadi da jawabin ka “” kuma nayaba da hankalinka!!! Na baka dama ka nemi soyayyar yata Shahrazad”” amma zakayi hakuri da yanayin ta, kamar yadda kace kana ganinta cikin damuwa”” wannan tabbas haka yake sakamakon rashin masoyinta da tayi.

Nan babana ya bamawa Muhammad sauban labarina, sai da ya zubar da hawaye sosai tare da kara tausaya min, yaji sona ya kara karuwa acikin zuciyan sa.

Yace baba insha allahu zansa mawa Shahrazad farin ciki azuciyar ta, fatana kawai baba kabani ita . baba yayi murnushin jin dadi nabaka ita sauban, amma ka nemi yardan ta, to nagode sai anjima.

Niko ina zaune adaki sai safa da marwa nake , saboda naji shiru baba bai shigo ba” ko lafiya?

Na kara lekawa inga ko yashigo , cikin zaure naji motsin mutum alamun za ashigo cikin”” nayi sauri nashiga cikin dakina!!! Ina lekansa ta window din dakina,, baba ne yashigo sai murmushi yake shi kadai””” cikin xuciyata nace ko lafiya baba ke murmushi .

Koma dai menene intayi tsami maji.

Ina ganin mama indo tashiga dakin baba, tace sannu mallam dama Naxo ne muyi magana akan Shahrazad, inajinki mallam ya kamata ace ka aurar da yarinyar nan, tunda taki ta fitar da miji , ya kamata kowaye ne muzaba mata mu bashi, ko ni insamo mata miji,  don nagaji da surutan mutane wallahi”” baba yace hakane karki damu insha allahu kwanan  xatayi aure don akwai Wanda yazo Neman aurenta yau”” mama indo tayi kicin kicin da fuska tace mallam yo ni ai har na Mata miji ai, dama Dan gidan kawata ma’u ne yazo wajena yana kuka wai shi inba abashi Shahrazad ba zai iya mutuwa,,  mallam yace tofa.

Su khausar suka kwashe da dariya suka ce amma wannan matan muguwa CE, gaskiya bata sonki da alkhairi,  naga alama mugunta take hada miki!! Nayi dariya nace sosaima kuwa.

Fatima yace aunty shazee wai meyasa baki kalla mutumin dayazo wajenki ba, Aida kin bayyana mana ya kamannin shi yake,, wallahi haka nan kawai natsani kallon mazane.

Ni’ima tace nikam yamin  kuma daga gani zaiyi kusan halin Yaya Khalid, ga sunan shi mai dadi *Muhammad* *sauban* nice name, dukkan su suka kwashe da dariya saboda yadda ta fadi sunan.

*taku* *Ummu* *ruman* (nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

 *BY* *NUSNIM*

        90 &100

Washegari ina zaune adakina , naji sallamar wani yaro atsakar gidan mu, mama indo ta amsa mashi”” yace wai ana sallama da Shahrazad awaje!!! Mama indo tace je kace injiwa, ya koma wajen shi , yace” kace inji Muhammad sauban.

Ya fada mawa mama indo daidai lokacin nafeesa ta fito zata fita,, mama indo tace yauwa nafeesa Dan Allah jeki duba wani kalan mutumine yake kiran Shahrazad!!!  Taya mutsa fuska  tare da cewa toh, duk akun nena ake abun,, nafeesa ta fita cikin yanga  da yauki kamar mai nemar kai.

Yana ganinta ya daure fusaka itama ta daure fuska tare da jan tsaki,, tace dama kai ke Neman Shahrazad, yace eh nine'”” ko ban isa bane? Ta bushe da dariya, injiwa harkayi yawa ma, kai amma naji dadin zuwanka saboda Kaine ka dace da wancan kucan shazee din, takara bushewa dariya, sannan ta wuce cikin gida, xuciyarta  cike da farin ciki, saboda kalan na mijin da take so in aura kenan.

Mama indo tace nafeesa lafiya naga kin shigo gida cikin annushuwa, ki fada min yaya mutumin yake mai kudine ko talaka, nafeesa tace hmm mama ki kwantar da hankalin ki.

Ai ingaya miki talaka ne shi jagab, sannan kuma ustaz ne, gashi bai iya Shiga ba kullum kya ganshi cikin jallabiya,, mama indo ta washe baki tace yauwa, har naji dadi.

To amma ke a ina kika sanshi, wallahi alayin su kawata bilki nake ganinshi malali,, gashi yasa mana ido nida ita, ba daman ya ganmu munci ado za mufita sai, ya dinga mana wani wa’azi ,, ko kuma ba dama yaga samarin mu sunxo daukan mu, ya dinga cemana kuji tsoron ,, sai kace munce mashi ba mujin tsoron Allah!! Yacika sa ido.

Duk ina jinsu ina Allah ya wadai da halin su,, mama indo naji ta kwala mun kira, nace na’am mama,, kifita waje ana sallama dake nace mata to”” cikin zunburo baki nafita!!!  Na karasa wajen shi tare da sallama , ko kallansa banyi ba, yace mallama har nagaji da jira da har ina shirin tafiya, sai nace mashi Aida ka tafi ma”” yayi murmushi yace saboda baki son zuwana ko, bance  komai ba.

Yace mallama Shahrazad kenen suna mai dadi, nace nagode,, da fari dai sunana muhammd sauban, Ina zaune a malali ,,ina yawan zuwa unguwan nan wajen abokina, nan ya bayyana mun komai kamar  yadda ya fada mawa babana,,  ina jinshi ban ce mashi komai ba.

Yaci gaba da cewa da fatan zaki taimaka mawa xuciyata ki bata matsugunni koyaya ne don Allah!! Wallahi Shahrazad ina sonki ina kaunar ki, kallamanshi sun sa xuciyata zafi tare da hawaye, ban San lokacin da na daga hannu na ba nace dakata sauban!!

Wannan Kalmar awajen mutum daya  nafiso injishi, awajen shi yake mun dadi shi daya tal”” kuma shine kadai yacika xuciyata, bai bar waje ko kadan ba,, duk yabi ya toshe ramukan dayasan wani Abu zaishiga,, yacinkushi , ya matse, ya manne, sannan yasa  Abu mai karfi ya rufe”” shin ka  gaya mun ta ina kake son na ijyeka sauban? Ta ina sauban? Ta ina sauban?

Please tell me sauban, na kara fashewa da kuka.

Cikin karayan zuciya yace shazee ki daina kuka please. Kukan ki yana daga mun hankali wallahi, shazee kefa musulmace kuma kin San ance muyi imani da kaddara mai kyau ko Mara kyau”” sannan kuma karki manta fa yau kusan shekaru hudu kenan babu Khalid babu alamarshi , kamar yadda baba ya fada mun, ina so ki nutsu kije kiyi tunani mai kyau,, kiga menene yakamata ki fuskanta  ayanxu? menene ya dace da rayuwarki? , Shahrazad kefa ba yarinya bace bafa yanxu. Nidai ki daure ki sama mun matsugunni ko kadan ne !!! Nace uhmm .

Yayi murnushin takaici, yarasa ma da mai zaiji, ga rashin kallon sa da takiyi”” ga rashin bashi dama  da takiyi “” yauwa shazee ni kam menene alakarki da wannan yarinyar da ta fito daxu, nace yar’uwa tace, sai yace gaskiya kudinga mata fada ta gyara halinta,  tana biyewa kawayen banxa alayinmu suna zuwa club, nayi saurin cewa , yanxu abunda nafeesa keyi kenan yace eh wallahi,, duk randa na gansu sai na musu nasiha, kuma su zageni, bashi kuma zai hana gobe inki musu magana ba.

Nace Allah ya kyauta, angode da kulawa, ni zanshiga gida, najuya zan tafi yace shazee please meyasa baki son kallona ?ko kamanni na baki saniba fa.

Nayi Dan yake, nace  mutun daya nake kallo, yace to Dan bani numbern ki, da kamar ta kyalesa, sai b nace bani da waya, yace to ga tawa dayan, na dafa goshina nace kash, wallahi kacika naci, nace ya bani wayan nashi nasaka mashi number Nah, da murnarsa yabada wayan!! Ina gama samashi nayi shigewata cikin gida ko sallama ba muyiba.

Yabi bayana da kallo yace shazee iyayen rigima gaskiya zanyi fama kafin na shawo kanta.

Fatima tace aunty shazee gaskiya baki kyauta mawa sauban, yaci ace ko yayane ki Dan sassauta mashi, kin San kowa da kalan da baiwar da Allah ya masa,.!! Khausar tace wallahi ya bani tausayi Allah.

Shahrazad tace haba Ku kuwa kawai sai, inbashi dama azuciyata, kai da wuya wlh , na Khalid ne kadai Nusaiba tace hmm aunty shazee ance kaso mai sonka fa,, kuma kifada mana dalilin kin kallon fuskan sauban, zakuji anan gaba.

Aiko mallam na dawowa mama indo tayi saurin Shiga dakinsa ta zauna, tace mallam da magana fa? Yace Allah yasa lfy indo , lafiya lau Dama zancen makane_____.

*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

    100 & 105

Mama indo tace mallam da magana fa? Yace Allah yasa dai lafiya indo, lafiya lau ba komai bane face maganar auren shahrazad*” yau naji gidan biki, kawai naga anata nuna ni abun ya daure mun kai, nace Niko menayi ake nuna ni?

Shine na tambayi wata mata tace, cewa ake kunki aurar da Shahrazad wai kuna jiran mai kudi, mai mota, Wanda zai dinga taimaka mana dawasu abubuwan!!! Har ana cewa wai duk samarin unguwan nan sunxo Neman aurenta ka hana sai mai kudi,, baba nah ya rike baki yana innalillahi wa’innailaihi raji’un”” kai mutane basu San komai sai Allah yayi ba,, tun kafin kazo duniya Allah ya Riga da ya rubuta maka abubuwan da zakayi,.

Baka da ikon yin Abu da kanka har sai Allah ya baka iko”” mama indo tace hakane,, amma mallam nikam dazu wani yazo wajen Shahrazad sunanshi kamar saudan ne ko saudin ne, oh dai bansani ba,, mallam yayi murmushi yace sauban sunan”” yauwa shi kuwa, mama indo tace wallahi nayaba da hankalin yaron ,”” kuma da alamun shi da gaske yake zai aureta.

Naga babu alamun wasa awajen sa,, gashi yana sonta sosai,, baba nah yaji dadin maganganun mama indo.

Baba nah yace tabbas kuwa Muhammad sauban yanada hankali da natsuwa da kuma addini, nima kaina na yaba dashi kuma nayiwa Shahrazad sha’awar auren sa,,, mama indo tace to mallam me zaihana kawai kace ya turo magabatan sa tunda ka gamsu da yaron!!! Mallam yace eh kuma hakane,, amma kafin nan bara nasa amin bincike akansa.

Mama indo ta ya mutse fuska, alamun bahaka taso ba, tace acikin zuciyarta bara dai nabi komai a hankali, don karna ruguza shirina, sai nayi yake nace hakane kam”” kayi gaskiya,, Allah ya taimaka ameeen.

Bayan kwana biyu babana  yasa an mishi binciken Muhammad sauban, anfada masa daga gidan mutunci ya fito, iyayen sa, dadtijan kirki ne yaji dadi sosai.

Kwance nake kan gadona ina tunanin menene mafita” gashi baba Nah ya takura mun akan sai na fidda miji”” ni kuma duk ba Wanda ya min!!!  Ga sauban nan ya takura mawa rayuwata, yahanani sukuni, ya matsamin!! Gashi ni bayyimun ba , bansan kamannin sa ba, ban San halinsa ba,!! Kuma bana bukatan na sani .

Wayyo Allah Nah na fashe da kuka, na jawo jakata  na Ciro hoton Khalid dina Wanda ya dauka da sallah, ba karamin kyau yayi ba”” andaukeshi yana murmushi , ban San lokacin da nima murmushi ya subuce munba.

Na Shafa hoton tare da cewa Khalid sonka Allah ne  ya sanya  min shi a cikin xuciyata, ya narkan mun dashi yadda babu wata hanya da za’a iya fitar dashi har abada.

Abin burina  Khalid , Khalid naka sance  cikin rashin walwala da nishadi , bani da wani abun tunani sai kai “” shin Yaya zanyi da kaina “!! Kaine tauraro daya mallakin xuciyata, babban ranar bakin cikina shine ranar da narasaka Dan Allah ka dawo gareni”” na fada kan gadona tare da rungume hoton a kirjina, da haka bacci mai dadi ya kwashe ni.

*wanene* *Muhammad* *sauban*

*Atakaice*

Muhammad sauban da ne ga alhaji aliyu, da naja’atu, asalinsu yana garin gashuwa ne, aikine ya kawo alhaji aliyu da iyalan sa Kaduna a unguwan malali laberia raod, babban dansa  shine Muhammad sauban, sai Saadiqa sai Yusuf sai Nabila, sannan sai autan su salim, Saadiqa ce kawai tayi aure acikin su,  yayin da Nabila take secondary school autan su salim yana j. S.S .1, Yusuf kuma yana jami’a nan kasu,, yanxu haka ana fama da sauban akan ya fito da matar aure sai dai yace had yau baiga wacce ta dace da rayuwar sa ba, ana haka Allah ya hadashi da Shahrazad Inda ya fada tarkon sonta!!! Wannan kenan.

Cikin bacci naji wayata tana kara da kyar na daga wayata nasaka akunne na tare da cewa hello”” wato bacci kike ko gimbiyata? Ban San lokacin dana ja tsaki ba tare da cewa kaga ni gaskiya kana takura mawa rayuwata dayawa fa!!! Dan Allah ka kyaleni sauban, tana kiran sunansa ya lumshe ido tare da jin dadin hakan.

Naci gaba da cewa haba haba na fada maka gaskiya amma duk da haka kaki ka kyaleni, sai kace ni kadai ce mace,  yayi saurin taran numfashina yace tabbas ke kadaice maccen danake gani”” sauran matan ina masu kallon maza ne yan’uwana !!! To ai sai kai tayi kit na kashe wayata, gaba daya .

Bangarenshi kuma wani siririn hawayene ya gangaro idanun sa, yace Allah kabani ikon cika wannan alkwarin Dana dauka,  ameen.

Baba Nah yasa nakira mashi sauban awaya yace yazo yana son ganin shi, gabana sai faduwa yakeyi saboda ban San me baba na zai ce masa ba.

Bayan sallar isha’i yazo wajen baba Nah yace mashi yabashi dama ya turo da magabatan sa ayi maganar aure, ba karamin dadi sauban ya tsinci kansa aciki ba”” sai godiya yakewa baba!!!! Baba yace bakomai duk anxama daya,, sauban ko tsayawa bayyi ba  sungaisa da shazee yayi tafiyar sa gida.

Yana shiga yaga ammin sa azaune ita dasu Nabila da salim, da sauri ya karasa wajen amminsa ya rungumeta cikin murna, tace son  lafiya wannan murna haka, ammina anbani shazee ance naturo magaba  tana””” Nabila tace wooow bros bravo alaika, gaskiya natayaka murna, salim yace me too bros am happy for you, thanks to you all.

Yanxu bara daddy ya dawo sai infada mashi, yauwa ammina, yanxu dai bara nayi wanka  sai inzo mu tsatstsara abunda zamuyi, OK son””‘ sauban nashiga  daki  ya danna wayansa yakira wani layi, tare da cewa komai yakusan dai daita fa, anbani ita, sai ya kyalkyale da dariya batare da nasan  me aka fada masa yasa shi dariya ba.

Ina zaune daki babana ya aiko mama indo takirani, muka taho tare, nagaishe shi, yace Shahrazad ba komai bane yasa nakira ki , illa infada miki na ba mawa sauban ke nace ya turo magabatan sa, za ‘asa ranar aure, nanda wata daya ko biyu, shine nace bara na fada maki”” kiyi hakuri haka Allah ya rubuta miki, aibansan lokacin da nafashe da kuka ba, nace baba kayi hakuri wlh bana sonshi.

Ka kara mun lokaci zanfitar da miji, baba nah ya harzuka ya fara fada”” yace maganar banxa zan zauna ne inxuba making ido kikiyin aure, mutane na zagina a unguwa to wallahi baki isaba kibar ganin ina lallabaki”” mama indo tace shashasha kawai ki godewa Allah kin sami saurayi wanda ke sonki, ba mai mata ba.

Da gudu na tashi na wuce dakina tare da tsanar sauban da mama indo, sai surutu nake  cikin bacin rai nace wallahi sauban bazan aureka ba,” sai dai ka mutu”” bangaren zuciya tane naji tana cewa, aiko in kina gidannan to dole sai kin auri sauban.

Shawara kawai ki gudu shine mafita, da Sauri na’aminta da sharrin xuciyata” sai ga murmushi ya kubuce mun, nagoge hawayena, nashiga hada abunda zan bukata nasa ajakata”” nafito gidan mu ba Wanda ya gani, har na wuce kofar gidan su Yaya Khalid ” sai nadawo baya  na kalli Inda Khalid ke zama, da Inda yake parking din motarsa!!! Kawai nafashe da kuka INA cikin kukane naji andafa ni”” da Sauri na juyo aunty amingi ce cikin murna na rungumeta, nace aunty amingi yaushe kika zo?

Tace dazo da rana ” ayya da mijinki kuka zo eh wlh,aunty amingi tace shazee meke damunki haka kike kuka, kuma INA zaki haka? nayi shiru ta kara tambaya ta””  naga bazan iya boye mata ba, kawai nafada mata halin Dana ke ciki da kuma Inda zani.

Ai bansan lokacin da aunty amingi ta daukeni da mariba  sau  biyu har sai da naga star.

