Uncategorized

Matar makaho Complete Novel

 πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―

             ~ Na~ 

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

 

✨✨Godiya ta tabbata ga Allah  da ya nuna mini wannan Rana da Zan fara rubuta lbr na na farko cikin hukuncin ubangiji Allah ka bani ikon gamawa lfy 🀲✨

✨Tsokaci wannan shine novel Ina na farko  Koh da za’a ga mistake Koh typing error amini afuwa πŸ‘Œ

Free page

Page 1️⃣

Kuka nake baji ba gani bakin ciki ke dankare a cikin zuciya ta Wanda in har banyi kuka ba bazanji saukin suba Wai ni ce amarya amaryan ma na makaho mara ido na daga lulubena kasanciwar dakin akwai wutan nepa  glop ya haska Koh ido shiya bani Daman ganin daki dakin da Koh a mafarki van taba tunanin akwai ranan da Zan iyya rayuwa a irin Shiba Wai yau shi ake Kira da dakina na aure ni sumayya bansan lokacin da wani irin kuka ya sarkeni ba cikin takaici Mai tarin yawa ya Allah me naiwa Yan uwan mahaifina  da suka sakamin da wannan rayuwa Mai na tsare musu da suke mini irin wannan muguwar tsana da hassada ya Allah duk wannan magana cikin kuka nake yinsu  

Tsaye yake yafi minutes 30 Amma ya kasa karasawa cikin kofar wani irin fargaba ne dankare a cikin ransa Wai yau shine da mata sukutum Koh a mafarki Bai taba tunanin aure ba  kasan shiwarsa makaho maraya kuma Mara galihu sai abinda ya nemawa kansa Amma yau har Mata aka basa wance Bai taba tunanin samun taba amasayinsa na miskini  Anya zata karbesa a matsayin miji zata yarda ta rayu dashi cikin akwai Koh babu wannan sune abinda suka tsaya masa a Rai yayi ta maza ya daga kafarsa hade da Bismillah Yana tafiya da sandar sa Yana ma kansa jagora zuwa filin  kewayayeyyen kofar su Dan madaidaici ya juya ya tura kofar ya rufe harda lalubar sakata ya saka  a sannu a hankali yake takawa har yaji ya taba Dan tudu kadan  hakan ya nuna Masa ya iso dakalin kufar daki haurawa yayi sama Yana lalube tar yaji ya laluba ginin daki Yana bin ginin a hankali har yaji ya shafa window yanabi a hankali har yaji ya Kama labule mai masifan laushi da kamshi Wanda tunda yake a rayuwarsa Bai taba tunanin zai taba irinsaba kasan shewarsa  mutunne shi Dan babu ruwana ba ya maula Koh bara baya neman taimakon kowa in dai na abin duniya ne sai dai na lalurarsa Wanda ya zamto Masa dole 

Da sallama a bakinsa ya daga labulen tare da jingina sandar sa a kofar dakin ta waji ciki ciki na amsa sallamar itama Dan ta zama dole na daga kaina ina kallon wanda Koh ba’a fadaba nasan shi ake nufi da ango makaho cikin wani irin takaici nake kallonsa don matashine Wanda bazai Gaza shikara 28 zuwa 30  ba laifi makanta da wahalan rayuwa su kadai za’a kira cikas a tare dashi don kyekkyewa ne na karshe dogo fari tas wanda wahala ta kodar da fatarsa Amma duk da haka fatar daga Gani zatayi matsifar laushi   gemu mayalwaci sosai  ga idanu masu girma da haske amma mara amfani a ganina bakinsa madaidaici Mai shegen kyau ga hanci har baka Mai yalwan gera don daga gani yanada yalwan gashi sosai sai gashin kansa Mai yawa amma rashin samun wadasheshen gera sai ya Yi wani iri Amma daga Gani gashine na Fulani  asali duk da babu datti don fes Kan take  kiransa na zaratan mazane masu Kiran karfin sosai na kurawa kayan jikinsa ido wani kudadden yadine na shadda wando da riga Mai guntun hannu Wanda suka Sha ruwa sosai wai su ya saka kenan ranan aurensa daga Gani sune na gindin akwatin sa Koh Bai fada ba ni Kam na raya a Raina  kauda fuska nayi kamar bansan mutun ya shigo ba shi kuma cikin sanyin jiki da lalube yaji ya taka wani cafet Mai shigin laushi a cikin dakin duk da baya gani yasan tabbas Mai tsadane Koh me na dakin Nan don Bai mantaba dazun khadija take Masa gulma wai dakin Aunty’amarya Mai kyau da Kaya irin na gidan murtala Hon na unguwan su harma nata yafi nasu kyau tun daga lokacin jikinsa ya kara sanyi don ya tabbatar ba yar kananun mutane bane aka aura Masa a matsayinsa na makaho  da lalube ya iso tsakiyar dakin Wanda yaji abubuwa Kamar filo a xuzxube a kasar cafet in dakin  a hankali ya zauna tare da aje ledan dake hannun sa baka cikin zazzakar muryarsa Mai cike da Kamala ya gai Dani Koh juyuwa vanyiba don bana son ganin sama  bare  na sake Jin ya sake furta Ina wuni nayi wani dogon tsaki  Jin haka yasa shi Jin wani mummunan faduwar gaba Amma baice kome ba yayi shuru  munkai minti goma babu Mai shiwa kome sai Karan fanka Kiran OX babba wance Taki bawa dakin wani irin iska Mai sanyi  sosai  cikin rawar murya yace ga kaza nan kici sai muyi nafina mu gode wa Allah cikin zafin nama da takaici na hayyaya Koh Masa cikin fada Wanda duk Wanda ya sanni yasan ba halina bane Kuma Koh kyau Bata mini ba nace baza’a ci matseyacin kazar kaba kuma sallah kayi tayi har alfijir ya ketoh Bai shemin kome ba Amma kallo daya namar nasan maganar ta dake sa sosai  a hankali ya laluba yafita waji yayi iyya nemar buta Koh Randa baiji inda aka aje ba saboda duk kayan kofar an sauya Mata zama kasanciwar sabbi aka kakkawo hakan yasa ya koma dakin a hankali da sallama Ina dai zaune Ina  kalonsa yazo ya fara lalube a hankali ya daga labulen ya tura kofar ya rufe harda sakata cikin nutsuwa Naga ya fara lalube  ban ankaraba naji ya lalubu ni cikin wani irin shock daga ni harshi muka Masa baya shikam harda buge kafar sa da katakun gado cikin i’ina nace meye haka cikin Dan sanyi jiki yace kiye hakuri ina neman gadone Zan kwanta cikin gadara nace  wallahih bazan kwanta dakai gado daya ba gadai kujira a Chan jika kwanta a hankali ya fara lalube Ina dai zaune Ina kallonsa  haka ya ringa zagaya dakin daker ya gane kujiran a hankali ya zauna ya cire rigansa ya kwanta  a hankali cikin lumsheshen kujira na alfarma 3sita Nima kayan na cire tunda dai ba idone dashiba na ragi daga ni sai brz da siket nayi adu’a  na kwanta a hankali nake sauke ajiyar zuciya har bacci ya dauke ni  shikam ya kasa bacci sai tunane tunane yake yanason yin lafilfilu Amma ba Hali tunda baisa inda zai samu ruwa ba a kofar tasu Kuma baison zuwa rijiya a Darin nan gudun wani a cikin mutanen gidan su gansa su Masa abinda suka Saba rashin mutunci  a sannu a sannu wani bacci Mai Dadi ya daukesa don a tsawon rayuwarsa Bai taba bacci ana zafi da fanka ba sai yau lol asuba da gari amarya da ango 

Free page ban yarda da a sayarmin da littafi ba😠pls

Jinjina ga Yan Free booksπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

Mom Abba πŸ™„

Mrs jabeer😘

Sarah πŸ˜’

Zee black🀐

Nafisa voice note 😜

KπŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―

             ~ Na ~

 πŸƒRukayya IbrahimπŸƒ

 

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

✨ Bismillalahih rahamani Rahim✨

Free page

 *More comments* 

 *More post* 

Page 2️⃣

Kiran farko akan kunnensa ya farka a hankali  tare da addu’an tashi daga bacci  kafarsa yazura ya sauke a kasan cafet da Bismillah ya mike saye ya fara laluben    rigarsa daya cire jiya da dare da zai kwanta cikin hukuncin Allah ya samu rigan ya saka a hankali ya nufi kofa cikin lalube ya gane kofar ya bude ya fita ya tuna baisan inda buta take ba don baiga tsohon tasaba sake dawowa yayi a  hankali yake lalube harya lalubo gado ba tare daya hauba yasa hannu yana laluben ta cikin sanyi Amma baijitaba a cikin ransa ya kitsima lallai wannan gadon babbane sosai  Hawa yayi a hankali Yana lalube har yaji hannunsa ya taba wani abu Mai masifan laushi sosai Kamar fatar jinjira  da sauri ya zari hannun cikin murya kasa kasa yake. Tattaba  filon da yaji kanta akai inda Allah ya Sosa ma Mai nauyin vaccine ita da Allah Bata San ya taba Mata jiki ba  cikin bacci take Jin ana bubuga Mata filo ido ta bude a hankali don baccin Bai ishitaba ta sauke idon ta a kansa Yana zaune kusa da ita cikin sauri ta Mike da masifa tace Kai lfy meya kahoka Kan gadona eye ,, cikin sanyi Wanda na Lura halittansane yace Daman buta nake so ki nuna mini na ibo Mana ruwa asuba tayi wani haushine ya kamani wannan miji ne Koh rainon sa zanyi Amma saboda albarkacin sallah yasa nace toh muje na dauki rigana nasa na fita a dakin nayi wajinda aka  kewayemin da fallange Dan madaidaici Wai kitchen na shiga kayan kitchen ne na alfarma kome yaji yar an rasa wajin sawa an koma da saura Kamar yanda aka maida kujiruna da wasu Abubuwan kayan dakina  masu yawan gaske na shiga na kunce butan a cikin kwalinsa na karfine cikin kayan da aka saimin da na roba na hada biyu na fitoh na samesa a saye yana jirana Mika Masa nayi cikin kaushin murya nace randuna na babu ruwa cikin lalube ya karbi butan hade da furta bara na ibo a rijiya kala bance Masa ba ya fita sai gasa ya dawo da ruwa a buta daya ya shigo ya ajimin ya koma ya dauko dayan ni kuma tuni na idar da alwala harna shiga daki na bude akwatina na dauki hijab da sallaya na shinfida na tada sallah 

Alwala yayi ya tafi masallaci  da sandar jagoransa  Ina idar da sallah nayi lazimi   har lokacin Bai dawo ba na daga idanu na na kalli agogon bango Wanda aka likawa bangon dakin karfi Shida saura  naja dogon tsaki Dan a lokacin aka dauke nepa ni kuma  bana iyya bacci ba AC Koh fanka Sam nasan Koh na kwanta bazan iyya bacci ba Ina zaune har karfi Shida lokacin gari ya waye dakin yayi haske  a hankali nake bin dakin da kallo dakine madaidaici sai gadona Wanda yaci Rabin dakin  da kujira dogo guda daya don sauran babu wajin zama Mai dasu akayi  plasma TV  ta gefin gadon aka makala don ba fili da waddrop ta daya gefen  sai kafet da su kushin da aka saka a tsakiyar dakin da karamin freezer ata bakin kofa  kayan sawana makil  a akwati set dake gefen Kan gado sai fankan kasa sune suka samu wajin zama a dakin  a hankali nakai hannu na dauki jakana na bude na dau waya ta Ina dannawa  tunda babu nepa bare na kunna TV an hadamin kayan kallo harda Star Time Ina  da sallama naji ya shigo dakin na amsa ya laluba kujira ya zauna cikin sanyi yace ina kwana kamar bazan amsa ba na amsa da lfy klau cikin sanyi yace me zakici na sai Miki  cikin mamaki da al’ajabi  Wai sayo abinci Ina amarya akawoni cikin gidansu Amma arasa Mai bani abinci sai ya siyo  duk da ban karewa gidan kallo ba nasan babbane tun jiya da dare  maganar sa ce ta dawo Tani daga duniyar tunani Dan wake Koh alele Koh kosai za’a karba miki cikin mamaki nake kallonsa sai Kuma naji ya bani tausayi tun jiya yake kokari yaga ya kyautata mini  yasa cikin sanyi nace Masa  

Gaisuwa ga  members😜

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― *

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book 🀧

Page 3️⃣

“Basai ka saya abinci ba, akwai kayan abinci, ruwa nake so, asaya da bread sai kayan meya” cike da kuzari ganin na masa magana, a taushashe sabanin jiya, ya Mike ya fita, Yana fita, ya laluba aljuhunsa Aiko Allah yasa,Yana da gudan dari biyu da dari, na cinikin mangoron sa na jiya, da safe da Yan change ya hada ya fita tsakar gidan, sai ji yayi an saka ihu da shewa, daga mata har matasan samarin, ana ga ango ga ango, wanda Koh tantama babu,duk wanda yaji yasan na raini wayo ne, da shikiyanci kasanciwar ya Saba da irin wannan tozarci na Yan gidansu, sai abin Bai  damunsa Sam, wuce warsa waji yayi, ya fita kofar gida, dayake bakin titi ne gidan nasu, yasa shi sayuwa a bakin kofar gidan, Bai jima ba dayake safiya ne, yaji Mai ruwa na bugawa kiransa yayi  duka ya saya,  ya hadasa da yaron makwantansu, ya nuna Masa kofar amarya, shi kuma ya shiga shagon haladu, sayan bread na dari Mai kyau ya hada da Lipton na goma, da sugan  hamsin, ya karasa table in gwanja yasai kayan meya ya hada ya kamo hanyan gida ,

Mai ruwa ya shigo da yaro “na tashi na fitar da randana, na roba Mai girma sosai irin Mai cin jarka Sha biyar innan, Mai ruwa na Gama juyewa, Yana shigowa ya biya kudin ruwan,  ya ajimin laidan cefenen “dauka nayi nawuce kitchen”, shi kuma ya fita, “kitchen na shiga kome an jiramin kuma ba laifi kitchen din ya dauki Rabin kayan da akai mini, gas na kunna na dauko dankalin turawa na fere na daura a tukunya, kwai na fasa na zuba kayan hadi na aji a gefe,  kettle na ruwan zafi, naso daurawa Amma ba nepa dole na daura bojuwa, ( tukunya) a dayan Kan gas in na zuba kayan kamshi da Lipton na rufe, naji” buruntun bude kofa lekawa nayi nagansa rike da Ghana must go na kaya madaidaici na kayansa ya shigo da lalube’ ya fada cikin dakin  yaje ya aje sai gasa ya fitoh yana lalube cikin Dan tausayin sa, wanda bansan Ina dashi ba, “nace maikake nema ne” ?   cikin sanyin halinsa yace bokati, “na mike na dauko masa” sabon boket, da kwandon soso, na kayana da soso sabo da sabulu, na wanka Mai sada  na akwatina,” hada a kwandon na Mika Masa” ya karba cikin lalube ya lalubi kwandon yace La!! ai Ina da soso  harda sabulu barshi kawai “cikin Jin haushi nace na sani ai na baka kayi dasu” Bai Musa ba ya karba yaje ya zuba ruwa a bokatin ya cika, da lalube ya shiga ban daki, ya ajiye ya dawo ya lalubi inda ya aji butar da yayi alwalan, asuba ya dauka ya cika ruwa ya wuce bayin, 

“Cikin kankanin lokaci na hada breakfast, Mai kyau na soyayyen dankali da kwai tie ga bread a gefe naji daki na dauko kazar dana Gama zagi jiya nazo na juye a kwando na makala gudun karya rube, da rana nayi meya dashi’ na fada dakin na kakkabe gado na jira filon Kan kujira, na share dakin na fesa turarukan daki, na fitoh na share baranda na hada da kasar kofar duk da ban taba share kasa ba,  sai dai tayis Koh seminti haka na lallaba na share,  Ina gamawa” Yana fituwa a wanka daure da zani, tsoho a kwankwaso hannunsa dauke da kayan sa daya cire, a boket Yana lalube ya dibe ruwa ya zuba a boket in, ya jika kayan ya mayar bayan gida ya aje, ya fito Ya shiga dakin, “na ibi ruwa Nima na shiga Wanka da soso da towel na  Ina fituwa na fada dakin, ban Damu ba, tunda ba kallo yakeye ba” “Ina shiga na gansa zaune a kasa ya chanja Kaya zuwa jallabiya fari duk da yasha ruwa jallabiyan, Amma a wanke tas, 

“na shiga na bude akwatina na dauki Kaya, rigane dogo na material Mai kyau  da tsantse, NASA na hada da hula fari na fita waji na shanya towel in a igiya da kayan da na cire samun kar suye tsami,  na shiga kitchen na dauko abincin na fada daki da  plet na zuzzuba karyawan na Mika Masa” “na ibi nawa nayi Bismillah Muka fara ci” babu Mai magana a tsakanin mu tunda yasa, abincin nan a bakinsa yake godiya wa Allah a zuciyan sa, daya mallaka Masa sumayya amasayin Mata, tunda zata iyya dafa Abu ta basa yaci Wanda rabon da adafa abasa tun kafun ummarsa tabar duniya shiyake sayawa kansa, abinci she yake nemawa kansa, 

 “muna tsaka dacin abinci naji an banko kofar shashin mu an shigo, ba sallama aka daga Mana labule dukkan mu dagowa mukayi don ganin wani ishanshen ne, haka sabanin shida Banga mamaki a fuskar Saba sai dai alamu sun nuna baiji Dadin hakan  ba, ya kurawa kofar ido Kamar Mai kallo yanda nayi sakake Ina kallon kofa cike da mamaki……. 

πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌYan free booksπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌNaga comments naku naji dadin karfafa mini gwuwa 

Mom Abba 

Umme 

Nafisa voice note

Dr humaira 

Da sauran su

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― *

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

Page 4️⃣ 

Budurwa ce  zata Kai kusan sa’ata cikin gadara da taunan cingum. tace amarsu ta ango karyawa ake ne? gashi nazo kallon dakin Amarya 

 ***kala bance Mata ba

 shema duk da baiji Dadin hakan ba Amma shuru yayi ba abinda yace ,haushi sosai naji Amma naja bakina nayi shuru don banda lokacin wannan Mai zubin karuwai,  abinci muka cigaba da ciii ba Wanda ya kulata cikin mu biyun,

cikin bacin Rai  tayi tsaki ta juya tafita.  Koh ido ba mudu bane yasan kema ni ba sa’ar yinta bane kallo daya tamin ta gane ni ba kallan raini wayo bane Kamar yanda suka Saba Raina Masa, 

**mamaki ne ya kamani, lallai sai nayi da gaske Zan iyya zama da Yan gidan nan. don dagani Basu da mutunci wallahiπŸ˜’

Muna Gama karyawa ya mike  ya dauki kwanukan da mukaci abinci harda nawa ha Hada ya fita dasu a kitchen ya Ajjye,

Dawowa cikin dakin Yayi cikin sanyin halinsa ya bude baki a Hankali ya furta Zan fita wajin sana’a Koh akwai abinda Zaki bukata,?

 Kamar bazan tanka ba Amma na daure nace “babu”Koh zaka dawo kaci abincin  Rana”?  cikin natsuwa  yace min ah..ah  Zan saya naci sai yamma Zan dawo,

  “har Ina ne  wajen sana’ar taka” ? Cikin D’anjin Dadi jin Ina kulasa yace bakin titin kofar gida ta gefen shagonan,  su haladu 

** Ni Kuma Ina nasan wani Haladu bare shagonsa😏a Raina nake fada

Amma a zahiri cewa nayi “toh Inna Gama ka tura yaro yazo ya karba maka abincin”

 da zumudi yace toh ……toh Zan turo bayan azahar. Ya sa Kai ya fita

 ***Daki na koma na bubbude akwatunan Kayana na bubbude kayan  Ina jirawa a whtdp  wasu a dressed mirror kayane na alfarma   atamfufe  dinkaku  da Wanda ba dinkaku ba  takalma da jakunKuna gyeleluka abaya material duka na shirya Kayana a nitse make-up kit na aje sa a drowarn mirror    mayuka da turaruka na jirasu saman mirror. sauran kayan da suka rage na mai dasu cikin akwaiti ba wajen jirawa duk  ya cika ba fili na rufe na Mai dasu saman whdrp “,

 yarane  suka fara shigowa ba sallama ba gaisuwa suka shigo mini daki  harda Yan matan gidan suka cika dakin Wai sunzo kallon daki ga makwanta nata shigowa da sunan ganin daki Koh gulma ne oho,  ana haka aka kawo NEPA Daya Daga cikin Yan matan ta Mike ta kunna  TV 

haka aka  sake cika Wai ana kallo har baranda nidai abin daya isheni kawai na dauki wayata na fita waje,

 ” kitchen na wuce kazar jiya nake son hada miya dashi Amma kayan miyar jiya tayi kadan dole na shiga daki jakana na hannu mai kyau na dauka na fito waje budewa nayi na dau gudan dubu daya na aiki yaro a cikin Yan kallo kayan Miya Mai Dan yawa na Kara Masa da dubu biyu ya sayo harda kaza, don so nake na Kara na jiya bazai isaba ga yara a kofar.

Yaron na dawo mini da kayan Miya na fara aiki ba wance ta taimake ni Koh da jijjigen kayan Miya ne

 shinkafa da miya na dafa Ina Gamawa  na zuba a sabon kula Mai kyau na saka a basket da shukali da plt, na Koma dakin na bude freezer na dauki ruwan gora, na hada Masa a basket in na Ajiye, d’aid’ai yaron da Zai  aika ya shigo na basa.

 sauran abincin na zuba a babban faranti na hadawa yaran daban na sawa manyan daban daya ke nayi abincin da yawa sosai, Mika musu nayi ba kunya suka amsa  gabaki daya Koh kwanukan Basu daga ba suka barsa a Inda suka ci sun batamin daki  da datti sosai,

 na ibi nawa na zauna a baranda kan darduma  nayi Bismillah na fara ci ban tashi agunba saiga wani yaro ya shigo da sallama  amsa Masa nayi, “waalaikumu salam”ya gaidani,  “amsa wa nayi don naji dadin gaidani da yayi kaf yaran gidan da suka shigo ba Wanda ya gaidani Koh sallama babu,

Wai inji inji MAKAHO Mai mangoro aban abinci,

Wani Takaici ne ya kamani Wai sunan sama da MAKAHO ake kira “shap wallahih bazaiyu ba watoh nima haka za’a na kwatantani da MATAR MAKAHO Ina bazaiyu ba” duk Araina nake zancen nan. 

 Mikewa nayi na dauko masa basket in, basa nayi ya wuce 

azahar yayi Amma kaf yaran gidan ba Wanda yayi Haraman Sallah Nima bance musu kome ba, na mike na dauro Alwala na koma dakin Hijab na dauka na fitoh waje nayi sallah na kwanta a sallayan  Ina Danna waya,

  

Mutane Basu bar mini kofa ba har na Gama Tuwon dare na kwashe sukaci tukun suka fara watsewa daya bayan daya.  Har suka watse suna fita na share dakina na goge, dakin Yayi kaca kaca sosai chanja zanin gado nayi yara sun kakama mini na jikin gadon da hannu yayi daud’a na fesa Turarukan daki na wanke dakalin kafun  naji kofar yamin dama daman  shekan iska Mai Dadi, wanka na shiga a gurguje nayi alwala na fada dakin na shirya  nazo daukan turare Naga an min satan Mai Harda turare,

 Raina ya kara baci don na tsani mutun ya dauki abuna ban basa ba, na kudurta Araina bazan sake Basu wannan fuskan ba tunda basuda mutunci gobe ba shegen da zai shigarmin kofaπŸ˜‚( tab kofarki Koh na makaho) Kaya nasa na jona wayata a cherge da laptop  duka,

 **na koma gefen gado na zauna

tunani na shiga yi lallai rayuwa ba tabbas yau Koh mutun daya daga cikin dangina Koh kawaye, babu Wanda yazo.  watoh tunda talaka na aura kenan,? 

 alhalin duk wance tayi aure zuwa ake washe gari kallon gida da masu sallaman Amarya, a ranan. Amma ni ba Wanda yazo kallon daki ma bare sallama uhmm, 

Karfe biyar da rabi  MAKAHO ya dawo gida da kwandon abinci a hannu sai sandar jagoransa da lalube yakai kulan kitchen ya aje,  wanka yayi ya fada dakin Yana shiga na fita na basa waje ya shirya,

 Tana fita ya lalube Ghana must go insa ya dauki Kaya yasa ya fitoh waji lalube yayi ya dauki buta ya Kama alwala. ya  wuce masallaci,don har an Tada  sallah,

 **lokacin Nima sallah na Tayar ,Bai dawo ba sai da ya hada da isha’i Tukun ya dawo,

*** abinci na zuba Masa 

***na Koma Kan gado na zauna  TV na kunna na kamo Tashar Arewa 24  Ana cikin  Shirin kaddaran rayuwa.  bayan ya Gama cin abincin, kwanukan ya dauka yakai kitchen  hade da wanke hannu ya Sha ruwan Randa, ya shigo dakin, 

cikin lalube ya lalubo kujira ya zauna a hankali cikin magana Mai sanyi yace nagode da abinci yayi Dadi sosai Allah ya biya.” Amin” nace hankalina nakan TV,

 jawo laidar da ya shigo da ita baka yayi ya fitar da sabulu da omo.   sai wata laidar  mangoron yako, ya Miko mini ta inda yake tsammanin  saitin nake,

Cikin sanyin jiki da zullumin zata Amsa kuwa?

Yace ga mangoro ba yawa

***ban gwatselesa  ba na karba na mike naje na bude firij na aje.

 fita waje yayi, ya hada kayansa daya jika a ban daki da safe da Wanda ya cire dazun ya wanke ya shanya ya sake dawowa dakin yayi cikin magana d’ari..d’ari  yace Koh Zaki kawo kayanki Mai datti na wanke miki, 

***cikin mamaki nake kallonsa Wai ya wanke mini Kaya, lallai da wani idon Zan basa Kayana na fada a Raina, Amma a zahiri nace “ah ah na gode Zan bada wanki inya taru” baice kome ba ya lalube kujira ya zauna kawai yayi shuru ya kurawa TV da yake aiki ido kamar Mai kallo,

 ***abin har yaso bani dariya Amma na maze. muna zaune har goma, bacci na faraji,

mikewa nayi na chanja kaya  zuwa na bacci,  kashe TV da glop nayi na Kara gudun fanka zuwa 3 Addu’a bacci nayi na shafa na kwanta,

 a hankali  ya Tashi yaje ya  rufe kofar duk Ina jinsa dawowa  yayi  kwanta, kwanta a kujira  addu’an bacci yayi shima ya shafa. 

**Nima  gyara  kwanciya nayi,

Tun daga jiya zuwa yau, a Takure nake Sam ban Saba kwana da  namiji a daki ba, Amma ya zanye, dole na kwanta tunda daki D’aya ne bare na koresa falo.

Misalin karfe biyu na dare ya farka………

My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― *

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧 

Page 5️⃣

Dan a irin lokacin da yake tashi sallolin dare,

 mikewa yayi  ya riga ya gane ma’ajiyin Randa da buta fita yayi a dakin alwala ya daura ya dawo dakin,ya tada sallah sai uku ya koma ya kwanta, Kiran farko na asuba ya farkar dashi, Addu’a tashi daga bacci yaye.

A hankali ya sauka a kujira cikin sanyi ya lalube gadon ya tsaya a bakin  don bazai iyya Hawa ba kar a maimaita irin na jiya a hankali yake kiranta

 **sumayya!! sumayya!! *

**A hankali na bude idanuna cikin bacci nace “naji habba” baice mini kome ba ya daga  kafarsa a hankali da lalube ya bude dakin ya fita  **Niko waya na laluba a gefen filo don dakin ba haske na kunna hasken ya haska dakin sauka nayi Nima nayi waje don d’auro Alwala, **fitana yayi daidai da kammala tasa alwalan mikewa yayi Yana laluben sandanrsa,Harna kammala alwala Bai gane sandar ba. 

*Ina kammala alwala  na shiga daki daukar wayata nayi na fitoh na haska kofar  aiko Naga sandar Ashe faduwa yayi a kasa, dauka nayi na zungure sa da sandar a hannu *

 da sauri ya mika hannunsa ya amsa cikin sanyi sanyin sa yace nagode,

* batare da nayi magana ba don takaice waini sumy nice yau da miji MAKAHO shap wannan ai abin kunya ne ma Wanda ya sanni ya gansa a matsayin mijina, Tabbas nayi Wasa da Damata a rayuwa, shiyasa Allah ya jarabce ni a lokacin da ban taba tsammani Koh tunanin hakan ba,

 **Da sauri nayi istigifari na kauda tunanin a Raina 

* Koh amsa Masa banyi ba nayi shege daki na tada sallah, Ina idarwa Qur’an na dauka cikin jakansa Mai kyau na bude,

*nayi azkar in safiya, dana sabayi kullun na mike nabi lfyn gado bacci ya dauke ni,

 sai shidda da rabi ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da bakar laida na kayan shaye da kayan miya Jin ba’a amsa ba  ya lalube kujira  ya zauna,  numfashi Daya ji kasa kasa hakan ya tabbatar Masa ta koma bacci a hankali ya mike,waje ya fita da lalube ya Isa kitchen aje laidan yayi ,

 shanyar kayansa ya dauko a igiya  ya nade ya shigo dakin ya lalube Ghana must go in sa  Daya aje a lungun kujira da firij yasaka kayan,ya dawo Kan kujiran ya kwanta a hankali wani irin bacci Mai Dadi ya sauke sa,

**Ban tashi ba, sai Takwas na safe shima ihu da ashariya na dandazon mutanen gidan Wanda Koh tantama banayi tambe ake, shiya farkar Dani,mikewa nayi sanye da kayan baccina Wanda na saka jiya da dare riga da wando Mai taushi sosai sai hulan bacci d’uka farare ne tas.

*  da sauri na dirko daga Kan  gado nafitoh dakin naje na rufe kofar shashen mu don nasha Alwashe yau bamai shigarmin kofa kallo Koh ganin daki bare naji yau da tambe aka tashi* πŸ˜‚ (Anya ba tsoro ba kuwa?)

*Kitchen na wuce, ganin laidan kayan Miya a kasa,

* dauka nayi na bude    kayan miyane su tarugu albasa da tattasai sai dayan kayan shaye ne yau harda Madara, na laida da bouviter, bread, sugar, da Lipton,

 ruwa na zuba a kettle nasa Lipton, don yau muntashi da NEPA  na jona a socket  bude caton  indomie, na kayan garana laida biyu na dauka manya shap shap na daura na dau kwai na soya cikin 40 minutes na Gama hada breakfast na Kama shara,

✨ (tabbas aiki a wajen mace ribace babba duk kudin gidan ku duk mulki Koh gata ilimi da kyau in har mace Bata iyya girki ba gtoh Bata cika macen da za’a kira Tauraruwa ba Yan Mata a Kara bada himma karki xamantu baki da aiki sai adafa a baki kici ki kwanta kina Danna waya.koh makaranta kike zuwa at lest ki ware wasu lokutan  a Rana kina Taya ma’aifiyarki, 

aikin da kika tsana kina ga ana matsamiki ana bautar dake wallahih ribarta na zuwa don bakisan inda Allah zai kaiki ba)✨ *shawarace* 

**Tun sa’ilin da aka fara Yar Hali watoh dambe, a tsakar gidansu ya farka Amma Bai Mike ba har **fitanta da rufe kofar duk akan kunnensa duk yanaji Yana kwance ,

a hankali ya mike ya fitoh cikin sanyin halinsa da nutsuwa ya bude baki yake gai Dani,

**shuru na Masa naki amsawa * 

baiyi fushi ba ya kara tambaya ta, Koh Zan Kama Miki wani aiki ? Abin nasa harda rainin wayyo kenan, Wai ya kamamin aiki? da wani idon Amma saina maze nace “wanke-wanke nakeso kamin” ba musu ya lalube sandarsa da takalminsa shinyayye ya saka 

Da lalube harya lalube boket, ya dauka ruwa ya Iba a Randa ya aje a gefe da laluba har yakai cikin kitchen nidai Ina binsa da ido kawai, ganin garajen sa,

cikin tsawa nace “kaiiii aje kulanan abincine a ciki”

” tsaya na nuna maka kwanukan da  zaka wanke”

” Wai baka ganewa ne?

 Hala  banda rashin gani ma? harda rashin basira? zaka dauki kula kaje da nauye basiranka bazai baka abincine a ciki ba zaka zungumu??

Kala baice mini ba ya ajiye kawai ya jingina a gefen kitchen ya tsaya,

Zuwa nayi na dauki kwanukan nakai masa gefe na hada ruwan kunfa na aje kwando da kujira na tsaya agefe cikin masifa masifa nace gashinan Bismillah sai kazo ka wanke jiki a sanyaye yazo da lalube harya zauna Niko Ina saye a gefe ina ganin ikon Allah wanke kwanuka yake Kamar Mai ido tas suke fita Yana kifewa Kai Koh Mai ido albarka, mamakine y kamani Amma ban nuna Masa ba,

**Shara na kammala na gera daki na na jona kask’wan lantarki na zuba Turarukan wuta  a dakin fita nayi Naga har yanzun Yana Kan wanke wanke

Kwanukan akwai Dan yawa na abincin jiya da yara sukaci ban samu na wanke ba Harda na dare,

 *Wanka na shiga Ina fitowa na tarar ya kammala Yana zaune a kujiran tsugunne,

” Koh Mai ban shafa ba na zura kaya atamfa super Mai kyau siket da riga Mai k’wala da hannun roba* dinkin zamani

 *abinci na zuba ina ci  daidai lokacin shima wankan ya shiga  yana fitowa  wanka ya shigo dakin, Alhamdulillah Koh ba kome na Lura Yana da tsafta duk da bana rayawa a Raina Koh da Wasa zanyi rayuwar aure dashi Mai tsayi dole ya sake ni yaje ya nemi miskiniya irinsa Amma kafun lokacin bazan cutu da wari ba tunda Yana wanka ( lolπŸ˜…uhmm muje zuwa zakiyi bayani )

*Fita nayi na basa waje*

Kaya ya saka wani jimemmen t-shirt da wando jeas duk da tsofene Amma sunyi Masa kyau sosai ya laluben kujira yayi ya zauna,

Ina waje ban kulasa ba naci gaba da cin abinci na kammala zamana nayi A wajen naki basa abinci shi kuma Bai tambaye ni ba   Danna waya nayitaye sai kusan goma na safe na iba Masa a plt da shaye a Kofi na shiga dakin na aje Masa na koma Kan gado na kwanta,

 ya jawo plt in yayi Bismillah ya fara ci

 

Yana tsaka dacin abinci  muka ji bugun  kofar shashen  mu mikewa yayi zaiji ya bude na dirko daka kan gado cikin fada fada nace “bazafa ka bude kofar nan ba don yau bamai shiga kofar nan ehen kaji na gaya maka don Naga alama Yan gidanku basuje islamiyya ba”

Baice mini kome ba ya koma ya zauna 

Jin Mai bugun yaki barin kunne na ya huta,

hijab na dauka na zura na fita ,don gani wani isheshshine,

Bude kofar naye idona y sauka akan wata yarinya kyakkyawa sosai  farace Mai Kama da MAKAHO sak banbancin ita mace Mai karancin shikaru 18 zuwa 19 she Kuma namiji ne sanye take cikin riga na kodadd’in shadda sai hijab wuyan duk ya sabule gashinta har ya leko ta gaban goshi,

*Tunda aka kawoni wanna kaddararerren gida ban ganta cikin yaran gidan da suka zo kofana ba,

Aunty Ina kwana tace 

hanya na Bata cikin dakewa nace “lafiya shigo”

Shigowa tayi daidai lokacin shi kuma ya fitoh cikin dakin murmushe dauke a fuskarsa itama murmushin take da sauri tazo ta amshi kwanukan hannunsa hade da gaishe sa ya amsa,Yana tambayar ta ya su Goggo Aminar,

Ta basa amsa 

Tace in nazo nace tana gaida Amarya,ta fada tana kallona 

Amsa Mata nayi ba yabo ba fallasa “Ina amsawa”

Fita zaiyi  hade da tambaya ta Koh akwai abinda za’a saya Kai tsaye nace “babu “sa Kai yaye ya fita hade da cewa Khadija in Zaki tafi ki biya ta guna, da toh ta amsa Masa

Nidai daki na wuce naje na kwanta  sai da Naji fitarsa tukum na kwala Mata Kira ” Khadija shigo daki Mana kina tsaye a waje” don haka kawai naji yarinyan ta kwantamin sosai a Rai duk da bansan Alakarsu ba amma nasan akwai alakar jini a tsakanin su,

Da sallama ta shigo dakin na amsa Mata tana kukarin zama a kasa nayi saurin cewa tahau kujira Amma Taki da kerta zauna, firij na bude na dauko mangoron jiya da yayanta ya kawo na hada Mata da drinks harda ruwa na aje mata hira take mini Kamar na saba da ganin akwai ta da surutu sosai tun Ina amsa Mata har bacci ya dauke ni,

Ban farka ba sai 1:30 na Rana shima kiraye kirayen sallane ya tashe ni sai a lokacin na tuna Ashe fa Ina da bakuwa,

A hankali na sauke idona akan kujiran da na barta akai da mamaki sai Naga wayam ba kome,

Sauka nayi a gadon na fita a dakin cike da mamaki nake bin kofar da kallo har idona ya sauka akanta cikin sabon mamaki ganin ta a cikin………………..