Hmm ana wata ga wata

*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

   105 & 110

Ai ban San lokacin da aunty amingi ta daukeni da mari har sau biyu sai da naga star.

Cikin mamaki na daga ido nake kallonta, ita kuma sai zubar da hawaye takeyi”  ta finciki hannuna ta jani gidan su har cikin dakinta, ta jefani kan gado,, sai a sannan na fashe da kuka, itama ta fashe da kuka.

Sai da mu kayi mai isar mu sannan mukayi shiru!! Aunty amingi ne tafara cewa haba  Shahrazad haba Shahrazad,, yanxu don baki da hankali saboda auren nan zaki bi  sharrin zuciyar ki ki  gudu kibar gidan iyayen ki?

In kin tafi kin San Inda zaki? Kin San me zaki hadu dashi? Kin San hannun wa zaki fada? Mecece ribarki inkin bar gidan iyayenki? 

Yau mahaifinki ya wayi gari yaga babu ke kin gudu, shin kin San me zaifaru dashi? Kin San kalan bakin cikin da zai kunsa? Kila saboda guduwan ki ya fada cikin mayuwacin hali? Kinyiwa Khalid adalci kenan in kin gudu, na tabbata da zaiji haka!!! Bazai taba barinki ki aikata haka ba.

Tunda babu shi to nima bazan taba barin ki aikata haka ba”” haba Shahrazad meyasa har yanxu kin kasa dangana ne, shekara hudu fa kenan babu Khalid babu alamun sa, kinga ko bazai taba dawowa garemu ba.

Ni Nafi  jin araina Khalid baida numfashi,, nayi saurin cewa aunty amingi kar kice haka”” Khalid dina yana nan kuma zai dawo gareni insha allahu.

Amingi tayi murmushi ta karatso kusa dani tana goge mun hawayena, tace shazee ban San wani irin so kike mawa Khalid ba, ko uwar data haifeshi ce sai haka, dake da aunty Hauwa wato(mahaifiyar Khalid) kun kasa yarda Khalid bazai dawo ba,, ina rokan Allah daya  cire mukushi.

Shazee kiyi hakuri kiyi hakuri” kibi zabin mahaifinki,, gaskiya yake fada miki, kuma shi mai sonki ne, ba zai so wani Abu ya cutar dake ba,,” yau da hajiya tana da rai ni natabbata baza ta taba barin kikai haka batare da kinyi aure ba”” nace tabbas maganarki gaskiyace aunty amingi hajiya baza ta bari ba.

To kin gani, kinga ko bakaramin kokari baba ya miki ba daya barki bakiyi aure ba, yanxu sai ki mashi biyayya kamar yadda kika saba, kiyi auren” kuma kiyi hakuri, kiyiwa mijinnan naki biyayya kamar yadda zakiyiwa Khalid.

Inkinyi haka ba karamun dadi zamuji ba, shima Khalid zaiji dadi sosai!! Na rungumeta nace nagode aunty nah   , insha Allah zanyi duk abunda kikace,, yauwa kanwar mu ko kefa.

Amma da wai zaki bar gida,, kuma yin haka ba karamin kasada bane,, don yanxu yawancin yan  mata haka sukeyi, subar gida, Wanda hakan baida kyau, gujewa umurnin iyaye,, sai kaga Allah ya jarabce ka da masifu kala kala, kabi karasa ya zakayi.

Amma idan mukayi hakuri sai muga Allah ya kawo mana sauyi da mafita cikin sauki.

Hakane aunty Nah ,, Allah ya bamu juriyan rashin Yaya Khalid, idan yana Raye Allah kayi gaggawan bayyana shi”” inkuma baya Raye Allah kayi masa Rahma ka kai haske kabarin sa ,da ga bakin kofa akayi saurin cewa ameee muka   juya kallon kofan aunty Hauwa ce da Umar suka karaso ciki, tare da zama!!! Aunty Hauwa tace duk naji abunda kuka tattaunawa, kuma naji dadi, da Allah yasa amingi kika ga shazee, da badan kun hadu da itaba da ba musan  Inda take ba.

Nan aunty Hauwa tamun fada da nasiha tanuna min illar guduwa, jikina duk yayi sanyi, kuma nayi Dana sani.

Taci gaba da cewa dama dazu alhaji yake fada mun za ayanke bikin  ki,, nanda wata daya ko biyu,,  naji dadi sosai Allah yasa muna Raye sukace amin.

Umar cikin wasa yace aunty shazee, kawai ki aureni tunda muna kama da Yaya Khalid, ga baki dayan su suka kwashe da dariya, nace kai Umar baka da dama.

Amingi tace mama yanxu sai ki fara gyara Yar taki   tunda baza adau lokaci ba , aikuwa”” yanxu dai shazee tashi ki koma gida don kar aga bakyanan to, natashi na dauki jakata,  aunty Hauwa tace ki ijye jakar taki  daga baya  sai amingi ta kawo miki, toh aunty.

Na fito don tafiya GDA abakin titi naga nafeesa anci kwalliya za afita ta gabanta na zo wuce wa nayi kamar banganta ba!!!  Sai ji nayi tace haba matar ustaz ko magana babu, tana magana tana dariya .

Ban bata amsa ba na wuce azaure naci karo da baba Nah yace ke kuma daga INA, nace naje wajen aunty Hauwa ne , yace to nashiga gida yana kallona  tausayina babana  yake .

Fatima , NI’IMAH, Nusaiba, khausar, duk kan su jikin su yayi sanyi, ko wanne acikin su suna Dana sanin baro gidan iyayen su, yanxu basu San halin da suka sa iyayen suba, khausar ce tafashe da kuka, gaskiya gobe zan koma gida innemi gafaran iyayena, gaba dayan su” haka suka fada, Shahrazad har zuciyarta taji dadi !!! Dama tana so sukoma ga iyayen su, su Neman yafiyar su, Fatima tace, gaskiya aunty shazee Allah ya taimakeki da baki bar gidaba, gaskiya aunty amingi suna sonki sosai.

Ni’ima tace wallahi nima nasihar da suka miki, shi yasa ni, Dana sani, da biyewa sharrin xuciyata, gaskiya mun tafka kuakure, Allah ka yafe mana.

Cikin kuka Fatima tace mu da auren mu ma muka gudo innalillahi wa’innailaihi raji’un, Allah kayafe mana.

 

SHAHRAZAD tace Ku godewa Allah da bai kawo muku tsanani ba, bayan barinku gidan iyayen Ku da mazajenku,, Allah yana so kushiryu Ku gane gaskiya, inaga shiyasa ya hadani daku”” Allah kaya femana baki daya ameeen.

Iyayen sauban sunzo anyanke biki nanda wata daya, komai ankawo  , lefene kawai suka rage”” haka innata suka kara zuwa biki, ni nace bazanyi taro ba,  aunty amingi tace ban isaba, tace washe gari tana ban zuwa, dayake a abuja take aure. 

Aunty Hauwa ta dage sai tsumani takeyi  , amingi tazo  anshirya komai event daya kawai za ayi, shine Wanda amingi tashirya *sisters* *day*

Yau saura sati biyu biki aka kawo lefe baba da innata suka ce agidan aunty Hauwa za akai, , taji dadin karramawan da aka mata,, mama indo tace ba lefen daza taje  gani, don tasan bazai wuce akwati daya ba”” don haka nafeesa ta fada mata.

Aranar ma unguwar tama ta tafi”” masu kawo lefen sunxo bakaramin tarba suka samu ba, su Kansu wayanda suka kawo lefen sun raina kan su!!! Akwatuna ne Seti biyu wato gudu shabiyu”” ko wanne kaya ne ciki makil, , su aunty Hauwa suma sunyi mamaki kuma sunji dadi”” mutane yan unguwa sai zuwa ganin gulma suke!! 

Aiko tuni u/k ta dauka da lefen Nah, anata kananan surutu,, wasu suna cewa yarinyar nan datayi kwantai itace  zata auri saurayi kuma mai dukiya, bayan indo tace mana ustaz ne mijin daza ta aura baifi akawo akwati daya ba.

Khausar ta kwashe da dariya tace kai mama indo wato ita taje ta baza a unguwa ustaz zaki aura kuma akwati daya za akawo miki  kuma yana da mata”” takara fashewa da dariya !!! Yanxu intaji labarin akwatunan da aka kawo ya zatayi?

Nusaiba tace aikuwa dai, sai zuciyarta ta fashe, Shahrazad tace ai bara kuji.

Tana unguwan da take mutane ke kiranta sukace mata ankawo akwatunan shazee guda talatin, suka kara gishiri Amiya!!! Ai mama indo ta zabura tana karya kuke bayan akwati daya aka kawo ai nafeesa taga akwatin”” taitayi surutai, har  ta dawo gida bata yarda ba akwati daya aka kawo ba”” hankakinta atashe.

Innata da ta fuskanci haka gun indo bataso nayi auren dadi, sai ta fakaici idonta tace Shahrazad yanxu fisabilillahi kirasa wazaki aura sai ustaz masu kawo akwati daya,, aiko sai ga mama indo ta tashi da sauri”” tace kulu dagaske akwati daya aka kawo, innata tace eh wlh!!! Sai ga mama indo na washe baki ta wuce zaki!! ” innata tasaki baki tana kallon ta cikin mamaki”” Niko abunma dariya ya bani.

Aunty amingi ne take cemun, shazee nikam ya kukayi da sauban ne game dashirye shiryen biki. Ko zaiyi event ne”” na tabe baki nace ni rabona dashi tun lokacin. Da baba yace nakira masa shi, banma San kamannin sa ba

.

Amingi ta bude baki tace kai to Allah ya kyauta maki shazee, bani number sa, cikin turo baki na mika mata wayata”” tare da cewa nifa karkice yazo “” Dalla rude mun baki.

Ringing daya ya dauka tare da sallama nanta  yi masa bayanin kanta, da sauri natashi daga wajen don karta hadani dashi.

*taku* *Ummu* *Ruman*

(NUSNIM)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

  110 & 115

Ringing daya ya dauka tare da sallama , nan ta fara yi masa bayanin kanta””  nayi sauri natashi daga wajen don karta hadani dashi.

Daga bangaren sauban yace tuba nake aunty mu na rashin zuwa na”” gimbiyar ce bata son ganina!! Shiyasa” dama ina ta tunanin tayaya zan bada kudin hidimar biki tunda ba sanin kawayenta nasa niba.

Aunty amingi tace sai kayi hakuri da kanwar tawa, insha allahu komai zai dai dai ta” yace toh ya tabbatar.

Dama zan ce maka ne  zamuyi sisters day, ko daga bangaren ka akwai wayanda zasu zo”” yace eh inada kannai mata biyu insha allahu za su zo, OK nagode .

Yauwa aunty Dan Allah Dan turo min account number dinki, don zan turowa Amarya sako .

OK yanxu zaka gani!! To nagode, ba damuwa.

Bayan sun gama waya  ta tura mashi  account dinta , dayake G.T take amfani dashi, shima haka, yayi mata transfer din kudi mai tsoka taji dadi sosai, takirani take fada mun”” nace ni ba abunda zanyi da kudi aunty amingi.

Shahrazad wallahi ki Shiga hankalin ki inba haka ba in saba maki don naga abun naki iskanci ,toh zan gyara miki zama sorry aunty meenatah.

Nafeesa ce tashigo dakin su ta ga mama indo sai murna take, tace mama shin lafiya na ganki  cikin annushuwa, mama indo ta washe  baki tare dacewa ai ankawo akwatin Shahrazad  nan dai mama indo ta fada mata komai!! Itama nafeesan taji dadi sosai.

Shagalin biki ya kanka ma,  ba abunda nake tabukawa, sai sana’a ta na kuka Dana sa agaba””  dayake banda kawaye, kawata ta kusa tayi aure wato ummin A.A kuma taje naija,, shiyasa aunty amingi ta gayyato  kawayenta amatsayin kawayena!! Sai dai kawai inbisu da ido.

Yaune ranar sisters day din da aunty amingi ta shirya Wanda za ayishi a  17 hotl dake u/rimi kufaina road , ba karamin haduwa yayi ba, ba a iya fadan yadda hall din ya kayatu.

Sadiqa da Nabila sai shiri suke , bakaramin kyau sukayi ba,, sauban ne ya karaso wajen su yace sisters gsky kunyi kyaufa, tanx bros!! Sadiqa tace bros kai zaka kaimu ko”” no bani zan kaiku ba Yusuf ne ni akwai abunda zanyi ne ok., suna cikin magana wayarshi tayi kara ” yafita daga Inda suke don ansa waya, hello yadai sai naji yayi shiru ban San abunda ake cemai ba a dayan bangaren!! Sai gani nayi yasaki murmushi tare da zubowan hawaye a fuskar sa, yace insha allahu  komai zai dai dai ta,, sai ya kashe wayan da tare da sauke numfashi.

Aunty amingi ne zaune gabana tana gyara mun dauran  Dan kwalina, tace woow sister kinga yadda ki kayi kyau kuwa “” naturo bakina, nace nidai kidaina cewa nayi kyau bana so, sai ta fashe da dariya tace kalle yadda kikayi kamar karamar yarinya”” wata kawar amingi CE tashigo, tace haba amina kunxauna sai hira kuke duk mutane sun gama zuwa Ku kadai ake jira kawai.

To gamunan zuwa oya shazee tashi, zainab Ku taka mata abaya toh , da haka har muka karasa cikin mota   xuciyata bata min dadi idan na tuno da sauban za ayi auren nan, munkarasa cikin hall din aka sake sauti ma dadi mai tsuma, can na hango yan GRP din 

All dostis of nusfulhayat, su aunty rabi, yayar cool, Fatima, Firdausi, fauziya , Ummu Arfat, da dai sauran su ,.

Ba sai na tsaya fada muku yadda sister day din ya hadu ba, wannan na bar muku.

Bayan angama kowa ya koma gida da abun arziki don ba karamin Abu aunty amingi tayiba da bikin nan yadda kuka San yayan tah ke aure.

Zaune nake cikin dakin Yaya Khalid na kulle kaina  sai kuka nakeyi , ina tunanin yanxu haka I gobe nazama matar sauban, ya ilahi, Allah ka kawo min sassauci, da haka har bacci ya dauke ni.

Amingi sai nemana takeyi, ko ina ta duba bana nan , ko ina shazee taje ne oho, har ta gota dakin Yaya Khalid sai ta dawo da baya”” ta karema kofan kallo da alamun anshiga dakin ? Ta karasa wajen kofan ta  murda taji shi arufe.

Ta koma dakin aunty Hauwa ta dauko dayan makullin ta bude dashi, can karshen gado ta hango ni kwance na kudundu ne da bargon Khalid sai kuma hoton sa dake kirjina rungume.

Amingi ta fashe da kuka tare da cewa Allah sarki, shazee abar tausayi, har yau  dai dai da kwaya dayan son Khalid baifita aranki ba,, shin yaushe zai fita  daga ranki  ” ta daga hannu sama tana roka min Allah  daya cire mun Khalid”” tayi mun addu’oi ta Shafa mun , tare da gyara mun kwanciya na, sannan ta fitar tare da jawo min kofa.

Washe gari ya kama asabar ranar daurin aure nah  da Muhammad sauban , mama indo andage  sai aikin abincin biki  take, sai wajajen sha daya natashi bacci, kasan cewa bana sallah aranar ,, ni kaina nayi mama kin baccin danayi, kuma ba Wanda ya tasheni.

Bayan nayi brush na fito na kulle dakin na karasa dakin aunty amingi, zaune na gansu suna karyawa!!! Tace a’a Amarya kintashi, gaskiya yau kinsha baccin gajiya”” nace aikuwa dai!! Na zauna cikin su muka karya tare.

Bayan mun gama ne kowa yayi wanka ya shirya  har nima nasa atamfana mai kyau, sai akayi min kwalliya duk inda na gota , to sai nabar kamshi, ni kaina nasan na hadu sosai,   kowa sai su yake ya daukeni hoto.

Hmmmmmmm

Karfe biyu Masallacin misbahul Islam cike yake da  mutane yan daurin aure, can Nagano ango sai kyalli yakeyi tare da washe baki ga abokanan sa duk sun mamaye sa , can naji a na cewa an daura auren Shahrazad abdulmaleek da angonta Muhammad sauban aliyu, abisa sadaki dubu hamsin  !! Sauban ne ya daga  hannu sama yace alhamdulillah , Allah nagode maka   daka cika mana burin mu”” ina kuma rokanka da ka cika mana dayan burin mu daya rage.

Hmm masu karatu, wai mai sauban ke nufi ne, nifa banyarda dashi ba, koza Ku iya lalubo mana amsan., sai najiku.

Kawu mamudu ne yashigo gida yana ina matar sauban ta fito angonta yazo yana son ganinta”” innata tace mamudu nikam har andaura auren ne,, eh Yaya andaura yanxu shazee tazama matar sauban.

Daam naji gabana ya fadi, nace innalillahi wa’innailaihi raji’un, yanxu ni shazee nazama matar sauban kaicona , na fashe da kuka me tsuma zuciya, amingi ne ke lallasha, tana bam baki, kiyi hakuri shazee komai yayi farko zayyi karshe.

Bayan isha’i , babana  ya kirani daki yayi mun nasiha sosai , hakama baban Khalid, ban San lokacin Dana fada jikin ABBAN Khalid ba na kara fashewa da kuka, yashiga lallashina, da kyar yake iya magana.

Su aunty Hauwa  da innata sai da suma suka min nasiha, sannan akace Amarya su fito anxo daukanta, dakyar aka rabani da innata da aunty Hauwa.

Su mama indo da nafeesa sune kan gaba akai Amarya don suje suga kalan gidan.