Good morning fan’s πŸŒ₯️

An gaishiku Yan free booksπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€MATAR MAKAHO FAN’S GROUP πŸ€

Naga comments naku naji Dadi Kuma Ya karfafa mini gwwa

πŸͺ€My WhatsApp number

08084453785080844537850808445378508084453785awata ta kaina Salma Adam Allah ya bar πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― *

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

πŸ˜’ *More comments* 

😏 *More post* 

Page6️⃣

 shanyan Kayana da sukaye datti harda zanin gado Ashanye a igiya an wanke  harda kayan yayan Khadija (MAKAHO) 

Khadija na gani cikin kitchen, tana aiki,

* a Hankali na daga kafata na Isa kitchen in,

 “Khadija kece akitchen?” da murmushi a fuskarta ta amsa mini da Aunty, Naga har Rana baki tashiba shine na daura Miki Abinci shinkafa da wake miyane ban Gama ba ya kusa,

“Kayan nan fa waya wanke ?”

Nice Aunty ta bani Amsa, *wallahih in banji Dadi ba nayi karya sosai naji yarinyar ta shiga Raina sosai da fara’a nace Mata” gaskiya Khadija nagode wallahih Amma aikin ya Miki yawa da baki wanke Kaya ba,

La Aunty babu yawa fa kayan, ta bani Amsa 

“Khadija tashi muyi Sallah tukum tunda miyar kin daura a wuta”

..Toh Aunty 

Sallah mukayi, na sauke abinci na raba na zuba Masa na hada Kamar jiya,  na Bata ta Kai Masa  ” in kin Kaifa ki dawo Khadija”  da toh ta amsa mini,

Tana dawowa na iba Mana nida ita a plt daya, Muka zauna a waje munaci muna Hira cikin hiran nema nakejin ainahin sunan sa a bakin Khadija Ashe   *Al’ameen* ne sunan sa saboda larurar da Allah ya daura Masa shine aka batar da sunan zuwa MAKAHO Kai duniya, 

“Tambayar ta nayi a gidan nan take”?

Ah ah Aunty ni agidan Goggon mu nake ,

“Har wani unguwa ne haka”?

Ta bayan layin nan ne tsakanin mu ba nisa sosai Aunty,

Sosai muke Hira Kamar mun Dade da sabawa,

 “Aikin dare na hanatayi nace ta Huta ni nashiga kitchen nakama girki* 

kin zama tayi dutsen guga ta dauka ta fara gogan kayan da ta shanya duk yanda na hanata sai da ta gogi,

4:10  na yamma tace min zata tafi hanata, nayi sai da na Gama girkin abinci na sata tayi wanka Kayana na Bata cikin dogayen rigunana nakanti na Bata daya Dayake tana da tsawo sosai ya zauna Mata na hada Mata da gyele medium size kalar fulawar rigan,

Sosai kayan ya karbe ta na hada Mata da Mai turare harda powder,man baki, da Jan baki biyu, maskaras da sauran kayayakina da basa cikin set na make-up kit Ina na babata daker ta karba sai godiya take min,

 *nayi nayi taci abinci dare  Amma Taki,zuba Mata nayi a kula Taki karba sai da nace Goggo zata kaiwa kafun ta Amsa ta wace,

Fitar Khadija sai da ta biya wajin yayanta sosai take basa lbrn abin arziki Dana Bata da irin sakar Mata fuska da nayi,

Har cikin ransa yaji dadin  daraja.masa kanwa danayi sosai,

Hatta damuwar da ya fita da ita na safiya ganin yanda yau na tashi da zafi zafina abin ya tsaya Masa a Rai,

Wannan abinda nama Yar uwarsa tilo da yafi so  sai yaji zuciyansa wasai. 

Mangoro ya bata hade da naira dare ta rike a hannunta ya kara Mata nasiya sosai da hakuri A duk inda Allah ya ajita  kafun ta wuce,

*Khadija na fita wanka nayi nasa siket in kanti da t-shirt Mai kyau na daura gyele karami a kaina laptop na…..

Sai kusan shidda ya dawo gida yauma da kwandon sa a hannu, da sallama a bakin sa *amsa Masa nayi, kaina nakan laptop, *

Wanka yayi ya tafi masallaci yauma Bai dawo ba sai Isha waje na fita ganin yau ba NEPA, na fitar Mana da babban darduma na shimfida, 

*abinci na iba masa, nasa nawa na aje  Mana tare da Masa Bismillah zama yayi shima Muka fara ci *

Khadija ta tsanar Dani abin arzikin da kika Bata na gode, naji muryansa cikin sanyi sanyin sanan,

Ba kome wallahih abinda ba yawa,

Jin yanda na Masa magana a mutunce abin sai ya Masa Dadi sosai, mun Gama cin abincin har lokacin NEPA shuru na kasa shiga dakin saboda tsananin zafi da ake yau ga sauro,

Tashi yayi ya fita yaje ya sai Mana maganin sauro, Yana dawowa na karba na kunna,

 kitchen na shiga na yaga caton in indomie, zanyi fifita dashe,

* Wanka na sake shiga tsaban zafin da nake ji Kaya nasa vest sai wando Yale yale dogo har kasa,

Kushin na dauko a daki na zuba akan cafet in na kwanta Ina fifita,Yana zaune a gefe shima ya jingina da jikin gini,

Shuru mukaye dukan mu ba Mai magana,shikam tunani yake azaman da yaye da Sumayya ya fahimci Abubuwa cikin halayan ta,

 in Abu ya Bata Mata Rai, toh kowa ta shafa, in aka faranta Mata kowa zaiga fara’ar ta akwai ta da tsafta akwai iyya girki ga nutsuwa sam.bata da rawan Kai,

*Har Sha biyu bamu shiga ba, ganin dare yayi  ban tashiba ya mike a hankali yaji ya rufe kofar shashen mu, ya dawo ya shiga dakin  ya cire kayan jikinsa yadau wando  iyya gwuiwa sai riga Mara nauye , ya dauko filon kujira ya rufe kofar dakin harda k’wado   key in yasa a cikin filon sa,

Dawowa yayi ya tsaya a gefe cikin sanyin jiki yace “uhmm Daman Naga Kamar baki shiga daki ba kwanan waje zamuyi kenan?

“Eh wallahih Amma tunda akwai maganin sauro”?

Sake tambaya yaye in akwai wani abin kwanciyan a bani,Gefen dardumar na nuna Masa ya kwanta hade da furta” ita dayace” kwanciya yayi tare da Addu’an bacci, a hankali bacci ya dauke sa

*Sai kusan karfe daya kafun bacci ya dauke ni da ker’

Saboda rashin samun bacci da wure da bayi ba shiyasa yau Bai tashi yin sallar dare ba 

*Nikam ban sake sanin kaina ba sai asuba……..

Ayi manage ba yawa😩

Masu complain in page na kadan 

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

🌿Jumma’at Mubarak to All my fan’s

Free book🀧

Page7️⃣

*A hankali nakejin sanyin asuba na  ratsani har cikin kashi kowa yasan yanda sanyin asuba yake alokacin zafi,

*Juyi nayi a hankali Amma sai me jina nayi Kamar Abu ya tukare ni, bude ido nayi sosai, me Zan gani ni Sumayya  a kwance rabe-rabe a jikin MAKAHO, ai bansan sa’ilinda da na wantsala gefe ba, kwalbar maganin sauro na buge harya fadi a simintin dakali, ya fashe

Jin Karan fashewan Abu shiya farkar dashi cikin sauri ya mike Yana tambaya ta lfy?

**Nikam na kasa basa amsa toh me zance? cewa zanyi ka tabani Koh Kuna nace ajikinka na farka na ganni *

Cikin Dan daburcewa nake magana” am am Babu fa Daman na tashine ban sani ba na buge kwalba ya fashe”

Bai dai ji Miki ciwo ba ya fada cikin hanzarin karasuwa wajen da yake jiyo muryata,

“Ah ah  banji ciwo ba”

Ok Allah ya kiyaye gaba, 

*Da Amin na amsa *

Daga ni harshi Alwala muka  hanzarta farawa Jin har anyi raka’a daya a masallaci,

Muna kammala Alwala daki ya bude ya cire kayan jikinsa yadau jallabiya ya saka ya,

 

*Nikam hijab kawai na dauka har kasa, sai sallaya biyu nazo na shinfida Mana Jin an sallame sallah a masallaci, 

*Na hau Kan sallaya Daya nayi gyran  murya *

Jin hakan yasa a hankali ya Suma takawa Yana nufo inda yaji nake tsaye ganin ni yake nufuwa yasa” nace ga sallah na shimfida maka tunda Naga baka samu jam’i ba”

Ba musu ya ringa lalube harya Ji kafarsa ya taka wani abu Mai laushi sosai Wanda laushin ya banbanta da cafet in dakin,hakan yasa she gane sallaya ne ” Hawa yayi ya saita gabar ya Tada sallah Ina binsa,

Muna idarwa Naga ya Kama karatun Alkur’ani cikin suratul Qafe cikin zazzakar muryarsa Mai dauke da nutsuwa irin na mamilallun maza,da Kai (hadda) 

Nima.mikewa nayi na dauko Qur’an na bude Ina duba ayoyin da yake karantawa,harya Kai karshe ba gargada Koh wani harafi an basa hakkinsa, 

sosai nayi mamaki Amma Dana tuna ido kawai Allah ya jarabcisa  ba zuciya Koh k’wakwalwa bane, ba abin mamaki bane, sai da yakai karshen surah.

*Mukaye azkar sai kusan bakwai na tashi nade sallaya nayi nayi waje,

Duk da akwai NEPA hakan Bai saka na kwanta ba fita waje nayi na tattara Mana shimfidar na mayar daki,

Tsintsiya na dauka na share baranda na fara sharan qasa,

Jin Bata dawo ta kwanta ba Kuma yaji tana shara yasa ya mike yayi waje shima,

Gaidani yaye na amsa ba yabo ba fallasa, takalmin sa ya saka cikin lalube yayi kitchen wajen da yasan Ina Tara kwanuka da bojuwaye yafara tattarawa Yana kawowa mawanki harya Gama kwashewa,

Boket ya dauka. Randa ya wuce a hankali ya dau Moda dake Kan randan da hannu daya ya bude randan da daya hannun sa,  moda ya zura a randa zai ibi ruwa yaji wayam,sai da ya rank’wafa kafun yaji  ruwa,

 hakan ya nuna masa  ruwan Randa saura kadan fasa iban yaye ya dauki boket in ya Kama hanyan fita”

Ganin ya Kama hanyan fitane,yasani tambayr sa” Ina zaka da boket kuma”?

Cikin sanyin sa na halitta yace, ruwan Randa saura kadan Inna iba bazaki samu na aiki ba shiyasa Zan Iba a rijiya”

“Rijiya”? Na sake tambayar sa,

Eh yaban amsa, Kamar Zan hanasa,sai kuma nayi shuru na Kama kwashe shara,

Jin bance kome ba yasa shi cigaba da tsayuwa,

*Ganin yaki tafiya yasani cewa “yakuma ka saya”

Fita yayi, ni Kuma na shiga kitchen na Kama hada breakfast,

Yana fita rijiya ya nufa da lalube harya Isa Dayake rijiyar ba bakwansa bane Yana gane hanya,  ya lalube guga a gyfen rijiya, ya zura hade da Bismillah,

sai da ya Bari na Yan second kad’an kafun ya sake dagawa Jin ta cika yasa yaja, sai da ya cika boket dam kafun ya sunkuce boket da hannu d’aya d’ayar hannun yana lalubar hanya har ya samu ya shigo kofar ya zuba a Randa, 

Ganin wahalan da yasha kafa d’aya ma kafun ya kawo duk rabi ya zube Masa a jiki gashe yafi minti 10 daga rijiya zuwa kofar mu Yana lalube kafun ya gane,

Haka kawai na tsinci kaina da” dakatar dashi ganin Yana kokarin juyawa ya karo

Ka bar iban ruwan nan an…. Ban karasa ba saboda ganin  d’aya Daga cikin yaran gidan budurwa ta shigo ba Koh sallama, tana cewa

Wai inji inno ka Bata d’ari biyu zata sai goro, 

Cikin sanyi yace  yau ban kwana da kudi ba sai naira d’ari d’aya kacal Kuma ita nake son saya Mana kayan miya zamu karya, tayi hakuri zuwa anjima inna fita na samu ciniki Zan bada a kawo mata,

Cikin bala’i take cewa eh lallai watoh matar ka tafi inno kenan, dadin abin munsan auren liki aka maka ba Wai don ka Kai abaka ba, shidai kala baice Mata ba.

Ke Kuma  duk kudin da kike dashi Koh nace gidanku suke dashi sai kin jira D’arin karyawa  mtwss,tana fada tana nunani,

*Ai bansan lokacin da nayi  super ba na saya a gaban ta ” keee karki kuskura ki sake sakani a cikin haukarki na jahilci karki yarda  in karta Miki layin rashin mutunci a gidan nan iskancin ku ya tsaya ku wak’u karku kuskura ku sani,

idan takamarku bariki da rashin kunya wallahih ni Zan gyara Miki zama,”

“bace min daga gani” cikin tsawa na karasa maganar,Ina nuna Mata kofa,

Tabbas ta tsorata Dani sosai don Bata dauka Ina da baki haka ba,da saurinta harda tuntube ta fita,

Juyawa nayi na kalle sa Yana tsaye Kamar ruwa yacisa,

Wani abu Mai kamada tausayi-tausayi takaici-takaici ya kamani, ganin kwata kwata na rasa me yasa Yan gidan nan suka Raina Masa wayone oho,

*Daki na shiga na d’au jakana gudan dubu na dauko * fitowa ta yayi daidai da shigowar wata dattijuwar Mata cikin bala’i ta,toh Ina kike karamar Mara kunya, harkin Isa ki shigo gida jiya jiya ki nuna Mana iskanci, Daman tunda Naga yau kwananki uku a gidan nan Koh gaishemu baki zo kinye ba nasan ba banza Kika rasa miji ba Rana tsaka aka lika Masa ke,

* ba tare da na kalle taba nace, 

“Yayan khadija pls ka Bata kudin da ya kwana a aljuhunkan, ba musu ya lalube jallabiyarsa ya d’auka ya Mika mata, fizga tayi tana ta tsababi zadai kaji da munafurcinka, 

*daga ni harshe bamu tanka mataba harta fita,

*Albarkacin girmanta yasa naja bakina bance kome ba,

Jin ta fita yasa na Mika Masa dubu d’ayar “gashi ka sai kayan Miya Mai D’an yawa  Dana shaye ka hada da Kiran Mai ruwa”

cikin sanyi yake cewa, kiye hakuri Sumayya Nike da alhakin daukar nauyinki akaina bazan iyya karban kudin kiba, sannan Ina Mai baki hakuri da abinda Yan gidan mu sukayi Miki,

Bari naje  na karbo kayan miyan da na shaye,

“Da wani kudi Koh ba yanzun naji kace D’arin ne da Kai ba”? 

Eh hakane Amma Zan karbi kayan a shago Inna fita sana’a Allah ya bada kasuwa tunda mak’wancina ne saina Mika Masa Amma ni bazan iyya karban kudinki ba.

“Au ni in cema akaye kyauta na baka ai bashine Inka tashi ka biyani” nace Masa ganin da gaske bashin xai fita ya karba,

D’an Jim yayi sai Kuma ya karba ya fita, kitchen na koma na sauke macaroni ganin ya nuna na juye a kwando,

Wanke wanken da ya Tara na Kama wanke wa da yake babu yawa plt ne biyu sai cup biyu shukali sai bojuwa biyu, kafun ya dawo harna kammala

 Yana dawowa nayi miyan stew da kefe busheshe manya-manya, guda biyu Wanda aka mini caton guda na gara

Wanka yayi ya chanja kaya  ya kwanta a kujiran daki,

Ina Gama girkin na zuba Masa na Kai Masa daki hade da gyran murya na fita 

Wanka nayi  na shiga daki da towel Mai Dan girma na daura yaukam zama nayi na shafa Mai da powder NASA kwalli sai man baki, 

Yana Gama ci ya ibi Kwanukan yakai waje, *Yana fita na ibi Kayana na saka rigane Abaya Mai kyau sosai ya karbi jikina gyelen na  daura a kaina,

Na kurawa kaina ido a madubi bansan lokacin da hawaye ya taru a idanuna ba,

 *Sun Rabani da aikina sun saka mahaifina ya datse mini Account Wanda da gumina na Tara Rabin kudin da ke ciki,sanan

Kaf jalingo su rasa mijin da zasu aura min sai MAKAHON miji Wanda Koh kwalliya nayi baisan nayi ba,  ni Karan kaina ma, sunar Ina matar sa Bai San ya nake ba, in badai muryata yaji ba bazaisan Ina wajen  ba, me nai musu a rayuwa mina tsare musu basa kaunan cigaba na komin kankantarsa, a matsayin su na Yan uwa ga mahaifina. Duk a Raina nake zancen nan hawaye nabin kumatuna,

Kinyi kyau,

*abazata na juya cikin mamaki jin muryansa a dakin wanda bansan yaushe ya shigo ba Yana tsaye idonsa a…….

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

Page8️⃣

Idon sa a saitin gado, Yana kyetkyet tasu, Anasa tunanin ta saitin inda nake kenan,

**Bansan lokacin da dariya ya kamanii ba hawaye nabin fuska ta duk a tare nace”da wani idon kaga nayi kyau wama yace maka kwalliya nayi nii Koh Kaya bansa ba” na fada ina dubansa, har lokacin bakina d’auke da murmushi Wanda har hakora na masu haske, d’auke da hakoran Gwal na makka har guda biyu a gyfe da gyfe na hakoran gaba,

suka bayana,  na  kasa  rike murmushin abin ya, bani dariya especially lokacin da ya furta Kuma idonsa na kallon wani wajen.

Sam ransa Bai baci ba da abinda nace asalima wani sanyi yaji a ransa Jin sautin dariyar ta na farko a Kan kunnensa,

Zuciya tane ya sanar dani kinye kyau 

“Aiku zuciyar taka Bata fada maka daidai ba, don ni banyi kwalliya ba atoh”

Zaki iyya rantsewa?

“na rantse nayi kwalliya Amma tsakaninka da Allah ya akayi ka gane”?

Uhmm bayan kin shiga dakin nan kin zauna akan dressed mirror Ina ji ki aje Abu kamar gwangwanin Mai kinfi minutes 17 kina ajewa da dauka,hakan ya tabbatar min kwalliya kike,

in Khadija tana kwalliya haka nakejin buruntun irin yanda naji d’azun,danake cin abincin

“Lallai fa,”kawai nace nayi shuru 

Zan fita me da me za’a bukata, yace mini

“No ba kome tunda kayan miyar safiya zai Mana kwana biyar Koh hudu” kaga daidai ya kare ka biyani kudina,

Ok sai na dawo”toh” nace Masa yasa kafa ya fita 

*Komawa nayi na zauna Ina maijin haushin kaina Dana sake baki Ina tanka masa, 

kunna TV nayi ga fanka na kadawa k’wanciya nayi Ina kallo,Tashar zee cinema ana kallon wani film Mai suna bang bang sosai film in yamin dadi,

10:00pm naji sallaman Khadija mikewa nayi Ina amsawa na fito waje itace tsaye hannunta d’auke da kulan jiya,

Ina kwana Aunty,

“Lafiya Alhamdulillah ya Goggo”?

Lafiya tace a gaidaki,

“Aiko Ina amsawa”

“Ki shigo mana” 

ah ah Aunty tafiya zanyi yanzun

” Aiko baki isaba shige muje ciki yau ini zamuyi”

Ba musu ta shigo dakin Muka zauna muna kallo sai 11:00 na mike na shiga kitchen Zan fara aiki, sai ganin Khadija nayi itama ta shigo,

“Ah ah fa Khadija yau Kam zama zakiyi ki huta” 

Yanzun Zan kammala “

Ah ah Aunty wallahih bazan iyya zama kina aiki ba Zan dai tayaki,

Ba yanda na iyya  haka Muka Kama aiki sai 1:30 Muka kammala tuwo da miyar kuka, nayi Tuwon da yawa harda na dare kawai, na huta d’aura sabo, zubawa yayan khadija,akula na zuba na dare a wani kulan  na rufe, mukayi sallah ta Kai masa nasa, 

tana  dawowa na zuba Mana  munaci muna Hira,

“Nikam Khadija wani school kike zuwane”?

Aunty bana zuwa makaranta ai

“Ban gane ba Khadija”

Eh na kammala junior set. 

“Shine zakice kin Gama karatu”?

Eh Aunty na Gama jss 3 Amma ban daura  senior set ba

“Me yasa”?

Shuru tamin Naga alama batason bani Amsa 

,Nima ban takurata ba,

Na chanja zancen da, wani,

“Khadija nikam akwai Wanda kika sani ne? ta iyya kitso, budurwa haka tazo tamin a gida Koh guda shida so nake na wanke kaina”  

Aunty Baga kanki a tsefe ba bazaki wanke ba sai an kitsa?

“Aii Khadija bana iyya wanke Kai a tsefe sani ciwon Kai yake” 

Lallai Kam aunty bara mu kammala ci na kama Maki  Kan in mun gama,

“Au kin iyya kitson kenan”?

Zandai Kama Miki, “Koh Zaki chanchara mini ba”

Hh toh na yarda.

Muna Gama cin abinci Khadija ta Kama mini kaina guda shida, na tashi naje nayi wanka na hada da Kai,

*Sai dana rike Khadija har yamma kafun na barta,ta tafi,

Sai yamma ya dawo  Kamar yanda ya Saba haka yauma yayi wanka da sallah sai Isha mukaci abinci yau akwai NEPA tun na safe har yanzun Basu dauke ba dukan mu muna zaune a daki Ina kallo shima dai idonsa biyu, sai 10:25 na sa kayan bacci  muka kwanta, 

Misalin karfe daya na dare na farka da wani irin azababben ciwon ciki Wanda tunda nake da wayo bantaba yin irinsa ba,

 Mai tsanani gaskiya tun Ina daurewa har dai na fara kuka Ina nishi duk iskan fankar da yake kadawa a dakin gumi nake,

Cikin bacci yakejin kuka-kuka, Nishi daga ji na azaba ne, cikin D’an hanzari ya mike ya sauka a kujiran cikin azama yake magana muryarsa na rawa,Jin da gaske Sumayya ce Mai kuka da Nishi 

Sumayya!! Sumayya!! Lafiya kuwa ya fada Yana laluben inda nake, 

nikam saban azaba nama tsullubo kasan cafet daga Kan gado Ina durkushe reke da ciki,Koh amsa na kasa basa,

Da lalube ya lalubo ni kafada ta ya dafa yana cewa, muryar sa na rawa,Sumayya lfy meke faruwa ne kimin magana mana,

“cikina ” nace Ina Kara fashewa da kuka,

Hankalin sa in yayi dubu ya tashi, hannu yasa ya dauke ni cak kamar ya dauki Yar baby da lalube ya daurani akan gado.

Nikam tashin hankali Bai barni nama San ya dauke ni ba, tsaban azaba, jikina har bari yake ,, sosai hankalinsa ya Tashi ,mikewa yayi zai fita cikin rawan jiki na kama Masa hannu na damke cikin nawa dake rawa sosai, ciki muryan ciwo yaci karfina nake cemai”D’an Allah karka tafi ka barni Zan mutu ka mikamin waya ta na Kira babana karna mutu”

Sosai zuciyarsa ta tsinke Jin tana am batar mutuwa,Amma ya daure cikin sanyi murya yake cemin Kinga yanzun dare ne Bai kamata ki kirasa a daga Masa hankali ba,

 bara naje Koh Allah zaisa na samu iro ya kaimu asibiti da keke napep NASA kinji, sannu,

**Gaskiya ya fada hakan yasa na sakar Masa hannu ya fita,

Waje ya fita Yana lalube ya dauki sandar sa a dakali da lalube ya fita a kofar shashen Yana lalube harya Isa hanyan kofar gida wanda ke dauke da d’akunan samarin  kusan bakwai,

 a kofar dakin iro ya tsaya ya fara buga Masa kofa Yana Kiran sunan sa,

Cikin bala’i ya bude kofar ya fitoh kai don Allah lafiya Ina cikin bacci karfe daya zakazo ka bugamin  kofa Dan wulakanci kome,?

Don Allah iro ka taimake matatace ba lfy sosai shine nace Koh zaka taimaka mini ka kaimu asibiti,

Buran uba a Daren nan ba shegen da ya isa yasani in fitoh wallahih Koh inno ne ba lfy ba inda zani bare wata banxa Wai matarka don Allah ware ka ban waje nikam, Yana Gama masifar ya koma daki ya banko kofar,

Haka ya juya don yasan tunda har iro yace bazai taimake Saba ba Wanda ya Isa yasa sa daukan su , waje ya fita Amma titi shuru. Ba motsin kome,yakai minutes 30 baiji motsi ba dole ya hakura haka ya juya da sanyin jiki ya koma cikin gidan,kofar ya shigo cikin hanzari ya Isa dakin har yanzun dai kukan take,gadon ya hau a hankali ya Isa gareta cikin sanyi yake ce mata, don Allah Sumayya kiye hakuri wallahih ban samu abin hawa ba,

cikin muryar kuka nace “ka dubamin wayata tana Kan dressed mirror,ka bani na Kira Abie”

Ba yanda ya iyya  dole ya Bata wayar  ganin irin azabar da take Sha gashi ya kasa Nemo Mata mafita ga ciwo na cinta,

Sauka yayi a gadon Yana lulube harya gane dressed mirror in, har Allah yasa ya samu wayar mikamata yayi,

Karba nayi cikin Nishi nake lalubo number Abie na na Kira yakai sau biyar baya dagawa Daman tun Randa aka kawoni gidan nan Koh na Kira sa baya dagawa sai ana biyar in nayi sa’a ya daga cikin muryar kuka nake cewa abie Zan mutu cikina ciwo kazo ka kaini asibiti,, 

abinda naji abina ya fada shiya Kara hargitsamin k’wak’walwa, yau nice yau abie ke cewa  Inna mutu baida asara Kuma karna sake kiransa tsakiyar dare Yana bacci,

**Anya abie nane kuwa? Mai Sona da tausayina Mai son ganin farin ciki na yake furta wannan magana gareni,shikinan shima abie yanzun baya Sona 😭 wayar na sake daurawa a kunne na Amma abie ya kashe call in ban daddara ba na sake kiransa wannan Karo Kam line busy ya Danna mini.

**Me nai Masa lfy lfy Muka rabu cikin kewan juna da Addu’a tare da fatan alkhari hade da nasiha,

bansan lokacin da wani sabon kukan ya barke,min ba

Sosai hankalin Al’ameen ya Tashi baisan lokacin da ya iso garita ba ya Kamata ya runguma cikin wani irin yanayi na tashin hankali yake lallashin ta,

**Kara rungumar  sa nayi na yenyene Masa  ajikinsa Ina kuka maitaba zuciya wannan kukan bana ciwo bane kadai  harda na bakin ciki Abiena shima ya juyamin baya adaidai lokacin da nafi bukatar sa,

Haka nayi ta fama da ciwo daga ni harshe bamu rintsa ba sai addu’i yake tufa mini har hudu na asuba,

Yaji taja numfashi da karfe sai Kuma yaji kome nata ya sake Daman har lokacin tana jikinsa,

 cikin wani irin rikice wa jinta ta Bata motse yasashi mikewa ya sabeta cak  a kafada Yana lalube ya fita a dakin Koh kofar Bai rufe ba tsabar tashin hankali,fita yayi a shashen  yayi hanyar kofar gida…………..

 *masu Tambaya na complete in MATAR MAKAHO* , 

 *A Ranan 30/8/2021 na fara Post na novel innan bani da complete* 

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

 *More comments* 😁

 *More post* πŸ€•

Page9️⃣

Haka ya ringa lalube don Koh sanda Bai rike ba ya fita waje, da ita,yaje

 titin shuru haka ya ringa takawa a Gefen titi ba tare da yasan inda zai nufa ba,

cikin ikon Allah sai ga wani Mai mota yazo wucewa ganinsu cikin wani Hali yasa shi tsayawa a saitin, Al’ameen Yana tambayar sa lfy kuwa ya gansa da mace a bakke a kafada Bata motse gashi Koh takalmi babu a kafarsa da asuban nan?

Da sauri ya juyo wajen da yakejin muryar Mai motan don Allah ranka shi Dade ka taimaka mini matatace ba lfy wallahih tun jiya yanzun haka Suma tayi Ina son kaita asibiti Amma ban samu abin hawa ba,

Allah sarki shiga muje Nima kwanace ta kamani a hanya sai yanzun na shigo gari,

Allah ya saka nagode,ya fada Yana laluben murfin mota tsabar tashin hankali Yama  kasa budewa ,abin ya bawa Mai mota mamaki, yadai malam lafiya Naga kana lalube baka shiga ba,?

Bana ganine,ka taimaka ka bude mini,

Ba karamin mamakine ya Kama Mai mota ba ace mutun Kamar Wannan baya gani lallai Koh wani bawa da kaddaransa,

Fita yayi yazo ya bude Masa 

A hankali ya shimfida Sumayya asset in baya shima ya shiga Mai mota ya rufe ya zagaya shima ya shiga mazauninsa yaja motar ,

Wani asibiti Zan kaiku?

Duk asibitin da yafi kusa damu ka kaimu 

Ok ya kara gudun motar lokaci kankani  suka iso FMC don yafi kusa da SINTALI ( sunan unguwansu Al’ameen)

Suna Isa emergency Mai motar ya kaisu fita yayi ya shiga Hall in ya Kira nurses za’a d’auki Mara lafiya suka fitoh da sauri aka aza Sumayya bisa keken marasa lfy aka wuce da ita dakin taimakon gaggawa,

Likituti suka,rufu a kanta don Bata taimakon. Gaggawa 

shi kuma nurse tace Masa yaje ya sai Mata card a bude mata file,

Wajen sai da card in ma da taimakon Mai motar ya gane, 

kudin card naira 300 matar da ke windown tace,

 ba karamin tsinkewa yayi ba sai yanzun tunaninsa ya dawo jikinsa, don Koh sisi baida shi sai naira dari da hamsin na cinikin jiya, ya Allah ka taimake ni abinda ya ke fada kenan a ransa,

Malam.koh bakaji bane nace 300 ne kudinka  shuru yayi Yama ya kasa magana,

Mai motar ne ya fahimci Koh sisi baida shi kenan

 fitar da dari uku ya Biya kudin card 

Menene sunan majinyacin?

 tambayar sa akaye me sunan Mara lafiya, Sumayya

,sunan surname?? Shuru yayi yana tunani a hankali yace Abdulsalam shugaba,ya fada Dan in Bai manta ba haka yaji agun daurin aure aka fada,sai da ta daga kai ta sake kallonsa Jin sunan da ya fada amasayin sunan mahaifin maralafiyar da suka kawo,

lokaci kankani aka bude Mata file in ,

Yama rasa bakin godiya sai gode ma mai motar yake, nagode nagode bawan Allah ba abinda zance maka sai Allah ya saka maka,

Ba kome ai ka gode Allah,

sunana Ammar Ina zaune da iyayena a unguwan millionaire’s sweet,ya fada Yana Kama hannun Al’ameen Yana Masa jahora zuwa masallacin asibitin sukayi sallah suka dawa Kan kujirun da ka jera a Hall in,suka zauna,

Nurse ce ta fitoh tana tambayar suwaye suka kawo Sumayya Abdulsalam shugaba?

Mekewa sukayi Ammar na rike da hannun Al’ameen suka Isa wajen da take 

Gamu nan 

Mika musu takardan magani,doctor yace ku saya  maza-maza don ana bukatar sa emergency,

Hannun Al’ameen na rawa ya amshi takardan hade da tambayar ta don Allah ta farfado ne ya jikin nata,??

Eh ta farfado Amma ana bukatan kuje ku sai Abubuwan da aka rubuta muku,..

Kama Masa hannu Ammar yayi suka wuce pharmacy suka je 

Mika takardan maganin sukayi

 karba sukayi suka duduba ruwane da allurai sai maganguna,

Kudin ku naira dubu bakwai da dari biyar,

Shikam Abu ya hade Masa goma da ishirin Ina zai samu kudi Mai dunbin yawa har dubu bakwai da dari biyar,

 Koh Kama sayar baidashi bare ya Kama ya sayar ya Saya mata magani Innalilahih wainnailaihir rajuun yake furtawa hade da karban takardan balance ya fita tsabar rudewa shikamma ya manta da wani Ammar suke tare,

Ammar ne ya biyosa ganin yana faman lalube zai fita a pharmacy in da sauri ya rike Masa hannu,

Habba Dan uwa karka dagawa kanka hankali Mana Yana fada  ya karbi takardar ya rike hannun Al’ameen suka shiga waje biyan kudi

Ammar ya biya kudin suka karbi magangunan da su ruwa da allurai suka Kai emergency, suka mikawa nurse in ta shiga dakin,

 sai a lokacin hankalin Al’ameen ya kwanta sosai yayita ma Ammar godiya shikam ma har kunya ya kamasa Kamar  Wanda ya bawa million biyar,. 

Sai 8:30 aka barsu suka shiga suka ganta  ta farfado Ansa Mata ruwa da alluran bacci don ta samu hutu sosai  ciwon ya lafa

Toh abokina Zan wuce Naga gari ya fara wayewa gashi sai kirana ake daga gida kasan Dana shigo *Jala* na Kira gida nace musu na shigo,

Ba kome wallahih nagode sosai Ammar Allah ya saka da alkhari 

Habba wanna godiya ya Isa haka,baka fadamin sunan kaba fa har yanzun?

Suna na Al’ameen,ya basa amsa

A unguwan da na dauke ku kake ? 

……Eh 

Ok toh insha Allah  Zan dawo na duba Mai jiki 

Nagode nagode Ammar

Sai anje ma, ya fada Yana kokarin fita a Hall in sai Kuma ya dawo,

  Koh xan kaika gida ka dauko Mata Kaya da Abubuwan bukata Kamar Kayan da zata chanja su maclen da brush da abubuwan bukata kaima ka samu ka kimtsa jikinka Naga Kamar a birkice ka fitoh Koh takalmi babu nasan har yanzun baka San kafarka ba takalmi ba hh ya fada cikin wasa Yana dariya,??

Shima Al’ameen in dariya yayi kawai, Yana cewa toh muje don wallahih rudewa Kam na rude,

Hannunsa Ammar ya rike masa suka fitoh ya bude Masa mota ya shiga ya ja suka wuce, suna tafiya suna Hira 

Amma dai ku sabbin aure ne Koh?

Eh yau kwanan mu hudu,

Kai kace ango ne da kansa Koh dai Mai kashane, amarya har asibiti

Dariya kawai Al’ameen yayi baice kome ba don bazai iyya fadawa Al’ameen sirrin Saba duk da yaji bawan Allah ya kwanta Masa arai Yana da kirki sosai koma zasuyi sa’o’in juna Amma hakan bazaisa ya tsake jiki dashi ba don mutumin duniya ba abin yarda bane lokaci guda,

Sun Isa har inda ya dauki Al’ameen tukunna ya tambaye sa sun iso wajen da ya dauke sa da asuba ata Ina gidan naku yake?

Ah ah Ammar sauke ni ma anan na gode 

ah  ah kaidai kamin kwatance 

Ah ah wallahih hakan ma nagode,ganin ya nace yasa Ammar sauke sa

Sukaye sallama

A hankali Al’ameen ke tafiya Yana Dan yaryarfa hannunsa don Ya tabbatar  inda yake sa kafarsa ba mutum Koh wani abu inda Allah ya Sosa ma tsallaken titine aka sauke sa ta barin gidansu a hankali yake tafiya Bai Ankara ba yaji an bangajesa haryaso faduwa saura kadan da yakai kasa, wani zafi yaji a yasansa don ya buge dutse sosai yatsan ke Masa zafi a hankali ya mike, Jin Wanda ya turesan Yana bala’i, ku wasu irin mutane ne in ka San baka gani wani rawan Kaine zaisa ka fitoh babu D’an jagora babu sanda, irin hakane ai sai ku hau titi mota yabi ta kanku kujawa mutum jaraban jinya inkun mutu Kuma kusa mutun azumin kaffara mtwss,,

Ya fada Yana tafiya 

A hankali Al’ameen ya d’uka ya taba yatsar Jin damshi yasashi gane jini ke zuba,

Bai damu ba ya cikaba da tafiya har Allah yasa ya iso kofar gidansu ya shiga,

Yana shiga cikin gidan ya samu Yan gidan a filin tsakar gida kowa na sha’aninsa daga masu wanke wanke sai masu wanki sai masu kitso masu Jan ruwa  wasu Kuma group aka hada ana ta gulma ana xagin juna,,,

Ganinsa ba takalmi sanan ga jini a kafa Yana zuba, yasa Rabi’u  fara magana Kai MAKAHO daga Ina haka a bujaje yau tun safe ma bamuga fitarka ba?

, kafun ma yayi magana iro dake goge takalminsa zai fita yace Wai fa D’an rainin wayon nan jiya Ina bacci yazo karfe kusan daya Wai nakai matar sa asibiti Bata da lfy kaji Dan rainin wayyo wama ya sani Koh turmushe Yar mutane yayi xaizo tsakan dare yana tashina,,gabaki dayan su suka saka dariya,

Shidai kala baice musu ba hanyan shashen su yayi da lalube harya shiga sai a lokacin ya tuna Ashe fa kofa a. Bude ya barta cikin D’an fargaba ya shiga dakin don shi tsoronsa ma kar Yan gidan su shigo su Ma Sumayya sata don shikam baida abinda za’a sata, wayarta daya Mika Mata jiya da dare shiya fara lalubawa akan kadon aiku yajisa, 

Hakan ya tabbatar Masa ba Wanda ya shigo tunda ga waya a fili Amma da an shigo wayar nan dake zaune a fili haka da an sabe sa hamdala yayi ya gode Allah Basu San ya fita ba,

 iban ruwa yayi yashiga bandaki yayi wanka yasa wasu Kayan  ya rufe kofar ya fita don bazai iyya gane inda kayanta suke ba,

Sandar sa ya dauka ya fita a gidan hanyar gidan Goggo Amina ya nufa,

Yana Isa kofar gidan ya tsaya a waje yayi sallama,

Shan cikin gidan kuwa Khadija nawa Goggo Amina kitso taji sallama Kamar ta yayanta Aiko ita ince amsawa tayi tare da daukan hijab inta ta fitoh waje 

Yana tsaya yaji isowar Khadija  bakin ta na amsa sallaman sa 

Ina kwana Yaya ya aunty?

 lafiya Alhamdulillah Khadija

Ka shigo mana Yaya Goggo ne kawai a gidan yau ?

Toh ya amsa Mata 

Ta Kama hannunsa suka shiga cikin gidan kujira ta aje Masa ya zauna Yana gaida Goggon tasu, Ina kwana Goggo?

 Ta amsa da kulawa 

Lafiya Alhamdulillah Muhammad y’ay’a  iyalin taka?

Lafiya Alhamdulillah sai dai bataji Dadi ba jiya da ciwon ciki ta kwana yanzun ma daga asibitin nake nazo na dauki Khadija tazo muje zata dauka Mata kayayyakinta Koh kadanne Zan Kai Mata asibitin,

Subhanallah Allah ya Bata lfy wani asibiti ne?

Ameen a FMC ne ya amsa Mata

Khadija tashi maza kuje, toh Goggo ta amsa Mata tana mikewa 

Shima Al’ameen mikewa yayi,hannunsa Khadija ta Kama suna tafiya a haka,

Yaya jikin nata da sauki Koh?

Da sauki Khadija Yaya zan bika muje asibitin?

Ah ah Khadija ki tsaya a gidan namu ke dafa mana abinci tunda Kinga asibitin FMC ne babu nisa saiki Kai Mana can,

A wani block ne yaya?

emergency ne

 har suka Isa gidan nasu suna Hira dakin ta shiga ta dau jakan Sumayya  mabi da ket ta Ajjye tana iban Kaya a whtdrp tana zubawa hijab D’aya, sai dogayan rikuna biyu, zani fille fille guda biyu,sabbine kal ta hada da t-shirt biyu, da hula biyu, sai maclen da brush ta hada Mata da kananan Kaya su pants brz da vest  ta rufe akwaitin,

Yaya na Gama Amma dai tunda kace tun asuba kuke asibiti baka samu kaci karyawa ba koh?

Kai Khadija kin cika surutu wallahih inkin gama kika kawo Mana ai zanci,

Amma yaya yanzun fa ana neman 09:30 na safe baka karya ba in kaje asibitin Yaya ka samu abinda zaka saya muku kuci Kaida Aunty kafun na Gama, 

Toh Addata Khadija

Hhh ye Hakuri yayana ..

Baice Mata kome ba illah daukar jakar da yayi Yana lalube zai fita a dakin idon Khadija ya sauka a Kan kafarsa a matsanancin damuwa ganin yatsan sa a kumbure gashi ya karce sosai,

Yaya meya same ka a kafa haka,?

Tuntube nayi kawai yace Mata Yana fita,,

 fita yayi bakin titi Yana tare keke da hannunsa har Allah yasa wani ya tsaya,

Malam Ina zuwa?

…FMC yace Masa 

Shiga muje, da lalube ya shiga keken suka wuce cikin kankanin lokaci suka Isa hospital ya sauke sa abakin get don in ba majinyaci bane a Keke ba’a Bari ta shiga asibitin, ya bawa Mai keken kudin sa naira 50,

Ya Kama hanya da lalube ya Isa cikin asibitin security n get yake tambaya don Allah wani shashine zaibi zuwa emergency don lokacin da suka zo da Ammar a motane bazai gane hanya ba gashi asibitin fadine dashi ga shashe daban daban,

Kabi nan ka Mike  har emergency zai kaika

  haka kuwa yayi har ya Isa emergency Yana shiga ya gane dakinda aka kwantar da ita

 yazo shigane ya hadu da nurse in d’azon tana ganinsa ta rufe sa da masifa

Kai wani irin mutum ne zaka kawo Mara lfy kasa kafa ka fice ka barmu da ita, tun dazun nemanka ake likita nason ganinka,

Kiye hakuri gida naje na dauko Mata kayane

Me yasa she dayan bazai je ya dauka mata ba Kai ka zauna?,

Taimakona yayi Kuma ya tafi,

Jeka aje kayan kazo   likita nason ganinka

Da toh ya amsa Mata da lalube ya Isa inda gadon ta yake har lokacin Bata farka ba,

Juyawa yayi ya fita a dakin sai da ya fita kafun, ya tuna baisan office in likitan bama tambayar wata nurse yayi da taimakon nurse innan ya gane office in doctor shiga yayi da sallama doctor ya amsa masa matashine kamarasa,

Kaine ka kawo Sumayya Abdulsalam shugaba?

Eh nine doctor ya basa amsa

..ok Sumayya na fama da apendes ya kunbura sosai don haka dole za’a Mata tiyata ga wannan sai kaje ka biya kudin,

Atake zufa ta fara karyo Masa Innalilahih wainnailaihir rajuun,likita kudin zai Kai nawa,yafada Yana tambayan sa?,

Bani bane Mai karban kudi  in kaje wajen biya za’a fada maka……………..

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

Page πŸ”Ÿ

Cikin tashin hankali ya mike ya fita Dayake shi mutum ne Mai saurin fahimta yasa dakansa ya wuce wajen biyan kudi,

Kudin 50k yaji ance Masa,

Innalilahih wainnailaihir rajuun take yaji Kamar kansa xai rabe biyu haka ya karbi takardan ya wuce zuciyansa sai rawa take, shi Ina yasan zai samu kudi gabaki daya jarinsa ma baifi dubu daya da dari biyar ba Ina zai samu dubu hamsin, Koh bashi zai karba wazai tinkara in ma an basa Ina zai samu kudin biya?

Har cikin ransa baya kaunan wani abin bukata ya Tashi ta bangarin Sumayya ya kasa Mata har sai Yan gidansu sun Mata duk da baisan dalilin da yasa duk cikin Jala Arasa mijinda zasu aura Mata sai shi suka zaba Mata Wanda har yau ya kasa samun Amsa dalilinsu,,

Kuma bayason Koh da Wasa ta Saida abinda tazo dashi daga gidansu,saboda gazawarsa wajen Bata kulawa Bai santa ba Bai ta ba ganinta ba Bai taba Jin lbrn taba Bai San ya take ba muryarta kawai ya sani Amma a D’an zaman da sukayi Yana jinta har cikin ransa,,

Ya Allah ka bani ikon kulawa da wannan Amanar da aka bani,

A hankali yake tafiya harya fita a get in hospital in da taimakon wani Almajiri ya tsallake titi 100 da ke hannunsa ya Saya Mata Ayaban 100 guda biyar aka basa ya baiwa Almajirin ayaba daya  ya sake tsallakar dashi, cikin hospital in ya shiga yanabi a hankali da sardarsa harya Isa kofar dakin da aka kwantar da ita da sallama ya shiga dakin,

“Waalaikumu salam” na amsa Masa cikin dishashesshen muryata dagaji kasan na Mara lfyne maijin jiki

Sannu Sumayya ya jikin ??.

“Da sauki Alhamdulillah”

Sannu ya sake cewa

**Kai kawai na iyya daga masa

Lalube ya fara Yana neman wajen zama,

“Kujiran na Gefen ka na dama”nace Masa

Laluben damansa yayi yaji kujiran plastic na roba ya matso dashi  Kusa da gadon inda yaji muryarta ya laluba ya aje kujiran kusa da gadon saitin kanta a hankali ya zauna,

Sannu Sumayya ga  ayaba na sai miki yafada yana bude laidan hade da fitar da Ayaban masu k’yau guda biyar zai bare mini,

“Ah ah ka ajiye,so nake sai nayi sallan asuba nayi brush da wanka Koh zanji dadin jikina kafun NASA Abu a bakina”

Toh bara na taimaka Miki ki shiga bandakin sai kiye wanka da brush in duk na kawo Miki harda Kaya

“Toh taimaka min na tashi “

A hankali a mike Yana lalube na harya lalubo hannuna ya Kama na mike a hankali na sauka a gadon Ina “takalmina”?

Na manta ban hada Miki ba komawa nayi na zauna a bakin gado “gaskiya ni bazan iyya taka tiles na asibiti ba takalmi  gaskiya” toh ga nawa kisa Yana fada Yana cire mini ciny’ayyen silifas  insa “ah ah innasa naka kaikuma fa”? ba damuwa Zan tafi haka

“Bazanfa saka ba sai dai ka saimin sabon silifas abakin get”

Wallahih ban fita da kudi ba sai dai in Khadija tazo taji da dauko Miki”toh” na basa amsa Ina k’wanciya a Kan gadon,

Khadija bayan fitar yayanta dakin ta fara kimtsawa ta share ta cire zanin godon ta shimfida wani  ta share baranda da kasa ta hada wanke wanke tayi kafun ta shiga kitchen,da yake akwai NEPA ruwa ta daura a hot-plate ta zuba ruwa ta rufe, ta dauko wani bojuwan daban ta daura shima ruwan ta saka ta rufe Daya ke hot-plate in Mai uku ne,

Tattasai ta dauka da dogo dogo sai albasa ta hada ta juye a blander Dayake taga yanda Sumayya tayi ranan da suka shiga kitchen kunnawa tayi ta markada she Kara Kara baiyi laushi ba dai dai irin na miyan taliya,

Sannu ishesheya munafukar yarinya uwar me kike a kofar har yanzun Naga fitar *makaho* tun dazun ya fita? Taji muryan inna asabe take fada tana shigowa kofar

Inna Aunty Sumayya ce ba lfy shine Yaya yace na musu girki,

Oh lallai ai sai ke in zai Kira don duk gidan nan ba bawan sa 

Kala Khadija batace Mata ba

Dan ubanki bara na kawo kwanona ki zubamin inkin gama saura kisamin kadan,

Kala Khadija batace ba tana cigaba da gyaran waken da ta iba cikin Kofi Daya da rabi 

Keee ishassheya bakiji me nace bane

Naji innah ,ta Bata amsa

Fita Inna asabe tayi sai gata ta dawo da katon kula ta ajema Khadija a gaba ta fita abinta

Ruwa na tafasa ta sauke taliya daya ta juye a tukunyan ta barbada gishiri ta rufe, dayan bujuwan wake ta wanke ta zuba ta rufe shima ta saka Masa gishiri,

Wani sabon bujuwa ta daura ta zuba Mai da albasa Yana soyuwa ta juye kayan miyarta ta soya ya soyu tukum ta saka ruwa ta bare Maggi tasa da onga classic Wanda ta gani duk a cikin kitchen in caton in kefe ta bude ta dau uku masu kyau ta aje a roba,ruwan zafi ta zuba a kettle Yana tafasa ta juye akan kefen ta barsa yadan d’auki seconds kafun ta tsame tasa a ruwan sanyi ta gyara ta juye a miyar ta rufe 

Daidai lokacin taliya ya nuna saukewa tayi ta juye a k’wando ta tsame,

Fita tayi a kitchen in ta dau omo da sabulu ta hada wankin yayanta Dana Sumayya harda zanin godo ta fitar waje ta aje ta fara iban ruwa a rijiya tana wanke kayan dashi lokaci kankani ta Gama wanke wa ta shanya a igiyar kofar shashen,

Kitchen ta shiga ta duba miyar ta nuna saukewa tayi,ta dauki wani kula a caton insa Mai azabar kyau har Yana daukar ido Mai guda hudune uku ta dauka ta wanke dayan ta zuba taliya daya Kuma Miya sauke waken tayi shima ta juye a dayan Kular,

K’wando babba na kaba Mai kyau ta  jera kulan a ciki sai lokacin ta Tuna kulan Inna asabe  zuba mata, tayi,

Ta shiga daki firij ta bude ta dauki drinks guda biyu sai ruwan gora biyu ta hada a k’wandon da plate biyu shukali biyu,..

Wanka ta shiga tana fita ta maida kayan da tazo dashi, Jin ana Kiran azahar tayi Alwala tayi sallah,

Ta dauki sallaya ta ninke tana kokarin  rufe kofar dakin  sai ga Inna asabe tana zuwa kitchen ta nufa ta bude kulanta ganin abinci a ciki Kuma Mai yawa yasata dauka tayi gaba abinta,

Rufe kofar tayi ta dauki k’wandon ta fita a shashen shima ta rufe kofar ta rike key in ta fita dashi lokacin karfe 1 na Rana hanyar FMC ta Kama da kafa,

***********Har lokacin muna zaune nida shi anzo an sake daura mini ruwa,Yana zaune cikin wani yanayi duk da na Saba ganinsa sanyi sanyi Amma nayau yafi na kullum Wanda bansan daliliba,

Jin an fara kiraye kirayen sallah yasashi tashi Yana lulube yake cemin bara yaje sallah ya dawo,da “toh” na amsa masa,

Fita yayi yaje masallaci yayi sallah ya zauna agun sai kusan 2 ya mike ya nufu Hall in emergency  har yayi nisa yaji muryan Khadija daga nesa tana k’wala Masa Kira,

Juyawa yayi saitin inda yake jiyo muryar Tata ya tsaya harta karaso Khadija kin isone?

Eh Yaya na karaso tun dazun Amma ban gane dakin da kuke ba,

Muje toh Khadija ya fada Yana tafiya,itama binsa tayi a baya,.

Yaya ya cikin nata?

….Da sauki Khadija

Yaya Yana ganka cikin damuwa haka meke faruwa ne Koh kudin magani ne baka dashi?

Khadija Ina Zan samu kudin magani in badon Allah ya rufamin asiri ba ya hadani da wani bawan Allah ba ya biya mini kome na magani,

A Ina ka Sansa Yaya?

Bansan Saba yadaice sunansa Ammar

Toh meke damunka?

Wallahih khadija appendix ke damun Aunty ki Kuma kudin operation naira dubu hamsin shine yake dagamin hankali banda sisi Koh abinda Zan sayar na biya

Amma yaya baka ganin gara a fadawa Aunty tunda bazata rasa kudi a hannunta ba, tabiya ??

Ah ah Khadija karki fada Mata yanzun Ina son in munje ki zauna agunta ni Zan fita Koh Allah zaisa na samu bashi,

Habba Yaya wazai baka bashi tsakani da Allah fa Kaida Koh sisi baka dashi in ba mangoron da ya rage jiya ba wazai baka bashi’

Khadija kedai ki tayani da Addu’a na Allah basa karewa

Hakane kam Yaya Allah yasa ka samu 

Yauwa ameen Khadija ta

Daidai lokacin suka iso dakin, shiga sukayi Ina kwance,sauke k’wandon Khadija tayi tana gaidani Aunty Ina kwana?

“Lafiya Khadija”

Ya jikin ki Aunty?

“Da sauki Alhamdulillah”

“Khadija kiramin nurse tazo ta cire mini ruwan nan na samu nayi Sallah”

Toh Aunty tace, tana fita,sai gata da nurse sun dawo cire mini sukayi, “Khadija hau godon ki zauna ki ban takalmin ki bara na shiga toilet” toh Aunty,

*Ta kalmin nata NASA

 shi Kuma ya bawa Khadija tasa ta saka ya lalube bakin gadon ya zauna 

**Da taimakon Khadija na shiga bandaki ta koma ta dauko mini brush da maclen,da kayan da Zan saka,

***Wanka nayi da brush nayi Alwala na fitoh a hankali nake takawa Ina bin bango harna bude kofar na fitoh 

Da sauri Khadija ta tashi tazo ta taimaka mini ta shimfida mini Sallayan da tazo dashi ta shimfida mini ta Mika min hijab na saka na Tada sallah harda na asuba na biya,ina idar wa na cire hijab in,

 Khadija ta mikamin hula nasa, na tashi na koma Kan gadon dukansu sukaimin sannu har suna hada baki, 

Khadija takalminta ta saka Wanda na cire ta bawa Al’ameen nasa,

Abinci ta iba min a plate ta Miko mini,

“Khadija bawa yayanki abincin nan bazan iyya ci ba bakina ba Dadi Sam”

Ah ah Sumayya ki karbi abinci kici ai ba’a jinya sai da abinci” Al’ameen yace 

Gaskiya ne Aunty rabonki da abinci tun jiya fa,ta fada tana aje mini,

“Wallahih Khadija bazan iyya ci ba kidai Mika mini ayabar nan naci”

Toh Aunty, 

Ayaban ta bani na samu naci uku ta Mika mini fresh milk in da tazo dashi daga gida nasha rabi  

Plate na abincin da ta bani ta Mika Masa karba yayi Bismillah ya fara ci,

“Khadija ya Naga kin zauna ki ibi abinci kici Mana” na Bata umurni

Iba tayi ta faraci, 

Yana Gama cin abinci ruwan gora daya Khadija ta bashi yasha, Khadija ki zauna da Aunty ki bara na fita sai na dawo,ya fada Yana tashi yayi hanyar waje,

Toh yaya Allah ya bada sa’a

…… Ameen Khadija

Nidai da ido na bisa harya fita na juya Ina kallon Khadija” Khadija waya biya kudin magangunan nan Naga harda ruwa duka”?

Nima ban sani ba Aunty yanzun nazo sai dai ki tambayi Yaya,

**Shuru kawai nayi na koma na kwanta

Al’ameen Bai Dade da fita ba, sai ga wani matashin saurayi baki k’yakk’yawa Mai matsakaicin tsayi da jiki ya shigo dakin mu da sallama a bakinsa 

Amsawa Khadija tayi nikam hannu nasa na dauki hijabina da na cire a jikin karfen gado nasa,

Shigowa yayi ,barka kudai ya jiki Sumayya?

Mamakine ya kamani Ina kuma wannan bawan Allah ya sanni,

“Da sauki Alhamdulillah”

Allah ya kara sauwa kewa

“Ameen” nace

Al’ameen ya fitane?

Eh wallahih yanzun ya fita baku hadu ba? Khadija ta basa amsa

Ah ah bamu hadu ba,

Koh Kaine Ammar?

Nine Hala lbrna ya baki haka kikayi saurin gane ni?

Eh yadai fadamin abin alkhari da ka Mana Allah ya kara bude,

…Ameen

Nidai shuru nayi na barsa da Khadija suna Hira Kamar Wanda suka San juna,

Khadija nikam Inaga Zan gudu fa har yanzun Al’ameen Bai dawo ba gashi Ina son muyi sallama  tafiya ne ta kamani wallahih gobe Zan wuce shiyasa naso mu hadu kafun na wuce,

Yace Yana zaro kudi a Aljuhunsa Yana mikawa Khadija ga wannan ba yawa a saiwa mara lfy lemo in yayan naki ya dawo kice Ina gaishe she ,

Mungode Allah ya saka Kuma zaiji sakon ka, 

Allah yasa yace Yana kokarin nufar kofa

“Nagode”  nace masa ba tare da na dago ba ganin irin kallona da yake tayi kamar ya samu TV tun dazun da suke hira da Khadija idonsa na kaina,

Ba kome yace yasa Kai ya fita………

πŸͺ€My WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

Page 1️⃣1️⃣

Bayan fitar Ammar Khadija ta kirga kudin dubu goma ne,Mika min tayi, Aunty ga kudin

“Ajjye Khadija in yayanki yazo ki basa tunda shike fama da zirga zirgan asibiti” toh Aunty ta bani Amsa tana aje kudin a cikin ak’watin Kayana,

Al’ameen na fita daga asibiti da kafa ya koma har gida Dayake akwai sanda in Kuma yazo titi sai ya Kama yara su tsallakar dashi Yana Isa unguwan su(sintali) wajen shagunan bakin titi ta inda yake sai da mangoro a bakin su,

Shagon malam shu’aibu ya fara zuwa don shine yafi masu shagunan abin arziki sosai alayin da sallama a bakinsa ya shiga shagon,

Assalamu alaikum malam shu’aibu

Waalaikumu salam Mai mangoro ne?

Eh nine malam shu’aibu barka da jama’a

Barka dai lafiya Kam Naga yau tun safe danazo bude shago Naga hulbairon ka a rufe dazun na aiki yaron gidana ya karbo mini yako yake fadamin baka nan?

Eh wallahih malam shu’aibu iyalina ne ba lfy jiya na kaita asibiti,

Allah sarki ya jikin nata?

Da sauki Daman nace bara nazo ka taimaka mini da kudi dubu hamsin za’a Mata aikine appendix ya kumbura a cikin ta don Allah ka taima kamin,

Kutt lallai ma a karnin nan da kowa ke takai takai Ina Zan iyya daukan kudi har 50k na baka da sunan bashi, bayan anyi operation in Ina zaka samu kudina ka biyani, gaskiya bazan boye maka ba ni nan Koh biyar bazan iyya baka ba banaji ance Yar masu kudi aka aura maka ba me yasa danginta bazasu Mata jinya ba tunda sunsan baka dashi Daman suka baka ita

Shikinan malam shu’aibu na gode, ya fada Yana fita ba tare da ya basa amsar tambayar Saba,

D’ayan shagon Al’ameen ya shiga  shagon gwanja bayan sun gaisa shima ya rokesa Koh zai samu bashin kudi

Amma Kai dai wallahih D’an rainin wayo ne ya Ina Saida kayan Miya zakace na baka dubu hamsin duk kayan shagon nan aka sayar Ina zaiyi dubu hamsin,

Haka yayita bin shagunan makwantansa Amma ba Wanda ya basa Koh sisi wasu kamma da bakar magana suke binsa dashi,

A haka ya iso shagon Haladu shima yace baidashi,. Wajen bairon mangoron sa yaje ya bude ya tataba mangoron rabi duk sun lalace saboda yini da sukayi a rana Kuma a rufe, zabe masu kyau yayi Yana,

D’auka yana sawa  a k’wando ya shiga shagon Haladu dashi, Yana cewa,

 don Allah Haladu Koh zaka sayar mini da mangoro na zanje na zauna a asibiti  na kwana biyu daidai Matata taji sauki 

Gaskiya bazan iyya sayar maka ba sai dai na saya kawai na sayar Nima na samu D’an riba,

Ba damuwa Al’ameen yace Masa

…..Nawane mangoron?

D’ari takwas da hansim

…..Zan baka dari biyar  don Naga wasu sunyi laushi?

Ba damuwa Allah ya saka musu albarka

……Ameen

Kudin Haladu ya basa ya karba gida ya shiga ya bude kofar,

 da yake ya karbi key a hannun Khadija wanka yayi ya saka kayansa Jin ana  Kiran la’asar yayi Alwala ya lalube takalmin Sumayya ya fita dashi a hannunsa, masallaci ya tafi yayi sallah ya wuce asibiti duk zuciyansa ba Dadi ya rasa wajen wa zai tinkara da zancen kudi,, yasan Koh mutuwa zaiyi Yan gidansu bazasu taimaka Masa ba bare Sumayya matar sa,

***Muna nan da Khadija har la’asar sallah mukayi dukan mu nurse tazo ta mayar mini da laidar ruwan a hannu na,

Na kwanta baccine ya dauken nabar Khadija na zaune,

Ya iso asibitin da sallama ya shigo dakin Khadija ta amsa masa.

Sannu yaya ka dawo?

Eh Khadija

Toh yaya ka samu kudin?

Wallahih Khadija sai addu’a naira 500 ne kadai na samu

Amma yaya ya kamata ka sanar da Aunty gaskiya don wallahih Yaya Ina Jin tsoro kaga ance appendix in ya kumbura fa tunda Allah Bai baka ikon samu ba, ka fada Mata ita sai ta biya?

Toh Khadija wallahih inajin kunya a matsayina na mijinta na kasa biya Mata kudin operation don samun lfyr ta,

Habba Yaya karfa ka manta Allah yaga zuciyar ka baka dashine Kuma ba abin kunya bane tunda itama tasan baka dashi,

Suna cikin Hira na farka a gigice Jin wani irin mahaukacin ciwon ciki ya tasarmin ” Innalilahih wainnailaihir rajuun wayyo Allah na cikina”

Subhanallah Sumayya cikin ne Al’ameen Daya Mike cikin tsananin tashin hankali yake lalubarta ,

Khadija ma da saurin ta ta iso ni,sannu Aunty take fada idon ta ya jika da hawaye

*****Nikam.na kasa Bata amsa kuka kawai nake hankali tashe

Khadija tashi kije ki Kira doctor eiiii sauri 

Toh yaya tace tana mikewa da saurin ta

Al’ameen Kam hannun Sumayya ya Kama sai sannu yake Mata a hakan likita yazo ya sameta a halinnan

Da sauri shida nurse suka rufu a kanta tare da K’ura Khadija da Al’ameen waje,allurai sukai Mata harda na bacci lokaci daya bacci ya dauke ta,

Khadija da Al’ameen na tsaye a  bakin kofa likita ya fitoh ya kira su zuwa office,

Malam Al’ameen majinyaciyar ka tana cikin condition Mai muni ya kamata ka samo kudin aiki nan da awa uku ba wallahih kome zai iyya faruwa,

 Innalilahih wainnailaihir rajuun kawai suke fada,

Suka mike zuka fita a office in Khadija Kam kuka ta fara abin Yama Al’ameen yawa ta Ina zai fara anya zai yafewa kansa kuwa in yar mutane ta mutu ata dalilin rashin kudin aikin da Bai samo ba,

Yaya ya kamata Aunty tasan abinda ke faruwa muje ka fada mata ta Kama hannunsa sukayi dakin 

Suna shiga suka samu Sumayya na bacci ……….

Yaya Ammar innan yazo baka nan  ya bawa Aunty kudi Amma Taki karba tace na baka 

Allah sarki Ammar yazo ne?

Eh yaya kana fita Yana shiga, yace ma Wai Daman Yaso kuyi sallama tafiya ne ya kamasa, na gaggawa,

Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari Yan kiyaye sa aduk inda yake,

Ameen yaya

 Khadija Miko min kudin na hada da dari biyar in hannu na naje na Basu Koh zasu mata daidai a Nemo sauran su bimu bashi,

Uhmm lallai yaya kadai San asibiti bata ma matum aiki ba tare da kudi bak’oh?

 Khadija bara dai naje na gwada Koh Allah zaisa a dace tunda kinga hour uku aka bamu kuma yanzun bacci take, bara naje na dawo ya fada Yana karban kudin da khadijar ke mika Masa,

Yana fita yaje wajen biyan kudi, 

don Allah Dan uwa kayi hakuri ga dubu goma da dari bayar a fara mata aikin in yaso za’a cikita muku daga baya Dan Allah ku taimaka min matatace ba lfy kuma hour 3 aka bani ake son mata operation?

Amma Kai *makahon* nan Ina ga baka zuwa asibiti ne taima?

Ina zuwa ranka shi Dade sai dai ban taba kawo majinyaci irin wannan ba

Toh gaskiya ka gannin nan Koh biyar naci a cikin kudin da nake karba wallahih Sai an daure ni

Kuma anan in baka biya kudiba wallahih baza’a Mata aiki ba Koh mutuwa zatayi gwara kaje ka Nemo duk in da kudi ya shiga ya fita shawara nake baka,Amma zance a taimaka maka toh hadai asibiti ba

Shikam tsabar damuwa har jiri yakeji yana ibansa ,a rayuwar yanzun in baka dashi kana ji kana gani harka mutu indai baka da kudin jinya ba Mai taimakon ka, zama yayi a bakin barandan pharmacy in yayi shuru cikin tashin hankali da alhini,

Bayan fitar Al’ameen khadija na zaune har lokaci hawaye baibar zuba ba sai ta gogi wani ya zuba, har  hour 1 yayanta Bai dawo ba,

*** A hankali nabude idona na sauke akan Khadija dake ta hawaye ido harya kumbura abinka da farin fata fuska tayi ja” khadija lafiya kuwa meya faru Naga kina kuka”??

Babu Aunty Daman na tsorata ne danaga cikin ki ya Tashi Ashe haka kike fama da Jin jiki sannu,

Murmushi nayi “haba Khadija Menene na kuka baki ga naji dauki ba” 

Toh Aunty,

“Yauwa khadija nikam likita ya fadi abinda ke damuna ne, Koh yake sani ciwon cikin nan”?

Kafun ta bude baki ma sai ga doctor ya shigo,Wai har yanzun baku samo kudin aikin ba Koh bakuji condition inda nace muku tana ciki ba Wai ina MAKAHON yake ne?

“Doctor ban gane mikake nufi ba” nace ina kallon sa?

Au baku fada mata bane? Yana kallon khadija alamar tambaya

Eh doctor bata sani ba khadija ta bashi Amsa,,

“Wai meke faruwa ne kun sani a duhu” waza’a ma aiki??

Kece appendix ya kumbura sosai tun jiya na sanar dasu Amma haryau shuru Basu biya kudiba yanzun haka  hour 3 na Basu su kawo kudin Dan kina bukatan aiki  gaggawa Amma an share hour 1  shuru, Banga alaman zasu biya ba

Da mamaki nake kallon khadija”yanzun khadija Ina fama da wannan babbar matsala irin wannan Amma kuke mini Wasa da rayuwa Ina da kudin da Zan iyya biya ba bandashi ba”

Kiye hakuri Aunty Daman Yaya ne yace shi yake son biya

” Koh ance lallai sai yayanki ne ya wajaba ya biya ai ni Karan kaina nasan Bai dashi don Bai biya ba ai bazai  zama wani abu na daban ba” menene riban ya fita yana neman bashi alhalin Ina da kudi”??

Kiye hakuri Aunty,ta fada jikinta a sanye ganin Raina ya baci

“Nawane akace kudin aikin”?

……50k ne

“Khadija tashi ki dauki key kije gida ki dauko mini jakana  wani yellow a cikin whtdp nawa ki dauko mini jakan akwai kudi a ciki”

Toh Aunty ta fada tana mikewa daukan key in tayi a jakan kayana ki hadamin da wayata ki dauko darduma babba da filo, ga kayan da nacire ma kikai mini gida kisa a basket in bayan kofa”

“Kihau nepep   ya kaiki kofar gida ki shiga in kin dauko kudin saiki shiga ya dawo dake ki basa 1k ya d’auki kudinsa karfa kice Zaki tafi da kafa”??

Toh Aunty ta d’auki  kayan nawa ta fita  a dakin, doctor Kam Dan kallo ya zama Daman tun da ya ganni yake ganin alamun Jin Dadi a tare Dani Amma abinda ya daure masa Kai mutanen da suka kawo ni asibitin abin yana bashi,mamaki harda Nurses Amma basuga fuskar tambaya ba

**komawa nayi na kwanta shima doctor fita yayi

 

Tsabar rudewa Khadija Koh yayanta Bata Lura dashi ba akan baranda ta wuce,

Shikam ganin lokaci na wucewa yasa ya Tashi ya shigo dakin,da sallama a bakin sa,

**Amsa Masa nayi Ina kallon sa yazo ya zauna a kujiran gefena,

 Sumayya,yakira sunana

“Na’am” na amsa Masa 

Kiye hakuri Sumayya na kasa kula dake wallahih nayi iyya kokari na Amma ban samu kudin ba Daman appendix ne ke damunki Kuma ya kumbura, shine ake son Miki aiki kuma……..

**Da nayi niyar rufesa da matsifa Amma sai jikina yayi sanyi Jin bayanin da yake mini” ban bare ya karasa ba na katse sa”ba kome, me amfanin Ina dashi kaje kana,.. baran attaimaka maka kazo ka biya mini kudin aiki”? Karka sake mini irin wannan banaso duk abin da zai taso a waje na Koh Khadija Koh Kai, in baka dashi  karka sake zuwa gun wani da sunan ya taimaka maka indai abin baifi karfina ba pls”

Kiye hakuri insha Allah bazan sake ba,

**Shuru na Masa

Jin Bata amsa ba ya sashi yin shuru

Khadija na Isa gida ta samu jama’a na cike a kofar gidan dam alamu dai wani  abinne ya furu don harda motar police ga jama’an unguwan makil……………

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense

πŸͺ€my WhatsApp number

     08084453785     08084453785     08084453785    0808445378508084453785    πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book 🀧

Page 1️⃣2️⃣

Cikin tashin hankali Khadija ta nufi kofar gidan tana isa taga an fitoh da inno Akan kadon asibiti da ake daukan gawa Koh Mara lfy tana kwance Koh motse batayi aka shigar da ita Ambulance sai su Inna asabe da baba lami suke ta rusan kuka Kamar ana yankasu,

Khadija Kam iyya rudewa ta rude ganin Yan matan gidan duka kuka suke harda wasu mazan ma

Bappa Dayyabu da bappa sulaiman harda kawu  tafawa suka shiga motar Yan sanda da gani dai abin Case ne babba 

Ta rasa wama zata tambaya ga Goggo Amina sai kuka take ,

Ganin lokaci na tafiya tasan yanzun bazata samu amsar tambayar taba yasa ta wuce kofar yayan ta shanyar kayan dazun da safe takai d’akin jakar ta dauka da Abubuwan da ta lissafa Mata duka,ta rufe kofar  tayi kofar gida

Da sauri ta fita daga gidan ganin har yanzun jama’a na tare Tam,

Hospital ta wuce direct tana isa dakin ta baiwa Sumayya jakar,

Budewa nayi na zaro kudi  50k  na mikawa yayan khadija “ga kudin ka dau takardan khadija ta rakaka kuje ku biya”

…Toh Al’ameen yace  Yana laluben kudin ya karba hade da zaro dubu goma da dari biyar in safiya da Khadija ta basa ya hada da dari biyar in mangoron sa,ki cire dubu goma da dari biyar a cikin kudin sai na hada Dana wajena na ciki ta na biya,

“Ka bar na wajen Kan ai ba’a sallame niba zasu bukace  mu Sai wasu abubuwan irin su hand gloves Koh ruwa da allurai duka ai bamu Gama kashe kudi ba ba iyya aikin bane kawai ka rike kudin a gunka,”

Toh khadija Tashi mu tafi 

Toh yaya, ta basa amsa

**Fita sukayi nikam zuciyata tsinkewa ya ringayi da fargaba gani nake kamar bazan rayu ba,

Waya ta da khadija ta kawo mini na dauka number abie na Kira Amma Bai dauka ba,

Sake Kira nayi harna fidda tsammani naji  ya dauka cikin sanyin jiki na Masa sallama”assalamu alaikum abie”

Waalaikumu salam ke lafiya?