 

An wuce dani unguwar malali inda gidana ke can kasan laberia raod , ana xuwa kofar gidan , mama indo tayi saurin cewa ai ba nan bane gidan, me tuka motan yace hajiya nan ne, ido ta zaro waje takasa magana, yayin da nafeesa ta sandare  azaune.

Mai gadi ya bude musu get  din gidan suka Shiga ciki, tsararren gidane Dan madaidai ci, mai tsari da fasali, ka shokoki kewaye da harabar gida, don haduwa kam gidan ya hadu, mama indo dakyar tafito daga mortar”” tare da sakin baki, kamar wawiya!!! Aka fito dani  har cikin dakina aka kaini , kayan dakin  , kayan dakin sun tsaro kuma ankashe kudi acikin,, wannan duk aikin iyayen Khalid ne, su sukace dole su zasu min kayan daki da komai na cikin gidan”” ba abunda zan cewa bayin allahn nan sai dai ince Allah yasaka masu da alheri ameen.

Bayan kowa yagama ganin dakin Amarya aka watse da kyar aka ja mama indo cikin mota, don ihu take tayi kamar mahaukaciya”” dagani sai aunty amingi sai kawayenta guda biyu.

Muna zaune har ango da abokansa sukazo, akayi siya baki, suka ga Amarya bayan sun bada kudi, daza su tafi da kyar aka rabani da amingi na kanka meta sai kuka nakeyi ,, itama kukan take,, ni kadai aka barni adakina sai tsoro nakeji,.

Bayan sun tafi sauban yashigo ya rurrufe ko ina na gidan, zai shigo dakina wayarshi tayi kara,ni kuma dake daki duk tsoro ya cikani, shine na fito don ba zan iya zama ba, fitowa ta kenan  naji”” sauban na cewa awaya ? zankiyaye .kuma ai alkwari na dauka don cimma buri, gaba nane ya fadi araina nace buri.

Jin magana abayanshi, yayi saurin jiyowa.

Hnmmmmm ana wata ga wata, mai karatu mai ka harsasu a wannan novel din INA kiran comment dinku, in ba haka ba baza kujini ba.

Ga mai son ganin sisters day din Shahrazad ya duba dp dina.

*taku* *ummu* *Ruman* (nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

   115 &120

 Jin magana abayan sa ya sashi juyowa, nace buri. 

Wani buri kake son cikawa , cikin takun kasaita ya taku wajenta, ya tsugunna fuskanshi dauke da murmushi,, a zuciya na ko cewa nake masha Allah yayi kyau anan, gsky sauban namijini mai kwarjini da haiba, na kafeshi da ido nima ya kafeni da ido”” kallon juna Muke kowannen mu da abunda yake saka wa a zuciyan sa.

Niko gabana sai harbawa yakeyi saboda kallon da yake mun irin na Yaya Khalid Sak, da badan kamanni ya banbanta ba”” to da babu abunda zai hanani cewa Khalid dina ne.

Ban ankaraba cak naji andaukeni kamar wata jaririya , ido kawai nake binshi dashi kamar wacce taga wani abun” ya direni kan gadona , na kara jeho mashi tambaya nace wani buri kake son cikawa?

Yace burin danake son cikawa shine, in rike Shahrazad tsakani da Allah, inbata  kula, in saka mata soyayyata, in share mata hawayenta, toh kinji, na sauke ajiyar xuciyata.

Yace toh ke me ya fito dake daga daki, na cinno bakina gaba nace, to ba tsoro naji”” gidan nan ma akwai aljanu Allah, sauban ya kwashe da dariya, yace, Ashe haka kike da tsoro tabdi jam zanyi fama .

Yanxu dai bara na dauko plate da cup da gazarki , ya miki kenan nima nayi zumbur na miki , yace lafiya kuma, ni wlh bazaka barni cikin dakin nan ni kadai , tare zamu.

Sauban yayi dariya cabdijam lalle shazee akwai Daru, toh muje yana gaba Ina binsa abaya ya dauko, tayashi da wani Abu dazamu dawo ciki, iskace  takada kofa, garam kakeji, ai bansan lokacin Dana ruga aguje na rungumeshi sosai , kayan hannu na, na watsar dasu.

Sauban ya rikice yace lafiya shazee, idona arufe yake gam, sai da ya girgizani sannan na bude ido “” nace wancan  kofan naji anturo da karfi.

Kai shazee iskane  fa , hadarine ya hadu sosai, ya tattaro kayan muka shige daki ,  na zauna akasa, shima ya zauna, yabude kazan , yazuba mana milk a cup,, nace nifa akoshi naki !! Yace ai kuwa baki isaba, sai kinci, inba haka ba infita daga dakin; duk abunda zai kama ki ya kamaki, yayi yunkurin tashi,  nayi saurin rike mashi Riga nace”” nace yi hakuri kazauna zanici.

Bayan mun gama ci, natashi nayi brush dina tare dayin alwala don banyi sallar isha’i ba,  bayan na tada sallah tah yayi min wayau  ya fita.  Dakinsa ya wuce yayi alwalar tare da wanka , ina kan abun sallata  ya shigo, nace shine ka gudu ka barni ko.

Tuba nake gimbiyata, natabe bakina, yace tashi muyi sallah mu godewa allah, ba musu natashi , amma gabana sai faduwa yakeyi.

Bayan mun idar yayi mana addu’oi, da kuma abubuwan ma aurata ke gabatar wa,,  zantashi ya rike mun hannu na”” yace ina zaki kuma, zan kwanta ne, ai bayanzu zaki kwantaba hira zamuyi. 

Hira kuma, yace eh , nifa gaskiya bacci nakeji, cikin muryan mai kama da kuka,, yace kefa baki rabuwa da shagwaba da girman ki, humm”” to Dan Allah zauna akwai maganar daza muyi , na zauna , tare da kallon shi “” yace shazee sai yaufa kika taba kallona , na miki kuwa? Ina cikin tsarin mazajen da kike so? Sannan kina sona kuwa? 

Na sadda kaina kasa ina wasa da yatsun hannu na”” ina tunanin me zan ce masa,, ya kinyi shiru shazee kibani amsa na mana, xuciyata tace Dan Allah karki gaya mai magana Mara dadi.

Nace sauban kayi hakuri da abunda zance ma, kai namiji ne wacce mace zatayi alfahari dashi, duk macen data ganka  baza tace bakayi mata ba”” hasalima mata rububinka zasu yi tayi,, sai washe baki yake tayi”” amma kuma ni xuciyata, sai nayi shiru nakasa karasawa.

Sauban yace amma kuma ke  zuciyarki Khalid kadai take so, shi kadai kike gani, gangar jikin ki na aura amma zuciyar ki tana wajen Khalid,, (kamar na Hanna abubakar imam da uncle haisam)  ya cigaba da cewa shazee bazan miki tilas da ki soni ba, amma xansu ki kyautatamin, kimin biyayya a matsayina na mijinki, sannan kuma Dan Allah ko yayane ki koyawa duciyarki sona koda Rabin rabine””  in magana ta ta bata miki rai kiyi hakuri, kalaman shi sun shigeni ya kuma bani tausayi”” kai kayi aure amma matar bata sonka, nace Allah ya bamu zaman lafiya.

Yace amin

Na tashi na haye gado, shima ya tashi ya haye gadon”” xuciyata ne naji tana harbawa yau gani daki daya da wani namijin, kuma mijina, tare zamu kwana,”” duk yagane a tsorace nake yayi murmushi, ya juya min baya.

Da tunani bacci ya kwashe ni, da asuba natashi yin sallah na duba gefen sauban naga baya nan, nace kila yaje masallaci ne.

Nayi alwalata nayi sallah, ina cikin karatuna yayi sallama ya shigo, Dana gama karatun, nagaishe shi . 

Ya amsa min, tare da cewa ya gajiyan biki da tsoro, nasadda kaina kasa nace lafiya to madallah, yace bara yaje dakin sa zai hada wasu takardune ,, nace toh, yace koxa ki rakanine? Nace a’a , xan kwanta, ne OK.

Gari yakara haske sai wajajen 10am natashi nayi wanka nayi kwalliya sannan nafito parlo, sauban ne zaune yana kallo  nakaraso parlo na zauna , yace Amarya harkin tashi nace mashi eh, to sannu my D .

Nayi saurin juyowa tare da zaro ido, nace sauban ina kasan sunan nan?  yace wani suna kuma, my d da kace, wani abune? “. Ina nufin fa my darling menene shazee, nace sunan da Khalid ke cemun ne fa, kai shazee wannan sunan fa kowa zai iya fada mawa nasoyin sa, “” cikin gajiya da maganar nace to ya isa, amma azuciyata ina ta tunani.

Yace ga breakfast dinmu can , ammi tasa ankawo mana nace to,, natashi na dauko abincin ba zuba mana waina CE da miyar taushe sai kamshin manshanu yake, sai kuma sai kuma soyayyar arish  da kwai ga kayan tea , na zuzzuba mana mukaci “” bayan mungama na kwashe kayan nakai na wanke .

Sannan na dawo na zauna , muna zaune  mukaji sallama, ya amsa tare da zuwa bude kofan, su Nabila ne da Sadiqa,,, sauban yace lafiya kuka zo mun gida da safe,, Nabila tace lallai ma, bros kace wani Abu, don kayi aure shine zakayi mana wulakanci, Sadiqa zo mutafi dama sallama nazo maka”” duk cikin wasa suke magana.

Yayi saurin cewa no sister karki tafi mana, nima wasa nake miki fa , dukkan su sukayi dariya, duk ina jinsu!!! Tare suka karatso cikin parlo din ” nace sannun Ku da zuwa , suka ce yauwa, nan muka gaggaisa, sannan muka Shiga hira””” can kuma sai ga aunty amingi tazo “”” wayyo dadi da gudu naje na rungumeta “”” ni sake ni karki karya ni ,, ta karaso suka gaisa da su Sadiqa,, nan hira ta barke,, lokacin tafiyan su Nabila yayi , na hada musu turarur ruka da kayan kwalliya.

Intakai ce muku, haka rayuwata taci gaba da tafiya agidan ,  har nayi wata biyar a gidan sauban, tsakanina da dangin mijinta mutun tawa da girmamawa”” suna sona kamar zasu cinye ni,, nima haka .

Mama indo kuwa kamar zautacciya ta dawo kullum sai ta dinga sambatu akaina, wai ina ina baza ta yarda nayi aure gidan kudi yar’ta bataji ba””baba na kallon. Mahaukaciya yake mata!!! Nafeesa kuwa Takara tabarbarewa sai yawonta take iya son ranta.

Kullum muna waya da aunty amingi, taitayi mun nasiha akan da inbi mijina inkyautata masa , insoshi, hakama aunty Hauwa fadanta kenan.

Har nakai wata goma dayin aure, nida kaina na zauna tunani don yin karatun ta nutsu, akan aurena,, naga bana kyautama sauban , amatsayin sa na mijina ya kamata iyanxu in hakura da wani Khalid, infuskanta gabana!!! Da haka na fara koyawa kaina son sauban amma ba sosai ba”” ranar ya tafi gun aiki, na tashi na gyara gidana yayi kyau, sannan nayi girki mai dadi, duk kamshi ya mamaye gidan!!  Sannan naje nayi wanka na tsantsara kwalliya, nasaka Riga da wondo  .

Wandon ya matseni sosai ya fitar da shape dina,  rigana Mara hannu sai igiyan wuya da ake daurewa, wandon baki, rigan red”” ba karamin kyau nayi ba.

Yau nayi niyan faranta mawa mijin , na fashe ko ina na jikina da turare, kamshine kawai ke tashi”” har dakin shi na gyara ko ina nagidan saida nasa turaren wuta.

Na zauna ina kallon TV can naji karan mota alamun ya dawo yana shigowa hara ban gidan yafara ganin canji”” ya karaso kofan da zata sadaka da parlo, ya kwankwasa, natashi kirjina sai harbawa yake yi ina tunanin tayaya zan iya hada ido dashi ahaka har na rungumeshi, , nakara kallon jikina”” gashi ko bra babu ajikina, Abu a tsaye gashi ana kallon shedan kan kirjina,, kara kwankwasa kofan da yayi”” ya dawo dani daga cikin hankalina.

Da sauri na bude kofan , zaiyi sallama kenan ya tsaya cak sakamakon rungumeshi da nayi, kirjina ne ya cakeshi , numfashin sa nason daukewa, jakar hannun sa ta fadi kasa. 

*taku*  *Ummu* *Ruman* (NUSNIM.)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD*❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     120 & 125

Jakar hannun sa ta fadi, hannu na, nakai tsakiyar bayan shi ina shafawa, zuwa saman Kansa, tare da rada mashi akannu ne, barka da dawowa my zauji”” na kama dayan hannun sa , na saka akan kwankwa so, sannan na jashi zuwa dakin sa.

Sauban ya kasa magana duk ilahirin jikin sa sai rawa yake,, bayan munshiga dakin,, nashiga balle mashi botur din rigansa, sannan nacire, na ijye gefe, idon sa aruntse!!! Sannan na kai hannu na kan belt din wandan sa zan cire, yayi saurin rike hannun na, yana sauke numfashi a hankali.

Cikin murya kasa kasa yace no shazee bashshi zanyi,, nima nace no sauban ,komai ni zan maka yanxu, please karka hanani!!! Da kyar ya barni nafara cire masa  ,dagashi sai gajeran  Wando da .

Sannan na jashi zuwa toilet, bayan na kaishi na fito naja mashi kofan “” na sauke ajiyar zuciya, duk abun nan danayi karfin haline wlh,!!! Sauban kuwa bayan nafita shima ya sauke ajiyar zuciya, tare da cewa, anya lafiyar shazee kuwa , da kyar inba wani Abu tasha ba.

Kai yarinyar nan zatasa na karya alkwari, kai anya zan iya yin wannan aikin,, don gaskiya da akwai wahala da hatsari, acikin”” kalli duk yadda tabi tasa na jike,, hmmm gaskiya da aiki agabana.

Na  bude wajen ijye kayansa, nafito masa da kaya mara nauyi nashan iska, sannan nima na koma dakina, na saki wanka  tare da kwalliya, Wanda yafi na dazu,”” siket nasaka dai dai iya cinyata, sa kuma wata Yar riga mara nauyi , kayan masu kyau, , bakara min kyau nayiba sai nadawo kamar Yar tsana”” ammafa inajin kunyan fita haka.

Da kyar nafito parlo, zan Shiga dakin sa kenan sai gashi ya fito mukayi karo ,, na tafi ta baya zan fadi kenen ya taroni,, ni kuma na rike goshina ina wash Allah, cikin muryan shagwaba nace kafasamin goshina ko, cak ya dagani muka karasa cikin parlon muka zauna ina kan jikin sa, cikin kasa kasa da murya yace sannu ko bara naga wajen .

Hannun sa yasaka asaitin wajen yana Dan daddan na min, nace wash da zafi fa allah , to sannu ko”” ya kare mun kallo ga santala santala santalan cinya na  awaje, azuciyar shi,, yace masha Allah.

Nafara kokarin tashi yace ina zaki abinci zan kawo mana , OK to,, haka na tashi ina tafiya ko ina na jikina sai juyawa yake, abunka da dirarriyar mace mai kira.

Jikina yabani Ana  kallona, na kara sauri,, shi abun ma dariya ya bashi!!! Na dawo dauke da kulan abinci kala kala”” da drinks na kwakwa da kunun aya mai dadi,,  tare mukaci abinci yana ci yana santi,, lallai shazee haka kika iya abinci, kai wai da mai da mai kikasa aciki ne, nace kai zauji kodai insa maka waigine? Yayi dariya.

Bayan mun gama ne, ya kura mun ido har naji kunya ,, nace kallon nan 

Yace bakomai shazee princess kinyi kyau, ta lumshe ido tareda budewa, wayar sa ce  tayi ringing don hk y mike ya nufi daki,

 Ganin haka yasa ta mike itama ta tattre kayan ta maida kitchen,

Bayan kwana biyu,

 Yau Saturday babu aiki,

 Sauban da guri  yafita exercise don dama du  weekend HK yakeyi,

Shazee na kwance yau ko fitowa batayi b, balle  ta hada musu breakfast

Batada lafiya tun  Daren jiya takejin ciwon mara kadan kadan to yau kuma ya karu,

Tun tn daurewa hr takasa Inda tafashe da kuka juyi  take itakai saman gado,

 Sauban bai shigo ba sai karfe goma na safe,

  Yana shigowa baiga shazee a falo ba kmr yarda y saba,

Sai ya Shiga dakin direct inda y hangota kangado tana juyi,

 Cikin sauri  ya karaso yn kiran sunanta shazee?  Shazee menene, lafiya?

Takasa mgn illah juyi  da take kawai,

Yaye blanket din yy da sauri  ya dagota, hankali a tashe bai San lokacin daya mannata a jikinsa b yana mai girgizata hankali tashe,

 Yace fadamin pls

Cikin yanayi najin ciwo tace c cik,,,cikinnaa, tafada cikeda rawar murya,yace subhanllahi tun  yaushe? Dama kinayine?