Lafiya Alhamdulillah abie Daman na kiraka ne nace maka za’a mini operation yau don Allah Abie in nayi maka ba daidai ba kayi hakuri abie ka yafe mini bansan Inna shiga operation room  xan fita da Rai Koh a mace ah ah shiyasa na kiraka naji muryarka abie ka samin albarka Koh xanga nasara a rayuwa ta Dan Allah”

Keeeeeee!!!! ce Miki akayi  in za’a ma mutum tiyata mutuwa yake ne kin wani kirani kina fadamin Zaki mutu ki mutum Mana keee!!!! bara ma na fada Miki daga yau karki sake kirana!!!!

 wallahih, tunda na aurar dake ki barni na huta mana,

***Hawaye ne keben fuskata Wai meke faruwa da rayuwa nane haka,,

Yanzun mahaifina in ma ya juyamin baya,

ganin shigowar Al’ameen da Khadija yasani share hawayen,

“Khadija kin biya”?

Eh Aunty…. Sunce 7:00 na dare za’a shiga operation room in,

“Toh bara nayi sallah mangariba Koh kafun Azo a dauke  ni” na fada zuciya takaraya sosai wallahih,

Shima masallaci ya tafi nida Khadija mukayi Sallah muna idarwa na sakasu suci abincin da ya rage tun safe Basu sake saka kome a cikin su tun karyawan safe na taliya da wake,,

Daker suka iyyaci Amma kadan nikam na kasaci tsabar fargaba,

Karfe bakwai akazo za’a dauke ni,

*** Da kafata na fitoh nurse suka sakani a gaba har nayi nisa Al’ameen ya k’wala mini Kira tsayawa nayi ya iso inda nake lalubar hannuna yayi ya rike cikin damuwa sosai nasan daurewa yake,

Sumayya insha Allah Zaki fitoh cikin nasara kinji ki cire tsoro a ranki kinji Allah ne ya jarabceki Kuma insha Allah shizai baki lfy kinji,

“Kukane ya k’wace mini yau wa’innan bayin Allah sune gatana a yau bani da kowa a kusa Dani sai su dame Zan biya su babu, Allah ne kawai xai biyasu” rungumar sa nayi cikin kuka nake  cemai “insha Allah insha Allah”

Lokaci fa na wuce wa ki shige mu tafi Naji muryan Nurse 

***Sakensa nayi na rungumi khadija wance tun tuni kuka take, 

***Na juya Ina tafiya a hankali Kamar wance k’wai ya fashewa a ciki sudai suna bin mu a baya har Muka Isa kofar operation room aka dakatar dasu tare da nuna musu su koma Kan kujirun d’ayan block in su zauna…… 

Bayan da Al’ameen baiyi ba Khadija ta koma gida taje ta kwanta Amma Taki tace anan zata kwana sai da ya nuna Mata Jan ido kafun ta yarda zata tafi 500 ya Bata ta hau nepep sauran change ta rike a hannun ta ,,,

. godiya ta Mar sosai ,ta dauki kula ta fita,…..

Zama Al’ameen yayi agun har akayi Kiran isha’i yaje yayi sallah yanata Addu’a Allah ya yasa aiyi aiki a sa’a ya Bata lfy(muma mukace Ameen) 

Bayan wasu hours Sumayya aka fitar akan gado tare da kayan tiyata da hulan duka Koh motse batayi aka kaita dakin da ake aje,wa’inda akama tiyata Basu farfado ba shima binsu yayi har dakin ya shiga sun dauke ta sun daura akan gadon dakin,

 kujira ya samu  a Gefen gadon ya zauna ganin an shanja musu daki ba dakin emergency bane tashi yayi yaje ya tattara kayansu na dakin emergency ya dawo dashi dakin da take yanzun, zama yayi a Kan kujira,

Har dare yayi sosai Bata farka ba,  sai karfe 2 na dare ta farka tana fizge fizge bakin ta dauke da salati tana ambatan sunan abie yayi hakuri karya gujita itama,,

Abirkice ya mike Yana kakamata ganin irin girgiza da take ya tsorata da sauri ya k’wala ma nurse inda ke dakin a zazzaune Kira ganin inyace zai tashi Sumayya zata iyya raunana kanta,

Da gudu suka yi kanta suka kakamata surutai tayita Yi Akan Abie da salati sai Shan anjima kadan Sumayya ta koma bacci,

Likita lafiya kam meke faruwa ne da Matata?ya fada hankalin sa a mugun tashe,

Ka kwantar da hankalinka ana samun haka Daman in dai mutun zai farfado sai yayi ta sambatu,..

Toh doctor yace Yana komawa Kan kujiran ya zauna hannunta ya laluba ya rike yanajin wani irin tsoro a ransa,

Har asuba Yana zaune sai da yaji ana Kiran sallah kafun. Ya Mike ya fita yaje yayi ya dawo  ya cigaba da zama…

Khadija Taki fadawa yayanta abinda ta gani a gidansu gudun kada hankalin sa ya tashi ta Sansa da saurin birkice wa gashi Yana fama da Sumayya tazo ta Kara Masa da wani Kuma,

Keke napep tahau  ta wuce a kofar gidan su Goggo Amina ta sauka ta biyasa kudinsa ta shiga gida da sallama. ……

Goggo Amina ta samu  zaune sai rusan kuka take Kamar wance ake yanka namar jikinta,

Da sauri ta karaso gareta cikin tashin hankali tana cewa Goggo Amina lfy menene ya farune wallahih tunda na tafi hankali na yaki k’wanciya?

Wallahih Khadija kedai ki bare kawai mutanen gidan mu sun dawo kashe junansu,

Kamarya Goggo ban gane ba?

Toh dazun bayan la’asar iro ya dawo daga aiki yazo zaici abincin ranan sa ashe suwaiba( yar baba lami) ta dauka taci shine da yazo dauka yaga babu yake tambayan inno ya abincin sa babu  a kula shine fati tace masa suwaiba ne taci, 

Tashin sa ba wani tunani ya zaro wayan wuta ainahin na bol ya zuba mata ita kuma da taji zafi tana ihu ta zari tabarya zata muka Masa,

Inno Kuma ganin za’a bugawa iron ta tabarya tazo zata k’wace kawai tabarya ya sauka a kanta,shine fa Kika ga ta mike Koh motse batayi, 

Ni tsorona ma yanda naga Kan Bai fitar da jini ba kinsan akwai babban hatsari ka bugu irin wannan ace jini Bai fitoh ba,

Shine iro ganin inno a yashe a kasa yaje ya ibo Yan sanda akazo aka tafi da suwaiba, gabaki daya gida ya hargitse su bappa nayinku duk sun bisu station wasu suna asibiti har hanzun ba’a San takamammen halinda inno ke ciki ba mutuwa Koh rayuwa😭😭😭 wayyo ni Aminatu,

ta fada tana sake rushewa da kuka ita dai Khadija Allah ya kiyaye na gaba tace ta Mike taje ta ajiye kulan Sumayya a kitchen sai gobe zataje kofarta da safe,wanka tayi, tayi isha’i ta kwanta don batajin yunwa taci a asibiti,haka tayita juyawa Amma bacci yaki daukan ta tashi tayi ta Kama lafilfilu tana nemawa Aunty Sumayyan ta lfy da nasaran aiki sai 1 ta kwanta

Bangaren Al’ameen bayan sallan asuba har lokacin yana zaune Dayake dakin da suke yanzun babban falo ne Mai dauke da majinyata masu yawa wa’inda aka ma operation shiyasa Basu kadai bane a dakin,

 sosai Yan dakin ke mamakin MAKAHON nan shin baida Yan uwane da zasu kula da wannan Mara lfy sai MAKAHO chap lallai Kam kowa gulma na cinsa( Niko nace gulma zai karku bazakuji kome ba) 

Tun asuba Khadija ta farka Bata koma. Bacci ba wanke wanken Goggo Amina ta fara ta hada harda kulan  aunty ta duka ta wanke tayi shara tana Gamawa ta daura dumame ganin yau Goggo Kamar Mara lfy haka da tashi ,tana Gamawa ta dauki key sai gidan yayan ta,

Yauma sai da tayi shara ta daura ruwan zafi Yana tafasa ta juye a flasks ta dafa indomie da kwai lokacin karfe 7:30 wanka tayi tasa kayan ta data dauko a gidan Goggon ta tadau abincin tayi hanyar FMC

****Da misalin karfe bakwai na safe na bude idona Wanda nakejin Kamar an zuba mini barkono a ciki a hankali na sauke k’wayan idanuna a kansa a zaune yake ya tasani a gaba Kamar wani Mai kallo yayi tagumi kallo daya zaka Masa kasan a cikin zullumi yake sosai…….

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin Koh kinsan mace sai da kamshi da* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turaren  Suna d’ayane Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin*

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da gyara*

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*

πŸ€ *Na tsunguno (habil)*

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam) (khumraBlack & while*)

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth*

πŸ€ *Na d’aki (halud Al’oud)*

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌ πŸ’ƒπŸΌ

πŸ€ *Suna bada kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*

 *Contact them vie*

08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧   

Page1️⃣4️⃣&1️⃣5️⃣   

Aunty’ inno ta rasu tace tana Kara karfin kukanta,

“Innalilahih wainnailaihir rajuun”   Allah ya jikanta da rahama yasa ta huta” nace 

Ameen Aunty tace tana mikewa tadau hijab inta ta nufi cikin gida,

**Banyi niyar zuwaba saboda jikina Amma ganin mutuwa ne Kuma Abu da  gida babba hakan zai iyya zama abin magana, yasa na mike na fita zuwa cikin gidan, 

Ai ban tashi sanin Yan gidan ba sai da Naga manya da yara Suna kuka harda na tashin hankali kuka suke ba manya ba yara Mai makon a ma mamaci Addu’a sai ihu da kuka nidai Ina zaune a Gefen matan makwanta da suke shishigowa Ina kallon ikon Allah

Al’ameen da wannan sanyin jikin ya iso kofar gida ya tarar da jama’a makil, inno ta rasu mutuwar ta dake sa sosai don alokacin sai da mutuwar mahaifiyar sa ta dawo Masa sabo,ganin yanda iro ke kuka Wanda yasan halin iro ba kome ke tsorata Sa  bama Amma yau kuka yake,

tabbas mutuwar iyaye akwai ciwo,(Allah kajikan iyayen mu)

Ankai inno gidan ta na gaskiya yau har anyi sadakar bakwai gida ya koma kamar yanda yake kowa na sha’aninsa sai yaranta da sukayi sanyi kadan na rashin uwa,

A tsawon satin nan na fahimci yayan Khadija baida aiki haka zaije yayi ta yawo Koh sisi bazai samuba ya dawo Yana kame kame taliya Koh Maggi Koh indomie nake iba  na bawa Khadija takaima masu shago su Saya da araha kafun mu samu na shifenen Miya,..

Duk da Al’ameen baisan Ina Saida garana ba,

karshe dai ajesa nayi nace ya fadamin me ke faruwa, dashine yanzun,duk lokacin da ya zauna baida aiki sai tunani,

Tukum yamin bayanin bashi da jari yaje tashan kayan marmari  sun hanasa bashi duk inda yaje su taimaka Masa sunki,

,”Amma   menace maka in Abu ya taso ta wajenka bance ka ringa fada mini ba”?

Hakane Sumayya Amma ni sai Inga Kamar ni ya dace in bukatar ki ya Tashi ki tambayi ni ba Zan ringa daura Miki nauyi ba,

“Au aini ma nufina bashi Zan baka Amma Ina ni Ina baka kyautar kudi sai dai bashi “

Duk da haka dai Sumayya….

Ban Bari ya karasa maganar Saba na tare sa “na baka bashin ne ka rufawa kanka asiri Koh na rike kudina ka cigaba da yawo ba aiki ga azumi saura wata biyu”

“Kuma bara na gaya maka in azumi yazo kayan Dadi zakana sai min Kuma kamin kayan sallah harda Khadija kaji dai na fada maka”  

Toh shikenan abani yace Yana gyara zama alamun dai baida mafita,

“Ka Bari sai gobe Zan baka”

Washe gari Khadija na tura yaro yace tazo, ba’a jima ba sai gata aikanta nayi   *say* *box* ta Kira mini Daya daga cikin yaran  masu shagunan sai da wayoyi da laptop’s suzo tare tace Masa amarya ce ni Kuma ban fara fita ba,

Don nasan in na Bata laptop innan za’a Mata cinikin wulakanci ne kawai Koh ma wani ya Mata wayo ya gudu da laptop in don nasan say box ba irin mutanen da babu a ciki,

Munyi ciniki da Mai sayan system in ganin  yanda Yama laptop in cinikin wulakanci yasa nace na fasa sayar wa,

Buhun flower na dauko a kitchen Daman ban taba bude Saba nace wa Khadija taje gun Haladu tace Masa xai Saya buhun flower Zan Masa sauki,

Bata jima ba ta dawo tace min yace ta kawo flowern ya gani, Bata buhun nayi taje shagon Haladu ta sayar mini shima naira dubu bakwai ya Saya ba yanda na iyya haka na sayar Masa Amma ni Karan kaina nasan ba haka kudin yake ba,

Yayan khadija na baiwa dubu uku yayi jari na rike dubu hudu na D’an Yi sayayyan abin bukata  nayi irin su pad omo sabulu na baiwa Khadija dubu D’aya, tunda har yanzun Basu gyara Mana NEPAn kofar muba  don sun biya ganin mu bamu biya ba sai suka yanke wayar kofar mu Khadija na baiwa dubu daya ta mikawa bappa sulaiman kudin wutan NEPAn mu aranan sukasa aka hada mana wayar aka gyara, na baiwa Khadija dari biyar itama  πŸ˜‰

Haka rayuwa tayi ta tafiya Rana ya wuce sati ya shude yau Dadi gobe Akatsen sa  har Muka cika wata Daya da sati biyu da aure, ba abinda ya taba shiga tsakanin mu Koh da kuwa hada gado ne, in munkwana waje D’aya toh ana zafi munyi kwanan waje ba nepa,

A y’an kwanakin nan na  fara fuskantan matsen rayuwa Wanda ban Saba ba,

Dole sai abinda ya samu zamuci wani sa’in ma in Bai samo kome ba haka zamuci indomie d’anye wani a dafe da ruwa, in ya samu D’an ciniki Kuma muci shinkafa da Mai da yaji,Inda Allah ya sumuma garana Bai kare ba akwai taliya Mai Maggi kefe shinkafa, Amma duk da haka na D’an fada  na chanjin yanayi,  saboda yanzun ya hanani Saida Kayana don har Yan unguwa sun fara gulman ya kasa rikeni Kayana nake sai dawa,maganan har kunnen da yashiga shiyasa ya nuna mini baya so ,

yau na shirya da niyar zuwa gidan Goggo Amina, da gidan mu tunda safe na kammala aikina yau mun Sami kudin kayan shaye mukasha da safe’ bayan ya fita na kammala aikina dake na sanar dashi Zan fita gidan Goggo Amina ( marikiyar Khadija ) Zan bi gidan mu d’uka Bai Musa ba saboda mun Riga munyi maganar dashi, dari da hamsin ya bani kudin Keke,

 Khadija zata rakani kasancewar yaune Zan fara fita, unguwa tunda nayi aure bayan asibiti ba inda naje,

Sai goma Khadija tazo lokacin na fitoh wanka, Muka gaisa ta shiga Wanka Dayake tun jiya ta zo ta guge kayanda zatasa d’aya Daga cikin Wanda nake Bata,

Shiryawa nayi cikin lufaya Mai tsada fari Mai Flowers brown NASA riga long sleeve brown NASA takalmi fari na dau jakama fari fuskata ba kome sai powder da man baki, Khadija dake gefe na tsaye baki bude tana kallona,

“Rufe bakin ga guda zai wuce ciki”nace Mata cikin murmushi Mai karawa fuskata kyau,

Hmm Aunty na gaskiya ke Mai kyauce Allah ne kadai yasan dalilin da yasa ya bawa yayana wannan k’yakk’yawar hallintar nan Ina ma Yana kallo yaga yaran da za’a Haifa Masa πŸ˜…

Murmushi kawai nayi bance kome ba  don na lura ita ta yara ma take,

” Khadija kiye sauri kisa kaya don Allah na masu na ganni a gidan mufa Naga abie na”

Toh Aunty tace tana saka dogon riganda na taba Bata,tayi shafe shafen ta tana Gama shiryawa, Muka  fita”

Yaune rana na farko Dana taba karewa unguwan sintali kallo unguwa ne da ya hada ruwa biyu masu kudi da talaka wa Yan kasuwa da ma’aikata da masu zaman banxa unguwan nada kyau sosai da fasali,..

Gidan Goggo Amina mukaje da kafa ,

Mun samu tarba Mai kyau ba laifi matar nada kirki sai dai na Lura ita mace ce da Bata shiga abinda Bai shafe taba Sam babu ruwanta,mun D’an jima a gidan kafun Muka Mata sallama na aje Mata laidan Turare Wanda na d’auka a kayan aure na,

ta rakomu har waje Muka tare keke napep ,

Hajiya Ina kukayi? Ya tambaye ni

“Specialist” zaka kaimu,

Ku hau muje yace,

Dukan mu Hawa mukai yaja machine insa muka nufe  unguwan specialist,

Muna shiga unguwan mu  na Masa kwatancen inda zai sauke mu,

“Yana sauke mu na tambayi sa “nawane kudin ka”  

Naira dari da  hamsin kudin ku kubiyu,

Sai a lokacin na tuna dari da hamsin inne a jikina kacal Wanda yayan Khadija ya bani Allah dai yasa abie na gida nasan zamu samu na dawowa don karyan mu taka da kafa daga specialist zuwa sintali,

biyansa nayi muka  nufi kofar gidan mu

Khadija mutuwar tsaye tayi ganin wani irin gida Mai bala’in kyau Wanda Koh a mafarki Bata  taba ganin irin Saba Daman ita ba yawo take ba iyya kacinta kasuwa sai unguwowin kusa da sintali  irin mafindi unguwa gadi da sauran unguwowin kusa da unguwan su,

Amma Bata taba zuwa unguwa Mai nisan nan ba sai dai tanaji a bakin Asma’u sunje unguwan specialist Koh millionaire’s sweet in suna Bata lbrn gidajin unguwan sai taga Kamar tatsuniya suke Bata bata taba zaton haka gine ginen unguwan yake ba Wai duka wannan a cikin Jala yake?

***Harna nufe get Amma sai naji Kamar ba Khadija a gefena juyawa nayi me Zan gani Khadija an sake hanci baki ido ana kalle kalle zuwa kawai nayi na jaho hannunta, sai a lokacin ta farga da kauyancin da ta nuna 

Cikin Jin kunya tace Aunty wallahih unguwan nan yayi kiga gidan da zamu shigan nan Kamar aljannan duniya,

Kai Khadija kin cika shirme wallahih mu tafi nikam,

**Get Muka nufa Mai girman gaskiya kamar get In gidan prison haka ma ginin gidan dogayene sosai anyi penti fari get in ma farine k’wank’wasa,makeken kofar get in,nayi

Wani farin buzune ya leko ganina yasa ya washe bakinsa cikin hausar sa da baya fita yake cewa laaa Amarya Kaine hajiya Sumayya wallah nayi kewanka shannu  da zuwa lale lalema barkama lale ya fada Yana bude mini get muka shiga,

Shiga cikin gidan mu ya sake ruda Khadija ganin filin gidan mu filine babban bana Wasa ba  Wanda yakai girman wani karamin unguwa,ga shuke shuke na Flowers ya kewaye gidan Wanda ya kara haska gidan sosai ga parking space babba Mai dauke da mototi na alfarma wanda akalla zasu Kai talatin duk ciki bamai araha,

Nidai Ina rike da hannun Khadija Muka nufi wani  babban part Wanda duk fadin gidan part inne kawai ba wasu Amma daga ganin part in kasan ba karamin duniya bace a ciki ganin shima ginine na gidan sama Mai Hawa uku,babban kofar falon NASA hannun na na bude da sallama a bakine duk da banida tabbacin za’a ji,saboda girman falon,

Khadija Kam mutuwar tsaye ta sake tayi ganin cikin falon gidan mu,

Kusa Kai mukayi cikin falon falone Mai girman gaskiya Wanda ke dauke da kujiru set biyar ga babban plasma na alfarma Kai fadar tsaruwar falon gidan mu Bata lokaci ne na barwa readers su keyasta,

Babban falon gidan mu Yana dauke da d’akuna kusan Sha biyar haka upstairs shima dakuna  goma Sha biyar ne Hawa na uku ma haka,Amma duk yawan d’akunan gidan munan falon mu dayane shine falon kasa, Wanda Koh a Hawa na uku kake kana hango falon,

 d’akunan kasa na samarine sai kakarmu dake zaune dasu a kasan Wai tana saka musu ido injita, dakunan Hawa na biyu na iyaye ne Hawa na uku shine na Yan Mata da d’akunan yaran gidan da sukayi aure maza,suna zaune da iyalansu ,..

duk yanda Zan fasalta muku gidan mu saifa na  rage wani abin,

Kaf gidan mu da colour D’aya aka kawatashi da white colour sai surkin baki Kama daga kujiru labule  Abubuwan da aka kawata gidan kome farine daga sama har kasa abin sai Wanda ya gani,

Jama’ar gidan mu duk Muka samu a falo da yake yau weekend ne ba aiki ba makaranta kowa na zaune wasu na kallo wasu na Danna waya wasu na Danna laptop yara na wasa wasu abinci suke ci ganin mu yasa dukansu barin abinda suke suka zuba Mana ido Kamar yau suka fara ganina,tunda Khadija ce Basu sani ba,

Idanuna ne ya sauka a Kan kakata dake zaune tanacin kefe sai uncle’s nawa dake zazaune wasu na cin abinci wasu na Hira wasu na duba takardu,

wani abune ya tsayamin a makoshi Mai kamada Takaici sun aurar Dani Basu damu da rayuwar da nake ashan ba gasuna suna zaunen su Kamar Basu San wata Sumayya da aka bawa MAKAHO ba Basu neme sanin ya rayuwa ta kare ba waima me dalilin auran Dani ne tunda gasu Aunty miemie sun girme ni nesa ba kusa ba Amma saini kadai aka aurar auren ma da MAKAHO ba lafiyaye ba,Koh don anga mahaifiyata Bata gidan ne Kai Koh mahaifiyata Bata gidan ai ubana nanan

Koh da kowa zai nuna Mini kiyayya dada zata sassauta tunda ita ta haifi babana amma Ina abin ba sauki,

“Ina kwana dada,”nace Ina zama a cikin Daya daga cikin kujirun falon,

Toh matan miskinai ne agidan namu yau Koh idonane,?

Ah ah Kaka ba idon ki bane kinsan azumi ya karatoh anzo amsan zakkah ne,

Hhhhhh Kai miemie baki da dama Amarya ce fa tazo ganin gida mutun da gidansu kece yazo karban zakkah,kubra ke fada tana dad’a tunsirewa da dariya

Waiku yaran nan wasu irin Yan iska ne me yasa baku da mutunci shegu kawai ai gwara ita tayi aure Koh?

Keee koh miskini kin samu yazo wajen kine da sunan aure, a cikin ku waye ta samu miskinin na zuwa wajenta,Yaya Abdu ya fada ransa a bace,

Ai itama ba zuwa yayi ba lika Masa akayi,miemie ta basa amsa,..

Rufe mini baki karna ci ubanki Yar iska Abdul yace Yana mikewa,

Ai duk laifin  dadane Sam bansan me yasaba, Dada (kakar mu)  itace babba Amma ita ke sasafo Mana bala’i yaya kabiru yace Yana maijin takicin ahlin gidansu,

Abubakar kanajin abinda shegen yaron Kan nan kabiru yake  shimin mutunci kayi shuru kana kallonsa,,,

Kiye hakuri Dada Kai kabiru zanci kaniyarka fa inka sake shiga abinda ba ruwanka uwarka aka zaga Koh me da zaka saka bakinka a ciki,

Mikewa Kabir da Abdul sukayi sukabar falon,

Ganin yanda aka Mai Dani Kamar kashi ba Wanda yabi ta kaina kowa na Harkan gabansa

Ganin Banga Abie na a cikin falon ba yasa na mike nayi hanyar upstairs na nufi d’akin sa nabar Khadija a falo wance ke rakube Kamar ace kitttt ta ruga,

Bude kofar d’akin nayi nasa kaina na shiga   Abie nane zaune a kasan tiles Yana duke da Kai sai momy (yadikko na) zaune a bakin gado daga Gani dai magana suke………………

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦― 

             ~ Na ~

 πŸƒ *Rukayya Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

Free book🀧

Page 1️⃣3️⃣

Bayan fitar Ammar Khadija ta kirga kudin dubu goma ne,Mika min tayi, Aunty ga kudin

“Ajjye Khadija in yayanki yazo ki basa tunda shike fama da zirga zirgan asibiti” toh Aunty ta bani Amsa tana aje kudin a cikin ak’watin Kayana,

Al’ameen na fita daga asibiti da kafa ya koma har gida Dayake akwai sanda in Kuma yazo titi sai ya Kama yara su tsallakar dashi Yana Isa unguwan su(sintali) wajen shagunan bakin titi ta inda yake sai da mangoro a bakin su,

Shagon malam shu’aibu ya fara zuwa don shine yafi masu shagunan abin arziki sosai alayin da sallama a bakinsa ya shiga shagon,

Assalamu alaikum malam shu’aibu

Waalaikumu salam Mai mangoro ne?

Eh nine malam shu’aibu barka da jama’a

Barka dai lafiya Kam Naga yau tun safe danazo bude shago Naga hulbairon ka a rufe dazun na aiki yaron gidana ya karbo mini yako yake fadamin baka nan?

Eh wallahih malam shu’aibu iyalina ne ba lfy jiya na kaita asibiti,

Allah sarki ya jikin nata?

Da sauki Daman nace bara nazo ka taimaka mini da kudi dubu hamsin za’a Mata aikine appendix ya kumbura a cikin ta don Allah ka taima kamin,

Kutt lallai ma a karnin nan da kowa ke takai takai Ina Zan iyya daukan kudi har 50k na baka da sunan bashi, bayan anyi operation in Ina zaka samu kudina ka biyani, gaskiya bazan boye maka ba ni nan Koh biyar bazan iyya baka ba banaji ance Yar masu kudi aka aura maka ba me yasa danginta bazasu Mata jinya ba tunda sunsan baka dashi Daman suka baka ita

Shikinan malam shu’aibu na gode, ya fada Yana fita ba tare da ya basa amsar tambayar Saba,

D’ayan shagon Al’ameen ya shiga  shagon gwanja bayan sun gaisa shima ya rokesa Koh zai samu bashin kudi

Amma Kai dai wallahih D’an rainin wayo ne ya Ina Saida kayan Miya zakace na baka dubu hamsin duk kayan shagon nan aka sayar Ina zaiyi dubu hamsin,

Haka yayita bin shagunan makwantansa Amma ba Wanda ya basa Koh sisi wasu kamma da bakar magana suke binsa dashi,

A haka ya iso shagon Haladu shima yace baidashi,. Wajen bairon mangoron sa yaje ya bude ya tataba mangoron rabi duk sun lalace saboda yini da sukayi a rana Kuma a rufe, zabe masu kyau yayi Yana,

D’auka yana sawa  a k’wando ya shiga shagon Haladu dashi, Yana cewa,

 don Allah Haladu Koh zaka sayar mini da mangoro na zanje na zauna a asibiti  na kwana biyu daidai Matata taji sauki 

Gaskiya bazan iyya sayar maka ba sai dai na saya kawai na sayar Nima na samu D’an riba,

Ba damuwa Al’ameen yace Masa

…..Nawane mangoron?

D’ari takwas da hansim

…..Zan baka dari biyar  don Naga wasu sunyi laushi?

Ba damuwa Allah ya saka musu albarka

……Ameen

Kudin Haladu ya basa ya karba gida ya shiga ya bude kofar,

 da yake ya karbi key a hannun Khadija wanka yayi ya saka kayansa Jin ana  Kiran la’asar yayi Alwala ya lalube takalmin Sumayya ya fita dashi a hannunsa, masallaci ya tafi yayi sallah ya wuce asibiti duk zuciyansa ba Dadi ya rasa wajen wa zai tinkara da zancen kudi,, yasan Koh mutuwa zaiyi Yan gidansu bazasu taimaka Masa ba bare Sumayya matar sa,

***Muna nan da Khadija har la’asar sallah mukayi dukan mu nurse tazo ta mayar mini da laidar ruwan a hannu na,

Na kwanta baccine ya dauken nabar Khadija na zaune,

Ya iso asibitin da sallama ya shigo dakin Khadija ta amsa masa.

Sannu yaya ka dawo?

Eh Khadija

Toh yaya ka samu kudin?

Wallahih Khadija sai addu’a naira 500 ne kadai na samu

Amma yaya ya kamata ka sanar da Aunty gaskiya don wallahih Yaya Ina Jin tsoro kaga ance appendix in ya kumbura fa tunda Allah Bai baka ikon samu ba, ka fada Mata ita sai ta biya?

Toh Khadija wallahih inajin kunya a matsayina na mijinta na kasa biya Mata kudin operation don samun lfyr ta,

Habba Yaya karfa ka manta Allah yaga zuciyar ka baka dashine Kuma ba abin kunya bane tunda itama tasan baka dashi,

Suna cikin Hira na farka a gigice Jin wani irin mahaukacin ciwon ciki ya tasarmin ” Innalilahih wainnailaihir rajuun wayyo Allah na cikina”

Subhanallah Sumayya cikin ne Al’ameen Daya Mike cikin tsananin tashin hankali yake lalubarta ,

Khadija ma da saurin ta ta iso ni,sannu Aunty take fada idon ta ya jika da hawaye

*****Nikam.na kasa Bata amsa kuka kawai nake hankali tashe

Khadija tashi kije ki Kira doctor eiiii sauri 

Toh yaya tace tana mikewa da saurin ta

Al’ameen Kam hannun Sumayya ya Kama sai sannu yake Mata a hakan likita yazo ya sameta a halinnan

Da sauri shida nurse suka rufu a kanta tare da K’ura Khadija da Al’ameen waje,allurai sukai Mata harda na bacci lokaci daya bacci ya dauke ta,

Khadija da Al’ameen na tsaye a  bakin kofa likita ya fitoh ya kira su zuwa office,

Malam Al’ameen majinyaciyar ka tana cikin condition Mai muni ya kamata ka samo kudin aiki nan da awa uku ba wallahih kome zai iyya faruwa,

 Innalilahih wainnailaihir rajuun kawai suke fada,

Suka mike zuka fita a office in Khadija Kam kuka ta fara abin Yama Al’ameen yawa ta Ina zai fara anya zai yafewa kansa kuwa in yar mutane ta mutu ata dalilin rashin kudin aikin da Bai samo ba,

Yaya ya kamata Aunty tasan abinda ke faruwa muje ka fada mata ta Kama hannunsa sukayi dakin 

Suna shiga suka samu Sumayya na bacci ……….

Yaya Ammar innan yazo baka nan  ya bawa Aunty kudi Amma Taki karba tace na baka 

Allah sarki Ammar yazo ne?

Eh yaya kana fita Yana shiga, yace ma Wai Daman Yaso kuyi sallama tafiya ne ya kamasa, na gaggawa,

Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari Yan kiyaye sa aduk inda yake,

Ameen yaya

 Khadija Miko min kudin na hada da dari biyar in hannu na naje na Basu Koh zasu mata daidai a Nemo sauran su bimu bashi,

Uhmm lallai yaya kadai San asibiti bata ma matum aiki ba tare da kudi bak’oh?

 Khadija bara dai naje na gwada Koh Allah zaisa a dace tunda kinga hour uku aka bamu kuma yanzun bacci take, bara naje na dawo ya fada Yana karban kudin da khadijar ke mika Masa,

Yana fita yaje wajen biyan kudi, 

don Allah Dan uwa kayi hakuri ga dubu goma da dari bayar a fara mata aikin in yaso za’a cikita muku daga baya Dan Allah ku taimaka min matatace ba lfy kuma hour 3 aka bani ake son mata operation?

Amma Kai *makahon* nan Ina ga baka zuwa asibiti ne taima?

Ina zuwa ranka shi Dade sai dai ban taba kawo majinyaci irin wannan ba

Toh gaskiya ka gannin nan Koh biyar naci a cikin kudin da nake karba wallahih Sai an daure ni

Kuma anan in baka biya kudiba wallahih baza’a Mata aiki ba Koh mutuwa zatayi gwara kaje ka Nemo duk in da kudi ya shiga ya fita shawara nake baka,Amma zance a taimaka maka toh hadai asibiti ba

Shikam tsabar damuwa har jiri yakeji yana ibansa ,a rayuwar yanzun in baka dashi kana ji kana gani harka mutu indai baka da kudin jinya ba Mai taimakon ka, zama yayi a bakin barandan pharmacy in yayi shuru cikin tashin hankali da alhini,

Bayan fitar Al’ameen khadija na zaune har lokaci hawaye baibar zuba ba sai ta gogi wani ya zuba, har  hour 1 yayanta Bai dawo ba,

*** A hankali nabude idona na sauke akan Khadija dake ta hawaye ido harya kumbura abinka da farin fata fuska tayi ja” khadija lafiya kuwa meya faru Naga kina kuka”??

Babu Aunty Daman na tsorata ne danaga cikin ki ya Tashi Ashe haka kike fama da Jin jiki sannu,

Murmushi nayi “haba Khadija Menene na kuka baki ga naji dauki ba” 

Toh Aunty,

“Yauwa khadija nikam likita ya fadi abinda ke damuna ne, Koh yake sani ciwon cikin nan”?

Kafun ta bude baki ma sai ga doctor ya shigo,Wai har yanzun baku samo kudin aikin ba Koh bakuji condition inda nace muku tana ciki ba Wai ina MAKAHON yake ne?

“Doctor ban gane mikake nufi ba” nace ina kallon sa?

Au baku fada mata bane? Yana kallon khadija alamar tambaya

Eh doctor bata sani ba khadija ta bashi Amsa,,

“Wai meke faruwa ne kun sani a duhu” waza’a ma aiki??

Kece appendix ya kumbura sosai tun jiya na sanar dasu Amma haryau shuru Basu biya kudiba yanzun haka  hour 3 na Basu su kawo kudin Dan kina bukatan aiki  gaggawa Amma an share hour 1  shuru, Banga alaman zasu biya ba

Da mamaki nake kallon khadija”yanzun khadija Ina fama da wannan babbar matsala irin wannan Amma kuke mini Wasa da rayuwa Ina da kudin da Zan iyya biya ba bandashi ba”

Kiye hakuri Aunty Daman Yaya ne yace shi yake son biya

” Koh ance lallai sai yayanki ne ya wajaba ya biya ai ni Karan kaina nasan Bai dashi don Bai biya ba ai bazai  zama wani abu na daban ba” menene riban ya fita yana neman bashi alhalin Ina da kudi”??

Kiye hakuri Aunty,ta fada jikinta a sanye ganin Raina ya baci

“Nawane akace kudin aikin”?

……50k ne

“Khadija tashi ki dauki key kije gida ki dauko mini jakana  wani yellow a cikin whtdp nawa ki dauko mini jakan akwai kudi a ciki”

Toh Aunty ta fada tana mikewa daukan key in tayi a jakan kayana ki hadamin da wayata ki dauko darduma babba da filo, ga kayan da nacire ma kikai mini gida kisa a basket in bayan kofa”

“Kihau nepep   ya kaiki kofar gida ki shiga in kin dauko kudin saiki shiga ya dawo dake ki basa 1k ya d’auki kudinsa karfa kice Zaki tafi da kafa”??