 Girgiza masa kai tayi

 Kwantar da ita yayi ya mike ya fice,  

Chemist yaje  ya siyo mata mgnin ciwon ciki,

 Yace sannu shazee daure muje kisamu kiyi wanka kidan ci abinci sai kisha magani,

 Koda ya mikar da ita, kasa  tsayawa tayi, koda ya lura da hakan sai kawai ya dauketa cak hr bandakin

 Ya hada mata ruwa, sannan ya Dan mtso cikin sanyin murya yace shazee kidain kuka, bari in taimka miki,  cikin tsoro tace zan zn  iya kaje kawai,

 Ya kalleta sosai yace are you sure? Kai ta daga  mishi,

 Fita yy a bndakin ya rufo mata kofa,

Yarasa me zaiyi sai yafara gyra mata gadon yana cikin gyarawa yaga digo  digon jini,

Kallon wajen yakeyi cikeda tunani,nan ya gano  abunda ya haddasa mata ciwon, 

Yaye bedsheets din yy ya shimfida wani,

 Nan da nan ya gyara, tana fitowa ta tashirya dakyar take kokarin zama a kasa, yayi saurin karasawa inda take ya sanya hannu ya dagota a hnkli yace sannu shazee

Ya kwantar da ita dakansa ya shiga kitchen y hada mata breakfast,

 Dakansa ya bata abaki, tanaci tana hawaye, ya sanya  hannu yana share mata hawayen,

Lokacin da cikin ya murda mata juyi  takarayi ajikinsa tare   da kifa  kanta ta tsakanin cinyoyinsa tana kuka, wani shock yaji lokacin da ta daura kanta bisa cinyoyinsa musamman data goge marar  sa, yrrr tsigar jikinsa ta tashi,

 Ganin hanklinsa na kokarin tashi yasa yadan janyeta,

Kwantr da ita yayi gefe, inda ya Dan Shiga bubbuga baynt alamun rarrashi

Tuni barci ya dauketa,

 Ganin HK yasa yamike shima wankn yashiga, ya fito ya shirya, sm yakasa cin komi sai ruwan tea, koda yakom falo, du  bayan minti biyar saiya leka yg kota tashi,

   Bata farkaba sai wajen karfe biyu,

 Kalau ta farka babu ciwon bandaki tashiga inda taga ta baci  sosai ta kimtsa knt sannan tafito,

Masu karatu bari in Dan huta daga  nan,

Haj ceeymer💁

 nagaisheki ba adadi Allah yabar zumunci,

 

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (Ruman)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

 125 & 130

Bayan ta fito ta shirya tasa kaya ta fito parlo, sauban dake zaune yayi sauri ya tashi don taroni, kamani yayi tare da cewa sannu ko shazee, ya jikin”” nace da sauki, ya zaunar dani kan kujera, tare da cewa ina yake miki ciwo yanxu?

Nace babu naji sauki sosai to madallah haka nake son ji , na Dan kura mashi ido, azuciya na nace Allah sarki sauban bawan Allah, kalla duk yadda ya rude akan Dan wannan ciwon danayi.

Ya ce shazee wannan kallon fa nayi saurin kakalo murmushi tare da cewa sauban nagode sosai Allah ubangiji ya biya ka, haba shazee godiyan me kike mu? In don wannan kulawar Dana baki kike godemun to ki daina”” saboda yazama dole in kula dake , ke amana ce awajena , alkhawari na daukar musu.

Nayi saurin cewa suwa ka daukar mawa alkhawari,, gaban shine yafadi, don baisan lokacin da maganar ta subuce masa ba,, yace su baba mana, ai nace musu bazan bari wani Abu ya tabaki ba.

Na zuba mashi ido ina son karantar wani Abu don banyarda da maganar saba, tunda nashigo gidan sauban ,, nafara lura da wasu abubuwa, yana min abunda Khalid ke mun, sannan kuma nakanji shi yana amsa waya, sannan kuma yana boye mun wani Abu”” kaai akwai wani Abu.

Wasa wasa nayi shekara daya da watanni agidan sauban wani Abu na auratayya bai taba shiga  tsakanina dashi ba””  sannan kuma naga ya canxa mun ,, kullum sai ya dinga zama nesa nesa dani,, ga yawan tunani da yakeyi ,,, duk yabi ya rame tun abun baya damuna har yafara damuna saboda ance ka damu da Wanda ya damu dai.

Duk macen data samu sauban a matsayin mijin aurenta, to wlh ta more bata da damuwa, saboda ya iya tattalin mace.

yau sati sauban ya wuni adaki bai fito parlo ba,, ganin haka yasa na Shiga dakin sa “” tare dayin sallama, yana kwance idon sa biyu yana kallon silin din dakin,, hawaye na gangara ,  yana jin motsina, yayi saurin goge hawayen sa cikin dabara don kar ingani.

Da sauri na karasa tare da zama kusa dashi na taba jikinsa duk na rude nace zauji lafiya, meke damunka,, kwana biyun nan duk ka canxa, kuma kaki kafada mun damuwar ka,,,kawai sai nafada jikin sa na fashe da kuka me tsuma zuciya.

Ya tashi cikin rudewa ya dagoni tare da cewa sorry my Shahrazad ki daina kuka please, don kukanki na daga mun hankali!!! Nace haba sauban tayaya ba zanyi kuka ba, kaki fada mun damuwar ka , kabar ni cikin duhu,  sannan kuma ina tuhumar ka da abubuwa masu yawa,,, xuciyata takasa yarda bakai bane Khalid dina, yayi saurin tureni tace shazee kin San me kike fada kuwa.

Nima na miki nace na sani,, sauban kai ne Khalid dina, kai ne masoyina ,, Kaine habibi na”‘ da soyayyar ka na girma”” kuma dashi nake rayuwa har yanxu””wlh bazan iya mantawa da kai ba.

Amma why Khalid meyasa zaka boye mun kan ka, kafito min amatsayin  sauban,, haba  ko baka yarda kai nake soba? Ka zo ne ka gwadani kaga ko zan so wani na miji bayan kai?

To bara kaji Khalid wallahi ban taba son wani da namijin arayuwata ba sai kai Khalid,  koda kaga ina baka kula amatsayin sauban daka zo min”” to ba so bane yasa nake haka,, kyauta tawa  ne, da kuma zamantowar ka amatsayin miji,, inayin hakane kada Allah ya kamani da laifi.

Sauban ne ke kuka kamar karamin yaro ya dur kusa kasa, nima kuka nake sosai, nima adurkushe nake “” na karaso wajen shi tare da ,, daga kasa ina share masa hawaye,, nace stop crryiny Khalid , ni naka CE,, kuma babu mai iya raba mu”” kamanta soyayyar da mukayi, kamanta har sashen ka akaina,, to bara na tuna maka .

Cewa kake shazee kin fi kudi, kinfi gida, kinfi mota, shazee ke rayuwa ce gabaki daya, shazee ina sonki kuma bazan taba rabuwa dake ba””  my d katuna fa,, na kara rungumeshi .

Sauban yayi saurin fincike ni daga jikin sa tare da matsawa baya ,cikin daga murya ya ce Shahrazad karki yaudari kanki”” wlh bani bane Khalid, bani bane Khalid bani ne khalid., ya kara fashewa da kuka.

Ni kuma sai girgixa kaina nake, no no no, banyarda ba,, sauban yaci gaba dacewa, shazee zamana dake ya nuna min baza ki iya zaman aure da kowani da namiji ba inba Khalid ba.

Son khalid ya miki babban rami azuciyar ki”” Wanda baki ganin kowa sai shi!! Gaskiya na jinjina miki shazee, Khalid yayi dacen mata,”” kidaina yaudaren kanki danine Khalid, no bani bane kuma bazan taba zama shiba har abada,, ni sunana Muhammad sauban kamar yadda kika sani.

Nace idan ba kai bane Khalid meyasa zaka dinga mun abubuwan da Khalid ke mun? Kana yawan Nuna min wasu abubuwa irin na Yaya Khalid dina.

Na share hawaye na, nace tunda kace ba kai bane Khalid ,, to da alamun kasan Khalid dina , kuma yana kusa dakai”” inba haka ba to bazan taba yarda bakai bane Khalid dina, masoyin asali”” sannan kuma in ba kai bane Khalid,  meyasa kwana biyu kashiga cikin damuwa,, kake mun wani irin kallo.

Shazee ki fahimce ni da kyau, kin San Allah daya ne ko,  to wallahi wallahi wallahi kinji na rantse bakya bina bashin rantsuwa, bantaba ganin Khalid ba,, ban sanshiba,, ban San a ina yake ba, sai ta dalilin ki nasan Khalid kuma a hoto nataba ganin shi.

Kuma damuwar nan da kika ga inayi,, inayin sane, saboda ke.

Nace ni kuma? Eh kefa, toh mena maka? Ba abunda kika min,, ya juya mun baya yace shazee lokacin rabuwa ta dake yazo””  dama  tun asali na aure ki ne amatsayin taimako, turoni akayi”” kuma a lokacin basanki nake ba!! Duk plan ne aka shirya”” na aurekine na Dan wani lokacin”” gashi kuma zan rabu dake ,, a lokacin danaji dadin zama dake!!! Ke macece da duk namijin daya zauna dake bazai so rabuwa dake ba.

To nima haka nakeji araina, amma ina rokon Allah da ya musanya mun irinki”” daga yau aikina ya kare”” ban San lokacin Dana zo wajen shi na dauke sauban da lafiyayyun mari ba guda biyu”” saura kadan ya fadi kasa.

Na kama rigarsa ina jijjigawa cikin kuka nace waya turo ka ka aure ni”” me na muka daza ku zo neman aurena ,, cikin daga murya nace sauban ka fada mun !! Dama ka shigo rayuwata ne, ka kuntata min, ka Shiga tsakanina da masoyina,, kafada  min waya  turo ka”” ji nayi ance  ni na turo shi”‘ juyawan dazanyi , na xaro ido waje bakina na rawa , xankira sunan nakasa, hawaye ne yakara gudu afuskata, kirjina kamar zai fashe sai harbawa yake.

*Taku*   *ummu* *Ruman* (nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD*❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

   130 & 135

Kirjina sai harbawa yake, kamar zai fito, kafafuwa na sun kasa dauka ta nayi saurin na dafa bakin gado “”da sauri ta karaso wajena don ta kamani”” daga mata hannu nayi sama alamun ta dakata.

Taja baya ta tsaya tana tsiyayar hawaye.

Nace aunty amingi Ashe dake za a iya hada baki aci amanata”” amina me na miki daza ku min haka,, amingi sai da tazaro ido waje saboda yaune rana na farko da na taba kiran sunan ta kai tsaye .

Naci gaba da cewa, Ashe baki son alakata da yayanki Khalid,, Ashe baza ki iya taimaka masa wajen mallakata ba? Ashe bazaki taya yayanki kishin wani ya rabe ni ba!!  Haba amingi, why me na miki haka daza kisa ayimin auren mutumin da bana so’

Ke kanki kin sani, Khalid kadai xuciyata keso dashi nake sha’awar aure!!! Amma ki kayi ruwa kikayi tsaki, har na auri sauban” haka  nayi ta gayawa aunty amingi maganganu marasa dadi.

Nace amina daga yau bani bake, har abada, tunda baki son farin cikin yayanki,, amingi ta durkusa kasa sai kuka take yi sosai, tace shazee ki fahimce ni””wlh Nafi kowa son ki aure Khalid, nayi saurin kara sowa kusa da ita na cakumi wuyar rigarta, nace karya kike muna fuka.

Fatima da ni’ima da Nusaiba da khausar sukayi saurin mikewa tsaye, cikin tashin hankali” sukace, amma aunty shazee idonki ya rufe ne haka, kikewa mai sonki amingi cin mutunci haka” hmm Ku zauna kuji kawai.

Na ci gaba da cewa wlh amina kinci amanar soyayya,, na daga hannu kenan zan mari amingi,, kawai sai naji saukan mari a fuskata, daga idon da zanyi, naga sauban ne, ya mareni yana hawaye!!! Ya jani gefe tare da jefar dani akan gado, cikin bacin rai ya fara magana kamar haka.

Shahrazad wai mai kika maida mutane ne? Kowa kika samu ki Mara, kuma alhalin ba abunda aka miki”” illa taimakon ki ma da akayi!!  Amingi bata cancanci haka daga wajenki ba.

Matar data dage wajen ne mami ki farin cikin rayuwar  ki”” matar da kullum cikin kuka take akanki, matar da kullum ne man mafita take akanki, matar data hana idon ta bacci akanki, matar data hana cikin ta abinci akanki, matar da kullum take yawo akantiti da garuruwa duk akan farin cikin ki.

Amma kirasa da mai zaki saka mata sai cin mutunci.

To bara kiji ki bude kunnan ki da kyau, don kiji abubuwa da dama, Wanda akarshe nasan sai kinyi da kin sani.

In baki manta ba, kishiyar hajiyarki wato mama indo, bata sonki da Khalid,, sai kuma yatta ta kamu da son Khalid, inda mama indo ta dau alwashin rabaki dashi, ta hadashi da nafeesa!!!

Tayi asirin farko bai ka mashi ba”” sai a asiri nabiyu ne yayi tasiri.

Wato a asiri na biyu, taje gun boka, don abatar mata dake kibi duniya kar aganki”  ita da kawarta ma’u sukaje, ya bata wani magani da suje makabarta su Burne, amma tsohuwar makabarta, ya gar gade.

Yace idan suka sa a sabuwar makabarta, to ba shakka Khalid ne zai bata, amma idan suka saka atsohuwar makabarta, to kece zaki bata.

Wato sai Allah ya mantar dasu, inda suka kuskure suka saka a sabuwar makabarta”‘ ta dalilin haka Khalid ya bata”” su mama indo basu tashi ganewa ba, sai bayan da akace musu Khalid ya bata!!!! Ba karamin tashin hankali, mama indo tashiga ba”” saboda alokacin  tana tunanin wani hali yarta nafeesa zata Shiga ba.

Sai daga baya kuma nafeesan  ta warke daga damuwar batan Khalid, har ta manta shi, shima ta dalilin mama indo, magani akamata ta manta shi.

 Shine mama indo daga baya ta dinga Neman hanyar daza a kuntata maki, tunda taga son Khalid ya hanaki tsayawa da kowa”” shiyasa kullum sai taje wajen babanki tayi ta mashi hudubar shaidanu, tace ana xaginsu agari, don sunki aurar dake, shiko babanku abun na damunshi”‘ shine yayanke shawaran da ki fitar da miji, yaje yasa mu baban Khalid ya fada masa abunda mutanan gari ke cewa.

Baban Khalid baiji dadi ba, shima yasanarwa da matarsa  aunty hauwa da yarsa  amingi”” tundaga wannan lokacin amingi ta dauki damaran taimaka miki, batare da sanin kowa ba, don tasan matsalar gidanku, don tana gudun kar mama indo tabi wata hanyar ta kuntata maki, tunda dama tasan da maganar maganin nan da aka zuba mawa Khalid azauren gidanku.

Ana haka, kawar mama indo wato ma’u, ta cewa mama indo me zai hana danta ya auri ki,, bayan Dan nata rikakkan barawo ne, gashi mashayi ne,, aiko ana haka amingi tasamu labarin abunda su mama indo suke shiryawa.

Dama a lokacin tazo ganin gidane sai taji mummunar labarin nan,, aiko ko dadewa batayi ba ta koma abuja gidanta, tasaka mijinta agaba sai kuka take, daya taimaka mata, karki fada wani hali.

Shine mijinta yace yana da Dan uwa yaron kanin baban sa mai suna Muhammad sauban, (wato ni),, zamu mishi magana akan dayaxo Neman auren ki, kuma yafito amatsayin ustaz, don  mama indo ta amince, dama bataso kije gidan Hutu,, amma akwai sharadi a auren, zan dau alkhawarin bazan taba yarda wani auratayya tashiga tsakanina dake ba.

Zan zauna dakene, har lokacin da Allah zaisa aga Khalid, in kuma baya Raye, sai afada maki gaskiya, in zaki iya zama dani amatsayin masoyi shi kenan, amma dama shekara biyu. Aka daukar mana a auren mu”” don baza mu cigaba dazama irin haka ba ,  amingi yaji dadin shawarar mijinta, kuma ta amince”” da haka har suka min magana, ni kuma dayake metausayi ne, na amince, zan dauki wannan kasadar,,  don wannan babbar kasada CE.

Mukayi mawa iyayena bayani suma suka yarda, don suna son aunty amingi, don macece mai son dangin mijinta.

Da hakane har nazo wajenki,, dama kuma nafeesa tana zuwa layinmu, INA ganinta, kuma duk lokacin daza mu hadu amatsayin ustaz take ganina, wannan kuma duk shirin amingi ne,, don yadda zamu samune musa mu Shiga wajen mama indo.

Sannan kuma amingi ta Nuna min hoton Khalid, da kuma abubuwan daya ke miki , duk aunty amingi ta fada min in dinga yimiki, don hankali ki ya karkato wajena”” sai Allah ya daurani akan yan gidanku, aka amince dani”” kece kawai kika ki aminta dani.

Sai daga baya daza ki gudu, Allah ya taimake mu, amingi ta ganki, da bata ganki ba da bamusan ya zamuyi ba, da haka su amingi da yan uwanta suka shawo kanki kika karbi aurena badan kin soba.

Mu kuma muna ta Neman Khalid don har karatu mukasa ake mana, don ance mana asiri akayiwa Khalid”” haka amingi take ta fafutukar nemo  Khalid ba dare ba rana,, ko wayar da kike ki nakeyi , da amingi nakeyi, akan na rike amanar yayanta .

Yanxu haka danake miki magana mama indo tana can gida cikin tashin hankali saboda yarta ta bace, shine duk ta tona ma kanta asiri”” shi kuma Khalid munganshi,nayi saurin mikewa da kyar na karasa wajen sa, adaburce nace yan yan yan in in Ina bakina sai rawa yake, yace shazee kiyi hakuri  Khal___ bai karasa ba nafadi kasa bana numfashi ,”” amingi da sauban sai girgixani suke tare da samun ruwa amma ina ban farfado ba.