Toh Aunty ta d’auki  kayan nawa ta fita  a dakin, doctor Kam Dan kallo ya zama Daman tun da ya ganni yake ganin alamun Jin Dadi a tare Dani Amma abinda ya daure masa Kai mutanen da suka kawo ni asibitin abin yana bashi,mamaki harda Nurses Amma basuga fuskar tambaya ba

**komawa nayi na kwanta shima doctor fita yayi

 

Tsabar rudewa Khadija Koh yayanta Bata Lura dashi ba akan baranda ta wuce,

Shikam ganin lokaci na wucewa yasa ya Tashi ya shigo dakin,da sallama a bakin sa,

**Amsa Masa nayi Ina kallon sa yazo ya zauna a kujiran gefena,

 Sumayya,yakira sunana

“Na’am” na amsa Masa 

Kiye hakuri Sumayya na kasa kula dake wallahih nayi iyya kokari na Amma ban samu kudin ba Daman appendix ne ke damunki Kuma ya kumbura, shine ake son Miki aiki kuma……..

**Da nayi niyar rufesa da matsifa Amma sai jikina yayi sanyi Jin bayanin da yake mini” ban bare ya karasa ba na katse sa”ba kome, me amfanin Ina dashi kaje kana,.. baran attaimaka maka kazo ka biya mini kudin aiki”? Karka sake mini irin wannan banaso duk abin da zai taso a waje na Koh Khadija Koh Kai, in baka dashi  karka sake zuwa gun wani da sunan ya taimaka maka indai abin baifi karfina ba pls”

Kiye hakuri insha Allah bazan sake ba,

**Shuru na Masa

Jin Bata amsa ba ya sashi yin shuru

Khadija na Isa gida ta samu jama’a na cike a kofar gidan dam alamu dai wani  abinne ya furu don harda motar police ga jama’an unguwan makil……………

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense

πŸͺ€my WhatsApp number

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧                       

Page1️⃣6️⃣&1️⃣7️⃣

Shigowa d’akin nayi cikin hanzari na karasa kusa da abie na banyi wata wata ba na rungume sa na fashe da kuka maicin Rai,,,,

Ji kawai nayi momy ta dakawa abie tsawa,

Kai Abdulsalam mainace maka akan yarinyar nan?,

Ai da sauri Naga Abie ya hankad’ani a jikinsa ya mike tsaye cikin wani irin hada fuska Wanda. Bansan abiena dashi ba Naga ya mike cikin hargage yake magana Sumayya fita a dakin nan banason ganin ki banace Miki bake bani ba Koh bance ki zauna a dakin kiba,

“Abie Kai nazo gani don Allah Abie Koh kowa zai juyamin baya Kai karka Bari a rabamu don Allah Abie,” nace Ina fashewa da kuka,

Waye uban naki?? keh daga yau niba ubanki bane bansan wata y’a Sumayya ba kaf zuriyan shugaba babu yarinya Mai suna Sumayya ki fita a gidan nan da zuriyan mu bake bani Koh mutuwa nayi banason ganinki akan gawata,yace idanunsa na taruwa da hawaye daga Gani dai maganar fatar bakine bana zuciya ba,

“Amma abie menene nai maka da har zaka yanke dukkan alakar ka Dani har haka atunani na Koh kashe mutum nayi bazaka yanke alaka Dani ba abie ka rabani da mahaifiyata tun bansan kaina ba yanzun Kuma ka sallamawa duniya ni” wa nake dashi in ba kaiba kaf duniya nan abie why Abie why”😭😭?? 

Nafada Ina kallonsa gani nayi hawaye nabin fuskar sa,ya daga ido Yana kallon momy,

Toh munafuki kallon me kake mini,Ke Kuma wuce ka sata a  gaba tabar Mana cikin gida yanzun,

Nikam mutuwar tsaye nayi nashiga uku yaushe abie ya zama haka zaushe ya koma  yaron momy,abie da na  sani ne kuwa kafun na bar gidan nan Koh maganar banxa momy Bata Isa tamin a gabansa ba bare yau har tana basa umurni  ya koreni,

Ban farga ba naji an janii kiiiiiii!!! Anyi hanyar steps Dani,

Cikin mamaki nake kallon abie yau ni yake ja Kamar wata saniya zai koreni a gidan sa lallai fa,

Jana yake tayi har Muka sauko falo abin gwanin tausayi,nikam kuka nake Kamar Raina zai fita gabaki d’aya naji duniya tamin zafi,

Ganin abie ya nufi kofar fita falo Dani yasa Khadija tasowa ta biyomu a baya Yan falonka da ido suka bimu wasu na dariya ganin yanda uba ke fincikar yarsa 

Fincike hannuna nayi na dawo cikin falon na tsaya a gaban babuji  (kanin babana) ” babuji abani ducument Ina, Ina bukatar su,”

Don ubanki lokacin da uwarki ta haife ki da results ta haifiki ne,,,,,

Don haka baza’a bayar ba koma bara ma kiji daga yau Koh a kasuwa ne karki sake hada sunanki da family shugaba,

“K’warai  kayi gaskiya babuji ba’a haifini da results ba Amma da kudin ubana na same su in Kuma hassadace yasa kuka k’wace karfa ku manta arziki nufin Allah ne in Allah ya tsaga da rabonka  sai kayi arziki ruwa da iska Koh guguwa bazai Hanaka samuba”,

“Ba karatu bane kadai abinda ke sa bawa arziki rabonsa baya wuce kansa”

“Baiwa ta jarina”sannan wannan tsinannen gidan naku wallahih ku rubuta ku aje sai yafi muku prison ganin………………

Tassss naji saukar wani azabebben Mari  a kumatu na Wanda yasani sumar wucen gadi,ba kowa bane yamin Marin nan sai sahabi yaron babuji,

Ke karamar Yar iska watoh kema harkin zama Yar bariki irin mutanen gidan da kike Koh zakizo nan ki gwada Mana kin falle toh baki Isa ba ki tsaya kina gayama ubana magana in barki ya fada Yana fincikata juyawa nayi Ina kallon abie Wanda ke tsaye kansa a duke,

 Bai tsaya aku Ina Dani ba har Saida ya dangana da get turani yayi waje Yana ma Mai gadi warning daga yau in ya sake barin Mai Kama Dani ya shigo gidan nan a bakin aikin sa,Yana fadan haka ya juya abinsa yayi cikin gida, ya dauko jakana da takalmi ya watso mini a jiki,

Baba buzune ya fitoh yazo inda nake zaune tunda ya jefoni ban matsa ba mamaki tsoro da kuma wani irin tsana naji ya tsargan mini na family mu duka ban cire kowa ba, aciki nayi alkawari daga yau na yanke duk wata alaka da shugaba family house,

Kayi hakuri yaro haka rayuwa take kaji,

 kayi zaman auren ka ka rike mijinka Allah zai baka mafita kaji hajiya Sumayya,kayita addu’a kaima Allah ya tsareka gidan nan yanzun sai abinda matar babanka yace,

ya fada cikin tausayi,nidai Ina duke dakai sai kuka nake inda Allah ya Soni ma unguwan mu ba irin sintali bane nan kowa na cikin gidan sa Babu mutane a waje,

Jin ana kamani anason mikar Dani yasa na daga kaina Khadija ce wance bansan yaushi ta fitoh ba ,Ashe tun Marin da aka kwada mini ta ruga tayi waje tazo ta Saya,…

*******””””

Banyi musu ba na nike tsaye Kayana ta hau karkade mini nidai sai kuka nake Kamar zararriya gashi bamuda Koh sisi da zamu tare abin Hawa ya kaimu gida gashi Koh a gidan  ma bani da kudin da Zan biyasa Kuma banda tabbacin yayan Khadija na dashi, yasa na Kama tafiya da kafa Ina kuka,

Dukawa Khadija tayi ta dauki jakana Dana Bari,sai hakuri take bani Amma nai Mata banza a haka muka fara fasa hanya,

Mota na gani Tasha gaban mu tayi packing Abdul ne ya fitoh a ciki ya nufe mu,

 don Allah Sumayya kiye hakuri da abinda kikaje Kika tarar a gida wallahih yanzun gidan mu sai addu’a abin sai gaba gaba yake, Kuma na rasa me yasa duk gidan mu ke suka tsana,

*****Kala bance Masa ba don shima wani tsanar sa nakeji a Raina Sam yanzun naji banason ahalina kwata kwata na yanke duk wata alaka dasu daga yau Kamar yanda Suma suka yanke Dani,

***Kaucewa nayi na fara tafiya bance Masa kala ba,

Biyo ni ya sake Yi Yana mini magiya, Sumayya don Allah badon ni ba kizo ki hau na kaiki gidanki Kinga yamma yayi bazaki samu Keke napep ba anjima anan,

Wallahih Abdul Ina Ganin kimarka Inka kuskura ka kaini bango Zan maka abinda bazaka manta Dani ba Kai asuwa zakazo ka tsaya kana bani umurni wallahih daga yau Babu ni Babu Kai Koh a hanya ban sanka ba na tsaneku mugaye kawai azzalumai wallahih ku jira karshin ku,

Habba Sumayya menene laifina in sun Bata Miki ni meyasa Zaki had’a Dani,..

“Ai Wanda suka Bata mini su waye ne a gunka”?na tambaye sa Ina kallon sa ido cikin ido,

Iyayen  mune da Yan uwan mu,ya bani Amsa,

“Iyayen kadai da Yan uwanka daga yau bana D’aya daga cikin family shugaba  in baka sani ba ka sani yanzun ka fita harka ta “

Sumayya kada bacin Rai yasa ki ringa furta maganganu da Basu dace ba,

“Na furta Abdul Koh kaima dukana zakayi” na fada Ina wuce sa

Shikam mamaki ne yake son kashesa Anya Sumayya da ya sani ce wannan shuru shurun ashe haka take ganin bazata yarda tahau motarba yasa ya zare kudi a Aljuhunsa ya mikawa Khadija gashi Yan Mata kuhau Keke Koh ya fada Yana duban Khadija,..

“Wallahih Khadija Kika karbi kudin nan sai na nuna Miki true colour na”

Khadija Kam ta tsorata da sauri tayi gaba kamar yanda taga nayi,

Muka barsa a tsaye kamar gunki,

Tafiya muke har lokacin hawaye baibar zuba a. Idanuna ba wani irin zafi nakeji a Raina a haka muka ringa fasa unguwa unguwa muna wucewa tafiyarda tunda nake. Bantaba yin irinsa ba yau shi nake kafafuna duk sun kumbura na rashin sabo, Amma yanda zuciya ke cina Bai bare naji wahalar ba, Khadija kam Koh a jikinta,

Har mangariba yayi bamu ma kusa Isa sintali ba

   Aunty Koh zamu tare kekene in munje gida Yaya ya biya Kinga fa mangariba yayi ga hadari sosai? Khadija tace

Kala bance Mata ba tafiya kawai na cigaba dayi don nasan Koh na hau munje bazamu samu kudi ba tunda cinikin nasa duka ya hada ya bani Ina zai samu wasu dari da hamsin,

Tafiya mukaci gaba dayi ga yunwa don rabona da abinci tun ruwan shayen safe Amma bacin Rai baisa naji ba har aka Kira Isha adaidai lokacin aka fara yayafi sai ruwa ya sauko Kamar da bakin k’warya ganin mun iso bakin kasuwa yasa ban tsaya wani labewa ruwa ya dauke ba tunda dare ne Babu Wanda zai gane mu gashi NEPA sun dauke a haka ruwa na dukan mu muka shiga sintali hanyar gidana muka nufa tun daga nesa Muka hangesa 

Al’ameen ne a tsaye a kofar gida ruwa na dukansa daga ka gansa kaga Wanda hankalin sa yake tashe,

Muna Isa Khadija ce ta fara Masa magana nikam cikin gidan na nufa don bana bukatar Jin kome,

Yaya ya Naga kana tsaye a cikin ruwa haka gashi duk ka jika lafiya Kam?

Ina Naga lfy Khadija baku dawo ba Ina Aunty take Allah dai yasa Yan gidan su basuce bazata dawo ba wallahih naji tsoro Khadija karsuce zasu rabamu?

Hhhh habba Yaya bafa wani abu da zai rabaka da matarka insha Allah sai mutuwa Kama daina mugun tunani irin wannan,

maganan dadewa Kuma abin hawane bamu Bamu ba da wure, shiyasa naso ma mu kwana Amma Aunty tace mu dawo kar hankalin ka ya Tashi(Tamar karya don ya kwantar da hankalin sa)

Shap in kuka kwana ai nashiga uku kenan ,

Amma me yasa baku Kama hanya da wure ba kuka bare sai yamma kuka fitoh,gashi ruwa ya muku duka,

..Kai Yaya abinci fa muka tsaya muka ci,

Yauwa Yaya kasan me yau ran aunty a bace yake don Allah ka bita. A hankali inda Hali ma karka Mata magana yanzun ka Bare sai da safe ka Mata magana in ma kaga change a tare da ita ka Mata uzuri,

Meya faru Khadija?

Ba kome Yaya kawai dai sun D’an samu matsala da yaran gidansu ne sai Randa ya baci,

Bai yarda ba don yasan halin Khadija akwai surutu akwai boye abinda ba’a sata fada ba,shiyasa kawai ya shanja zancen,

Toh khadija muje ciki in ruwan ya tsakai ta sai na raka ki gida

Ah ah Yaya dare yayi fa yanzun ana neman 8:00 na dare nikam Zan koma Goggo zatayi fada,

Muje na rakaki gida  sai nama  Goggo bayanin dalilin jimawar ki karta Miki fada,

toh yaya,ta fada tana Kama hannunsa suka nufi layin su Goggo Amina,

Nikam Ina shiga cikin gidan da yake ana ruwa ba kowa a tsakar gida shashen mu na nufa,aje jakana da  takalmi nayi a baranda na kwabe lufayar jikina da yajika jakaf da ruwa na makala a igiya,

 dakin na shiga nadau towel na daura na zame  dogon wando da NASA   da under wear na makala a igiyar kofa ,

Kitchen na shiga na kunna gas na daura bojuwa (tukunya) na zuba ruwa a ciki,boket na dauko na ibi ruwa a Randa na tsaya a cikin kitchen in ruwan na tafasa na juye a boket in daidai yanda zanyi wanka na dauki boket in nayi bandaki,wanka nayi  na fitoh,har lokacin ruwa ake Alwala nayi,jakana na dauka a baranda na shiga dakin,

 Jin dis dis Kamar panfo yazo daukewa yasa na lalube  wayata  a jaka na haska dakin idona ya sauka akan kujiran da yayan khadija ke k’wanciya  ya jika jakaf da ruwa  saitin wajen na yoyo fita waje nayi da sauri na d’auko baf nazo na tare ruwan,kaya na dauka na bacci na saka da hula harda socks don wani irin sanyi nakeji har cikin k’ashina sallaya na shinfida na Tada sallah mangariba da Isha nayi shafa’i da wutire ,

blanket na dauko nahau gadon na lullubu abina na kwanta da wani irin ciwon Kai da zazzabi nakeji gashi kafafuna sai zuge suke mini nama rasa meke mini Dadi 

Al’ameen suna tafiya da Khadija Chan dai Khadija ta kasa hakuri tace ,Yaya nikam na tambaye ka Mana?

Allah yasa na sani dija,

Kai Yaya ni banason dijan nan ai sunan tsofine,

Toh hadixa Ina jinki,

Habba yaya ta fada tana hada fuska,

Sorry toh kanwata Ina jinki

Yauwa Yaya nikam Aina ka hadu da Aunty Sumayyan ne harkace kana Sonta?

….Dam dam haka gabansa ke bugawa , Khadija meyasa Kika mini wannan tambayar,?

Ba kome Yaya kawai na tambaye Kane ,

Ah ah Khadija fad’amin gaskiya nasan baki tambayar Abu banza,

Am Yaya Naga baka taba bani lbrn kana da budurwa ba kawai sai naji Wai kayi aure za’a kawo Amarya,

Toh Khadija ke abokina ne da saina fada Miki Ina da budurwa,

 auren Kuma yazone a bazata ban dauka iyayen ta zasu bani ita lokaci d’aya ba, 

Amma yaya kaga gidansu aunty kuwa Mai azaban kyau ga Yan gayu k’yawawa  a gidan Kuma Aunty ma kyakkyawa fa Yaya toh ma  Ina kake zuwa daga Tashar kayan marmari sai wajen sana’ar ka Ina kaga aunty har kuka fara soyayya?

Ikon Allah Khadija Wai tambayar nan Kam na lfy kin sani a gaba da tambaya sai kace wani sa’anki ,

Kayi hakuri Yaya dai dai lokacin suna iso kofar gidan Goggo Amina,

Muje Khadija na rakaki cikin gidan nama Goggo bayanin dalilin yin darenki ,

Toh Yaya ,

shiga sukayi cikin gidan tare,

Goggo Amina ce ta amsa sallaman tasu tana fama da icce a runfar girkin ta

Isa sukayi ya gaishe da ta Yamata bayanin dalilin yin Daren Khadija,..

Wallahih Muhammad Nima sai da na tura yaro yajimin lfy Khadija har dare Bata dawo ba ga aikin dare da tace zata dawo ta Kama mini, ya dawo yace min ba kowa a shashen ku,

Kiyi hakuri Goggo, Basu dawo ba sai yanzun Al’ameen yace Yana mike wa,

Ba kome muhammad  shine ka tasata a gaba a ruwan nan Maimakon ku bare Sai ya tsakaita,

Goggo Nima haka nace Mata Amma tace Zaki Mata Holo itakam sai gidan Goggo shine na rakota

Gggo ruwan da yawansa bansan karfe nawa zai dauke ba  shiyasa nace gwara na dawo

 

Hakane Kam  da gaskiyar ki Khadija

Toh sai da safe, Goggo

Allah bamu alkhari

Ameen suka amsa ita da Khadija shikam fita yayi ya Kama  hanyar gida,

Ina kwance Amma ba bacci nake ba tunani kawai na fada  nayi zugum gabaki daya gari yamin zafi,

daidai lokacin ya shigo kofar duk ya jike Daman jallabiya ne a jikinsa ,,

 hauro wa dakalin  Yayi ya zare jallabiyar sa ya aje a cikin boket in wanka dakin ya shigo daga shi Sai gajirin wando, da sallama a bakinsa

Ina kwance cikin duhu don na kashe hasken wayana naji buruntu ana kokarin shigowa dakin  don ni Sam banji sallamar ba, hasken wayata na kunna me Zan gani yayan Khadija ba Kaya, murd’adden damtsen hannunsa naci Karo a waje ga fafad’an kirjinsa mai cike da yalwan gashi,baki sitik kwance akan farar fatarsa kafarsa farare tas sai gashi ke kwance a lallausar fatar kafar tasa ai bansan lokacin da na k’wala ihu ba na dirko a saman gadon,na Kama hanyar waje don ni sai ma gani nake kamar ba wando a jikinsa don ajike wandon yake tsabar birkita hanyar kofa na nufa zanfita na bar Masa dakin,

Jin ihunta sai ya birkitasa ya dauka Koh wani abune ya sameta Jin ihun take  akai akai hakan yasa ya gigice shima ya fara neman hanyar kofa cikin lalube,da D’an saurin sa Jin itama kofar ta nufo tana  ihu har lokacin,

Ji kake gauuuu! sun garu da juna a kofa daga shi har ita ihu suka saka a tare, sai kawai suka kuma zubuwa ji kake timmmmmmm…………

 *Gobe Monday Ina da jarabawa bazakuga update ba fan’s* πŸƒβ€β™€οΈ

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧     

Page1️⃣8️⃣&1️⃣9️⃣

Washhhh yace jinsa a k’asan cafet  ya zube,Bai farga ba Yana kokarin mikewa, yaji ta Fad’i a kansa  daga shi har ita Kara suka saka sai Kuma sukayi shuru tare,

 ido na ware jina a jikinsa cikin rawan jiki duk na rikice na fara chuku chukun mikewa naji yasa hannu ya zagaye hips ina,

 sosai ya kara matsota kusa dashi,

“Kai me haka” ? Ka sakeni Mana, Mena rike min……..sai Kuma tayi shuru ta kasa karasawa, 

Cikin sanyin halinsa ga jikinsa na wani irin rawa Jin mace a jikinsa a karon farko a tarihin rayuwar sa kenan, yaji mace a kwance a jikinsa, Mena rike Miki? Ya tambaye ta Yana yawo da fuskarsa a kafadar ta Yana neman fuskarta, so yake ya Hada fuskar ta da tasa,

“Wai ma Ina ruwanka ne don Allah nikam sakeni haii”   nace cikin ihu 

Jin muryarta hakan ya tabbatar Masa da inda saitin fuskarta yake hada fuskar yayi da tasa har suna Jin numfashin juna,

“Wai menene haka bazaka sak”………bai bare na karasaba naji saukan lips nashi masu uban dume akan nawa lips in wani abu naji ya tsargar Mini daga tsakar kaina har farcen kafana cikin wani irin birkita na yunkura zanbar jikinsa zan mike ji kawai tayi ya fisgoni gabaki d’ayana na  zube Akansa ,

cikin wani irin zafin nama da kuzari ya cafke lallausan bakinta cikin nasa da wani irin zafi zafi yake tsotsarta  Jin sai k’okarin mikewa take a jikinsa yasa kafa ya harde kafarta da nasa kafar,daga ita harshe rawa jikinsu yake,

Tashin hankali da nake ciki ba’a saka Masa Rana kuka nake so nayi Amma ba Hali hawayene kawai kebin kumatuna,

Jin saukar hawayenta akan face nasa ya saka sa sassauta Mata riko a hankali ya zame bakinsa cikin nata,

Ai da wani irin azabebben sauri na mike  tsalle D’aya  nayi na fita a d’akin na tsaya a baranda duk sanyi da ake da ruwanda ake zugawa na g’wammaci na kwana a waje Data kwana a d’akin nan inaaaaa, 

Sumayya!!! Sumayya!!! yake kiranta cikin tsarkewar murya shima ya mike Yana lalube ya fitoh wajen,

 ganinsa ya sakani zabura Amma tunawa da nayi baya gani yasa na tsaya naki Koh motse kirki Ina jinsa sai kirana yake Yana lulube na a baranda in yazo lalubar Gefen da nake saina matsa a hankali na koma inda ya laluba,jikina nata rawa,

Jin baijita ba don karfin ruwanda ake Bai bare yaji Koh D’an motsen taba don ruwa ake harda tsawa,sauka yayi a baranda yanakan lalube,

 ruwa na dukansa Yana zaga kofar Amma Bai jita ba har kofar shashen ya taba Jin kofar a rufe yasa ya gane Bata fita a kofar ba,

Don Allah Sumayya ki kulani Koh zanji hankali na ya kwanta don nasan kina jina kina ganina,

Wani irin tausayin sa naji ya kamani ,cikin sanyin jiki da fargaba nace “ganinan anan,”

Ai da hanzarinsa ya nufi barandan jikinsa ya jike jakaf da ruwa haryana diga ga gashin kansa da gemunsa duk ya jike ya k’wanta   g’wanin sha’awa ,

Da hanzari ya iso wajen ta cikin rawan murya ya fara magana, Sumayya pls mu koma d’aki kinji,

“Nidai yau bazan k’wana da kaiba a d’aki D’aya ba “nace Ina kuka Kamar karaman yarinya,

Kiye hakuri kinji Sumayya muje mu k’wanta Allah bazan miki kome ba kinji Koh,

“Wallahih nidai bazan shigaba” Ina fada Ina kuka, ganin Yana matsowa kusa Dani yasa na k’wala Kara Zan ruga cikin ruwa naji anyi sama Dani,

D’aukarta yayi duk yanda take kuke kukenta kin kulata yayi sai ihu take tana ya sauke ta, sosai ya riketa Gam a kirjinsa Yana lalube har suka shiga dakin ya tura kofar da hannunsa d’aya d’ayan na rike da ita  ,

A hankali yake lalube harya Iso bakin gado a hankali ya haura saman gadon kwantar da ita yayi a hankali ya lalube blanket inta ya rufa Mata ,ya sauka Akan gadon cikin lalube ya shiga neman Ghana must go in kayansa wani jallabiyan ya dauka a wanke tas ya zura ya zame jikekken gajeren wandon sa,

lalube yayi ya fita waje a aje a cikin kayansa jikakko daya aje a boket,

Nikam tunda ya saukeni a Kan gadon jikina yake ta rawa sosai naji wani irin tsoron Daren nan, zazzabinane ya  Tashi sosai nakejin kaina na Sara mini yau tension Yama kaina yawa,

Dawowa yayi Kan kujira zai k’wanta Amma yaji baho a saitin wajen, lalubawa yayi yaji kujiran a jike hakan ya tabbatar Masa lalai yo-yo wajin ya ke  filon kujiran da yake k’wanciya dashi ya dauka ya lalube cafet ya aje ya k’wanta a kasan dakin wani irin sanyi ne ke shigar sa don a lokacin baiki ya samu abin rufuwa ba Amma Bai dashi Kuma baida karfin gwuwar tambayar Sumayya tunda ba ita tayi niyar basa ba,

Jin motsen yayan Khadija yaki natsuwa sai jujuyawa yake ga atishawa akai akai alamudai murace ta kamasa,

Wayarda na wancakalar  dashi na dauka na haska inda nakejin motsen sa ganinsa nayi a kwance sai jujuyawa yake alamudai sanyi yakeji,

D’an tausayi ya bani sai Kuma na tuna lokacin da bani da lfy dashi da Yar uwarsa su sukayita d’awainiya Dani Amma yau shine na Bare a kwance a kasa ga sanyi,

ni Ina kwance a gado da bargo,

 Kamar bazanyi magana ba a hankali nace “,kazo ka kwanta a gadon kasan nan akwai sanyi Kuma naji Kamar mura nason kamaka”

A hankali ya mike ya Soma lalube harya Iso bakin gadon cikin nutsuwa ya haura dai dai ta bakin ya kwanta,

Nikam Ina karshen gado ta wajen jikin gini ganin Bai taba blanket in ba bare ya rufa, yasa na mike na dauko wani a whdrp na aje Masa a kansa na wuce filina na kwanta addu’ar bacci nayi na shafa na juya masa baya ,

Jin ta aje Masa blanket yasa she d’auka ya lulluba shima addu’ar bacci yayi ya lumshe idonsa Sam yaji bacci ya kaurace Masa wani irin yanayi yau ya tsinci kansa  a ciki,Mai ban Al’ajabi

Daga shi harni Babu Wanda ya rintsa har 1:00 na dare kafun bacci ya dauke ni shikam bansan lokacin da yayi bacci ba,

*********

Yaukam dagani harshe sai kusan 6 mukayi sallan asuba a dadafe dukan mu biyu da ciwo Muka kwana ga yunwa don tun karyawan safe dagani harshe bamu sake saka kome a bakin mu ba,

muna idarwa gado Muka koma muka sake k’wanciya don baccine ya cika Mana ido na rashin Yi da wure jiya,

Jin Yana matsowa kusa Dani yasani matsawa da sauri ji kawai nayi ya mike zaune ya zura hannunsa ta saitin da nake ya jawoni duka jikinsa a hankali ya koma ya kwanta Dani a jikinsa ,

Yanzun Kam ban neme k’wace jikina  ba saboda zazzabinda nake fama dashi ma ya isheni,

A hankali nace Masa”Wai meke damunka ne tun jiya kake ta tabani”?

Nima ban sani ba haka kawai nakejin inason kusanci dake,ya fada da muryarsa da ta dishe  don mura kamasa Tay sosai ga fuska jazur kamar ka taba jini ya zuba,

Kala bance Masa ba don ni jikina ne ya dameni,shuru mukaye gabaki d’ayan mu har bacci ya dauke mu a haka,

 sallama nake ji kamar muryar Khadija sama sama cikin bacci sai Kuma naji yayan Khadija na zame jikinsa a nawa,

Bude ido nayi Wanda nakejin nauyinsa sosai ga xaxxabi,

Khadija Kam ganin takalmin Aunty da na yayanta a bakin dakali yasa ta juya zata fita Amma dai tana mamakin har 10:10 na safe yayan ta Bai fita ba,

Mikewa Al’ameen yayi ya fita a d’akin Jin alamun Mai sallamar na kokarin fita a shashen Kuma ya shaide muryar Khadija ne,

Waalaikumu salam Khadija ya kina komawa kuma?

La Yaya Daman nace bara nazo na duba Aunty jiya kafarta tun a hanya ya kumbura Amma dai ba kome anjima Zan dawo,

Saboda me?

Naga baku tashi ba Yaya,

Ah ah ai gwarama da kikazo Nima Yanzun nakeson fita na nemi yaro ya kiramin ke,

Lafiya Kam Koh? Naga fuskarka ta kumbura tayi ja ga murya a dishe Daman Saida na tuna haka wallahih ruwan jiyan nan ya kare a kanka,

Ai bani kadai bane Khadija Aunty kima ba lfy  ,

Subhanallah meke damunta Hala kafar ke ciwo,?

Ah ah Khadija zazzabine,

Meya faru da kafartan ne da kike ta cewa Yana ciwo,?

Ba kome kasan jiya bamu samu Keke da wure ba Koh?da kafa Muka ringa takawa,

Uhmm lallai fa,yace Yana dafe kansa dake Sara Masa,

Sannu yaya kanne?

Wallahih Khadija,

Toh kaje ka kwanta Mana bara na gyara kofar,

Khadija Aunty ki tun karyawan jiya bataci kome ba zoki karbi D’arin nan ki sai Madara 50 da bornvite 50 akwai sugar n jiya da safiya da Lipton ki hada Mata tie Koh zata iyya Sha?

Toh Yaya Kaifa,

Khadija hada Mata kawai taima kayan shayen bazai Isa ba?

Zai Isa Yaya,

Toh shikinan ki hada hardani

Toh  

D’akin ya shiga yadau kudin ya mikowa Khadija ya dawo ya kwanta, tare da matsowa kusa dani

Nidai Ina jinsu shuru kawai nayi,

10:30 Khadija ta dafa Mana shaye harda k’wai  ta soya dayake jiya yasai kayan Miya na dare yazo ya samu bamu dawo ba,

Tana Gama shirya kayan Karin ta nufi dakin,

A bakin kofa ta tsaya tana sallama Bata shigo ba ,

Mikewa yayi ya zauna a bakin gadon ya sauke fararen kafarsa a kasan cafet,amsa Mata yayi hade da Bata izzinin ta shigo, Khadija ki shigo mana,yace Jin Taki shiga,

Da sallama a bakinta ta shigo d’akin aje kayan hannunta tayi akan cafet,zata juya,

Khadija d’auki baf in Kan kujiran nan kikai waje kizo ki jona fanka naji Kamar an kawo NEPA  ki juyashi saitin kujiran samun ya bushe,

Toh Yaya tace tana daukan baf in tayi waje dashi zubar da ruwan tayi ,

Ta dauki tsintsiya ta shigo dakin tire in kayan karyawan ta dauka ta daura akan kujiran ta share dakin,

  fanka ta kunna ta matso dashi Kusa da kujiran,Kamar yanda yace

Turarukan UMSAD INCENSE da ta Gani a jere akan mirror ta d’auka na d’aki jona kaskun lantarki tayi  Aiko take dakin ya dauki kamshi Mai Dadi (kowa yasan yanda Turaren wuta yake da kamshi a d’aki especially a damuna),

Khadija na fita ya matsoni a hankali hannu yasa Yana laluba ta nikam sai matsawa nake duk inda naga hannunsa zai taba saina matsa agun,.

Don Allah Sumayya ki tsaya Mana kaina ciwo yake wallahih Koh motsasa bana sonyi kina ta bani wahala yace Yana dafe Kan,

Toh ni sai ka min magana da hannune bazaka mini da baki ba saikayita tabani,

Sorry tashi kije ki wanke bakinki ga breakfast Khadija ta hada Mana yace Yana kwanciya,

Toh Kaifa bazaka wanke bakin bane kake k’wanciya sai yayi ware? nace Masa Babu alamar Wasa,

Murmushi yayi har fararen hakoransa masu tsananin kyau suka bayyana,ai kinfi kowa sanin bakina nada ware Koh babu tunda kin d’and’ana jiya , ya fada muryarsa a shake

Ohon maka dai nace cikin Jin haushi mikewa nayi a hankali na nufi kofa shima mikewar yayi yabi bayana ,

Kofata nabi da kallo tasss Khadija ta share samunta ma nayi tana wanke wanke ga kayan na data cicire a igiya ta zuba a boket,

Khadija kibar d’aurayan nan  don Allah daga kin wanke Kwanukan nan ya Isa haka ke baki gajiya da aikine,

Toh aunty tace mini,

Wanke baki mukayi muka koma daki abincin na jawo Mana ganin hadamu tayi plate d’aya tie ne kawai kowa da cup nashi,

,k’wala Mata Kira nayi”Khadija Khadija”

Na’am Aunty ganinan zuwa,, tace

Tana shigowa dakin 

“Jiki  d’auko wani cup da plate”toh tace ta fita sai gata ta dawo dasu

  Ajjyemin tayi zata fita,

“Tsaya Khadija”  nace  zuba Mata tie nayi na ibi k’wai  data soya Mana NASA Mata a plate itama” d’auka kije kici nasan dafawa kikayi baki ibi naki ba Khadija kullum Ina gayamiki in kin girka Abu ki ringa zuba rabonki kinji Koh kin manta nan ma gidanku ne”?

Toh Aunty tace tana karban plate da cup in tayi waje,

Bismillah na Masa ya matso yasa hannu kad’an naci,naji ya isheni don bakina ba Dadi sam tie kawai nashanye duka, Koh aje cup banyi ba wani irin amai ya tasar mini da gudu na fita waje na ringa shika Amain sosai,

Mikewa yayi yabi bayana daga shi har Khadija sai sannu sake mini Mika min ruwa tayi na wanke bakina na koma d’aki

 duk k’wanciya Muka sake don shima bazai iyya fita wajen sana’a ba,

Misalin karfe d’aya na Rana ana kiraye kirayen sallah azahar ya mike ya fita, wanka yayi a dadafe ya nufi waje zaije chemist in  jambusko Koh zai basa bashin  magani Koh iyya  Sumayya kawai ma in zai samu a Bata ya gode Allah duk da yasan halin inyamurin daker ya ya basa bashi,

Yana fita Nima mikewa nayi Ina Jin jiri jiri na fitoh waje Jin ana kiraye kirayen sallah Khadija na samu ta wanke Mana kayan mu daya jike jiya,tana kitchen wani aikin Kuma take,

“Khadija Wai me yasa bakiji ne nace Miki kibar aikin haka ” 

“Ke kullum kikazo guna baki abinyi sai aiki”

Toh Aunty in ban Miki ba wazan ma ba lfy bane dake ga kofa kasha kasha Koh  abincin da zakuci bazaki iyya girkawa ba toh Aunty in ban muku ba wazai muku

A gaskiya bansan dame Zan sakawa Khadija ba Allah ne kawai xai biyata 

Nagode Khadija Allah ya barmu tare ya nuna mini auren ki in ban mutuba,hhhhhh nace Ina dariya

Kai Aunty tace tana rufe fuska Wai kunya,

Yana fita gida massalaci ya shiga ana idar da Sallah yanufi chemist in jambusko,

Yana Isa sanin ba musulmi bane yasa ya ce Masa , excuse,?

Yes wanene?

Nine jambusko,ya basa amsa Dayake inyamurin ya Dad’e a Jala yanajin hausa sosai ,

Wai MAKAHO Kaine anan yau kuma?

Eh wallahih madam ce ba lfy zazzabi ke damunta……..

Bai bare ya karasa bama ya ce kaima ai harda Kai bakaga muryarka ba ga fuska yayi ja ido ya kumbura,kana mura,

Eh harda ciwon kaima shiyasa nazo wajen ka ka taimaka kaban bashi inna d’an ji sauki zuwa anjima zanfito in Allah yasa na samu kasuwa saina biyaka, ya fada cikin zullumi don shi kansa Allah ya gani kwata kwata bayason roko Koh bashi Amma ya zaiyi bazai iyya zuba ido Yar mutane ba lfy ya barta haka na shi Karan kansa Saida lfyr zai nema musu abinci

Heeeee chinekeeeee gaskiya MAKAHO nii………..

 *Gaisuwa na musamman gareki ummee zariya Naga special comments naki Kuma  Nima na yaba Miki sosai naji dadi* πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincenseIG @umsadincense     08084453785IG @umsadincenseIG πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧

Page2️⃣2️⃣&2️⃣3️⃣ 

Yau da Matata Zan kwana gaskiya

Da mamaki nake kallonsa”waye matarka”?

Ga tanan ya fada Yana kwanciya Da ita a jikinsa 

“Wai menene haka ka matseni fa” nace Ina kukarin tashi a jikinsa

Fuska ta ya hada da tasa fuskar har hancin su na gogan na juna,

Karan in TV nan Kam kyakkyawa ne shiyasa yake burgeki?

Ikon Allah yanzun Kam na gane inda mutumin nan ya dosa, maganan Karan innan ya damesa”mummuna ne kamar Kai”na basa amsa,har lokacin Ina kwance a jikinsa don karfe ya saka mini sosai

Murmushi yayi a hankali yake goga Mata gashin gemunsa  a Gefen fuskarta

Wani  Abu nakeji sosai  a tare dani”Kai me haka”?

“Kana goga mini gonan ciyawa a fuskata Koh so kake ya garceni ni” 

Kinji Dadi kenan?

Kuma ni ba mummuna bane sai dai kece mummuna

Hhhh shap ai in fada maka “Kai mummuna ne sosai gaka bak’i,gajere, Mai guntun hanci, ga tumbi”

Wannan Karo Kam dariya ya kamayi don sosai yake cikin nishadi, ganin ya samu abokiyar Hira 

Farine ni, Kuma hancina dogone Ina da ido bakina irin na khadijata fuskata dogone  Mai dauke da gashin gemu Mai yawa haka na kaima, akwai tabon sallah a goshina,ya Bata Amsa yana Kai hannunsa kanta ya zame hularda ta saka a hankali ya Kama gashinta da khadija ta kitsa Mata har gadon baya,

Da Ina Tara gashi sai yafi naki yawa

“Kutt wallahih bazaifi ba duk ma Wanda ya farfada maka haka kamannin ka yake  kawai zaginka yayi Amma ba wani yanda na fadan nan dai haka kake”

Dariya kawai yayi sai Kuma yace,

Da ace ban taba ganin kaina a madubi ba dayau kinyi Dani don d’auka zanyi da gaske hakan nake

“Au Daman ka taba kallone kafun ka makance”?

Shikarata 18 na zama MAKAHO Kinga ai zuwa yanzun kamannin Bai sauyaba

“Ya sauya kam gashi harda tumbi kayi”na fada Ina murmushi haka kawai na tsinci kaina cikin farin ciki yau na samu abokin Hira Wanda rabon da nayi harna manta sai in khadija tazo

Cikin hanzari ya birkitota zuwa kasa shi kuma ya koma Saman ta,

Zaro ido nayi cikin Al’ajabi da tsoro bakina har rawa yake”yayan khadija me haka wayyo kirjina nauyi ka d’agani”

Ina da tumbi Koh Babu kinsan ba gani nake ba shiyasa na saka Miki tumbin don kiji akwai Koh Babu

“Wayyo Allah cikina kirjina nauyi ka sauka a kaina wallahih baka da tumbi washhhh numfashina xai d’auke”

Jin yanda duk tabi ta gigice yasa a hankali ya d’aga nauyinsa akanta Amma Bai sauka ba,

“Ashhhhh toh ka sauka a kaina Mana”

Shuru yayi yaki magana yanajin ta sai masifa take, ya sauka a kanta ya Mata banza don yanzun Sam baicika Jin shakkarta ba Kamar da

“Ina Jin fitsari”

Yayi shuru don yasan ba fitsarin zatayi ba muddin ya saketa guduwa zatayi

“Koh bakaji bane, ya matseni fa”

Kiyi anan kawai, ya Bata Amsa

Ganin ya manna mini hauka yasa nayi shuru ganin da gaske fa ba sauka zaiyi a kaina ba bare akan gadon,ganin baida niyar yimin kome yasa hankali na ya kwanta har kusan 1 na dare idanun mu biyu daga karshe dai bacci barawo yayi gaba Dani,

Jin saukar numfashin ta ya tabbata tayi bacci a hankali shima ya ringajin bacci na d’aukarsa zamewa yayi ya kwanta a gefe ya dagota ya d’aurata a kansa ya lumshe idanunsa har yaji babushi,

Kiran farko na Assalatu shiya sauka akan kunne na a hankali na bude idanuna na,masu cike da bacci jina ajikin mutum yasani tunawa Ashe fa jiya tare muka kwanta zame jikina nayi a hankali Zan mike

Jin tana zame jikinta a nashe ya sakasa bude ido sai alokacin yaji Kiran sallah ake

Daga ni harshe waje mukayi na ibi ruwa a buta na aje Masa”ga ruwan Alwala kar a shiga sallah baka Kama Alwala ba ka rasa jam’i”Na fad’a Wai karya tuna wani abu, don yau na iba Masa ruwan Alwala

Butan ya d’auka Alwala yayi ya tafi massalaci sai tunanin abinda zasu karya yake baida Koh sisi Kuma inya bude Mangoro da safe ma ba ciniki yake ba kwana biyu nan,   amfiya D’an Saya da rana Koh yamma

Alwala nayi na shiga d’aki,

 Ina iddar da sallah na kwanta a Kan sallayan don harga Allah bacci nakeji jiya ban kwanta da wure ba

Gida ya shigo don ya rasa mafita Sam baisan me zayi ba,a Ina zai samo musu na karyawa tsoro yake kar hakurin Ta ya Kare wata Rana ta guje sa, da sallama ya shigo d’akin Jin Bata amsa ba yasa ya fara laluben ta akan gado Amma Bai jita ba ya sauka Yanata tattaba kujira a tunaninsa Koh tana jinsa kin amsawa tayi, 

Sumayya!! Sumayya!! ya kirata baki biyu Amma shuru,hankalin sa a tashe ya shiga tattaba kome na d’akin Yana nemanta hardai yajita a kwance akasan cafet,sosai hankalinsa ya kwanta shi Karan kansa ya rasa meke damunsa akan Sumayya Sam baida jarumta akan lamarin ta, Koh  don ta kasance mutum na farko dake da kusanci dashi a duniyarsa ta yanzun ne oho,hannu yasa a hankali ya cicibeta Yana lalube harya Isa bakin gado kwantar da ita yayi,ya fita waje,boket ya d’auko ruwa ya ringa ja a rijiya harya cika Randa ya wanke kwanuka harda shara yayi Amma dai sharan Koh na yara albarka saboda kwata kwata batayi kyau ba (sharan Mara ido)

Yana Gamawa d’akin ya shigo  da lalube ya isa Kan gadon Hawa yayi,hannu yasa ya fara tataba ta Yana neman fuskarta har hannunsa ya sauka akan kirjinta 

Waro ido nayi Ina kallonsa Jin yaki cire hannunsa a kirjina yasa na buge hannun”me haka don Allah”?

Da nayi me?ya sake tambayar ta

“Ai kafini sani waima menene kake ta faman laluba ta  Ina bacci”

Nidai bansan kome ba tunda ba gani nake ba nadai San na taba Abu mai laushi Amma bansan kome Nene ba,ya Bata Amsa

Lallai mutumin nan ya Raina mini wayo ai Koh Bai taba kallo ba a rayuwar sa yasan meya taba bare harya Kai 18 Yana kallo,jin rainin wayone ma ban sake magana ba

Kin tashi lfy?

“Lafiya Alhamdulillah”

Uhmm Sumayya Zan fita, Koh zan samu na karyawa anjima Zan dawa insha Allah ban kwana da kudi ba

“Sai ka dawo” nace Masa Ina sauka a Kan gadon don wallahih yunwa nakeji ba kadan ba

Allah ya yasa,Yace Yana  fita a d’akin harya bude kofar shashen zai fita yaji Sumayya na kiransa tsayawa yayi 

“Am Daman nace in ka fita pls ka tura yaro ya kiramin khadija”Ina magana Ina bin kofar da kallo da mamaki 

Toh,yace mini zai juya

“Wai waye yayi aikin nan duka haka”?na fada Ina murmushi ganin sharan Kamar wata yarinya Yar 3 ce tayi 

Nine na Miki aiki yau dai ki huta

“Aiko naji Dadi na” nace Masa don na gane so yake ya burgeni 😌

Da gaske?ya tambaye ta

“Sosai ma,ka tafi Mana samun mu samu na karyawan ka tsaya surutu yanzun ana neman 8:10 na safe”

Ok.toh sai na dawo

“Yauwa”

Yana fita a kofar gida ya aiki yaro gidan Goggo Amina ya Kira Khadija

Nikam tsintsiya na d’auka na sake share kofar na gyara d’aki sosai kwana biyu nan. Nake jina a sake sosai 

Khadija ce ta shigo bakinta dauke da sallama,

Assalamu alaikum

“Waalaikumu salam”khadin Goggo

Kai Aunty ni banso sunan fa nasan a bakin Yaya kikaji duk shike Bata mini suna

“Toh khadin Yaya”

Aunty ai khadin ne banaso

“Toh khadija shikenan”?

Eh Aunty Ina kwana ?

“Lafiya khadija ya goggo”

Lafiya Alhamdulillah,tace tana zama a bakin dakali

“Wai ni khadija ya Fulani Dance in dai su kawayen Amarya jiya an rabashe kenan”?

Shuru tayi sai Kuma Naga hawaye ya cika idanunta..

Da mamaki nake kallonta “Khadija me ya faru kuma daga tambaya sai kuka wani abin na Miki”?

Aunty don Allah nida yayana muna da wani abin kyemane a jikin mu, da mutane ke wulakanta mu Koh saboda mun kasance Marayu ne, Koh Kuma don Yaya baya kallo ne, ta fada tana fashewa da kuka

“Subhanallah khadija meyasa Kika Fadin irin wannan kalaman haka”

Dole na fada Aunty kaf unguwan nan yayana baida aboki Sam ba Wanda keson rabarsa gani ake Kamar Inka jashi a jiki zai zama maka kaya, Amma wallahih Aunty yayana baida zuciyan kwad’ayi kullun so yake yaga ya neme na kansa Amma duk da haka in Kinga yayana na Hira toh ta miskinai ne irinsa Amma bayansu ba Mai son Koh Hira da yaya, shiyasa har kullum nake mamakin auren ki,

Ni Karan kaina mujiyace a cikin kawaye, me laifin mu aunty mu muka d’aurawa Kan mu Talauci ne Koh akwai Wanda yafi karfin maraici ne?

“Gaskiya Babu khadija Amma meya faru ne haka”?

Na tambaye ta idanuna na cika da hawaye tabbas khadija Allah ne ya tsare ta a irin zamanin da muke cikin nan yanda Yan Mata suka baci da son kyelekyele Amma ita ta kauda fuska ta cire buri a ranta ta zauna a matsayin da Allah ya d’aurata,samun irin khadija kalilan ne a yanzun yarinya Mai hakuri

Aunty Kinga wulakancin da kawayen Amarya suka mini jiya a wajen bikin nan? ta fada tana kuka

“Ah ah khadija me suka Miki”

Aunty’ Wai daga zuwana naje na tsaya agun da kawaye ke tsaye kawai Ina zuwa suka mimmike suka  koma wani wajen  Wai kunya suke kar abokan ango suganni a cikin kawaye za’a Raina class nasu,kinsan ma Aunty me yafi Bata mini Rai?

“Ah ah khadija”

Wai Aunty danaga duk sun watse saina koma cikin mutane na tsaya kawai kowa na tsaya kusa dashe sai ya Kama matsawa Wai kar ace tare Dani yazo, don ban saka kayan Fulani ba koma banyi ado ba

Sosai naji wani irin haushi kamar zai kashe ni

Aunty bazan sake zuwa bikin kowa ba daga yau

“Yau me za’a yi”?

Kamu,ta bani Amsa

“Zaki je bikin nan khadija har a Gama dake za’a Gama insha Allah”

Aunty ni bazan sake zuwa ba a wulakanta ni,don Yaya yace Koh mutun baida kudi in dai ya rike mutuncin sa bazai wulakanta ba

“Ki kwantar da hankalinki insha Allah bazasu sake wulakanta kiba” na fada Ina Mai Jin tausayin baiwar Allah nan

D’aki na shiga na barta tana kuka akwatina na bude Kaya na d’auka Atamfa da les masu azaban kyau a dinke sai Turare na d’auka guda D’aya na fitoh a d’akin dasu a hannuna 

“Khadija rike kayan nan Naga kamar akwai tailoli a tsallaken titi ki Kai musu wa’innan kayan su rage Miki yayi daidan ki yanzun in Kika fita,

wannan Turare Kuma kasuwa nakeso ki Kai shagunan masu Turare Koh zasu Saya kudin sa 20k ne Amma Koh 10k Kika samu Koh kasa dashe ki karba kawai”

Aunty ba Yaya yace ki daina Saida kayanki ba?

“Khadija Zan zauna da yunwa ne Ina da abinda Zan tsayar naci a cikina sai na zauna”

Gaskiya ne Aunty Amma fa Yan kasuwa bazasu Saya ba don yanzun Suma tsoron sayan kayan hannu suke karsu Saya na sata,sai dai akwai wata Mata dillaliya ta bayan kasuwa sai na Kai Mata don ance itakam Koh kayan satane Saya take don Yar rikici ce sosai

“Yauwa khadija Allah yasa ta Saya wannan kayan in kin fita ki fara kaisu shagunan dinki”

Aunty wazaki bawa kayan Kuma ai Naga daidan kine naji kince a maidashe daidai na?

“Ina ruwan Ki,nidai tashi kije mini aika na,

 sannan in ta Saya Turaren ki shiga kasuwa ki sai Gam bak’i Mai kyau ki hada da Turaren lalle,sajan,tsamiyan kanti, ki sai bakin lalle guda biyu shima”

Aunty lalle zakije ne?

“Kai Khadija banson tambaya ki sai mini kayan Miya duka,in kin dawo ki biya tailan kudinsa ki karbi kayan Saiki saimin doya soyayye  a bakin titi na karya”

Toh Aunty tace ta karbi kayan tasa a laida ta fita

D’aki na shiga Ina ta tunanin halin rayuwa da khadija ke ciki

Sai karfe 10 khadija ta dawo kayan na bubbude na Bata ta gwada Aiko yayi Mata daidai jikinta sosai kayan ya karbe ta,doyan na bude Mana mukaci tare

Kam in na manna a tire na kwaba Jan lalle, “khadija zoki zauna na Miki lalle”nace  Mata Ina zama akan dakali

Aunty Daman ni Zaki ma lallen ne har Kika Saida Turaren ki Mai tsada a naira 5k?

“Khadija bazan d’auki wulakanci ba Sam insha Allah yau saikin fi Amaryar kyau bama kawayen ba” 

Daman kin iyya lalle ne Aunty?ta fada tana zama

“Sosai ma khadija ai lokacin da nake primary school innaje makaranta sai nayita zana flower lalle a takanda na Inna dawo gida sai ummie na tace zata buge ni sai abie ya k’waceni  yace bazata bugeni ba ai batasan Koh baiwar da Allah ya mini ba kenan,

sai ya sai mini takkadar lalle daban duk lokacin da zanyi Zane saina dawo makaranta sai ya bani takardar na zana, lokacin da na Gama primary sai ya sai k’wallon dayes ya baiwa Mai aikin mu ta dafa mini da lalle,sai nayi mole na zuba a ciki,abie ke saimin hydrogen Ina ma yaran gidan mu lalle harda yaran makwanta,

harna girma Ina lalle duk yaran gidan mu da aka aurar Mata Ninake musu lallen aure da make-up haka kawaye na da Yan unguwan mu sosai nake Alfahari da lalle khadija”nace Ina manna Mata Gam a gafa

Kenan Aunty kina sana’an lalle da kwalliya?

“Ban taba yin lalle kudi ba Koh make-up khadija don ba abinda na nema na rasa a rayuwa a lokacin”

Allah sarki, tace 

Lalle na tsarawa khadija sosai bak’i da ja sai bayan azahar Muka Gama, tunda nake da khadija ban taba ganin farin cikin  Dana gani a lokacin da na Gama Mata lalle ba bini bini saita duba lallen tayi murmushi

“Wai nikam khadija baki taba lalle bane”

Aunty Kenan Koh a sallah bana lallle in Kinga nayi lalle toh gaggo ne ta mini yabe

“Toh yaukam kinyi design na flower”nace Ina mikewa

 sallah Mukayi kafun Muka girka abincin Rana har lokacin yayan Khadija Bai dawo ba,

Sai biyu da rabi na Gama abinci zuba Mana nayi mukaci har lokacin fuskar khadija na d’auke da murmushi 

***Nima sai naji Ina cikin farin ciki ganinta tana walwala

“Khadija ga abincin yayanki kikai Masa”

Toh Aunty ta d’auki kulan tana kukarin fita,”yauwa khadija in kinje ki dawo da wure samun mu fara make-up in da wure”

Toh Aunty nagode,tace tana fita,cikin farin ciki duk Wanda ya ganta yau yasan Bata da wata damuwa

Tun daga nesa ta hango yayanta a zaune g’wanin tausayi sai zufa yake…………….

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧     

Page2️⃣4️⃣&2️⃣5️⃣   

Karasawa tayi kusa dashi, Assalamu alaikum

Waalaikumu salam khadija

Na’am yaya, lfy Kam na ganka haka a zaune, a Rana gashi sai zufa kake

Lafiya khadija wallahih Ina cikin damuwa ne, tun safe na fita nabar Aunty ki Koh karyawa batayi ba gashi har ana neman la’asar banyi cinikin Koh biyar ba

Yaya gaskiya ya kamata ka shanja sana’a yanzun mangoro yayi a raha ba lallai bane kana cini ki sosai

Gaskiya ne khadija Nima Yanzun so nake na sare lemo in gwada na gani Amma bani da jarin,

Toh Yaya Allah dai ya Bud’a maka kaji kabar saka kanka a tunani kaje ka jawa kanka ciwo a banza

Allah yasa khadija

Yauwa gashe Aunty ta bani abinci na kawo maka

Abinci kuma?ai na ta samu kudi har taye cefene?

Ina Zan sani Yaya nidai data kirani saita aike ni kasuwa(ta Masa karya karyace Sumayya batajin maganar sa)

Koh dai kayanta ta sayar ne khadija?

Kai.yaya bana tunanin haka fa,ga abincin kaci pls kaji yayana sannan ka tashi a ranan nan ka koma Gefen shagon Haladu ka zauna

Toh khadija,yace   Yana karbar kulan da take hannunta, 

khadija Turaren wa Kika saka ne naji kina kamshi?

Hh wayyo yayana lalle ne Aunty ta mini, yanzun ma kwalliya zata mini Inna koma

Lalle Kuma khadija kuma yake kamshi?

Eh Yaya Turare aka saka sai aka kwaba dashi

Inta Miki kwalliyar Ina zakije?

Kamun Asma’u Mana Yaya ka manta

Ban manta ba sha’afa nayi khadija, Amma ya za’a yi bani da kudin machine in da Zan baki fa

Yaya za’a d’auke mu a mota gidansu Amarya,kasan yaufa zansha kyau,ta fada cikin farin ciki, zanje sai mu tafi tare…

Sai kin dawo Allah ya tsare mini ke kanwata,yace yanajin wani Annashuwa, kanwarsa na farin ciki Kuma Sumayya ce sanadi, gaskiya Sumayya Rahama ce Allah ya masa,daya basa ita

Ameen Yaya,tace tana tafiya

Bayan fitar khadija wanka nayi na chanja Kaya wando nasa da riga t-shirt   na kwanta akan kujira Ina jiranta,

Assalamu alaikum Aunty na dawo Aunty

“Waalaikumu salam khadija kiyi Alwala sai kizo mu fara make-up in Kinga Koh an Kira Sallah sai kiye kawai”

Toh Aunty, tace tana iban ruwa  Alwala tayi ta shigo d’akin 

Make-up kit nawa dana aje a cikin drawer na d’auko budesa nayi babbane ba abinda babu na make-up a ciki,zama nayi na tsarawa khadija makeover,

Kai Masha Allah duk Wanda yaga khadija mundin ba mugun sani ya Mata ba bazai taba zato Koh tsammanin ita bace heavy make-up na Mata irin na Amare, amaren ma sai agun dinner,”khadija muyi sallah sai kisa Kaya Koh”

Toh Aunty, tace sai murmushi take

Bayan mun iddar da sallah

Less in na Bata ta saka black ne Mai ratsin pink, gel na samata a gashi na d’aura Mata dankwali Mai ubansu,

sarka da d’ankunne warwaro, zube, na Bata dukansu golden colour,takalmi pink, gyale da purse black,Kai duk Wanda yaga khadija a yau Koh shakka bazaiyi ba zaice Amarya ce, Ina Gama shiryata

Tsayawa tayi tana kallon kanta a mirror, kamar taga abin tsoro, Innalilahih Aunty nice na koma haka? Aunty Kinga yanda na koma kamar ba ni ba,ta fada hawaye na cika Mata ido 

“Kece khadija ki share hawayen nan karya Bata Miki kwalliya kinji maza share”

Toh Aunty,tace tana goge hawayen ta

Wayata Kiran iPhone na d’auko”tsaya Khadija na Miki hoto”nace Ina gyara Mata gyelenta

Tsayawa tayi,Aunty ta ta Mata hotona harda video  sosai tayi kyau

“A Ina za’ayi kamun ne”?

A Taraba hotel ne,Wai ta hanyar government house

“Hhh ba Taraba hotel ba, Taraba motel ake cewa sannan Bata government house bane,hanyar ne Amma ta Amazon yake “

Au nikam Ina Zan sani Aunty ba zuwa nake ba, kawai nima naji jiya ana fad’ane

“Ga 200 ki hau machine kije kinji ki dawo da wure fa khadija karki Kai mangariba”na fada Ina Mika Mata kudin

Ki bare Aunty mota za’a kawo a gidansu amarya zai d’auke kawaye

“Aikam yau  a motar zaki,maza ki hanzarta Amma ki.karbi kudin Incase

Toh aunty sai na dawo,tace tana fita a d’akin 

“Toh khadija Allah ya dawo dake lfy”

Ameen, khadija na fita a kofar shashen yayanta, duk Yan gidan suna zaune a tsakar gida daga maza har Mata,ido suka bita dashe kureeeee suna mamakin bakuwar nan Sam tun safe suke zaune Amma basuga wucewar taba,baki a tsake suka bi khadija da ido harta fita,

Khadija Kam duk tabi ta tsargu don Sam tunda take da wayonta Bata taba kwalliya irin na yau ba har kofar gida ta fita duk masu shaguna suka bita da ido suna mamakin Wannan kyakkyawar meya shigo da ita gidan Adara,

Amma wasu basa mamaki in sun tuna MATAR MAKAHO fa Yar manya ce Kamar yanda aka saigunta musu, Kuma sun rasa dalilin auren nan Basu mamaki yake,mutum talaka miskini,a d’auki lafiyayye ya abasa Kuma Yar masu kudi,masu kudin ma zuriyan shugaba,abin nan na mugun Basu mamaki,Amma Basu da halin sani

Khadija Kam ganin ido caaaa akanta yasa ta ruga gida da gudu ta koma kofar Sumayya

“Kee khadija lfy meya faru Naga kin shigo kofa Koh sallama Babu Kamar an koroki”

Aunty duk inda na wuce bina fa ake da ido,ni gaskiya tsoro nake ji

“Kai khadija akwai wauta,don ana kallonki saiki kame jikinki ki nuna musu kauyanci,ai dakewa zakiye kici bom”

“Koh gun kamu kikaje neman kujira zakiyi ki zauna abinki karki kuskura kicewa kowa kome Wanda ya gaidake ki amsa Wanda Bai Miki magana ba karki Masa kinji”

Toh Aunty,tace tana fita

Sai yanzun Yan gidan suka gane ta cikin mamaki Iro yace,buran uba muna d irin wannan kayan a gida Amma ace har yanzun banyi aure ba aradun Allah Naga Mata

Kutumar ubanka iro D’an iska watoh kaga kasa ya rufe idon uwarka shine bare ka karya alkawarin da mukayi akan auren ka da salame,watoh munafurcine kullum akace ka fitoh a muku aure,sai kace baka da kudi,

 ah ah sai kayi gini ashe iskancine,baba lami tace

Kinga baba lami wallahih kibini a hankali Daman ni har yanzun haushin ku nakeji,

Aini ba shege bane dazan aure kanwar Wanda tayi sanadin mutuwar inno na ba,

Koh inno ne ta dawo nasan bazata yafe mini ba Inna aure yarki, iro yace 

Kai karamin D’an Tasha wallahih karka kuskura, kace zaka zagarmin uwa inba haka ba naci ubanka a gidan nan, manu ya fada,babban yaron Inna asabe

Inka fasa shege kake,iro yace Yana huci

Ai Bai Gama rufe baki ba manu ya shakumosa suka hau dambe

Duk yanda matasan ke ta kokarin rabasu abin ya faskara abinka da tamben maza,

Mazan ma masu zuciya

Hatta iyayensu maza an Kira Amma duk sunki rabuwa sai an rabasu an Kama D’aya sai D’aya ya fizge ya shakumo D’aya Inka shiga tsakani duka ya sauka akan ka

Abin da yafi karfin Yan unguwan police aka Kira,suka zo suka kwashe su,inda sabo an Saba da ganin fiye da hakama agidan Adara

*******************

Bayan fitar khadija kwanciya nayi don yau dai naji na gaji da cin cimar mu tunda inada sauran 2k Kuma akwai kayan Miya da yawa,don haka yaudai zanci wani abin special

Duk abinda ke faruwa Ina kwance Ina jinsu sai dai.bansan ainahin abinda ya had’asu ba”garin kallon fad’a a kasheni a banxa ” nace Ina gyara kwanciya na

sai kusan 5:30 Al’ameen ya koma gida kwata kwata naira 30 yayi ciniki Sam yau Kam sai a hankali,ya shigo gidan jiki a sanyaye hannunsa d’auke da kwandon kwanuka,bakinsa dauke da sallama

“Waalaikumu salam,sai yanzun”nace masa

Eh Sumayya yau inne ba kasuwa shiyasa ban dawo Koh da Rana ba

“Toh Allah ya bada kasuwa gobe”

Ameen yace Yana aje Kwanukan a mawanki,Mika Mata talatin in yayi

“Ka rike kawai agunka”

Ok yace,boket ya d’auka ya ibi ruwa, band’aki ya shiga yayi wanka Yana fitowa yayi Alwala,daidai lokacin aka Kira mangari ba, masallaci ya wuce

“Sallan mangariba,nayi wanka Nima zani na d’auka fille D’aya na had’a da t-shirt sai hulan bacci, Jin ana kukarin shiga sallan isha’i,

Ina da Alwala hijab kawai nasa na Tada sallah,

7:40 Al’ameen ya shigo d’akin bakinsa d’auke da sallama

Amsa Masa nayi”yauwa jiranka nake ka dawo daman”nace Ina mikewa

Toh Allah dai yasa lfy?yace

“Kasan inda ake Saida tsire”?

Tsire Kuma Sumayya?

Eh “tsire de”

Hmm eh na sani a tsallaken titi akwai Mai nama, kusa damai shayi

Yauwa karbi kudin nan 2k ne ka sai Mana tsiren 1500 sai Kuma  ka sama Mana drinks Mai Dadi guda biyu yau Dadi zamuci gaskiya”

sai ka sai  Madara bornviter da sugar in change ya rage kasai bread Nokia Ina da ruwan zafi a flasks,sai mu karya dashe gobe da safe”

A Ina Kika samu kudin nan? haka Sumayya don khadija tace mini ba kayanki Kika sayarba 

Sosai naji Ina Kara kaunar Khadija yarinya Mai hankali hartasan ta rufa mini asiri agun D’an uwanta,

Amma ni bazan Masa karya ba”uhmm uhmm nidai gaskiya bazan maka karya ba Turarena na sayar”

Amma Sumayya banace ki daina Saida kayanki ba ,ni ban Kara Miki ba, Bai kamata in rage Miki ba

“Habba ya Ina da abinda Zan sayar na saka abakin salati saina zauna da yunwa tsakani da Allah fa, yau baka samu kome ba da haka Zan zauna tun safiya har warhaka banci kome ba kenan”na fada Ina Bata Rai

Ganin Kamar taji haushi sai ya sassauta murya,toh Yi hakuri kawo kudin naje na saya Miki

Mika Masa nayi bance kome Ba

Lalubar kudin yayi harya rike,ya fita

Baifi hour 1 ba ya dawo lokacin Ina kallo a d’aki 

Shigowa yayi da sallama

Amsa Masa nayi,Ina karban laidodi Daya ke mika mini, karba nayi, na mike waje na fita na d’auko plates da cups harda flasks na shigo d’akin,

bude laidan tsiren na zuzzuba a plate,Goran pineapple juice in Mai sanyi na juye Mana a cup,d’aukan NASA nayi na Mika masa,”gashi naka”

karba yayi hade da Mata godiya,a hankali yasa hannunsa a cikin plate in ya dauki Naman da Bismillah yasaka a bakinsa

,lumshe ido yayi,rabonsa da yaci tsire tun  lokacin da mahaifinsa kenan,bazai manta ba shike sayo musu duk dare, lokacin ma ba’a haifi Khadija ba

Nima cin namana nake Ina korawa da drinks ba karamin Dadi naji ba kai.talauci ba kyau talaka sai yafi wata baici nama ba,

Ashe haka talakawa keji,tabbas badon jarabawar da Allah ya jarabceta ba bazata taba sanin rayuwan Talauci haka yake ba Alhamdulillah Alah kulli halim

Daga ni harshi duk nacin mu bamu iyya cinye namarnan ba, sai da muka rage wani,nikam har zafi hakorina naji yake mini kafun na aje Naman don yau cin yunwa na masa,sabanin da, da nake ma nama cin kwad’ayi kawai

Jin ta aje plate nata yasashe magana,sumy Wai harkin cinye ne ga nawa ki Kara wallahih na kasa cinye wa,

“Kutt bazanci sauran abinda kaci ba,Kuma nima ga nawa ban ciny………

Bai bare ta Gama magana ba taji ya fizgota sosai suka zube akan gado kanta yahau cikin gaggawa ya hada bakin su waje D’aya y’awonsa ya juye Mata a baki

Ware ido nayi Jin y’awonsa cike a bakina so nake na zubar Amma ba Hali har lokacin bakin mu a hade,ji nayi kamar numfashina xai d’auke ai da sauri na had’iye Ina rumtsa idanuna

Jin ta had’iye yasa a hankali ya kamo harshen ta sosai yake tsotsarta cikin zafi zafi..

Fizge bakina nayi,”don Allah ka Bari banason abinda kake minin nan”na fada Ina ta kukarin turesa a kaina

Ni Kuma inaso,ya Bata Amsa,Yana Kai hannunsa, akan t-shirt nata Yana kokarin cirewa

Ai bansan lokacin da na Kama kokarin fizgo kaina ba ganin da gaske fa mutumin nan riga zai cire mini

Jin ta isheshe da fizge fizge shima ya biye Mata inya d’aga riga sai yaji ta jawo rigan kasa,inya cire hannu D’aya sai tasa d’ayan

Tambe muka fara sosai abin dariya abin haushi,daga ni harshi mun jikkata sosai Amma ba Wanda yayi niyar barwa Dan uwansa dama

ni naki yarda ya cire mini riga shi Kuma yaki yarda ya hakura,

Hannu yasa da karfi ya fizge zanin jikinta,

Gwalalo ido nayi jina ba zani,wani yunkuruwa nayi da karfin gaske Zan mike zaune 

Cikin  zafi nama ya maidata kwance  Yana Kara Hawa kanta,

daidai lokacin mukaji sallama na muryoyin Yan Mata a kofar mu….,…..

🌾 *Juma’at Mubarak* 🌾

 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* 

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧

Page 2️⃣6️⃣&2️⃣7️⃣

Ba karamin Dadi naji ba,da saurina Amsa musu sallamar muryata na rawa”waalaikumu salam”nace Ina kallonsa ganin baiyi niyar sakeni ba,”toh ka tashi Mana naje naji suwa ke sallama”

Wayace kiyi magana?

“Au amsa sallaman ne,laifi”   

Toh ai badon Allah kika.amsa ba ya fada Yana sauka a hankali ya kwanta a Gefen ta

Jin ya sauka akaina ai da sauri na mike zanina da ya yasar a kasa na tsunguna na d’auka,fita nayi a d’akin duk jikina sai rawa yake, na barsa a  kwance akan 

Gadon.

Yan matane zasu Kai su biyar gabaki D’aya bazasu wuce sa’o’in Khadija ba,”sunnunku da zuwa”

Sukam mamakine ya cikasu,wannan ne MATAR MAKAHO Mata Kamar balarabiya Aiko Mai kudi lafiyayye ba kowa bani yake sa’ar samun mace Mai kyaun Sumayya, yauwa,Ina wuni Aunty sumy? Suna had’a baki

“Lafiya Alhamdulillah bara na d’auko muku abin zama”  

La ki barshi kawai Aunty,sauri muke ma dare yayi.

“Gaskiya Kam Kuna Mata yanzun ana neman 10 na dare fa,kuna waje”

Eh wallahih Aunty nasan bazaki ganemu ba,Daman mu kawayen Khadija ne,wata acikinsu tace

“Kawayen Khadija Kuma aini Khadija batace mini tanada kawaye ba bayan Asma’u”nace musu haka don na gane kawayen Amaryar ne,ganinsu da Anko

Eh Aunty dukan mu kawayen Khadijan ne harda Asma’u,

“Toh Allah dai yasa lfy ba wani abin bane ya faru”nace Ina zullumi kar wani abinne ya samu khadija

Eh Aunty yanzun ma gidan su khadija Muka fitoh akan ta rakamu wajen ki,shine tace Wai yayanta ya hanata fitan dare

“Gaskiya ne Bata fita bayan mangariba, Allah dai yasa lfy kuke son ganina”?

Eh lfy Daman mun tambaye tane akan inda tayi lalle da make-up jiya,

Shine tace Mana Wai agun matar yayanta,.

Shine mukazo mu tambaya Koh zamu samu lalle gobe,da kwalliya in Allah ya kaimu?

“Bazaku samuba” nace Ina zuyawa na shiga d’aki Koh bin ta kansu banyi ba, saboda sanin da na musu sune suka ma khadija rashin mutunci jiya agun Fulani Dance.

Ina shiga d’aki akan kujira na zauna, gaskiya Ina son yin lalle Koh don na samu na biyan bukata Amma bazan ma Yan iskan nan ba.

Sumayya meyasa bazaki musu lallen ba? Al’ameen ya tambaye ta

“Ina ruwanka watoh ka fara sa ido Koh”

Ina Naga idon bare na saka ni duhu nake gani,ya Bata Amsa

“Watoh kaima ka iyya bakar magana Koh”

Ai agunki na koya

“Badai aguna ba malam ehen”

Amma Sumayya dakin musu lallen ai.

“Bafa Zan musu ba Yan iskan yara bakasan me suka mini bane,”

Yaushe sukazo gidan nan har suka Miki Abu?

“Kai jama’a yaushe ka koma D’an jaridane ban sani ba”

Baimin magana ba mikewa Naga yayi Yana kokarin sauka a gadon ai ihu na saka na mike zanyi waje.

Wallahih Kika fita a d’akin nan saina Miki abinda bakiso

“Me kenan”?

Kin fini sani,yace Yana nufar kofa, waje ya fita yaje ya rufe shashen mu ya dawo ya rufe kofan d’aki 

Ina dai zaune sai raba ido nake,ganin ya nufu kujiran,da nake yasa na mike a hankali na lallaba na chanja waje, zuwa gaban mirror na tsaya,

Jin motsen takunta yasa ya gane lallai tabar Kan kujiran..

Fara lalube yayi nidai sai chanja waje nake in ya nufi inda nake saina chanja waje,duk magiyar da yake min, kin tsayawa nayi.

Muna cikin zagaya d’akin kawai aka d’auke NEPA gashe ban San takamemmen inda na aje wayata ba.

Jin tsayawar fanka,yasa ya gane an d’auke NEPA ne, shiyasa ya fara tafiya a hankali Yana laluben ta sanin da yayi yanzun itama ba ganinsa zatanayi ba.

Raraba ido nake ta faman Yi banajin motsensa Sam sannan Banga wayata ba.matsawa nayi sosai jikin kujira na sunguna Zan duba wayata,ji kawai nayi ya rungumeni ta baya

“Wayyo Allah nikam ka sakeni wallahih banaso”

 yanzun dai kema baki ganin kome kamarni.