*TAKU* *UMMU* *RUMAN* (Nusnim)

08064481931

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

  135 & 140

Sauban ya dauke ni,, yayin da amingi tayi waje da sauri don bude mota, yana zuwa yasaka ni aciki” yashiga amingi ma ta Shiga, sai asibitin garkuwa”” da gudu gudu aka karbe mu don taimakon rai na.

Da kyar aka samu numfashi na, sannan akamin alluran bacci, likitan yace nanda anjima kadan zan farfado,, yawan damuwa ne yasa min dogon suma,, Allah ne kawai ya kare ni”” sannan hankalin su amingi ya kwanta.

Can da yamma, nafara bude idona, sauban ne ya lura da hakan”” yayi saurin kara sowa wajen, aunty amingi ma tana ganin hakan itama ta karaso”” suna sannu shazee, ido kawai nabisu dashi, alamun mai son tuno wani Abu.

Ina kokarin tashi amingi ta taimaka min tasa min pilo  abayana na jingina”” sai binsu nake da kallo sunnu suke tace mun 

Sauban yace ina yake miki ciwo yanxu na girgiza kai na, alamun babu “” nazuba musu ido, ina kallon inda nake”” azuciyata nace mai ya kawo ni asibiti?  Can na dan yi shiru na Shiga tunani” tuni na tuno abunda ya faru na rushe da kuka ina cewa shi kenan ya mutu  ya barni.

Nima yazama dole in mutum” amingi ne ta rungumeni tana bubbuga min baya na” kiyi hakuri shazee, Khalid dinki bai mutu ba”” nayi saurin daga ido ina kallon ta nace da gaske bai mutu ba? Tace eh!! Sai ga murmushi ya kubuce mun a fuskata sai washe baki nake.

Amingi tace sai dai baida lafiya yana kwance a gida , amma yakusan tashi tunda an mishi turare, da magungunan Islamic chemist “” don tun barin shi gida  , yafita hayacin sa””  sunanki kawai yake kira yanxu , alamun sauki yazo, tunda da baya magana.

Nace Allah sarki Yaya Nah. Mai sona, nace aunty amingi tayaya kika Ganshi”” tace   akwai watarana, inata mafarkin sa , yana kirana acikin garin kano.

Aiko inatashi daga bacci nafada mawa mijina. Yace shirmen yace shirmen nafarki ne,, nikuma nace INA da gaske ne Dan uwana yana Neman taimakona”” shine fa muka shirya muka kama hanyar kano , sai dube dube nake a hanya, da haka har muka iso cikin garin kano, shima inata waige waige ,, kamar ance in waiga hannun dama na.

Na hango wani mutum cikin bola yana cin abinci hannu baka” nacewa mijina ya dakatar da motan  , nayi saurin fita shima ya biyoni”” mukayi saurin karasawa inda yake “” wazan gani inba Khalid ba, na fadi akasa sai kuka nakeyi”” shiku Khalid ganin mutane agabansa kuma yaga ina kuka,, ya karaso inda nake, yazo yana min dariya hannun sa rike da Leda wai zai share min hawaye”” duk tsorone ya cika xuciyata”” haka ya goge mun hawayena, yana girgixa min kai alamun indaina  kuka”” a haka dai muka mashi wayau mukasa shi amota tare da dawowa Kaduna,, kai tsaye wajen mai magani muka kaishi.

Sai da aka mai rukiya, aka babbashi  magani, yanxu haka yana GDA yana kwance, sati daya baya magana, sai yau da safen nan ,mukaji yana Shahrazad Shahrazad”” sunanki kawai yake ambato” dalilin dayasa nakira sauban na fada masa, daya kawo ki,, sai naji shiru Baku zo, shine nazo da kaina don ganin ko lafiya, sai natarar da Ku cikin tashin hankali.

Sauban yace shazee yanxu kin tabbatar da amingi mai kaunar kice ko, kin tabbatar tafi kowa sanki da Khalid ko.

Na fashe da kuka, ina aunty amingi kiya fe min Dan Allah, sharrin zuciya CE tasani fada maganganu marasa dadi da kuma son Khalid!!! Kiyi hakuri  kiyi hakuri kiyi hakuri ki yafeni!!! Natuba na dinga bubbuga kaina ajikin gadon asibitin.

Aunty amingi tayi saurin hanani tare da rungumoni, tace bakomai shazee , wallahi ban rike ki araina ba , nasan bayin kanki bane”” kuma na tabbatar komin rintsi baza ki taba gujewa Dan uwana ba”” gaskiya Khalid yayi dace , kin zama abun alfahari a family din mu”” Shahrazad muna sonki sosai .

Nima ina son Ku aunty amingi, bayan mutuwar hajiyata, Ku kuka zame mun uwata, nima ina alfahari da kasan cewa a cikin Ku, muka kara rungume juna  muna kuka.

Sauban ne ya sulale ya fita waje sakamakon kukan daya ci karfinsa”” yasami inda ba kowa ya tsugunna sai kuka yake sosai”” yana fadin ya Allah!!! Ka cire mun son abunda bai dace dani ba'” ya Allah kana gani taimako nayi niyyan yi tsakani da Allah”” ya Allah kaji tausayi na ka cire mun son shazee ka musanya mun da wata.

Kabani hakuri da juriya allahumma amin.

Mu kuwa ba musan sauban baya nan ba, saida muka gama kukan mu, har muka Shiga hira, nake tambayan aunty amingi,, yanxu kowa yasan Khalid ya dawo nice kawai ban sani ba sai yanxu “” tace eh ke kadai ne baki sani ba, ance kar afada  maki, don yanxu ke matar wani ce”” basu San auren ki, ni na hada ba.

Amma yanxu in muka koma gida zan fada masu,, nace dama ance ka gina ramin mugunta dai dai kai”” kuma dama ance abunda ka shuka  shi zaka  girba .

Amma bazan taba yafewa mama indo ba, sai Allah yasaka mana tunda tajefa mu wani hali”” amingi tace , karkice haka shazee Allah yana son mai yafiya, kiya fe mata, tunda gashi Allah ya Nina mata kuranta, gatacan kamar mahaukaciya take” saboda bacewar yarta nafeesa, kuma kinsan  duk cikin ya’yanta ba Wanda take so irin nafeesa””” kuma hannun ka baya rubewa kayardar, tunda komin Yaya ne, mama indo jininki CE”” fatan dai kiyi musu addu’a Allah ya shirya su, ya kuma bayyana nafeesa a duk inda take, nace amin.

Sauban ne yashigo fuskar sa  dauke da murmushin  karfin hali, yace dafatan  dai kun shirya, suka ce eh suna dariya.

Na kalli sauban da kyau nace sauban , ina   rokan  ka da kaima kaya fe min, don ban kyauta maka ba, kaima ka taimake ni arayuwa, samun  irinka yana da wuya, na jinjina maka sauban ba karamin namijin kokari kayi ba , nagode nagode sauban Allah ubangiji ya   saka da alkhairi  ya baka mata mai kaunar ka,, na fashe da kuka”” yayi saurin kara sowa wajena, har zai rungume ni, sai kuma ya fasa tare da kakalo murmushin karfin hali, yasa hannu ya dago habata muka kura mawa juna ido, yasa Dan yatsan sa ya share mun hawaye na,, yayin da ni kuma nake kallon kaunata cikin kwayar idon sa.

Kirjina ne yafara harbawa, na fashe da kuka, amingi tayi saurin barin dakin tana hawaye, tare da fadin ya Allah wayyo ni amina nasaka bawan Allah cikin damuwa , gashi daga gani ya kamu da son shazee,, ya Allah kayi gaggawan cire mishi.

Cikin murya can kasa kasa yace shazee bakomai ni ban rikeki da komai ba, kidaina kuka, don bana son kukan nan”” nace to,, na kara kallon sa nace sauban ka kamu da sona ko?

Yayi saurin cewa shazee kin San abunda kike  fada kuwa ,, ni bantaba ji INA sonki ba ko kadan, hasalima inada Wanda nake so murmushi nayi,, nakalle shi nakuma yin murmushi”” nace shi kenan.

Likita ya sallame  ni,, muka dunguma sai gidan su Yaya Khalid ko gama tsayawa motar batayi ba, na fito da gudu nashiga cikin gida, ina Shiga parlo naci karo da aunty Hauwa da babana  da baban Khalid da mijin aunty amingi sai iyayen sauban, duk suna zaune, nafada jikin aunty Hauwa na saki kuka mai tsuma zuciya,aunty Hauwa Ashe anga Khalid, eh shazee , Allah y bayyana mana shi.

Su sauban suka karaso falon, aka gaggaisa , sannan mijin aunty amingi yafara yi musu bayani akan auren na da sauban, ta yadda akayishi,, dukkan su sun girgixa kuma sun jinjinawa amingi da sauban”” tare da tausaya mawa sauban din.

Baban Khalid yace amma sauban ba amaka adalci ba idan aka rabaka da MATAR ka, babana ma yace hakane.

Sauban yace wlh ba komai, yayi musu karya akwai wacce yake so tana jiranshi yanxu hakan, dama ya barine ya gama wannan aikin , sukace to tunda haka kace mungode, yaciro takardan saki yabani, na karba ina tausayinshi.

Yayi musu sallama yace yana da uxuri yayi saurin fita, ni kuma da gudu na tashi na fada dakin Khalid kwance na ganshi nafada kanshi, ina kuka, yayanah, farin cikina my d dina, ina kaunar ka”” kamar daga sama yaji muryan da bazai taba mantawa ba, ya bude ido”” yana sha sha shazee dina, ya idonshi ya bude akaina, wani karfine ya zo mashi ya rungumeni, yana kuka ina kuka.

Sauban dakyar ya hau motarsa ya je gida,, dakina ya wuce, ya dauko kayan bacci na, ya rungume, yana kuka sosai , yana tuna ranar danayi ciwo” da ranar dana rungumeshi, kuka yake yana kiran Shahrazad Shahrazad Shahrazad.

*taku* *Ummu* *Ruman* (nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

  140 & 145

Sauban yace Shahrazad, yanxu shikenan kin tafi kin barni kenan, wallahi ina sonki shazee ina kaunarki, ban San ya zanyi ba”” amma xuciyata bata min adalci ba” me yasa zata kamu da abunda bai dace dani ba.

Sadiqa ce tayi sallama tashigo don ammin su ce ta turo ta,  don tace tazo taga halin da yake ciki”” ganin halin dayake ciki yasa takarasa wajen  shi,, tana bros please ka daina kukan nan, kayi hakuri ka dau dangana, watarana sai labarin,, Allah na kallon ka bazai taba barin ka haka ba.

Yace Sadiqa lallai xuciyata ta kamu da son shazee, cikin lokaci kankani,, gashi yanxu tamin nisa, amma bakomai, Allah ya musanya mun amin bros” zaka sha mamakin kalan matar dazaka aura, Allah ya tabbatar kanwata.

Fatima tace aunty shazee gaskiya ni banji dadin rabuwan Ku da sauban ba”” wlh duk tausayinsa ya kamani, nifa Nafi sonki dashi fa” 

Khausar tayi saurin cewa haba aunty Fatima, karkiyi son zuciya mana” idan aunty shazee ta zabi sauban, to gaskiya batayiwa Khalid adalci ba, kina ga a tasanadiyar ta, ya fada cikin wannan halin”” da baice yana sonta ba, to dahakan bazata kasance dashi ba”” kuma fa yan uwanshi suka dage kan nema  mata farin ciki”” dabadan aunty amingi ba, da bamusan wani hali aunty shazee zata fada ba”” gaskiya bakaramin kokari aunty amingi tayi ba, mace kamar namiji”” Allah ubangiji yasaka mata da alkhairi ameen.

Ni’ima tace tabbas maganar ki gaskiyace khausar ana barin halal don kunya,, kuma gsky sauban ya masu halacci.

Nusaiba tace hakikanin gaskiya sauban yayi jarumta, shekara daya da rabi kana zaune da mace a gida daya, kuma abunda ya hadaku da ita na auratayya”” gskya na jinjina mawa sauban, don ba karamin kasada yayi ba”” sai gani sukayi Nusaiba na kuka” shazee tace Nusaiba lafiya kike kuka, Nusaiba tayi murmushin yake kawai.

Nim tace aunty shazee muna jinki cigaba

Nida yayana muna zaune kamar zamu hadiye junan mu, sai ga amingi ta shigo da dakin, tana cewa hmm romeo and Juliet anan anfara sana’an ko”” to mudai kar a kona  mana gida” dukkan mu muka kwace da dariya .

Sai ga aunty Hauwa tashigo ita da Umar , umar ne ya karaso wajen Khalid tare da rungumeshi” yana hawayen farin ciki!!! Yace wato Yaya aunty shazee ta dagaka, da ko tashi bakayi, wato soyayya ta dagaka yanxu.

Khalid ya kaimai duka abaya,tare da cewa lallai Umar yaushe kazama hakane, hahaha ya Khalid ni yanxu na girma fa, sanin dda kamin!!!  Lallai kam.

Nandai aka bamawa Khalid labarin abubuwan da suka faru” yayi kuka sosai, tare da tausaya mawa sauban,, lallai ya kamata ya hadu da sauban** sannan kuma ya jinjina mawa kanwarsa amingi”” ya tabbatar yasami Yar’ uwa mai kaunar sa  sosai, ya rungume amingi suna kukan farin ciki”” sannan ya dinga bina da ido ya rasa da mai zai saka min, muna haka sai mijin amingi ya shigo ya, sukayi musabaha da Khalid. Ya mishi godiya.

Aunty amingi ne tace intaso mushiga gidan mu, nace mata baza Niba ni anan zan kwana, aunty Hauwa tace, ai zakije ne ki dawo, zaki gaida mama indo da jiki don bata da lafiya,, sai da Khalid yasa baki tukunna na yarda naje.

Muna tafe muna Dan hiran mu da aunty amingi har muka karasa , akofan gida naga baba na yana zaune, muka gaisa dashi, yace me kikazoyi an an, ai acan zaki kwana, nace nazo duba jikin mama indo ne,, yace Allah sarki kin kyauta da baki riketa aranki ba”” Allah ya miki albarka, mukace amin.

Sannan muka karasa ciki, tana tsakar gida akwance ita da ya’yanta maza sai kuma kanwarta, tana ganina ta fashe da kuka,  muka karasa inda suke tare da gaggaisawa, nan mama indo ta rokeni gafara na yafe mata, tare da rokon Allah ya bayyana nafeesa a duk inda take, dukkan mu mukace ameen.

Khalid mun hadashi da sauban inda ya masa godiya sosai tare da nuna masa farin cikin sa”” sannan sauban yacewa Khalid da ya rikeni amana” kar yasake ya bari na kubuce masa akaro na biyu, don bakaramin dace yayi ba”” Khalid yace nagode sosai sauban Allah ya musanya maka da mafi alkhairi yace amin, tundaga lokacin Khalid da sauban suka zama aminai””

Tun daga ranar rayuwata tafara canxawa, damuwata ta tafi”” illa Abu daya wato shine, sauban ina so in sama masa mata , wacce zata kwantar masa da hankali, ta zauna dashi tsakani da Allah, amma ina mun kawo masa yan  mata kala kala shi yace ba wacce ta masa, shi yasan matar sa tananan zuwa insha allahu, haka nan muka zuba masa ido ba don mun so ba, don da mun so a hada bikin mu tare.

Nice zaune da Yaya Khalid a parlo muna hira, yace my d mu godewa Allah, daya kara hadamu akaro nabiyu, lallai Allah na sanmu ,hakane my d.

Khalid yace shazee ganin ki kan Kore min duk wani bakin cikin datake  dauke da xuciyata, don haka nakira ki da wacce tafi kowa sa’a a duniya!! Ina sonki koma  zanci ga ba  sonki koda zaki juya min baya.

Yayana bazan taba iya juya maka baya ba , sonka ya zamo walwalata , ya zamo Bargon rufata, yayanah bani da aiki akowace rana sai na begenka, bazan iya mallaka mawa wani namiji soyayyata ba inba kaiba.

Nagode my xclusive  one shazee be loved one queen you are my royal highness, my excellency my lady” fiency love you , my wife to be insha arrahman.

Nace tanx habibty Nah ana hubbiq tartir.

Akwana atashi ba wuya, an saka bikin mu, nanda sati biyu, sai shirye  shirye akeyi” yayin da sauban yake shirin barin kasar don baya so ayi bikin yana kasar, don har yanxu zuciyar sa bata gama warkewa daga sona ba”” mama indo ta Dan sami lfy don da itama ake shirye shiryen bikin, amma tunanin yatta bai saketa ba” a kullum addu’a ake Allah ya bayyana nafeesa, ana gobe bikin mu  sauban yazo gida wajen mu ya kawo mana gift din bikin mu”” bayan mun gaisa, dashi, yace min ina angon nawa, nace ya fita, OK kila bazamu  samu haduwa ba don gobe zan wuce u.s don akwai abunda zanyi”” na zuba mashi ido Ina kallon sa ” nace sauban ni nasan saboda bikin mu zaka tafi, kuma bazan hanaka tafiya ba, amma karka manta ka kasance mai tawakkali, nasan haryanzu kana sona sauban kuma saboda nine kakiyin aure, amma ina kara baka hakuri Dana shigo rayuwarka ban maka adalci ba, kayi hakuri sauban pls karka rikeni aranka.

Yayi saurin cewa shazee ki daina damun kanki, wlh ban rike kiba, kuma baki da laifi, ba yadda Allah bayayi, kowa da tasa kaddaran hakane”” yace ka gift dina adinga sakamawa Khalid nasan zayyaba, nakarba ledan  ina duddubawa ne, sai da kunya takamani, rigunan bacci ne masu kyau, da turare, sai kuma kudi dubu dari, daya bani”” nayi godiya sosai naji dadi sosai araina.