“Allah ba kamar Kai bakam”

Koma yayane dai baki gani 

“Nikam sakeni hai”

Naki yace Yana dagata 

“Wayyo nashiga uku,ka saukeni”nace Ina ta faman mutsu mutsu

Kiye shuru Mana mu k’wanta

“Niki shurun nikam ka sakeni”

Kin saketa yayi duk yanda tayi ya saketa ki yayi 

Ina ji Ina gani ya kwanta akan kujira d’aurani yayi akansa,tun Ina masifa harnayi shuru Jin ana iska da yayafi ,sanan aka kece da ruwan sama,

Baccine ya d’auke mu dukan mu biyu akan kujiran muka kwana

Da safe,shayi mukasha da bread,wanke wanke na fitar Ina wanke wa

Sanin da yayi Koh ya fita ba lallai bane yayi ciniki sai wani ikon Allah da safen nan, gashe mangoron duk sunyi labo labo.

Kayansa ya fitar Wanda Bai wuce kala hudu ba a igiyar bayan gida inda take Tara kayansa masu datti,d’aukar basket in kayan Sumayya yayi ya fitar dashe waje ya zuye a dakali,ibo ruwa yayi ya fara wanke musu kayan.

Ina wanke wanke,Yana wanki,dukan mu shuru Babu Mai magana

Assalamu alaikum, khadija ce tayi sallama hannunta d’auke da laida

“Waalaikumu salam khadija”

Ina kwana Yaya?

Lafiya khadin Goggo

Ina kwana Aunty,tace tana murmushi

“Lafiya khadija ya Goggo”

Tana gaisheki,tace tana zama a Gefen yayanta dake zaune abakin dakali da boket in ruwan kumfa

“Aiko Ina amsa wa”

Aunty kinsan me? Kai jiya Naga abin mamaki,tace d’auraye kayanda yayanta ke wankewa

“Me Kika gani haka”? Na tambaye ta

Aunty kinsan Allah Ina fita a gidan nan,na wuce gidansu Asma’u duk inda na wuce sai ayita kallona ,

Ina Isa na samu an kawo mototi sunkai ashirin,kinsan Aunty mijin Asma’u shima Mai kudine?

“Ina Zan sani khadija ai sai kin fad’amin”?

Ina isowa wajen mototi sun cika har ana kokarin tafiya,kawai saina nemi gefe na tsaya, kawai wani abokin Ango yazo kusa Dani,Wai hajiya baki samu mota bane?

Nace eh ban samu ba ku tafi kawai Zan hau machine,

Wai harda cewa Wai babban Dani ba girma na bane Hawa machine bara  a sama mini wajen zama,

Kawai yaje ya fidda kawar amarya ya sani a motar

“Hhhhhh Kai habba dai khadija”nace Ina dariya

Yanzun abin dariyane agunki Sumayya an fidda wani Ansa wata,Koh ke zakiji d’adi a Miki haka, Al’ameen ya fada Yana Bata Rai

Khadija Kam tsoro ne ya kamata Sam ta manta da yayanta agun ta sake baki tana zuba

“Kasan me suka matane”?

Koma me suka Mata hakan Bai kamata ba cin fuska ne,

Fad’a Masa kome nayi akan abinda suka ma khadija

Koma me suka Mata banji Dadi ba

“Khadija tashi mu shiga ciki muye sirri”nace Mata Ina Kama hannunta Muka shiga d’aki

“Khadija karasa mini sai akayi yaya”na tambaye ta

Ai Aunty in gaya Miki kawai na Shiga abina kawayen fa Basu gagane niba sai da Muka Isa Taraba motel in da Muka fifita a motar,duk Saida suka Raina wankan su Aunty kaf insu  harda Amarya Babu Wanda kwalliyar ta yayi kyau irin nawa,

Sai da nama Amarya magana kafun suka gane nice, wallahih Aunty baki ga yanda aka maida ni abin kallo ba masu vedion aure sai d’aukana suke harda hotuna,Kinga agun kawaye uku nayi yaran masu kudi,samari Kuma sai turawa suke Wai suna son magana Dani a waje.

Kin zuwa nayi kawayen ma naki kulasu,ai Aunty badon Allah ba kenan suke Sona, tunda Basu Soni a khadija ta ba Saida suka ga nayi kyau,ta karasa maganar tana washe baki

“Gaskiya ne khadija bare ma insha Allah karatu zakiye insha Allah”nace Ina murmushi don tabbas khadija akwai kaifin tunani

Aunty jiya fa goshin mangariba na fitoh a Hall in Zan dawo gida Kinga yanda abokan Ango ke ribibin zasu kawoni gida,.

Amma naki,

“Gwara da Kika ki khadija yanzun mutum ake kiwo. Ba dabba kad’ai ba”

Wallahih kuwa Aunty kawai da dare saiga wani yazo gidan mu bansan ma waya nuna Masa ba Wai ana sallama dani,

“Lallai kanwata tayi goshi”

Allah Aunty kin fita nayi Goggo tayita fad’a 

“Don me khadija wulakanci ba kyau fa dakin fitan ai” 

Gaskiya ni Aunty banason Abu da masu kudi, 

don mudi yace mini da babban mota yazo,Kinga masu kudin nan in Kika aure su wallahih Kina Yar talaka,basa ganin daraja. Yan uwanki

Ah ah khadija ba duka aka zama D’aya ba indai da kyakkyawan Niya akayi aure badon kyau Koh kwad’ayi ba,insha Allah ba abinda zai faru

Hakane Kam aunty,au Ashe fa na had’a da Aunty a magana ta am sorry (don tace auren masu kudi basa ganin darajan Yan uwan matan su,in talaka wa ne)

“Uhmm khadija kenan,ai Nima na zama talaka yanzun”

Amma ai gidan ku akwai kudi?

“Gidan mijina babu”

Aunty jiya wasu sunzo wajenki karfe kusan 10?

“Eh Khadija”

Nima jiya suka zo gidan mu Wai na fad’a musu Wanda tamin lalle,da Wanda tamin make-up

“Kawayen Amarya Koh”?

Eh Aunty sune,suka mini wulakanci agun Fulani Dance

“Aiko shiyasa nayi maganin su nace bazan musu lalle ba”

Meyasa Aunty

“Saboda kee kad’ai Zan ma kwalliya har Agama programs na auren Asma’u”

Kiye hakuri ki musu Aunty Zaki samu kudi sosai fa yau HENNA DAY, Kuma da yamma za’ayi Algaita

“Gaskiya khadija bazan musu ba ” 

Shikinan Aunty ga kayanki nan na dawo Miki dasu

“Habba khadija ki rike na bar miki”Daman kyauta na baki ba aro ba”

Aunty’ ai yayi yawa 

“Ki rike duka”

Allah ya……….

Bata karasaba mukaji sallama na muryar mace babba

Al’ameen dake zaune a waje ne, ya amsa 

Sannu Ina kwana hajiya,yace Yana tsame hannunsa a wankin

Lafiya Alhamdulillah don Allah nan ne kofar MATAR MAKAHO?don ita Bata zata Al’ameen baya kallo ba

Kafun Al’ameen ya Bata Amsa Muka fitoh a d’akin dagani har khadija kallon matar muke hajiyace Kuma hamshakiya daga ganinta naira ya zauna

“Hajiya lfy” nace Ina kallon ta  dajin haushin sunan da ta kirani Wai MATAR MAKAHO mtwss

 yauwa wajenki nazo 

“Ok Bismillah khadija d’auko Mata darduma” nace  saboda d’akin mu D’ayane bazan iyya saka baki a ciki ba

“Bismillah hajiya ga wajen zama”

Zama tayi Muka gaisa

Ni sunana hajiya sa’a findon Asma’u kawar Khadija kanwar mijinki nasan khadija Kam ta ganeni Koh? tace tana kallon khadija

Eh Aunty sa’a, khadija tace

Yauwa Daman nazone akan in ba damuwa,Koh Asma’u zata samu lalle inda halima harda mu,don jiya na turo kawayen ta sunce Wai bazakiyi ba shiyasa nazo da kaina,

“Gaskiya hajiya ni Ina da aure bazan iyya zuwa in ma amarya lalle ba,tunda Henna day ne yau”

Habba wallahih ba kome zamu zo har gida ki Mana itama Amaryar zatazo saiki mata,tunda ba’a d’aura aure ba kuma gida baki da hanci

“Shikinan hajiya”

Yauwa nace zata iyya zuwa yanzun don anjima akwai Algaita da yamma,saiki Mata kwalliya ma duka

“Toh hajiya gaskiya bazaku samu lalle yauba don indai lallen Amarya ne Dole za’a jima ga kwalliya duka”

Saiki Mana gobe da safe,tunda Walima ne kwalliya kawai zaki Mana da yamma saiki Mana lalle da safe,

“Ku nawa ne”?

Mu bakwai Zaki ma lalle da Amarya 8 Amma bansan kawayen ta mutun nawa ba

“Ok za’a ma Amarya lalle da kwalliya yau”In yaso ku sai amuku gobe hannu bibiyu sai kwalliyar walima,saboda time”Amma banda kawayen don bazasu samu ba

Ba damuwa Daman booking mukayi har Agama bikin zakina Mana kwalliya in ba damuwa

“Ok shikinan”

Nawane kudin ki?

“Hajiya kwalliyar Amarya kashi biyu ne ana heavy make-up a dinner, bud’an Kai, kamu sai light make-up anayi a Walima, Algaita, Arab night

Kinga kenan light make-up Zan mata yau”

“Kudin kwalliyar yau 5k ne, lalle 10k na Amarya”

“Kwalliyar ku 3k ne Koh wani mutum D’aya”

Ok na gobe fa ?

“Lallen ku na gobe hannu bibiyu ne Kuma ja da baki za’a muku a hannun dubu D’aya da d’ari biyar ne, in da lalle na Kuma 2k Koh wani mutum D’aya”

Ok tace ta hada lissafi ta bani kudin a hannun,gashe kudin kwalliyar Amarya da lallen ta nayau da kwalliyar mu sai na lallen mu na gobe,in mukazo kwalliyar walima sai muyi lissafi harda na dinner,tace tana mamakin wayewar Sumayya,

 da akace mata MATAR MAKAHO ne ta d’auka Koh zatazo taga bagidajiya sai taga hatta MAKAHO ma bazaka zata baya gani ba

Ok hajiya” nace Ina karban kudin kirgawa nayi Naga ya cika,hajiya watoh harda kudin lalle Kika bayar kenan”?

Eh zuwa kawai zamuyi goben,Amma Amarya na zuwa da lallen ta,kinsan ana  kawo kayan rufi da lallen Amarya ?

“Gaskiya ne shikenan saina ganku anjiman”

Allah yasa tace tana Mike wa ta tafi

Khadija Kam da Al’ameen mutuwar tsaye sukayi,Wai kwalliyar da ake gogiwa shine za’a biya dubu biyar ayi ai gwara ma lalle zaiyi sati..

Aunty yanzun duk wannan kudin na lalle ne kawai da kitso? khadija ta tambaye Sumayya

“Kai Khadija ba abin yayi bane,Kuma kayan kwalliyar ma tsadane dashi”

Ikon Allah,tace

“Kinga khadija tashi maza kije kasuwa ki mini sayayyan lalle sai ki sai Mana semolina yau tuwo zanyi na gaji da shinkafan nan na fada Ina Mika Mata 10k ki sai Mana harda kaji biyu a gyara Miki a kasuwan,ki hada mana da kayan Miya harda su vegetable”

Toh Aunty tace tana karban kudin 

Al’ameen Kam baice kome ba ,Yana shanya kayanda yawanke

Khadija na fita Koh minutes uku batayi ba mukaji Karan faduwa timmm sai muryar Khadija data k’wala Kara,irin na azabar nan,dagani harshi da gudu Muka nufi kofar fita a shashen mu, ganin tsabar rudewa Bai gane hanyar kofa ba yasa na Kama Masa hannu na Masa jagora Muka fitoh,

 me Zan gani khadija ce a……….

                 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧 

Page 2️⃣8️⃣&2️⃣9️⃣      

Khadija ce a zube a kasa cikin ruwan cab’alin rijiya,salame na ruwan cikin ta,ta hakikance sai jibganta take

Sake hannun yayan khadija nayi Da wani irin gudu nayi Kan salame,don na fahimci Yan gidan nan in har baka koma irinsu ba zasu kasheka,yarinya sa’ar khadija Amma khadija ta sake jiki tana dukanta Koh martani Bata mayarwa sai k’okarin Kare kanta,kafun na Isa ba zatoh ba tsammani sai kawai Naga  Iro ya kwashe salame da kafa daga Kan khadija yayi ball da ita sai da ta zube a Gefen  rijiya bakin ta ya sare simintin rijiya,kafun kace me tuni ya rufe salame da duka sai a lokacin Yan gidan suka firfito,Abu kamar Wasa fad’a ya zama babba,don fadan yanzun Kam mutane sunkai biyar suke dambe,kama khadija nayi wance tunda Iro yayi ball da salame take gefe tana kuka duk jikinta sai rawa yake, “khadija  tashi mu shiga kofata sannu”

Mikewa tayi a hankali,suka nufi kofar shashensu

Al’ameen Kam Yana tsaya Kamar andasa sa don baya gane kome tsabar yanda surutai da koke koke  ke tashi a tsakar gidan,sai raba ido yake kawai

Muna zuwa saitin inda yake hannu kawai nasa na Kama NASA Muka shiga cikin kofar tare,

Sake hannunsa nayi, 

Ruwa na iba na Kai Mata band’aki na Kama hannunta muka shiga, kanta na wanke Mata kafun na fita na barta tayi wanka

Kaya na makala Mata a jikin kofar band’akin,

Tana fitowa.

D’aki Muka shiga zaunar da ita nayi da sauri na d’auko D’an kwalina na d’aura Mata akanta dake ta zubar da jini”khadija meya hadaku meya faru?

Wallahih   Aunty Ina fitowa kofarki kawai nazo wuce gindin rijiya,Daman salame na iban ruwa kawai ta kwashi kafafuna na zube shine tahau kaina tana dukana,kallifa Aunty ta fasamin Kai,ta fad’a tana Kara karfin kukanta

“Kiye Shuru khadija,share hawayen ki yanzun za’a bi Miki hakkinki wallahih in sunsan wata Basu San wata ba” nace Ina duba inda na aje wayata

In Raina dubune yau ya baci na gaji da bala’in Yan gidan nan da Talaucin da muke ciki zamuji Koh da tashin hankali’wayana na d’auka tunawa da nayi,da wani school mate nawa lokacin da na shiga jami’a shi Kuma Yana final year insa,yanzun police ne yana da babban mukami a hukuma, muna mutunci sosai kamar yan   uwa danayi aure ne dai bamu sake magana dashi ba.

Me zakiye Sumayya? Al’ameen dake zaune a kujira yayi tagumi ya tambaye ta 

“Mataki Zan d’auka”

Wani irin mataki?

Akwai Wanda Zan Kira wallahih Koh tantama banayi  daga gidan nan direct sai prison Koh station bazata shiga ba Kuma sai naso za’a bada belin ta”. 

Wa Zaki Kira?

“Wani friend Ina ne”

Toh wallahih ba’a gidan nan ba

“Ban gane ba’a gidan nan ba kenan kana nufin abarsu suci bulus kenan kaga yanda suka fasawa yarinya Kai kace a barsu”

Ina dai kanwata aka fasawa Kuma nace bana bukatar ki d’auki mataki

“Ok nuna mini kake khadija ba kanwata ba koh”fine shikenan gaka ga Yan gidan naku,Daman nice bare”nace Ina aje wayata na fita waje sosai maganar Al’ameen tamin zafi Wai kanwarsa Kuma yace baya bukatar mataki,watoh ba ruwana kenan a maganar

Al’ameen Kam harga Allah Bai Fad’a,don wani abuba kawai ya fad’ane don ta janye maganar rufe salame,baisan maganar zai Mata zafi harta fassarasa wani iri ba

Khadija Kam sosai taji Bata kyauta ba a  sanadin ta ma’aurata sun samu sabani,mikewa tayi ta fita  waje,

wajen da Sumayya ke zaune ta karasa

Aunty bara naje kasuwar

“Khadija Wai kina nufin kudin nan na hannunki”?

Ni na d’auka ma Koh kin yasar dashine tuntuni”

Ah ah Aunty Daman a bakin zanina na soke Kuma Allah ya taimakeni Bai fad’ ba

“Ok kibar zuwa cefenen”nace Ina karban kudin hannunta

Ah ah Aunty maganar Yan lallen fa,don Allah Aunty karki fasa lallen nan,Akan abinda ya faru.

“Ah ah khadija rike 1k innan kije chemist a Miki dressed in wajen Naga har yanzun jini Bai tsaya ba”

Toh Aunty na gode tace tana mikewa zata fita

Khadija tsaya muje na rakaki, Sumayya ki kawo cefenen Inna rakata chemist sai na wuce kasuwar, Al’ameen yace

Kala bance Masa ba don haushin sa nakeji sosai,hakurin sa yayi yawa shiyasa ake cutar sa kullum

Aunty Yaya na magana Wai zaije kasuwan,

“Ka barshi kawai gobe Zan aiki Yan lallen suje kasuwa su sai mini abin hadin”

Toh Aunty ki basa kudin cefenen sai ya sayo muku,ya iyya zuwa kasuwa, khadija tace cikin rashin Jin Dadi ganin yanda na Had’awa yayanta fuska

“Ungo”na Mika Masa 6k

Matsowa yayi Yana lalube ya karbi kudin a hannuna

Me da me Zan Saya?

“Ka tamabaye khadija na Mata lissafi “

Ok yace cikin sanyin jiki don wallahih Bai d’auka maganar zatayi zafi haka ba

Suna kokarin fita Asma’u na shigowa da kawayen ta,suka gaisa da Al’ameen kafun suka shigo,khadija kuma suka fita

Shimfid’a musu darduma nayi,suka zazzauna

Tashi nayi naje na chanja kaya,na manna Gam a faranti,na kwaba lalle,Muka fara

Khadija ta dawo lokacin kusan karfe 10

“khadija ki shige d’aki kije ki kwanta Naga an kawo NEPA ki huta kinji”nace Mata Ina kallon kanta da aka mannawa plaster

Toh Aunty tace tana shigewa d’akin, kwanciya tayi a kujira,banci ya d’auke ta

Al’ameen Kam kasuwa ya wuce yaje yayi sayayan kayan abinci,Amma Sam yau Baya cikin walwala tunda suka D’an samu sabani da Sumayya,don shi Sam bayason yayi abinda zai bawa wani haushi harya kullace sa abin damunsa yake

Yan matan sunata Hira,inama Amarya lalle,saiga Al’ameen ya dawo da laidodi a hannunsa na sayayyan kasuwa,mikewa nayi na karbi laidan gudun kar na tozartashi a gaban su,kitchen na shiga da laidodin shima bayana yabi 

Yan Mata Kam sai ido suke bin MAKAHO da MATARSA suna mamaki

Muna shiga kitchen in,na aje laidodin 

Sumayya Naga Yan sana’ar sunzo Koh Zaki kawo na girka Mana abincin? in yaso

“Kai bazaka fita bane”?

Zan fita Amma sai bayan azahar

“Toh ka iyya girkine? koh da wani idon zaka girka Mana abinci muci”?

Eh na iyya girki,sai ki jera mini Abubuwan da Zan girka Zan iyya

“Bana bukata”nace Ina Shirin fita

Jin Amsar da ta Bashi ya tabbatar har yanzun haushi takeji,hannu yasa a hankali ya rikota Jin zata fita a kitchen in

“Ka sakeni”nace ba Wasa a muryata

Sumayya kiye hakuri in abinda na fada Bai Miki Dadi ba

“Ka sakeni nace maka”

Am sorry

“Ka sakeni”

Baki hakura ba?

“Ka sakeni”

Toh innaki fa,ba Matata na rike ba

“Matar ka ai da Ina da wannan matsayin da gaske da bazaka nuna mini banda matsayi agun khadija ba”

Amma ba nace kiye hakuri ba,yace Yana jawota jikinsa

“Nima ai bance maka naji haushi ba”

Amma gashe sai fushi kike

Haka dai Kai kake gani,nikam sakeni Rana yayi bamu karasa lalle ba

Bana gani sai dai ji

“Oho maka dai”

Mana dai,ba ni kadai ba

“Toh sakeni Mana”,nace Ina banbare jikina a nasa

Sumayya abinda yasa Kika ga naki ki d’auki mataki,da hukuma toh a gidan nan Babu Mai tsoron station Koh prison don ba bako bane agunsu, bare ya saka musu tsoro don kinsa an rufe salame,wata fitinar kika kunna,zaman gidan nan sai ya gagare mu

“Kai kake tsoron fitina bani ba’ akan gaskiya na Koh Ina zanje”

In Miki girkin?yace Yana kauda maganar

“Ka bare Zan girka”

Toh shikinan,yace Yana saketa,

Tsayawa nayi ya rigani fita a kitchen in,

Ya Kama hanyar kofar fita a shashen mu

Nima fita nayi,”am please bara na d’aura Abinci, Rana yayi sai nazo mu karasa”

Aunty bara na d’aura miki,wata Yan Mata a cikinsu tace

“Ah ah ki bare kawai”nace Ina tunanin karfa Bata iyya girki ba ta Bata mini kaji a banza 

Kai Aunty Koh dai kina tunanin ban iyya girki bane?

Ba haka bane,Daman Ina tunanin karna takura Miki ne,Amma  tunda kina sonyi shikenan,ki tuka semo laida babban duka,

Kitchen ta shiga

 ni Kuma d’aki na shiga naje na leka khadija har lokacin bacci take

Sai azahar  na kammala lallen Amarya,na tashe khadija mukayi sallah abincin da farida kawai Amarya ta girka na zubawa yayan Khadija nasa, na zuba na Daren mu, sauran na zuba ma kawayen, na ibawa Amarya na zuba Mana da khadija,sosai Tuwon yayi Dadi,bamu Gama ciba aka turo yara da kulolin Abinci daga gidansu Amarya shinkafa muka dad’a,

yaran na baiwa na yayan Khadija su Kai masa

Ganin da sauran lokaci yasa nama farida lalle (wance tamin girki)

Sai la’asar Asma’u tayi wanka sosai na zuba Mata light make-up tayi kyau Kamar me,ganin kawayen nata d’aukar ta hoto yasa Nima na fitar da wayata,na d’ad’auki hotonan lallen ta da kwalliyar da na Mata duk da hoto nason gida Mai kyau Amma wanka na gyara hoto ma ba gida kawai ba

************

Bayan tafiyar Amarya da kawayen ta, wanke wanke nayi na share kofar don yayi kaca kace,kowa yasan gidan Mai lalle in ta Tara customers,yanda yake baci

Wanka nayi,donna gaji sosai yau innan,vest nasa na d’aura zani don ba kowa a kofar nawa khadija ma ta tafi gida,don yau ba zuwa program Kai ya fashe

Bayan sallar mangariba ya dawo Kamar kullum wanka yayi mukaci Tuwon da farida ta dafa Mana da rana

Bayan sallan isha’i yau Koh jiran ya dawo masallaci banyi ba na kwanta don gabaki d’aya bacci nakeji ba kad’an ba ga gajiya sosai.

Yana dawowa ya tarar tayi bacci shima gadon ya hau don tabbas yau yasan ta gaji,tabata yayi yaji alamun bacci take,a hankali ya cire mata vest in jikinta daga ita sai wandon bacci,shima kayansa ya cire dagashi sai guntun wando a hankali ya rumgumeta,kome a hankali yake gudun karya ta tashi,sosai yaji wani irin yanayi Mai matukar shauki a tare dashe,amam haka yake dannewa,har bacci ya dauke sa

Misalin karfe 3 na asuba kamar a mafarki naji ana tattaba min kirji da sauri na bude ido,tashi nayi na zauna jina ba riga,sake taba jikina nayi don na tabbatar Aiko da gasken bani da riga,

“Wai meyasa kwana biyun nan ka chanja ne kanamin abinda ranka yake so”?

Mutum da halaliyarsa, ya Bata Amsa Kamar Wanda tama Dole

“Ka tashi mini a wajen kwanciya”

Ina kenan?

“Gado”

Naki, gaskiya yanzun bazanna kwana ni kadai ba alhalin Ina da mata.

“Don Allah nikam ka tashi, kaga yanzun ma Banga rigata ba ga d’akin duhu”

Saiki kwana haka

“Akan wani dalili Zan kwana ba riga,Kuma karka sake ciremin riga in Ina bacci banaso”

Inna cire fa?

“Au tamabaya ma kake sai me?

Eh tambaya nayi

“ka Dameni sai surutu kake sani tsakar dare”

Wani dare ai na yau ya wuce sai dai na gobe

“Ka tashi nace”

Naki

“sauka zanyi na bar maka d’akin ma in baka sauka ba”

Toh na hanaki ne

Mikewa nayi na sauka akan gadon nayi hanyar kofa Koh riga ban dashi,

Ba riga Zaki fita waje?

“Ai baka fini ido ba”nace Ina kokarin bude d’aki, kawai ji nayi y………..

 *Aye manage in page bani da charge* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincenseIG @umsadincenseIG @umsadincenseIG πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧  

Page3️⃣0️⃣&3️⃣1️⃣

Ji kawai nayi ya rumgume ni ta baya,

zare ido nayi jinsa shima ba riga,mannani yayi da jikin kofar shi koma ya rumgume ni sosai ya d’aura kansa a kafad’ata

“Wai menene haka don Allah” ?

Dadi ne,ya Bata Amsa

“Dad’au matau”    

Jin Amsar da ta Bashi yasa ya juyo da ita da karbi ya rungume ta

Ware ido nayi jina sukutum a kirjinsa dukan mu ba riga

“Wayyo Allah meye haka” 

Mele,shima ya Rama

“Nikam.ka sakeni”   

Bakinsu ya hada,a hankali yake kissing in lips nata na sama

Bansan garin Yaya ba Koh yaushe ba na tsinci kaina da Kama lips nashi na kasa Nima na shiga tsotsa

Jin ta Kama Masa lips yasa a hankali ya zame bakinsa cikin nata,ai da sauri yaji ta kamo kansa ta sake maisa bakinsa cikin nata 

Sosai suka shiga farantawa junan su Rai ,

ba zatoh Koh tsammani   muka zube a kasan cafet,nice a sama shi koma a kasa,

da sauri ya birkitota kasa Yana lalube da D’an kokarinsa zai zame Mata wandon baccin da ke jikinta

Da sauri na Kama hannunsa Jin aika aikan da yake so yayi

Don Allah ki bari musamu nutsuwa

“Nidai wallahih ah ah”

Please kinji

Kokarin mikewa na fara a jikinsa,

Da sauri ya kamota,Ina Zaki

“Anafa Kiran sallah”   

Sakinta yayi Jin da gaske Kiran Assalatu ake

Mikewa nayi a hankali daga jikinsa Jin ya sake ni,”d’akin ba haske fa”

 

Ki kunna glop Mana

“Bana gani” 

Ok bara na lalubo glop in

“Toh,Ina rigana”?

Bara na kunna wutan sai ki duba,yace Yana mikewa daga kasan cafet

Mikewa yayi Yana lalube ya Isa wajen makunnen NEPA ya kunna

D’akin ya gauraye da haske,da sauri na rufe kirjina da hannu sai koma nayi tsaki tunawa da nayi bama gani yake ba

Menene kike tsaki kuma?

“Banga rigana ba”

Riga Koh vest?

“Oho”

Wai kikam wace irin matane Mai tsewa

“Green in Mata ka aura”

Toh Green Sumayya,mu fita kar ashiga sallah?

“Kai ka fita Mana Koh na d’aureka ne”

Toh Green sumy

Lalle mutumin nan ya Raina mini wayo,ji kawai nayi ya kamo mini hannu Yana kokarin fita Dani a d’akin cikin lalube

“Ban saka rigaba ka sakeni Mana pls”

Sakin ta yayi Jin Wai Bata da rigan da gaske

Bayan fitar shi rigana na d’auka na fitoh Jin harya kammala Alwala ya wuce masallaci

Bayan idar da sallah dukan mu bacci muka koma 

Misalin karfe 7:00 na safe aka doka Mana sallama a kofar d’aki,bude ido nayi a hankali ganin Yana kokarin sauka a gadon yasa na gyara kwanciya

Amsa musu yayi ya zura jallabiyar sa ya fitoh,

Ina kwana yayan Khadija?

Lafiya Alhamdulillah

Gun Aunty Sumayya mukazo,Yan matan sukace

Ok,bara na kirata yace Yana komawa d’akin

Hawa gadon yayi,ya yaye blanket inda ta rufu 

“Menene”?

Baki kikaye,Kamar Yan lallen ne fa

“Gaskiya bazan tashi ba suje su dawo anjima”

Ah ah Sumayya wulakanci ba kyau ki lallaba dai ki tashi kinji Green sumy

“Wallahih Inka sake fad’amin sunan nan Mai rabani da Kai sai Allah”

Me Zaki mini ai Babu abinda Zaki mini sai abinda Allah yaso

“Hmm” kawai nace na mike,fitowa nayi na shimfid’a musu darduma muka gaisa Yan matane guda biyu Amma ba kawaye bane,

“ban fa Saya lalle jiya ba bansamu D’an aika ba gashi 8:00 ake bude kasuwa Koh zaku karba kuje ku sayo”?

Eh Daman mu biyu mukace bara muzo kafun a Gama Mana kafun sauran su karaso,ba damuwa a bamu kudin bara muje mu sayo in 

“Ok bara na kawo muku kudin”dakin na shiga na d’auko musu kudin,suna fita wanka nayi na kimtsa kofata yayan Khadija ya ibo Mana ruwa,

Shinkafa da wake dafa duka na dafa Mana direct harda na Rana 

Bayan mun karya fita yayi, ni Kuma muka fara lalle,

Sai kusan 3 na karasawa matan lallen su dukansu su bakwai kowa hannu hannu na Masa ja da baki,sai kwalliyar walima 

Gaskiya yauma ba laifi na damka kudi Mai tsoka sosai..

Naso.muyi cefene Amma yau khadija batazo ba ni koma ba fita nake ba bare na aiki yaro

Yayan Khadija Kam Yana fita yaje ya bude mangoron sa duk sun rube haka ya zubar dasu don Koh ya bude ba Saya za’a yi ba haka yayita zama har yamma don yasan tabbas Sumayya zata sama musu na abinci Amma yanajin kunya ace kullum ita ke ciyar dashi 

Haka yayita zama sai mangari ba ya mike bayan yaje masallaci ya kamo hanyar gida jiki a sabule

Bayan sallar mangari ba ruwa na Ina na shiga wanka

Yana shiga gidan da sallama ya shigo kofar Jin shuru Bata Amsa ba ya zata Koh tana d’aki ne,ruwa ya Iba ya shiga ban d’akin

Goga soso nake a zaune kawai naji mutum ya shigo bayan gidan

A matukar tsorace na kwana Kara,”wayyooo”

Shikam zuciya D’aya ya shiga bandakin Bai d’auka tana ciki ba shiyasa ihun yazo Masa unexpected,yasa ya gigice, Sam Bai d’auka dalilin shigarsa bane yasata ihun,d’auka  yayi Koh wani mummunan abune ya same ta

Subhanallah Sumayya lafiya? yade?

yace Yana matsowa inda yaji ihun nata

“Wallahih Inka zo inda nake saina kwara maka  ruwan nan”,nace cikin tsawa Ina d’aukar bokatin ruwan wanka na in,damuwa na kawai na ja towel inda na makala a saman kofar band’akin,na d’aura

Sai yanzun ya gane dalilin ihun nata,manna Mata hauka kawai yayi ya Kama cire riga

“Wallahi ka fita a toilet innan na ratse Zan kwara maka ruwan nan”,duk tabi ta rikice

Ikon Allah waini idone Dani bare na kalli abinda kike boye wan

Kuturu,kawai nace,Ina daga boket in ruwan ganin Yana matsowa inda nake

Jii kawai yayi shaaaaaaaa Sumayya ta kwarara Masa ruwa,Bai d’auka da gaske take zata kwara Masa ruwan ba,

Nikam ganin Yana ta faman sharte ruwan fuskar sa yasa,na ruga zanyi waje da gudu Koh Kaya bansa ba ,

Ai.jin gudunta yasa ya bita shima da gudun 

Ina kokarin fita a band’akin kawai naji ya jawoni ciki, Allah yasa Ina kusa ta towel jawosa nayi a hannusa

Wallahih Sumayya baki Isa ba ki kwaramin ruwa Kuma ki.gudu

Ganin fa na shiga hannu,inda Allah yasoni ma na d’aura towel in”don Allah kayi hakuri yayan Khadija kuskure ne”

Kuskure ai baki isaba kinji na rantse

Kuka na fara ganinsa in yaci serious,Babu Wasa a fuskarsa da gaske yake b barina zaiyi naci bulus ba

“To Kayi hakuri”

Naki,ke Inna Miki Abu ai baki hakura

“Wallahih inayi kaji yayan khadija”

Bazanfa hakura ba malama

To me koma Zan maka Koh dukana zakayi ne?

Ah ah wanka Zaki mini

“Wanka”😳?

Eh Kinga Daman ba gani nake ba kullum.bayana baya fita

“Nima ai bana ganin bayana kuma ni ban iyya ma manya wanka ba”

Ah ah kina kallo Mana,Kuma Zaki koya

“Wallahih ni banason irin abinnan,  nace maka ka sakeni kanaji fa ana Kiran isha’i Kuma sai magana kake sani a bayan gida kasan ba kyau fa”

Tsakanin nida ke waya fara magana a ban d’akin nan tunda ba idone Dani ba, ba kallo Miki abin zanyi ba me na ihu harda kwara mini ruwaπŸ€₯

“Toh kayi hakuri kaji yayan Khadija wallahih mantawa nayi baka kallo”

Da gaske kina mantawa bana gani?

“Eh sosai ma,ai ba kowa.ke.ganinka yasan baka kallo ba”nace don ya barni

Ok wayo Zaki mini kenan harda wani yabona toh naki wayon in Kinga na barki kin fita toh kin zabi Daya a cikin ukun nan,

Koh ki wanke mini baya

Koh ki wanke mini Kai

Koh ki haske mini gemu

Lallai mutumin nan yaga wajen baccina nice ma Zan wanke Masa baya Kai Koh aski,

Toh Zan maka aski Amma sai gobe kasan yanzun dare ne bazaiyi kyau ba gashi ba NEPA Kai Kuma bakada shaver”

Kinyi Alkawari Zaki aske mini gobe?

“Eh”

Toh wanke mini

“Toh,ka sake mini hannu Mana saika zauna na wanke maka”

Na sakeki ki gudu

“Allah bazan gudu ba”

Ban yarda ba

Yace Yana Jan hannuta,ya zauna akan kujiran hannunsa na rike da nata

“Toh a hakan Zan wanke maka Kai kana rike da hannuna”

Ai Inna sakeki nasan guduwa zakiye

“Allah bazan guduba”

Toh tunda kikace Allah na sakeki,yace Yana sake Mata hannu

“Ina abin wanke Kai in”?

Gashe yace Yasa hannu a k’wandon soson nasa ya d’auko guntun soda,gashi nan

“Kana nufin da soda Zan wanke maka Kai”?

Eh man ba Yana kunfa da cire datti ba

“Uhmm Ina zuwa”,nace Ina kokarin nufar kofar band’akin

Kinye alkawari fa Zaki wanke mini,shine kike son gudu

“Abu Zan d’auko na dawo”

Toh yace Yana kokarin cire jikekken rigansa

Ina fita a band’akin na shiga d’aki bude akwatina nayi na d’auko Abubuwan wanke gashi, na Mata masu kyau da shaver,na dawo ban d’akin wayata na kunna na jinginasa da jikin gini matsowa  nayi inda yake zaune daga shi Sai wando dogo na jeans

Rangwafawa nayi na fara wanke Masa gashinsa sosai na zuzzuba Masa Abubuwan wanke Kai gashinsa mai yawa irin na Fulani,sosai ya fita nasa Masa Abubuwan laushin gashi cikin Yan minutes gashinsa yayi masifar kyau, shaver da na d’auko na saka Masa a fuska zan aske Masa gemu

Ke sumayya ragewa fa zakiye ba askewa ba 

“Na sani ai”nace Ina gyara Masa gashin gemun

Ina Gamawa nace NASA”ka duba Koh yayi”

Ina Naga idon dubawa sai dai na taba,ya Bata Amsa Yana tana fuskar sa, gaskiya kin iyya gyaran fuska

“Uhmm kasan me”?

ah ah saikin fada

“Ai…….ban karasa ba Jin ana kokarin shiga masallaci sallan isha’i yasa ban karasa maganar da nakeson Yi ba,

“kaYi sauri ka kwara ruwa ana shiga sallah”Ina maganar na fita a band’akin

Jin fitarta yayi wanka shap shap ya tafi masallaci

Yana fita ruwan wanka na Kuma ibo wa na Shiga band’aki,Ina wanka inata tunanin shin yau meke damuna ne Abubuwan da suka faru sai bani mamaki suke

Ina fita na shiga d’aki bayan nayi Alwala sallan nayi na kwanta akan kujira don yau ba karamin gajiya nayi ba don Koh girkin dare bansamu nayi ba gashi inason zuwa gidan Goggo Amina na duba Kan khadija yau kwata kwata ban ganta ba

Sai kusan 8 ya shigo d’akin, Sumayya kin kwanta ne?