Yace wannan kuma ki ijyewa Khalid, shima turare ne sai agogo mai kyau, nakara masa godiya, sannan na rakasa mota yashiga, yana daga mun hannu nima ina daga masa.

Intakai ta muku yau jumma’a itace ranar da aka daura auren khalid tanko soba, da amaryar sa SHAHRAZAD abdulmaleek, , bakaramin dadi masoyannan sukaji ba.

Ankaini gidan mijina dake kabala, gidane nagani nafada hadade, gidan sama, tsayawa fadan kyanshi bata bakina, gani da ido shi yafi dacewa,, kannan sauban suna cikin mutanan da suka min kawance don aunty amingi, ta bar musu wannan fannin” haka mutanan dasu ka kawoni sukaita  yabon gdan , harda mama indo acikin kawoni gidan mijina, sai hawaye kawai takeyi, tace Allah sarki natauyewa yarinyar nan hakinta, da yanxu tana gidan nan da yaranta, amma nabi sharrin zuciya na aikata abunda bai dace ba. Gashi ya koma kaina.

Yan kawo Amarya sun watse, sai Amarya kadai adakinta, Khalid ne yashigo cikin sallama na amsa masa, yasha fararen kaya, ba karamin kyau yayi ba 

Ya zauna kusa dani, tare da janyoni jikinsa, ya cire mun mayafina yana kallon yace baby kin hadu fa”” yacire Dan kwalina, yana Shafa kaina tare da shinshinawa, yana lumshe ido, ni kuma na kara lamo akirjin sa, yace my d yau ranace ta farin cikin mu, tashi muje muyi sallah mugodewa Allah , nace to, na yunkura zan tashi ya dagani cak, sai toilet dakansa ya min alwala, sannan ya daukoni, ya shimfida mana abun sallah!!!! Mukayi sallah bayan mun Idar yayi mana addu”zaman lfy.

Sannan ya tashi ya dauko mana kazar mu da drinks,, ya zaunar dani kan cinyar sa, yana, bani ina ci, shima haka nabashi, da haka har muka koshi, yace my d bara naje na miki wanka”” na zaro ido waje nace habadai sai kace karamar yarinya”” yace to ni sai na maki, bai jira abunda zance ba ya sunku ceni, sai toilet ina zillo tare da kukan shagwaba, nace nidai ka saukeni Allah da kaina zanyi”” da kyar ya kyaleni, ya fita yana dariyar mugunta yace yarinya zaki sani ne ai. 

Akwatina ya bude ya fito min da rigar barci cikin wayanda sauban ya kawo min, , rigar daidai cinya, kuma shara shara CE” ana ganin komai na mutum wuyanta abude, dai dai cibiya akwai rami zaka iya sa hannu”” sannan kuma dai dai inda kan mamanta zai zauna shima andan  mai rami, inkasa zai fito waje””  kallon rigan yayi yana dariya, sannan ya ijye ya fita zuwa dakin sa don watsa ruwa.

Bayan nafito nayi Shafa ko ina na jikina sai da na budesa da kamshi,, kayan bacci naga kan gadona, na dauka, Rigan tamin kyau, ballura da hujin dake jikin Rigan ba”” nasaka Rigan, na kalli kaina a madubi nace subhanallah, dai dai kan mamana awaje yake, kamar zai tsole maka ido, dai dai cibiyata shima akwai huji zaka iya sa hannu””.

Gaba nane ya dinga faduwa ni gsky bazan iya kallon yayana da wannan kayan jikin nawa ba” na juya kenan naga mutum tsaye saura kadan in sake ihu, da sauri ya manna ni jikin bango yasaka bakin sa cikin nawa yana wasa da harshena, sai aika min sakwanni yake”” tare da Shafa ni, cikin Shafa ni dayake, hannun sa yaji ya tabo wani Dan karamin Abu , ya kara tabawa kan mamanane daya fitowaje, aiko tuni yara murzasu yana gurnani, tureshi nake Amman ina yafi karfina, gashi ya mannani jikin Bango kamar za mushige, ga kunya duk tabi ta hanani sukuni”” da haka har ya sauko da bakinsa  kan kirjina, yafara caccaka da hakoransa yana gurnani dayan hannu sa ne yakai kan cibiyata.

*taku* *Ummu* *ruman* (nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

      150 & 155

Ni’ima tace aunty shazee yanxu ina sauban, shazee tace yanxu ko zaki ga ya shigo bata gama rufe baki ba yayi sallama” ga baki dayan su ido suka tsurawa bakin kofan shigowa” Shahrazad tace wa’alaikumus salam.

Tace Dan halak kaki ambato yanxun nan muka gama maganar ka, ya karatso ciki yana murmushi yace wato gulmata kikeyi”” daga sama sukaji murya abayan su , akace haba dai zaujatul da’iman bata gulma, ya karaso yana murmushi, suka rungume juna shida sauban, khalid ne” Khalid yace  hmm mutanan u.s wato kaki zama kasan ka ko” to zamu cika taranka”

Shazee tace my d duk yadda akayi yan matan u.s ne suka rike shi” sauban ya tuntsire da dariya, yace shazee kin fara ko, bara na kira amingi itace daidai dake, Khalid yace Ashe zamu muku runduna kenan.

Fatima, NI’IMAH, Nusaiba, khausar haka suka zuba ido suna kallon 3 star din nan cikin birgewa , sun matukar basu sha’awa, tare da mamaki.

Shazee CE tace AF na mance fa, kun sani na shagala ina biye muku, alhalin inada baki” sauban ne da Khalid suka jiyo inda su Fatima ke zaune” tuni idanuwan saban ya sarke danata, yayin da itama haka, tun shigowar sa, gabanta ke harbawa” sai kuma yanxu da sukayi 4eyes ” ita dashi sukace ya ilahi azukatan su.

Shahrazad tace my friends ga Yaya Khalid dina Angona, sannan kuma ga yayana Muhammad sauban” su Fatima sukayi murmushi tare da gaida sauban da Khalid, suka amsa cikin fara’a, shazee ta kalli sauban da Khalid tace wayannan kawaye nane da muka hadu a skull din mu, sakamakon wani hali da suka fada kwatan kwacin nawa.

Khalid yace garin Yaya hakan ta faru, nan dukan su suka zauna shazee ta warware wa sauban da Khalid komai”” sun tausaya musu kuma basuji dadi ba.

Khalid da sauban suka masu nasiha da fada, tare da cewa insha allahu zasu taimake su , zasu maida su gidan iyayen su “” sannan kuma zasu dawo gidan Shahrazad da zama, kafin asan abunda za ayi”  sauban yace ke Fatima da NI’IMAH, auren dake kanku shine Matsala dole sai mun shigo da iyayen mu cikin lamarinku, don asan yadda za abullowa lamarin”” don wanna. Maganar babbace.

Fatima tace mun gode sosai tabbas haduwar mu da aunty shazee alkhairine” da badan itaba da ba Masan kuskuren da muka aikata ba.

Ni’ima tace tabbas hakane, yanxu duk hankalin mu ya koma ga iyayen mu , don musan halin da suke ciki.

Khausar tace mungode sosai gsky munji dadin labarin Ku mai dauke da darasi, Allah ubangiji ya kara hada kanku,, aunty shazee bamu da kamar ki” kin taimake mu” Allah ubangiji ya barki da Yaya Khalid dinki ,, Yaya sauban kuma Allah ubangiji yayi maka zabi na alkhairi, kai saudaki ne’ inama inama?

Nusaiba CE ta fashe da kuka  yayin da kowa ya juyo wajenta hankalin su tashe, cikin rudewa Fatima da shazee suka ce lafiya Nusaiba meke damunki, ganin kukan na Neman fin karfinta, ta tashi ta fita da gudu waje, tare da toshe bakinta.

Su shazee ne zasu bita Khalid ya dakatar dasu yace kukyaleta, kar kubita tana  bukatan kemewa, akwai abunda ke damunta.

Ni’imah tace tabbas akwai abunda ke damun Nusaiba, tun lokacin da aunty shazee ke bamu labarin ta, tashiga wani hali, Fatima tace tabbas hakane nima ina ganinta ta gefen ido ” a lokacin naso na tambayeta kuma sai na share.

Shahrazad tace oh ni yasu meke damun Nusaiba, bayan sauban yagama jin su ya sulale ya fita waje, yayin da Nusaiba ta jingine jikin mota, Ashe motan sauban ne, yazo zai Shiga ya wuce gida don yara meke damunsa” rabon dayaji wannan yanayin ya manta, sai kuma yanxu da idonsa yayi arba Dana ta kwayar idon ,zai bude motar kenan yaji shashshekar kuka tare da cewa, wayyo Allah ni Nusaiba, meyasa xuciyata zaki min haka, daga jin labarin sa sai kisa min son sa” wlh ina son sauban ina kaunar Muhammad”” yadda take fadar sunan yaji duk duniya babu macen data iya kiran sunanshi.

Nan ta durkusa tana kuka mai tsuma zuciya, yayi saurin bude mota batare dataji ba, ya zagayo inda take, hannun sa yana rawa yasa ya dagota, daga kasa” zabura tayi” don kallon waye ido hudu sukayi”” idon sa jajur, itama haka, sun dau mintina suna kallon juna, yayi mata nuni da hannu tashiga gaban mota ta zauna” ba gardama Nusaiba tashiga.

Ta zauna tare da kifa kanta kan cinyoyinta , takara fashewa,, yace ya ilahi,, yace Nusaiba , ta dago tana kallon sa, tare da cewa na’am.

Yace meke damunki har kike kuka haka, me aka miki, pls ki fada min kinji, cikin raunin murya yake magana.

Takalleshi da kyau tana magana acikin zuciyarta, tana cewa sauban cikin lokaci kankani, xuciyata ta jarabtu da sonka, gashi nikuma ba ajinka bace, , yace injiwa yace ke ba ajinane ba”” Ashe maganar xucin da take yafito fili tayi saurin rufe bakin, tare da zaro idanu waje, yayi mata wani irin murmushi mai mika sako ya juyo dakai, tare da rike hannun ta yace Nusaiba nasan sona kike””, kuma kin Riga da kin samu don shigo wata gidan xuciyata tamin arba da matata uwar ya’yana”  nima haka Nusaiba ina sonki ina kaunar ki.

Bantaba  tunanin zan samu wacce zanso ba bayan shazee sai gashi ban ma taba jin yanayin danakeji ayanxuba.

Ya kara rausayar da kansa kasa yace nuscy zaki auri tuxuru, zaki zauna dani, ina kaunar ki nusaiba””.

Nusaiba ce ke murmushi tare da rufe fuskarta, ,tana murna, yace ki bani amsa mana.

Dakyar ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da ya sunta tace”” a hakan naga tuxuron na haukace ason sa, ina sonka zan zauna dakai har abada, yace promise tace yes promise nusban ever in love.

Kawai basu Ankara ba sukaji shewa da tafi, shazee ta rungume Khalid dinta, sai murna  suke, Khalid yace lallai Allah ya amsa addu’ar mu”” komai lokacine sai Allah yayi.

Nusaiba wani uban kunya taji, shiko sauban ko ajikinsa” su Fatima sukace wato dama Nusaiba ciwon sune ya kamaki,  suka kwashe da dariya”” Nusaiba jitayi kamar kasa ya bude ta rufe kanta.

Aiko sauban ganin iskancin da suke mata, yayi wa motar key yaja da gudu ya bar gidan, Khalid sai cewa yake kai mallam ba afa daura auren ba daza ka tafi mana da ita.

Me shazee zatayi inba dariya ba” khausar tace abun mamaki baya karewa, ni dama nayi tunanin haka”” Nusaiba jin ana tafiya amota ta dago ido tana kallon sa cikin mamaki.

To INA zasu

*taku* *ummu* *Ruman* muyi hakuri da wannan wlh ban jin dadi ne.

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

    145 & 150

Dayan hannun sa na kan cibiya ta sai wasa yake dashi shi, yana min tafiyar tsusa, danaga abun na son ya wuce gona da iri wani karfi ya zomin na Dan ture shi kadan, tare da fara kukan shagwaba, shiko duk a wahalce, sai bubbuga kafata nakeyi”” tare da cewa Yaya Nah tsoro fa nakeji” shiko haka ya zuba min ido yana kallona saka makon bubbuga kafan da nakeyi, haka kirjina ya dinga sama yana kasa, ko ina sai rawa yake”” ni shaf na manta ma ” kalan kayan dake jikina.

Cikin kasa kasa da murya Khalid yace in bakyaso in miki komai ina so kimin tafiya daga nan zuwa bakin kofa in gani””  sai a lokacin na kalli kayan dake jikina”” nayi saurin nasa hannu na don kare jikina” tare da cewa wayyo Allah.

Yayi dariya yace na yaushe kuma, ai naga kayana””  yanxu in baki so in kara ta baki to kiyi mun abunda nace miki inko ba haka ba” zaki sha mamaki.

Dayake ina tsoro Dan yi shiru ina tunani gani nayi kamar yana alaman  tashi , ai ban San lokacin Dana fara tafiya ba ” na juya baya ko ina na jikina sai girgixa yake”” shiko sai lashe leben sa yake.

Aiko ban Ankara ba naji an fisgoni nafada jikinsa, nace wayyo my pls ka kyaleni wlh tsoro nakeji” yace karki damu baza kiji zafi ba” cikin dabara ya cire mun rigata, yashi ga kissing na ko ina na jikina, hannu sa na sarrafani, Niko mutuwar tsaye nayi, danaji bakina sa kan na Fulani na, tuni na sake masa jikina, wasa yake dani baije ga babban hanya ba”” sai da yasa na jiki na kamu Allah Allah nake ____ ? Uhmm Ku karasa kayan Ku cool shugaba, Yar Mulki rabi’ah, nan kukafi auki.

Asuba ta gari, khalid ne yatashi yayi wanka, ya dauro alwala, ya gabatar da sallah “” ya tashe ni, da kyar na bude idona don bacci ne a idona SBD ban samu bacci ba jiya, da kyar na diro kafafuwata kasa zan tashi na sake wata Yar kara, da sauri ya karaso inda nake yace sannu ko my baby, cak ya daukeni, sai toilet y direni cikin ruwan da ya hada mun, shi ya min wankan Niko sai kara langwabewa nake.

Ya gasa min jikina, sannan yace nayi wankan tsarki, shi kuma ya fito ya gyara gadon da muka kwanta ya cire zanin gadon ya shimfida wani.

Bayan nagama na fito ya taimaka min nasaka kayana  sannan nayi sallah, shi kuma ya Shiga dakin sa, bayan ya dawo ne ya ganni akwance  akasa ina bacci.

Yazo ya daukeni muka hau gado muka kwanta ya jamana bargo bacci mai dadi yayi awon gaba damu.

Bamu muka tashi ba sai wajajen sha daya , Donni na rigashi tashi ma, naje nayi wankana, nafito na Shafa mai na tsantsara kwaliyata, “” na zabo kaya mai kyau nasa ka tare da kashe Dauri na feshe  jikina da turare, sai kamshi nake 

Na kalli kaina a madubi nida kaina nasan na hadu”” sai murmushi nakeyi da na tuno Daren jiya nayi saurin rufe fuskata.

Ni nusnim nace wannan murmushin menene, ban sani ba sai su hjy ceeymer da cool da Yar Mulki da Sadiya da rabi’ah.

Na tashi naje kusa da Yaya Khalid na zauna ina kallon sa, sonshi na fuzgata  na saka bakina dai dai kunnan sa ina hura mai tare dasa hannu na afaskar sa ina shafawa” na gangaro kan leben bakin sa sai waiwayi nake masa, karaf kuwa yasaka yatsata cikin bakin sa, yana tsotsa kamar karamin yaro mai shan nono, nayi nayi na kwace hannun nakasa ya bude idon sa yana jifata da wani zazzafan kallo mai kashe jiki.

Yasa hannun sa ya janyo ni na fada jikin sa yace my shazee kinyi kyau sosai fa, sai kamshin dadi kikayi , kin tada min da hankali fa,, ya kamata in ya mutsa kwalliyan nan yanxu.

Ganin yana kokarin saka hannun shi cikin rigata, cikin shagwaba nace my d yunwa fa nakeji, kuma ni wlh nagaji, ya fashe da dariya yana kwaikwayen muryata, yace nima my baby ina bukatar kine. Yadda yayi maganar yabani   dariya, dukkan mu mukayi dariya”” yace bara baje nayi wanka ko tace to , na kara gyara dakin nawa “” na fito parlo,,, na fito ba da dadewa ba, naji Ana kwankwasa kofa, na karasa wajen don budewa.

Su aunty amingi ne. Da kannan sauban nabila da Sadiqa, ihun murna mukayi tare da rungume juna, kamar wayanda suka Dade basu hadu ba, sauban ne ya karaso da gudu jin ihun da yayi “” yayi zaton wani abune ya sameni”” yana my d my d lfy mai ya sameki”” baimaga su amingi yazo yana tattabani duk ya rikice ya rungumeni yana bubbuga bayana””  tafi da shewa yaji abayansa ana cewa , wo bros wannan soyayya haka da bata boyiwa, hmm I like that, saadiqa CE barama mu kashe muku hoton”” binsu da ido yayi galala yana kallon su, “” yace yaushe kuka zo?

Amingi tace kuna can kuna soyayya tayaya zakusan munzo” to awan mu daya zaune kofar parlon Ku muna jiran Ku”” saura kadan mu tafi shine muka kara bubbuga kofan, sai ga Shahrazad ta bude mana!!! Kunya duk tabi ta ishemu”  Khalid ne yayi karfin hali yace ke dama amingi kincika sa idon bala’i mijinki ya Shiga uku wlh, suka kwashe da dariya.

Suka shigo cikin parlon shi kuma Khalid ya wuce dakin sa don karasa shirya wa.

Amingi ne ta zungure ni tare da daga min gira tana cewa yane matar bros da fatan dai an ba mawa Yaya Nah abunda yakeso ba aja mashi aji ba” Nabila kanwar sauban tace lallai ma amingi, ke tayayan ki ma kike bata Amarya ba”” aji kuwa dole sai anja mashi, don mace sai da aji”” hahaha lallai Nabila wato abun saniyar ware ce ko, to zaki Shiga hannu na, muka kwashe da dariya”” cikina ne yayi kugi, nace wash Allah sukace lfy nace yunwa nakeji”” Khalid ne ya karaso yace kunki ba matata abinci kun sata gaba sai surutu kuke mata”” saadiqa  tace bros maida wukan ga abinci can an kawo muku, ya tashi ya dauko ya zuba mana abincin sannan ya janyo ni”” kancinyar shi yafara bani abaki inaci”” abun ya burgesu haka suka Shiga yi mana video da hotona, suna mana kirari kamar agidan sarauta.

Rayuwar aure mai dadi wasa wasa har nayi shekara biyu a gidan Khalid muna dirzan soyayyar mu””  kuma ya mai ya cikama hajiya alkwarin cigaba da karatuna , inda aka samamin admission a masu”” lokacin ina da ciki”” sauban ya kanxo gidana muxauna muyi ta hirarmu”” saida yayi da kyar sannan soyayya ta tafiya azuciyar sa”” zaman u.s yasa shi ya kara kyau da kwarjini.

Kullum nida Khalid sai mun mishi magana akan yayi aure sai dai yace mana aure lokaci ne in lokacin yayi ba makawa sai yayi”‘ Sadiqa kanwarsa tayi aure”” haka kazalika nima na haihu na haifi Dana na miji mai kama da Khalid, yaro yaci suna Umar farouq “” Khalid ya rushe gidan babana an gyara yayi kyau”” babana kuma ya auri innata kanwar hajiyata, dayake mijinta ya rasu.

Suna zaune lfy da mama indo har yau ba labarin nafeesa ,, har an fitar da rai”” rayuwa mai dadi muke yanxu haka Khalid ne mijina.

To kunji labarin”” su Fatima sukace woow aunty shazee gaskiya munji dadin labarin ki mai dauke da darasi da abun al’ajabi, kuma muma munyi da mun sanin barin gidan iyayen mu.

Ni’ima tace aunty shazee yanxu INA sauban, shazee tace yanxu ko zaki ga ya shigo aiko bata gama rufe baki ba yayi sallama.

*taku* *Ummu* *Ruman*

(Nusnim)

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

    155 & 160

Nusaiba  jin ana tafiya a mota ta dago ido tana kallon, shiko ya daga mata, yace yane” tace INA zamuje haka , yace wajen ammina  zamuje” naga sun saki agaba da tsokana!! Nusaiba tace haban sauban, yanxu ko kunya sai ka kaini wajen ammi?

Yace to menene, ai ranar da suke sun gani ne yazo”” nasan ba karamin murna zasuyi ba!! Nace kayi hakuri don Allah kabari ba yanxu ba” tunda kaga ba mu koma gidan iyayen muba!! Kuma ba musan andaura mana aure ko ba adaura mana ba” wani irin Jan birki yayi , kiiiiiiiiiiiiiiiii,  sai data tsora ta!! Cikin tashin hankali ya juyo yana kallon Nusaiba, yace ai bazai taba yauwa ba, wannan karan bazan taba yarda ba.

Kota halin kaka sai na aure ki Nusaiba, bazan kara yin asara ba””kisa aranki nanda sati biyu insha allahu kinxama matar sauban.

Haka Nusaiba ta zuba mishi ido tana kallon sa kamar Wanda ya haukace , sai huci yake, yabata tausayi sosai “” cikin lokaci kankani haka har ya kamu da sonta”” sai hamdala take azuciyar ta.

Cikin sanyin murya tace my sauban insha allahu kamar mungama mallakar juna!!! In Allah ya yarda wannan karan baza ka taba kara rashin masoyiya ba!!! Sai a lokacin yaji zuciyar sa ta masa sanyi”” yace nagode Nusaiba Allah ya barmu tare ameen.

Yaja motan  ya tsaya awani super market , yace mata yana zuwa shi kadai ya Shiga ya jido kayan kwalliya, dasu turarur ruka masu kamshi, wajen Leda 6, kasa mashi abayan mota, ya Shiga motar, sai tudun wada wajen masu gasa gaji yaje *taraba* *suya* wani kam shine mai dadin ji  ke tashi awurin, manyan motocine da hamshaqai ke layi awajen, can na gano cool da Yar Mulki sai rabi’ah, suna wanke wanke sai lashe bakisuke,  aunty rabice tazo ta Dan gutsuran masu nata data siya.

Bayan ya siya suka wuce GDA”” suko su Shahrazad , ankira su aunty amingi da Nabila da Sadiqa ta fada masu, sauban yayi mata fa.

Bakaramin dadi sukaji ba, Khalid ne zaune kusa da matars shazee da dansu Umar farouq “” dayan bangaren kuma su Fatima ne , hira suke su duka  .

NI’IMAH tace oh su Nusaiba shiru fa, SHAHRAZAD tace aikuwa dai , inaga sunbiya wani wajena”” Khalid yace kudaina damun kanku suna can sun samu lambun soyayya sun baje.

Sai ji sukayi ance  eh wlh mun samu wajen daza mu baza soyayyar mu batare da an samana ido ba”” daga ido sukayi don ganin waye sauban ne ke wannan maganar” sai ya bone kamar bashi yayi ba”” Nusaiba na gefenshi suka karaso ciki” suka zauna kujera daya” dama tun amota sauban yacewa Nusaiba bonewa zasuyi su nuna musu sun fisu  iskanci”” inba haka ba toh baza su barsu su zauna lfy ba.

Cikin mamaki shazee tace lallai kam  kunfi karfin mu, tace my d kallafa kujera daya suka zauna kamar ba yau suka hadu ba, ko irin kunyannan”” Nusaiba CE tace aunty shazee dane ake wannan kamar yadda kukayi da Yaya Khalid gida danci cikin zolaya Nusaiba ke wannan maganar,  Khalid yace my shazee wlh muyi shiru don wayannan masoyan sunfi karfin mu, naga Kansu na hayaki kadan ya rage su kona mu fa.””‘ Khausar tace aikuwa Yaya Khalid, nida nasan Nusaiba da kunya amma yanxu ta bada mawa idanunta toka.

Sauban yace inba haka muka muku ba, to baza Ku barmu  mu huta ba, xaku samu agabane, shiyasa muka muku haka, gaba ki yansu suka kwashe da dariya!!! Me gadine ya gama shigo da kayayyakin da su sauban suka siyo.

Ko wacce ya mika mata leda daya na nusaibace Leda biyu, bakaramin dadi sukaji ba, nan aka Shiga cin taraba suya.

Washe gari su Fatima sun kwaso kayan su dake gdajen da suka kama, hajiya tayi kewar su, bataso tashin su ba,, amma sunce mata zasu dinga zuwa gaisheta, taji dadi har ta masu alheri”‘ sun dawo sunga gidan cike da hayaniya , su amingi da yaranta hudu, sai Nabila da yaranta uku, sai saadiqa  da yaranta biyu, cikin sallama suka kara sa cikin parlon”” amingi ta tashi da murnanta kamar ta sansu din nan, kowacce sada ta rungume tare da cewa wellcome my sister, su Nabila da Sadiqa ma haka”” nan aka Shiga gaggaisawa.

Sadaqi tace wacece Amaryan Yaya sauban, ni’imah tace, ki cinka mun baki zabi” tace to , suka tsaya suna kallon ta suga wa zata zaba, ta nuna Fatima, amingi tace kai ba wannan bace ta sakiyar Ku CE, wato Nusaiba, shazee ne tace tayaya kika sani.

Tayi murmushi tace ai tun lokacin da suka shigo naga take Dan jin kunya tanan Nagano”” Nabila tace Nusaiba muna sonki, don kyau tace ke awajen mu, don kinrudar da yayan mu, dole muma mu soki, gashi kina da kyau.

Ai tuni Nusaiba ta bar wajen don kunya, Shahrazad tace Nabila kinga kinsa taji kunya ko”” Sadiqa tace damma ba aunty amingi CE tasa ta gaba ba, Aida inaga sai ta nutse katsa” sukayi dariya, amingi tace kin samun idofa saadiqa keda Yaya Khalid kamar ciki daya kuka fito.

Su Khalid sunyiwa iyayen su magana akan su NI’IMAH , anyanke kowacce zasu je gun iyayen ta, haka nan aka dunguma  , akace za afara zuwa garin  su Fatima, sun kama hanyar zuwa garin ,, gaban Fatima sai fuduwa yake, har unguwarsu sukaje, tunda ga nesa ta hango gdansu , hawayene ya silalo mata .

Baban Shahrazad ne yace nan ne gidan Ku tace eh,, sai akace su mata su fara Shiga, da yake da aunty Hauwa aka taho sai Shahrazad dasu Nusaiba” Fatima ke gaba, atsakar GDA ta hango mahaifiyarta na kwashe abinci, sallamar da akayi ne ta dago kai, waza ta gani kamar yarta Fatima, wacce ta Dade da begenta.

Aida gudu Fatima taje ta rungume mahaifiyarta tana kuka, itama mahaifiyar kuka take, tana cewa Fati Nah ina kika Shiga kisamu a damuwa     munyi Neman har mun gaji, aunty hauwace tace me gidan na nan akwai baki maza awaje,  sai a lokacin suka dawo cikin hankalin su””  tace yananan ta masa magana shima cikin murna ya fito dayake da baki awaje shiyasa baibi takan Fatima ba.

Aka shigo dasu cikin parlon Gidan intakai ta maku , nan dai aka bayyana masu komai, sunyi kuka kuma sunyi da sun sanin auren dauka mata”” ayanxu , hakama tun bayan tahowar Fatima mijinta ya saketa, ba aure akanta.

Komai ya daidaita washe  gari suka kama hanyar suleja garin su NI’IMAH, sun bar Fatima a can akan zatayi sati daya ta dawo Kaduna saboda zasu fara jarabawa.

Sun iya garin su ni’imah lfy itama andaidaita da iyayen ta, ,, itama bata da aure tuni mijin ya saketa, kwanan su daya suka wuce Adamawa mubi garin su khausar, itama NI’IMAH anbarta a can”” iyayen khausar sunyi murnan ganin yarsu, dama ita ba adaura mata auren ba ta gudu”” nanma kwanan su daya, sai ya rage Nusaiba kadai, tayi kewar yan’uwanta sabo turkin wawa” dukkan su sai da sukayi kuka.

Nan akaje jigawa garin su Nusaiba,ita harda Neman aurenta ma”” ita kadaice iyayen ta, suka so bada Matsala don da iyayen ta cewa sukayi dole sai sun mata auren nan da bataso har ta gudu, ganin sauban na kuka yana rokansu shine ya basu tausayi, har suka ammin  ce, ba karamin dadi sukaji ba”” baban Nusaiba ya kalli baban Shahrazad yace mallam nikam kamar naso ingane ka wlh, baban shazee yace aikuwa nima, inata maka kallon   sani, kamar munyi karatu an an *guri* ko secondry skull din nan na yan maza dake garin hadeja, kaman sulaiman ko, haka kuwa kai kuma abdulmaleek ko , kwarai kuwa, nanfa aka kara gaisawa , yace SULAIMAN yanxu Nusaiba Yar kace, shine kaso kayi sakaci” gaskiya ka godewa Allah da ya hadata da Yar wajena wato Shahrazad”” baban shazee ya kara masa nasiha da bashi shawarwari!!! Yayi godiya sosai.

Shazee da Nusaiba sai murna suke sakamakon iyayen su maza abokanaine”” baban Nusaiba ya damkawa baban shazee komai nadangane da auren Nusaiba da sauban, yaji dadi sosai””saida sukayi kwana biyu sannan suka shirya tafiya dakyar Khalid ya lallabe sauban su tafi,”” don yace shi  bazai tafi ba, har sai ranar da Nusaiba zata koma sai su koma** saida baban sa ya lallabesa sannan suka wuce kaduna tare sa kawar juna, Nusaiba da sauban harda kwalla.

*taku* *Ummu* *Ruman*

Nusnim

Ana hubbiq aunty Shahrazad Allah ya barmana ke

Amarya agun farouq dinta

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     165 & 170

Najib yace Fatima dama kina nan?

Ina nan wlh , ayya ya kk ya kwana biyu, ya yara?

Lafiya lau amma banda yara single nake, najib yace da kamar naso naji kinyi aure ko?

Fatima tace eh, nayi amma auren ya mutu, yace ashsha Allah yasa shine mafi alkhairi ameen.

Yace biki kema kikazo kenan”eh kawata ke aure ayya ni kuma oga nane ke aure ” Fatima tace. Sauban kake nufi” yace eh shine, ko shine mijin kawar taki ” eh shine.

Ayya Allah ya basu zaman lafiya ameen “” su ni’ima ne suka karaso inda take, sallama suk masu” najib ya amsa ” Fatima tayi saurin cewa har kungama abunda kukeyi ne? Suka ce eh .

Tace naji ga kawayena , ni’imah ga najibullah nagarin mu”” khausar tace woow Fatima shine najib din nan naki?

Fatima tayi saurin cewa ke uwar surutu, najib dai sai murmushi yake , yayi kamar baiji abunda khausar ta fada ba ya basar da maganar”” tuni khausar ta bar wajen don zuwa shaida mawa aunty shazee da Khalid, don ga dama tazo kar su bari najib ya subucewa Fatima.

Bayan tafiyarta najib yace Fatima ko zan iya samun number ki, “” tace ba damuwa nan ta bashi number ta ya kira layin , number sa ne ya fito akan  wayan!!! Khausar tagama fada mawa su shazee suka tsaya nesa da su suna kallon Fatima da najib.

Bayan najib ya tafi Fatima ta fara Dan tsallen murna, tare da daga hannu sama tana rokon Allah ya bata najibullah amatsayin mijinta amin.

An watse daga dinner kowa ya dawo gida agajiye, nan aka baje da hira ana tsokanar SHAHRAZAD da Nusaiba , tun suna jin kunya har suka daina.

Khalid ya sami sauban ya fada masa haduwanta da najib tunda yana aiki akanfanin sauban din,, nan sauban ya nuna murnar sa yace insha allahu bayan biki zan masa magana.

Najib kuwa yana can yana zancen zuci tare da tuno maganar khausar ashe  Fatima na sona? Indai ko hakane, bakaramin dadi najiba, don ni ma ina sonta.

Washe gari aka kama hanyar zuwa jigawa don daurin aure, mutane dayawa sun hallara, anyi biki sosai a jigawa,, dauran aure ya Tara dunbin jama’a sosai, bayan andara da la’asar aka dauko Amarya zuwa kaduna “” kai tsaye aka wuce da ita gidan mijinta dake malali, Nusaiba tayi kukan rabuwa da iyayenta.

Gidan Nusaiba mai kyau yadda baza a iya fadan kyawun gidan ba” wannan na barma masu karatu, da kyar su Fatima suka yi mawa Nusaiba wayau suka gudu, taci kuka har ta gode mawa Allah”  gidan ya rage sai ita kadai’ “” sauban ne yashigo cikin sallama a hankali ta amsa mashi.

Sai murmushi yake ya karaso kusa da Nusaiba tare da daga mayafinta yana Amarya kinsha kamshi bakya laifi koda kin kashe Dan masu gida, Nusaiba tace habadai sai dai inban kashe ba, dukan  su sukayi dariya.

Sauban yace Nusaiba yau gamu amatsayin ma’aurata cikin inuwa daya, gaskiya ba karamin murna na tsinci kaina ba”” yanxu tashi muje mu godewa Allah, sun gabatar da sallah tare da karantu  addu’oi na zaman lfy  da samun zuri’a dayyiba.

Bayan sun gama sunci sunsha, sauban yace yana zuwa bayan fitar shi Nusaiba tashiga toilet don wasa ruwa, bayan ta gama ta fito ta feshe ko ina na jikinta da turare, tasa kayan bacci taga babu maraba da tsirara , tayi sauri ta dauki zani ta daura, ta saka hijabi sannan ta hau gado ta kwanta.

Bayan sauban ya gama shirin bacci ya shigo dakin can karshen gado ya hangota ta dukunkune”” yayi murmushin mugunta tare dafadin azuciyar sa, lallai za’ayi fama,  tana jinsa ya hau kan gadon   ya janyota jikin sa, kirjinta sai bugawa yakeyi .

Yace baby nuscy ya kikasa hijabi zai shake miki wuya fa, ko zafi bakya ji cikin murya kasa kasa tace bana jin zafi” yayi murmushi.

Yace yi hakuri kicire nifa mijin kine kidaina jin kunyata yau ranace da zamu raya sunna””” Dan Allah karki bare wannan lokacin ya wuce mu, kiji tausayina Nusaiba “” haka yabi ya lallameta da dadin baki , da dabara ya cire hijabin da zanin”” kirjinta ne abayya ne.

Ai tuni hankalin sa ya tashi, ya kai masu cafka, kamar wani zaki, da zafi zafi yake aika mata sakonni abunka da mayun waci”” Nusaiba sai kuka take tana bashi hakuri ai ina bai masan tanayi ba,””taga ba sarki sai Allah.

Haka nan ta mika masa kanta, sai da ya rabata da komai na jikinta  , ko ina saida ya lashe daga sama har kasa , itama tafara biye masa’ yaji dadi sosai amma yana Shiga babban hanya ta saki kara , sai da ya toshe  mata baki , sun batu yake shi kadai, sauban yaji shi awata duniyar.

Hmmm Ku karasa wannan Harkan.

Washe gari da Kansa ya mata wanka, ya shirya ta kamar wata Yar baby, breakfast ma shi ya hada masu, don yana kowa yazo da safe don kar  a takura su, yazo yana bata  ita kuma sai langwabewa yakeyi”” saida sukayi sati daya suna durzan amarci batare da kowa yazo gidan ba. 

Su Shahrazad ne zaune suna cewa oh su Nusaiba da sauban shiru kake jin su, sun kashe waya, don kar adamesu”” dama duk shuru din mutum kaidai kawai bisu da ido” khausar tace aikuwa, mu ma dai bara muzo muyi auren nan. Muji  me akeji haka, suka kwashe da dariya.

Bayan sati biyu da auren su Nusaiba sauban ya kira Khalid sukagaisa, Khalid yace woow mutumina an shigo sahun manya , kaje birnin maji dadi, sauban ya kwashe da dariya yace sosaima kuwa”” yanxun ma da kyar na iya kiran ka don yanxu mun  kusa dayin harka .

Hahaha amma kai Dan iskane fa gskya kafi karfina sai anjima”” ya kashe wayan yana dariya.

Akwana antashi babu waya wajan Allah Fatima da najibullah sun hada kai tare da taimakon su Khalid, haka su ni’imah da khausar duk sun fitar  da mazajen aure, anyenke biki bayan sun kammala degree dinsu tunda saura wata biyu.

Nusaiba kuma tana dauke da Dan karamin ciki, Wanda ya kara mata kyau”” amma kuma ga laulayi” shine aka nema mata mai aiki , wata yar budurwan yarinya bazata wuce shekara ashirin da hubu ba.

Amma kana ganin yarinyar kaga alamun  damuwa, kuma bata fiye magana ba, kullum cikin kuka take” Nusaiba tayi tambayen har ta gaji, ” shine tajewa da Shahrazad da zancen yarinyar ita dai tana bata tausayi gata da girmama mutane” Shahrazad sarkin  tausayi da taimako ta shirya tazo gidan Nusaiba don taga mai aikin nata.

Nusaiba taji dadin zuwanta, ta kira mai aikin nata don ka mawa aunty shazee lemo, kanta akasa tashigo parlon har gaban shazee ya ijye zata juya .

Shazee tace baiwar Allah yarinyar tayi saurin daga kai don gasgata mai muryan nan , ido hudu sukayi, dukan  suka razana tare da mikewa tsaye, shazee tace nafeesa dama kina Raye , itama nafeesa tace Shahrazad Ashe zamu sake Haduwa”” suka rungume juna tare da sakin kuka,  nafeesa tace kiya femin Shahrazad , nida mahaifiyata  munbiyewa sharrin zuciya mun rabaki da masoyin  ki,”” sai gashi cikin sauki Allah ya saka maki”” nan nafisa tafara  ba mawa shazee labarin ta, Ashe ta Dade cikin hauka inda kullum cikin bola nake zama, da haka har wani Mara tsoran Allah ya min ciki , wajen  haihuwa na warke daga haukan wata matace ta taimakeni “” dayake ina yawan zama alayin su har yara na tsokanata , itace takan ban abinci”” data ga zan haihu ne shine ta taimaka min,” na haifi diyata mace!!

Matar ta tambayeni gidan iyayena nace ban sani ba don bani so indawo gda, da yarinya a hannuna , ace aina nasamu, don cewa karuwanci natafiye Wanda kuma ba asan hauka nayi”” da haka naci gaba da zama wajen matar , ta rikeni tsakani da Allah, dayake bata da karfi shine tasa mamin aiki anan gidan.

Shahrazad ta kara fashewa da kuka, nan ta ba mawa nafeesa labarin dalilin haukanta, harda canjin rayuwa daya zo musu.

Cikin kuka nafeesa tace mahaifiyata ta cuce ni , talala tamin rayuwa, gashi asanadiyarta na haifi Yar da ban San ubantaba”” dakyar dai aka rarrashi nafeesa akan data yafewa mahaifiyarta.

Khalid da sauban sun dawo tasanar dasu komai, aka tafi da nafeesa GDA,mama indo na ganinta ta rugo aguje tana tattabata don ta tabbatar ba mafarki takeyi ba.

Suka rungume juna suna kuka , ta rungume baban shazee wato kawunta, tare daneman gafara, nan shazee ta kora masu bayani kamar yadda nafeesa nafada masu.

Mama indo tayi kuka kuma tayi da tasani, tunda abunda ta suka shi ta giba tunda gashi harda yarinya nafeesa ta samu, duk ta sanadinta!!!

Dakyardai aka kwantar masu da hankali, baban shazee ya kara masu nasiha,  yace ita duniya nan fadice gareta, Allah baitaba bari azalunci bawansa batare daya saka masa ba”” a kullum musaka tsoran Allah azuciyar mu, KAR muce  ai ba bu  me ganin mu inxamu yi mugunta”” ina ba haka bane, Allah na kallon mu” sannan kuma muyawaita istigfari don naiman yafiya, mudaina biyewa sharrin zuciyar mu don zata kaimu ta baru mu”” duk lokacin dakaji zuciyarka ta ayyano maka Abu Mara kyau to ka gaggauta fadin auxubillahi minalshainanil rajeem”” muna rukon Allah ya karemu daga sharrin mugayen mutane, da dabbobi da aljan ameen

Su Nusaiba naga kasu sun fita da result mai kyau, kowa cikin farin ciki yake, anti auren su Fatima, su Nusaiba da shazee sun taka rawar gani abikin.

Bayan biki da sati uku Nusaiba ta haifi kyakkyawar yarta mai kama da sauban, inda taci suna Shahrazad “” bakaramin dadi su Khalid da shazee sukaji ba!!

Small SHAHRAZAD tasamu kyaututtuka daya wa” su Nusaiba suna rokon Allah daya bamawa yarsu hali na taimako irin na shazee.

Bayan shekara daya nafeesa tasami miji tayi aure, yarta kuma tana wajen mama indo, Allah kuma ya Dora mawa mama indo son yarinyar nafeesa.

Itama Fatima ta haihu  da namiji yaro yaci sunan babban najib.

Rayuwa mai dadi Khalid ne zaune amota da matarsa shazee sai yaransu guda biyu Umar faruq sai Hauwa, sai abdulmaleek shine auta” khaleed yace my d kinga yadda rayuwa ta sauya ko, yau gamu da Yaya harku, Allah ubangiji ya daya mana su amin

Ta Dan kwanta kan kafadansa tana murmushi tace  Allah ya barminkai  my d dina jarumin jarumai, Dan kwalisan matasa, da bazarka nake taka rawa, INA sonka my Khalid.

Yasa dayan hannun sa yaja hancina tare da cewa , shazee kinfi kudi kinfi gida kinfi mota, ke rayuwa ce shazee, don kin min babban kyauta har guda uku, ayau da daddare zancika na hudun , suka kwashe da dariya.

*ALHAMDULILLAH*

Anan nakawo karshen labarin nan, badon naso bamawa ba” amma insha Allah zakujini awani sabon novel dina” inafatan zaku dauki darussan dayake ciki”” in nayi kuskuren ayafemin”” nagode sosai makarantana

Group dina na all dostis of nusfulhayat INA kara gode muku da kuka bani goyon baya, cool Yar Mulki fauxiya, rabi’a, aunty rabi, hauwa’u Nuhu” yayar cool , Fatima , Ummu Ilham ” Ummu anas da sauran members din NASA kuna raina nagode sosai.

Ban manta da kuba Sadiya ta GRP din m Jabo

Da ameera , da billy s Fari , da sauranku.

Sai kuma Dan uwana, me son novel dina,nagode maka dama kirani , da kuma kullum in banyi post ba, sai ka tambaya nagode sosai..

Wannan littafi nakine don ke nayi, kina cikin raina masoyiyata, Allah y barmu tare shona Shahrazad dina” 

Ina sonki aunty Shahrazad Allah ya barki da farouq dinki,, much of luv Shahrazad.

Kawayena 

Miss zozo

Hafsat Rano

Ummu Yahaya

Ummu Adnan

Ayusha ilyasu

Maman Bobo 

Nafi Anka

My Qurratul ayni

Much of luve all

Saini marubuciyar.

*Nusaiba* *SULAIMAN* 

Wacce  akafi sani da *Ummu* *Ruman* *nusnim*

08064481931

Love u all

[4/15, 10:03 PM] ‪+234 806 448 1931‬: ❣ *SHAHRAZAD* ❣

(Labarin sharrin zuciya)

*BY* *NUSNIM*

     160 & 165

Fatima NI’IMAH, Nusaiba khausar bakaramin kewar gidajen iyayen su sukayi ba, sunyi da sun sani, sannan kuma sun godewa Allah dayasa babu wani Abu daya faru dasu “” kuma suna kara godewa aunty shazee.

Bangaren sauban kuwa ana can ana shirye  shiryen biki”” haka Shahrazad ba abarta abaya ba, duk abunda tasan Amarya na bukata shi take Adanawa, don sun kusa dawowa , SBD skull”” Fatima acan garin su take tambayar wata kawarta  bilki take ce mata , niko bilki najibulla yana nan kuwa?

Yayi aure ne?

Bilki tace ai najibullah yana Kaduna dazama yanxu, yasa mi aikin gwamnati, sai ya samu Hutu yake zuwa gaida iyayen sa”” amma kuma har yau bayyi aure ba , yace har yanxu baiga wacce yake so ba.

Fatima tace Allah sarki najibullah, bilkisu tace Fatima badai har yanxu kina son sa ba, Fatima tace tabbas har yau ina son sa, amma ba zan taba fada masa, har inshi da kansa yace yana sona, kin San ban son raini, don yanxu kika cewa namiji kina son sa, to kin Shiga uku wlh don wata rana sai ya goranta maki, amma zanyi tayin addu’a har Allah yayi min zabi mafi alkhairi”” Donni yanxu ko wani auren akace za asake min ga mutum da banso, tsab zan zauna kuma in masa biyayya irin ta aure” nasan komai mukaddari ne daga Allah, ba abunda Allah bazai jarabce ka dashi ba don yaga zaka karba ko baza ka karba.

Bilki tace hakane kawata, gsky yanxu kinyi sanyi , ba dole ba , bilki tace gsky aunty Shahrazad alkhairice arayuwarku, tunda gashi ta sanadiyarta tacanxa min kawata, ta dawo min da ita har gida, Fatima CE ta kaiwa bilki duka abaya, tace kin fara tsokananki ko.

Kinga yanxu saura kwana biyu mu koma Kaduna SBD muna da jarabawan Shiga level 4 final kenan , ga kuma bikin Nusaiba da sauban kinga ko hidimace agaban mu.

Bilki tace hakane kam nima dai zan daure inxo in ba mawa idona abinci, inga jarumai uku din nan wato Khalid Shahrazad sauban, Fatima tace aiko Dana ji dadin zuwanki.

Yau lahadi ranan da su Nusaiba zasu koma Kaduna, , khausar tafisu nisa ita tun ranar sati tazo kano gidan su Fatima washe gari kuma suka dauko hanya zuwa Kaduna”” gaba ki dayan su sun hadu a tashan kawo, ba karamin murnan ganin juna sukayi ba , cikakkun mata masu haiba tafiya suke cikin kasaita, kowacce da akwatin ta Tanaja har suka isa gun motar da aunty Shahrazad ta aiko adauke su.

Can gida kuwa su amingi dasu bila sunzo gidan shazee don karban baki, gda ya bude da kamshin girke girke, yadda kuka San wasu baki za ayi daga kasashen waje, kuma ina duk sabagen son da SHAHRAZAD ke musane shine ta shirya musu haka.

Sun iso har cikin haraban gidan suka fito daga cikin motan shazee ce tafito da gudu gudun ta tare da cewa oyoyo my sister  nayi kewarku, duk saida suka rungumeta .

Harda su amingima saida suka rungume su, aka dunguma ciki. Nusaiba sai ware ido take taga ko zata ga sauban duk suna lura da ita, shazee ne tace Amaryan mu karki damu yanxu angon naki zaizo, cikin jin kunya Nusaiba ta sunkuyar da kai tare da cewa kai aunty shazee bashi nake nema ba fa, Umar dinki nake son inganshi fa”” suka kwashe da dariya amingi tace rabu da wannan shazee itama ta koyi sa’ido, Khalid ne yace ba irin nakiba da , ya karaso yana dariya, aka gaggaisa” yayi shigewar sa daki.

Sauban ma yazo suka kebe da amaryarsa suna hirarra soyayyar su.

Wasa wasa su Fatima har sungama  jarabawan su, yayin da Shahrazad itama tagama degree dinta, ta fito da result me kyau , sai datayi kukan murna tana inama hajiyata na nan, baban ta ya tayata farin ciki tare dayi mata fatan alkhairi arayuwarta , takara rungumar mijinta tana me gode masa da yatsaya  mata har tagama, lallai Shahrazad tayi dacen miji nagari Wanda zakayi alfahari dashi.

Saura sati biyu bikin Nusaiba, sauban yazo ya kaita wajen ammin sa, taji dadin ganinta kuma tayaba da hankalin Nusaiba dayake ya’yanta su Nabila suna bata labarin ta, tun bata gantaba  tayi na’am da’ita.

Khalid da Shahrazad su suka dauki nauyin kayan dakin Nusaiba sun hana iyaye yin komai, dayake yanzo arzikin Khalid sai kara karuwa yake yi.

Iyayen Nusaiba har Kaduna sukazo godiya dayake suma rufin asiri gare su,, yadda aka kasa bikin Nusaiba shine, za’ayi sisters day, sai kuma dinner daza ayi, kafin adaura auren, ana kuma gobe daurin aure a tafi jigawa can mahaifan Nusaiba, adaura aure, daga can kuma sai akawota gidan mijinta sauban , dake malali. Haka aka tsara.

Har GDA shazee ta kawo me gyaran jiki ta gyara Amarya da kawayenta, bilki kawar Fatima tazo  itama, agidan shazee akayi sister day, yasha kayan ado antsara dakyau, dayake  babban gidane sai kayi zaton a hall, yadda wajen ya tsaru, ba abar su yan GRP din ne all dostis of nusfulhayat ba , sunzo bawa idanunsu abinci, yayin da guda uku suka zo Neman sauban wato cool da yarmaulki da rabi’a.

The next day kuma aka tafi dinner , ,, sauban da Nusaiba sai daukan ido suke motar da suka hauma abun kallo ne, yaro Dan kwalisan matasa mai sabon jin, duk inda ya wuce sai yabar abun magana, kamar king laisu, hannun sa yasa ya kama hannun Nusaiba suna tafiya  a hankali don Shiga hall din’ sunxo daidai Shiga hall yasa dayan hannun sa akan   kwan kwason ta, ya Dan jawota jikinsa kamar wata Yar baby zuka zuba mawa juna ido sai karan daukan hotuna kakeji bakaramin bada style sukayi ba,”” ahaka har suka isa mazaunin su.dije sai wasasu yake,  kawar Amarya tazo tabada tarihinta hakama abokin ango, sannan aka saka kida, waje yacika da jikakkun yan gayu, Khalid ne yace shifa adole sai sun fito fili sunyi rawa don taya abokin sa murna, ba musu shazee ta amince, don gwanace wajen rawa  haka suka shika shigo fili suna rawa cikin girma, ba irin gajagan gajagan ba, suna cikin rawa ne, amingi tacewa m.c din ya sama wa su Khalid wakan , *kashiga* *raina*

Habawa ana sawa zancen ya canxa salo jin su suke kamar sukadai ne afili, rawa suka Shiga yi, batare da sun San mutane n wajen ba, haka Khalid ya daga shazee cak yana jujjuyata, yayin da hannu watan biyu, sun dafa kafadan sa, shi kuma hannu sa yana kan kwankwa sonta “” ya daga kai sama yana kallon ta itama tana kallonsa suna aikawa junayen sakonni, aiko tuni kallo ya dawo Kansu, su sauban sukazo suna masu liki amingi ne tasa aka watsa masu abun nan mai kyalli kalli daga sama.

Alokacin ne suka dawo hankalin su ya sauketa , ai fuskarta ta boye cikin kirjinsa don kunya” su sauban suka kwashe da dariya, Khalid ma karfin hali yayi, dayake aunty Hauwa tazo itama, agabanta akayi wannan fitsaran”” sauban ya daga mashi gira yana murmushi . amingi ne tacewa shazee ja’ira kamar ba ita bace  suka gama soyewa saura kadan fa kuyi kiss, ko kunyi zaton kuna kan gado ne, hahaha.

Shazee da ba bakin magana don ta hada ido da aunty Hauwa ,sai tayi mata murmushi. Shiyasa Takarajin kunya, ganin haka Khalid yaja matarsa suka bar cikin hall din.

Khausar tace kai yau ana soyayya a dinner din nan , NI’IMAH tace aikuwa aini saida na dauka awayata Dana Nusaiba da sauban Dana Khalid da shazee, sukayi dariya, Fatima natafiya zataje ta dauki drinks kawai aukaci karo da wani har wayanta ya fadi, tace auzubillah ya hakuri bawan Allah, ya tsugunna ya dauko mata wayarta  yace LA bakomai nida nafadar miki da waya, dagowan da zayyi sukayi ido hudu , gabanta ne ya fadi ta nusa  sa da yatsa tace najibullah, shima yace Fatima, sai sukayi dariya.

Insha Allah inaga gobe zan kammala novel Dina

 *taku* *Ummu* *Ruman* nusnim

Back to top button