“Eh Amma idanuna biyu”

Jin muryar ta saitin kujira,yasa ya nufo inda take 

Ina kallonsa harya ido wajen kujiran Yana kokarin zama mini akan kafafu da sauri na mike zaune na nade kafafun nawa”yanzun zama mini zakaye akan kafafu daban d’aga ba ka karyamin kasusuwa Koh me”?

Au kafarki nagun ne?ya  tamaya 

“Kaji nace maka Ina kwance sannan kazo zaka zauna akujiran”

Sanann yanzun kana tambaya ta Ina kwance ne”

Sorry yace Yana zama a inda ta d’aga kafartata, Sumayya!!

Na’am

Sumayya Ina Mai baki hakuri nasan tabbas band’auke Miki nauyin da ya rataya akaina a matsayina na mijinki b Ina Mai neman afuwanki wallahih Sumayya bani dashine shiyasa yau kwana biyu ban baki kome ba

“Ba kome ai nasan baka dashin ne sannan ni don na samu na sai Mana abinda zamuci ai ba kome wata Rana Allah zai baka kaima sauka sai mana”nace Ina kallonsa

Nagode Sumayya Allah ya saka mini da alkhari

“Ameeeeeen Daman jiranka nake kazo muje mu duba jikin khadija kasan yau ban samu zama ba tun safe”

Amma bakin gaji ba ki bari gobe Mana sai muje

 “ah ah  muje dai, gobe ma akwai masu zuwa kwalliyar bud’an Kai dana dinner har dare Ina busy”

Ok toh yace Yana mikewa

Hijjab nawa har kasa na d’auka nasa da karamin purse

D’aukar sandar sa yayi ya tsaya Yana jiranta a kofar d’akin

“Yau fa bazaka tafi da sandar nan ba atoh”

Akan me?

“Akan zaka fita Dani”

Ke asuwa?

“Asu masu ido” nace Ina kamo hannunsa ba musu  ya aje sandar

Tsaya na rufe kofar, yace

Sake Masa hannun nayi ya rufe mana kofar,Yana rufewa sake kama Masa hannun nayi Muka fita a shashen mu 

Tsakar gidan kaman ba dare ba duk jama’ar gidan na zazaune wasu a taburma wasu a kujira,nidai ganinsu baisa na sake hannunsa ba

Ke fasuma Wai me kika ganine a tare da miskini kike zaune dashi kamar auren tsafi,d’aya daga cikin Yan gidan Tama Sumayya gogar zana 

Ai toh auren tsafinne Mana inba haka ba mutun da arziki ya zabi Talauci,fasuma ta bata amsa..

Nikam ban tanka musu ba Donna fahimci Yan gidan nan sai shiriyar Allah don mutum Kam sai wani ikon Allah,tunda mutuwar inno Bai saka sun tsakaita da dambe da cacar baki ba ai hukuma ma bazata iyya dasu ba, kamar yanda Al’ameen yace

Waje muka fita,Ina rike da hannunsa muna tafiya,duk.inda muka wuce sai an bimu da kallo bare ga mazan unguwan da Basu sanni ba suna Daijin kwatance a bakin matansu,duk.madalisan da Muka wuce bin mu ake da kallo ga hasken sola ya haska Koh Ina, a hakan har muka shigo layin su Goggo Amina, na saima Khadija kankana da lemo,

da sallama a bakina na shiga gidan,don shi yace bazai shiga ba sai ammasa iso

“Assalamu alaikum”

Waalaikumu salam barka dai Sumayya sannu da zuwa Goggo Amina ta fad’a tana shimfid’a mini taburma

“Yauwa Goggo Ina wunin ku”

“Lafiya Alhamdulillah Sumayya kece da Daren nan”

Eh Goggo tare muka taho na fad’a Ina sunkuyar da Kai,(Wai kunyaπŸ€₯)

Shine ya tsaya a waje ai aikin muhammad kenan kamar gidan bakonsa ne,kice ya shigo

“Toh Goggo” nace na koma kofar gida

“Ka shigo”nace Ina juyawa

Toh kin hanani rike sanda sanna kin tafi kin barni

“Yanzun bazaka iyya shiga da kanka ba”?

Eh bazan iyya ba

Uhmm kawai nace na Kama hannunsa da yake dare ne koma ba NEPA sai da muka kusa isa kusa da Goggo na sake Masa hnnu,

Zama nayi a taburman shi Kuma ya zauna a kujira,

Goggon Ina wuni?

Lafiya Muhammad hala kunzo duba khadija ne?

“Eh wallahih Goggo shuru yau najita bata zoba shine muka taho mu duba Koh kan nata ne har yanzun”?

Wallahih Sumayya ta fad’amin abinda ya faru,zaman gidan mu sai hakuri kuma.ku Kara hakuri kinji kome zai wuce

“Ba kome gaggo”

Aiko khadija kam.na kwance a d’aki yau Koh fita batayi ba Kai na ciwo ga zazzabi duka,Daman khadija akwai raki ku shiga ku duba ta,inji Goggo

Mikewa mukayi, muka shiga d’akin

Khadija ce a kwance tana bacci,

Fita mukaye don bamu tashe taba 

“Toh Goggo zamu tafi ga wannan ba yawa Allah ya Bata lfy wannan Kuma 5k ne yayanta ya bani Wai na baki koh gobe saita je asibiti”nace Ina aje laidan da na shigo dashi,hade da mikawa Goggo kudin

Wai Al’ameen d’awainiyane har haka daka bare Koh chemist taje goben sun Kara Mata wasu magani Koh na 200 ma

Al’ameen Kam mamakine ya kamasa yaushi ya samu kudi har 5k da zai bawa khadija,Amma Sumayya tace in jisa,

“Goggo taje asibitin dai zaifi tunda jiya chemist in ta fara zuwa ba’a dace ba”na fada Ina taka kafar yayan Khadija Jin yayi shuru baice kome ba

Am am gaskiya ne Goggo ki karbi kudin inyaso taje asibitin

Amma kudin yayi yawa ai muhammad

Ba wani yawa Goggo In change ya rage ku rike zai D’an rage muku wasu Abubuwan 

Kai Amma mungode muhammad, Sumayya Allah ya saka 

“Ameeeeeen” har muna hada baki dashi

Fita mukaye daga gidan Goggo Amina kafun na rike Masa hannu

Jin tayi hanyar titi ba hanyar gida ba yasa yace Mata Sumayya Ina zamuje koma bafa nan bane hanyar?

Sai da Kai zanyi nace Ina tare keke napep…………

🏡️🏡️ *Gaisuwa na musamman da fatan Alkhari ga special FAN’S na MATAR MAKAHO Naga sakonku, Allah yabar kauna,Ina godiya* 🏡️🏡️

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

 *Contact them vie* 

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧 

Page3️⃣2️⃣&3️⃣3️⃣  

Keke napep na sayar ban kulasa ba

Hajiya Ina Zaki?Mai napep in ya tambaye Sumayya.

“MEGA restaurant” na basa Amsa

Ok hau muje

Sumayya restaurant Kuma?Koh dai banji daidai bane? Al’ameen ya tambaye ta

“Daidai kaji,yau agun zamuci abincin dare,banyi girki ba”

Sumayya ai akwai wajen Saida abinci Koh round about ana sai dawa basai munje restaurant ba.

“Nidai gun zamu Kuma sai kaje”   

Wai hajiya bazaku hau bane? Koh nayi tafiya tane? ,kun tsaidani Kuna Bata mini lokaci ga dare nayi  

“Yi Hakuri.

 yayan Khadija muje”  nace Ina Kama hannunsa muka shiga keken        

 A MEGA restaurant, Mai keke ya saukesu

Biyansa nayi kudinsa bayan mun sauka,Kama hannunsa nayi muka shiga ciki,

Al’ameen Kam binta kawai yake baida baki ,sai dai yaji sun shiga wani waje Mai mugun sanyi sai Kuma D’an motsen jama’a d’aid’ai ku

Har lokacin Ina rike da hannunsa,D’aya daga cikin kujerun dinning table dake wajen,na nufa ja Masa kujera nayi”ka zauna”nace Ina zama a nawa kujeran

Ok , yanzun cikin inda muke nan shine restaurant in? ya tambaye ta Yana zama

“Eh Mana Hala baka taba zuwa ba”?

Nasan restaurant Amma bana shiga.

“Toh yau ka shiga”

Waiter ne yazo, sannunku da zuwa mega restaurant,ga list nan ka duba abinda za’a kawo muku,yafada Yana mikawa Al’ameen Takardan hannunsa

“Yauwa bani Anan”nace Ina karban list in.

“Me za’a kawo maka”? 

Duk abinda kike so, Al’ameen ya Bata Amsa

“Tamabyar ka fa nayi”

Amsa na b’aki 

“Ok toh a kawo maka tuwo Koh shinkafa Koh doya”?

Aban doya 

Ok,mikawa waiter in nayi hade da basa amsa”ka kawo plate biyu D’aya na doya da miyar kaza,D’aya Kuma fried rice with chicken  yaji vegetable sosai,in Kuna da exotic a had’a mana da ruwa”

Ok ma, an gama,ya karbi takardan in ya wuce

Sosai mutanen restaurant in suka bisu da ido tun shigarsu kowa yake gulman su da ido wasu Kam har kasa hakuri sukaye sunayi da baki,abin mamaki ya Basu ganin matsiyacin MAKAHO Koh suturar arziki Babu a jikinsa,mace Kamar Sumayya tana rike da hannunsa Koh tantama Babu daga ka gansu kasan ma’aurata ne,Amma kallo D’aya zakama Sumayya kasan ba karamar classic bane 

Bayan an kawo Mana abincin,tura Masa nayi nasa a gabansa shukali na Mika Masa”ungo shukalinka abinci na gaban ka”

Abinci muka faraci a nitse idon mutane na Kan mu sosai har abin ya takurani

Sumayya!!

“Na’am”

Nikam wajen nan akwai mutane sosai ne?

“Eh akwai Amma ba sosai ba kasan yanzun dare ne”

Amma dai kallon mu suke koh?

Mamakine ya kamani Amma na maze, “ah ah ba Wanda ke kallon mu kowa harkar gabansa yake,Amma meyasa ka tambaya”

Jikina ya bani ana kallo nane tunda muka shigon nan

“Aiko ba Wanda ke kallon mu”,na basa amsa

Taima ke kike kallona.

“Akan me Zan kalleka Kuma”πŸ˜’?

Waya sani Koh kyau na Miki,Kinga dogon hanci

“Ina abin yake bare a yabasa”

Abinci muke ci muna Hira har muka Gama Amma dukan mu bamu cinye duka ba,

list aka akawo mana,na duba kudin mu dubu 3,800 ne, bude Purse nayi nabiya kudin, ordern ice cream nayi aka Mana takeaway a laida

Mamakine ya Kama Al’ameen yanzun abincin da sukacin nan shine 3800 ,ai cefenen dubu uku da dari takwas zai musu wata ma suna dafawa.

Suna fitowa a restaurant in ganin titi ba napep yasa Sumayya duba wayar ta

Karfe 10:3 na dare ne,”asaifa mun jima a wajen nan 8 fa Muka bar gida”

Gaskiya Kam Kuma bana majin dirin machine sai mototi

“Ba machine Kam sai dai mu taka da kafa”na basa amsa Ina Kama hannunsa muna tafiya inda Allah ya somu ma tsakanin sintali da mega ba nisa sosai 

“Nikam azumi saura wata nawane”?

Saura sati nawa dai?ya Bata Amsa

“Satitika kenan baikai wata ba?Ashe shiyasa aketa aure aure”

Gaskiya Kam saura sati uku da kwana hudu

Lalle kam,”kasan yanzun haka gobe, za’a yi bud’an kan Amarya da yamma,sai ayi fitan Angonci duka,da dare Kuma dinner,Kuma nice duka Zan musu kwalliya, shiyasa nake son in Allah ya kaimu gobe sai ka nemo mini yaro yaje Mana kasuwa Ina son Gama girki da wure”

Yaro Kuma wani yaro.kike ga Zan iyya aika a unguwan mun nan har kasuwa ,sai dai naje kawai tunda khadija ba lfy.

“Toh Allah ya kaimu,ni chemist ma nakeson mu shiga nasai maganin gajiya,Amma dare yayi”

Ah ah Sumayya da kankantan shikarunki karki Bata shi dashan maganguna, don kina aikin gajiya,in Kika riga Kika saba,toh zai biki Koh yaushe kikaye aiki sai kinsha 

“Gaskiya ne Amma wallahih bayana ya tokare ni sosai,gashi yanzun ma sai tafiya muke da kafa”

Da kafa suka taka har sintali suna tafiya suna Hira,Dayake gidan Adara ba’a rufesa Koh karfe d’ayan dare ne yasa suka samu kofa a bude,

Shigan su, suka shige shashen su bakin su d’auke da sallama

Al’ameen ne ya bude d’akin 

Muna isa ruwa na iba duk yanda nake tsoron toilet in dare yayi Amma zafin da nakeji Bai barni naji tsoron ba,

band’akin na shiga na kwara ruwan na fito,

d’akin na shiga.

Al’ameen na zaune a Kan kujera Yana jiran Sumayya ta fito shima ya shiga Wanka don yaukam ba NEPA an d’auke

“Assalamu alaikum”nace Ina shigowa d’akin

Waalaikumu salam, gaskiya yau Kam Alhamdulillah akwai.zafi Kam

“Gaskiya ni a waje ma zanyi shimfid’a yanzun”

Ok.bara nayi wanka daidai kinyi shimfid’ar?yace Yana fita a d’akin ban d’aki ya shiga bayan ya ibi ruwan shima

Yayan khadija na fita na saka.kayana saboda zafin da ake have vest na saka ,da wandon bacci fankalele shara shara har kasa,kayan shinfid’a na fitar na shinfid’a mana darduma a baranda na shinfid’a zanin gado da filoluka, kwanciya nayi a gefe tsabar gajiya Koh hula ban saka ba,bayana sai damuna yake koh bacci na kasa.

Yana fitowa d’akin ya shiga 3quiter yasa Koh riga baisa ba ya rufe kofar, ya nufi inda yake kyautata zaton agun ta musu shimfid’a

Ina kwance Ina kallonsa harya matso inda nake kwance hannu yasa ya tattaba shimfid’ar sai Kuma ya fara laluben Kan shinfid’ar  bayan ya xauna.

Jin ya tabata yasashe Hawa Kan shinfidar kwanciya yayi a Gefen pillow n da ta d’aura kanta akai

“Bakaji pillow da na aje maka bane”

Naji Mana Amma a naki nakeson kwanciya

“Kaga ka rabu Dani jikina ciwo yake mini”

Hannu kawai naji yasa a bayana Yana mammatsa mini baya,naso hanasa amma Jin yanda message in ke kauda tsamin da bayana yake mini yasa nayi Shuru

Yana ta mamatse Mata baya da kafa duka har yaji tayi bacci, gyara Mata kwanciya yayi,daga kefuwarda tayi shima ya kwanta a Gefen ta bacci ya d’aukesa.

Misalin karfe biyu na dare ya farka Jin iska na kad’awa ga kamshin kasa na tashi bude ido yayi sosai, ya mike zaune hannu yasa ya taba Sumayya Aiko tana kwance Koh juyawa Bata sake ba tun gyarata da yayi, Sumayya!! Sumayya!!

“Ummmm menene”nace cikin magagin bacci don harga Allah yau dai baccin gajiya nake

Ana iska ga hadari,ki tashi mu shiga d’aki

“Da wani idon kaga hadarin ni wallahih ka barni nayi bacci”,na fada Ina gyara kwanciya

Sumayya ruwane fa da gaske

Shuru na Masa abina na koma bacci 

Jin Taki tashi yasa ya mike key ya d’auka ya bude d’akin, d’aukarta yayi a hannu a hankali yake tafiya Yana lalube harya shiga da ita d’akin,Kan gado ya haura ya kwantar da ita,Jin an Soma yayafi da sauri ya fitoh a d’akin shimfid’ar su ya tattara ya Kai d’aki randar robansu ya zubar da ruwan ya hada da bokataye ya jejjera a bakin baranda,daidai lokacin aka fara ruwa sosai Kamar me .

Alwala yayi ya shiga d’akin sallaya ya d’auka ya shimfid’a wa yayi ya Tada kabbara,lafilfilu yake har kusan karfe uku na dare kafun ya kwanta shima a gefenta 

 *Washe gari*

Kamar kullum yaukam da safe kudi na basa yasai Mana manya manyan gongomin Madara da bornviter  na sai suga Rabin kwano Lipton kwali d’aya na had’a da cornflakes,dashi muka karya ya fita

Al’ameen kam yasan baida abinda zaiyi haka ya fita yaje ya zauna a bakin titi ya rasa mafita Allah ya gani Yana iyya bakin kokarinsa wajen niman abinda zai rufawa kansa asiri,Amma abin yaki yasan kome na Allah ne Kuma Bai manta dashi ba a hakan ma yana kara godewa Allah tunda Sumayya nada rufin asiri da ace Bata sana’a a war yanzun da kayan abincin ta ya fara karewa baisan yanda zaiyi ba.

***********

Khadija ce ta shigo bayan sallan azahar lokacin Ina kanwa matan da suka zo make-up, Assalamu alaikum

“Waalaikumu salam” dukan mu muka amsa Mata

“Ah ah khadin Goggo idonki kenan”?nace Ina kallonta sanye take da atamfar dana Bata riga da zani sai gyle da takalmi harda jaka sai laida Mai tambarin asibiti a hannunta sosai tayi kyau fuskarta tayi fayau alamu dai batajin dadi,abinka da farin fata

Wallahih Aunty na fitoh asibitine nace bara dai nashigo yau Goggo takece mini kun shigo da dare Ina bacci.

“Eh wallahih mun shigo da yayanki nace abarki kawai kar a tasheki”

Allah sarki,tace tana gaida matan dake zazaune suna jiran na Gama wa Wanda

 nakema make-up 

“Khadija ki shiga d’aki Mana akwai NEPA ki jona kittle akwai kayan shayi asaman freezer”

Aunty bazan iyya shaba bakina ba dadi Sam shiyasa koh abincin dare ban iyya ciba Haka karyawa ma.

Ah ah khadija dadai kin daure kinsha shayin Daya fi Amma ace bakinki ba Dadi saiki kicin abinci,ai ko magani in ba abinci baya aiki,D’aya daga cikin customers nawa ta fad’a

“Gaskiya ne  khadija,ki shiga in kinsha saiki kwanta ki huta”

Toh Aunty tace tana shiga d’akin, kittle in ta d’auko ta zuba ruwa ta jona,shayi ta hada kad’an ta iyya Sha ta balle maganin Tasha  kwanciya taye  lokaci D’aya bacci ya d’auke ta

Sai kusan 4:30 na Kamala wa sauran kwalliyansu Daman Amarya tun 3 na yamma na Gama Mata saboda bud’an Kai,

Gaskiya yau  na damki rabona mutane kusan goma nama makeup heavy make-up

Simple make-up

Light make-up

Duk yau ba Wanda banyi ba sosai na samu kudi 50k yau na damka nan ma banyi na dinner ba kenan.

Misalin karfe biyar khadija ta mike zata wuce gida Aunty nikam Zan wuce sai gobe 

“Toh khadija Allah ya Kara lafiya ga wannan ki D’an samu abinda kike bukata ki Saya dashi” nace Ina Mika Mata 10k

 Aunty ki barshi kawai d’awainiyar tayi yawa jiyama fa Goggo tace mini kun kawo Mana 5k naje asibiti danaje in ma,Ina saurayin da nace Miki yazo guna?

“Eh na tuna har kikace bazaki fita ba”na Bata Amsa

Ashe Dr ne Ina zuwa na gansa shine ya sayo mini magani  kyauta,

“Allah sarki, Allah ya saka Masa da alkhari”

Ameen Aunty

“Wancan yayan kine ya baki wannan Kuma nawane,ki karba khadija kid’an Saya Abubuwan da baki dasu”

Gaskiya Aunty nagode Allah ya saka da alkhari,tasa hannu ta karbi kudin

“Ameen khadija”

Yauwa aunty nace Koh Zaki aje mini tunda Naga azumi ya kusa Inna tashi zuwa kasuwa saina karba naje na sai kaya,samun na samu dinki da wure?

“Ah ah khadija insha Allah, Allah zai Bud’a Mana har yayanki ya sai Miki kayan Sallah, wannan dai ki sai Abubuwan bukata irinsu kananan Kaya da mayuka Turare pad omo sabulu ke dai irin Abubuwan bukatar Yan Mata haka”

Toh shikinan Aunty Daman bani da kananan Kaya sai na saya pant biyu Brz sai vest shima biyu Amma na gwanjo Zan Saya aunty sauran chanjen, Ina materials da ake yayi yanzun ana yankawa a dinka dogayen riguna dasu?

“Eh khadija”na gane su 

Yauwa yadi d’aya dari uku su Zan Saya kala biyar na dinka 

“Gaskiya khadija kinye tunani Mai kyau kema saiki samu na chanjawa kwana biyu”

Toh Aunty Zan tafi nagode Allah ya Karo customers

“Ameen khadija yanzun ma wasu na zuwa da dare maganar dinner aike alkhari ce tunda sanadin ki nake samun kudin”

Ah ah Aunty Allah ne ya tsaga da rabonki , shiyasa kike ci

“Hakane Kam khadija” nace Ina shiga kitchen da sauri nake na d’aura Mana abincin da zamuci

Bayan fitar khadija girki na Gama na juye Mana a kula,sai goshin mangari ba yayan Khadija ya dawo

Sumayya sannu da gida?

“Yauwa sannu yayan Khadija sai yanzun”

Eh wallahih ya aiki?

“Lafiya klau” nace Ina kallon sa ganin Kamar a cikin damuwa yake

D’azun Bashir wani makwancin mu ke tambaya ta Wai MATAR sace taji labarin Wai kina lalle ke kikama Asma’u na aure shine Wai yake tambaya ta zata samu lalle gobe,make-up jibi da Rana?

nace ya bari saina tambaye ki inyaso in mun hadu a masallaci anjima na fad’a Masa amsar ki.

“Lallen me za’a ma MATAR tasa”?

Suna ne haihuwa tayi jibi suna

“Gaskiya nifa bazanje home service ba,in mutum nason lalle Koh kwalliya yazo ya same ni a gidana”

Amfa Sumayya haihuwa ne ya za’a yi mace maijego tazo lalle gidanki?

“Wallahih yayan Khadija ni raini ne banaso a rayuwa na kar mutun yaga kaje Masa lalle ya Raina ka” 

Kai Sumayya ba wani raini ai sana’a ce ta kaiki ba maula ba,ki daure kije ki Mata kinji?

“Shikenan Allah ya kaimu goben Amma bansan gidansu ba da yamma ta tura yaro yazo ya kaini”

Sumayya har yamma?ya tambaye ta

“Eh man saina Gama aikina,Koh so kake na tafi da safene,jibine fa sunan”

Toh shikenan Allah ya kaimu yace Yana mikewa ,ruwa ya ibo a boket ya shiga bandaki

Muna idar da sallan mangariba Koh abinci bamu ciba Yan make-up na dinner suka zo su biyar ne dukansu harda Amarya heavy make-up suke so,Dole tasa na hakura dacin nawa zuba Masa nayi na d’auko Masa ruwa a freezer na jira Masa,a d’aki na fitoh waje,don ni bana saka baki a dakina Sam kowa ya zauna a waje kawai

Sai da yaye isha’i kafun ya shigo gidan, gaisawa sukaye da customers nawa,don na fahimci yanzun mutane na ganin kirmansa tunda kofarsa suka shigo

“Abincin ka na d’aki yayan Khadija”nace Masa ganin ya nufi d’akin kar yaje ya zubar da abincin tunda a kasa na jira.

Toh yace Mata Yana shiga d’akin

Make-up na Amarya na fara, Gamawa ta biyani akazo aka d’auketa saura hudun ma duk na Gama musu kafun 9:00,kudin da suka bani 25k Inna hada Dana d’azun kusan dubu saba’in na samu kenan Alhamdulillah yau kawai na tashi da kudi dubu sittin da biyar in aka cire 10k Dana bawa khadija

Wani tunanine ya fado mini akan kudin, murmushi kawai nayi na nufi d’akin

Ina bude labulin idona ya sauka Akan plate inda nasama yayan Khadija abinci nakai dubana garesa da mamaki ganinsa a…………..

 *My Real and special Fan’S* 

 *Princess* 🏡️

 *Maryam najibu* 🏡️

 *Mummy*🏡️ 

 *Shamsiyya Gombe* 🏡️

 *Ummu na’eem*🏡️ 

 *Faeexetion* 🏡️

 *Zainab*🏡️ 

 *Bebi* 🏡️

 *Maman khairat*🏡️ 

 *Oum Abdullahi*🏡️ 

 *UMSAD INCENSE* 🏡️

 *Ummul husnah*🏡️ 

 *Duk Naga comments naku Allah ya bar kauna Nima Ina yinku* 🏡️🏡️

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna  bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧     

πŸ€ *Wannan shafin  sadaukarwa ne gareki haj j Aisha Ahmad Allah yabar kauna* πŸ€

Page3️⃣4️⃣&3️⃣5️⃣     

Al’ameen ne, Sumayya ta gani zaune ya zuba tagumi Koh abincin Bai d’and’ana ba.

Cikin mamaki ta karaso cikin dakin”yayan Khadija lafiya kuwa”? tace tana matsowa kusa dashi  

Firgigit ya dawo hayyacinsa,  Sumayya har kun Gama kwalliyar?

“Eh mun gama,Naga bakaci abincin kaba Allah dai yasa lfy Koh” ta Kara tambayar sa.  

Lafiya Sumayya jiranki nake  in kuka Gama saimuci”ya Bata Amsa

Da mamaki sumayya ke kallonsa”banace kaci ba”? 

Sumayya na kasaci ne, kece Kika nema Kika dafa Taya zanyi na rigaki ci bayan ke kina ta faman aiki.

“Karka Kara fad’amin irin wannan magana daga yau”

Don me?ya tambaye ta

“Saboda duk abinda na baka ni gani nake kamar kaika bani mukeci banason Kara Jin irin maganar nan,Ina zaune itdakai ne badon kome ba sai don Allah,rufin asirin ka nawa ne nawa nakane”ta fada tana kallonsa

Shikenan Sumayya nagode,

“Bana bukatar godiyan ka ka gode Allah”tace tana matsowa kusa da abincin budewa tayi tasa shukali”Bismillah muci”tace tana iba 

Toh yace Yana laluben nasa shukalin

Abinci sukaci Amma cikinsu Babu Mai magana kowa Yana cin abinci ne,bare Hajiya sumy 

Suna Gama cin abincin Al’ameen ne ya tattara Kwanukan yafita dasu waje 

Sumayya Kam wanka ta shiga,tana fita tayi Alwala,kayan bacci tasa ta kwanta 

Al’ameen Jin ta kwanta yasa shima fita wajen ruwa ya Iba yayi wanka.kamar yanda yazamo musu Al’ada wankan dare kafun su kwanta,Yana fitowa ban d’akin kofar shashen su ya rufe,ya shigo d’akin,rufewa yayi a hankali yake takawa Yana laluben gadon harya iso, Hawa gadon yayi ya kwanta a hankali,

Sumayya Kam mamakine ya kamata ganin sa a hakan Sannan yahau gadon ma Bai Saba Mata yanda yake Mata ba, watoh son mannuwa kusa da ita.

A hankali ta mirgina kusa dashi hannu tasa ta Kama NASA hannun”yayan Khadija”

Cikin sanyin halinsan nan ya amsa mata, na’am.

“Menene yake damunka ne Wai” ?

Ba kome Sumayya me Kika gani?ya tambaye ta Yana Mai dagota ya d’aurata a jikinsa gabaki d’aya

“Ba kome, yauwa nace kanada National ID card ne”?

Sai dai voters card bani da National ID card

“Ok shima zaiyi Daman inason na bude account a bank ne kasan banzo da details nawa ba”

Toh shikenan Allah ya kaimu goben saina baki 

“Zaka rakani bank in? Koh naje da kaina”ta fada tana gyara kwanciyar ta akansa 

Duk yanda Kika gani goben ne Zaki bank in Koh yaushe?

“Sai na Gama lallen da akayi booking innan”

Toh shikenan Allah ya kaimu saina rakaki,in khadija taji sauki Kuma sai kuje tare kinsan me?ya tambaye Sumayya

“Ah ah”

Khadija na son zuwa bank Kamar me haka lokacin kudin covid 19 ta dameni Wai sai naje mun bude account muma,mun cika Koh zamu samu kudi,Amma da mukaje bank hanani Shiga sukayi security Wai ba’a bara a banki,Kuma su tsaya su saurare mu sunki Haka suka kuramu waje.

Sosai naji maganar ta tabamin rai”aiko Insha Allah da ita zani taga bank,Amma kaima fa Dole zamuje tare tunda account Kai za’a budewa ba niba.

Toh Allah ya nuna Mana yace Yana zura hannunsa a cikin rigan bacci dake jikinta

Jin hannunsa a riganta unexpected yasa ta zabura sai Kuma ta koma ta kwanta a hankali ta lumshe ido Jin abinda yake Mata da hannunsa a cikin riga”kasan me”?

Ah ah ya Bata Amsa

“Nikam Ina ga Zan Saida laptop Ina da waya”

Akan me Zaki saidasu toh?

“Saboda Banga amfanin suba inba kallo ba me nake dasu shiyasa Zan sayar”tace. Tana taimaka Masa ganin Yana kokarin zare rigar Tata

Umm umm Sumayya waike bazaki ringa d’aukar kwalliya kina sawa a media ba Koh Allah zaisa asamu location naki Kinga ai sai afi saninki sosai a Jala

“Kasan ba kowa keson  asa hotonsa a social media ba shiyasa ban fara posted ba,Nima nayi wannan tunanin”

Eh ai tambayan su zakinayi Zaki d’aura hotonsu kiyi Tallah Amma fa Yan Mata banda matan aure, insun Amince shikinan,tunda wasu da yawa in sunyi kwalliyar ma post suke.

“Gaskiya ne Amma waya fad’a maka ana d’aura kwalliya a online?

Kuma ya akayi kasan ana Post”?Sumayya ta tambaye sa tana kakkama Masa gashin kai Jin wani magic dake bin jikinta a sanadin abinda yake Mata

Uhmmm ai inaji ana Hira koma ni lokacin da na makance ma waya tayi araha a hannun kowa ba,Kamar yanzun

Washhhh toh,uhmm tace tana zillewa daga kansa ta sauka a gefe.

Jin ta zame yasa ya bita shima, tana kwanciya ya kwanta akanta rumfa ya Mata da kirjinsa,ya had’a fuskarsa da Tata fuskar yayi Yana tsintsinar bakinta,dake kamshi 

“Wayyo ka sauka nauye”tace tana mutsu mutsu tana damke damtsen hannunsa

Shagwaba Koh bafa nauyina na d’aura miki ba

“Nidai ka sauka,kawai tsoro nakeji”

Tsoron me?ko ni dodone?ya tambaye ta Yana Mai Kara matsota garesa

“Ka sauka”

Naki,yace Yana Kara Danna kansa akanta

“Nifa bacci nakeji kaji muye bacci”

Nikam banajin bacci

“Nikam ai inaji Koh”?

Sai kiye ai na hanaki ne?

“Amma ai ka tokareni”

Shuru ya Mata yaki kulata sai bidirinsa yake a kanta jifa jifa tana taimaka Masa 

Jin abin NASA ya fara yawa yasa ta fashe Masa da kuka

A tsorace ya mike a kanta sauka yayi gefe cikin tsoro,yake tambayar ta,ke Sumayya menene,Yana tattabata yaji Koh lfy

Saura kad’an dariya ya kubucewa Sumayya Jin yanda duk ya tsorata dagajin kukanta kawai,ta rasa ma wani irin namiji ne Mai shegen tsoro haka

“Toh ba Kaine ba nace maka inajin bacci sai matseni kake”ta fada da muryar kuka tana kallonsa tana Masa gwalo ganin yanda sai zazzare ido yake kamar kace kittt ya ruga

Shine abinda ya saki kuka?

“Eh Mana”

Toh Yi hakuri kwanta toh.

Dariyace ta subuce mata Jin abinda yace Yana kwanciya a gefenta baima mannu kusa da itaba

Cikin mamaki ya Tashi zaune Jin tana dariya, Sumayya Anya lfy kuwa daga kuka saiki koma dariya?

Shuru tayi gudun karya harbo jirginta”babu kawai ji nayi kamar jakulkule ake mini a ciki”

Shuru yayi baice kome ba illah rufe ido da yayi Yana nazarin Rayuwa yau Wai shine da Mata,Ashe haka zama da mace yakeda Dadi duk halinda kake ciki muddin ka samu mace na gari ka Gama samun Jin dadi,duk halinda namiji zai shiga mundin dare yayi zata ga tayi kokarin kauda damuwar tasa Koh Bata cireba,zatayi iyya bakin kokarin ta taga ta d’auke Masa hankali

Jin yanda Sumayya keta motse yasa shi kiranta, Sumayya!!

“Na’am”ta amsa tana gyara kwanciya

Bakiyi bacci ba?

“Umm banyi ba”

Saboda me?

“Haka kawai”

Jin Amsar da ta basa yasa a hankali ya matso gareta,lumshe ido tayi Jin yanda tsikar jikinta ke tashi,Jin gashin kirjinsa na goguwa da bayan ta

Hannu yasa a hankali ya Kama waist inta d’an zabura tayi kad’an,yasa hannu ya maidata,watoh kukan shugwaba Koh?

“Bawani shugwaba,Kuma ni ba shagwabebbiya bace atoh”

Shugwabebbiyace Mana ai duk lukutaye akwai shagwaba

“Waye lukutar”?ta tambaye sa tana juyowa suka fuskanci juna

Daga Sumayya har Al’ameen wani yanayi sukaji a tare da junan su sosai kusancin su yayi yawa akwance da suken nan

Kece Mana, lukuta kiga nan naki fa Kato,yace Yana Kama Mata bombs,

Hannu tasa ta buge Masa hannu”ai naka yafi nawa girma”

Zare ido yayi Kamar tana ganinsa,ai Dana shiga uku ai,sai wando Mai shape za’ana dinka min.

Hhhhh Sumayya ta Kama dariya “Wai wando Mai shape waya ganka kana tafiya kana murgud’asu a cikin jallabiya”ta karasa maganar da kamo hannunsa dake Kan kirjinta don wallahih kirjin zafi yake Mata 

Shi Karan kansa Al’ameen abin sai da ya basa dariya,Amma yakiye, murmushi kawai yayi,Jin ta Kama Masa hannu kafarsa ya daura Mata akan kafa.

Kokarin mikewa ta fara har lokacin hannunsa na rike a nata Wai don karya taba Mata inda bataso

Jin tana kokarin tashi yasa sa tambayar ta,Ina Zaki Kuma dare fa yayi.

“Rigata nake nema”

Kiye me dashi?

“Me ake da riga”

 Sawa, ya Bata Amsa

“Nima sawan zanyi”

Nikam gaskiya banso kawai mu k’wanta haka.

“Jikinka Koh nawa?wato mu k’wanta haka ka karasani ba”

Sorry zafi yake mikine?

“Eh Mana duk ka mammasa mini jiki”

Amma ai kinji Dadi

“Banjiba”ta basa amsa tana mikewa zaune

Ai da sauri yasa hannu ya rike Tata hannun,yana kwance  Bai tashi ba,kiyi hakuri mu k’wanta haka ba abinda Zan sake Miki.

“Ai kasan bakyau kwana ba Kaya”

Menene a jikinki Koh tsirara kike yanzun?

“Rigan fa”

Ai nace bazan miki kome ba yace Yana jawota jikinsa matseta yayi a hankali ya jawo blanket inda ke Kan kadon ya rufe jikinsu.

***********

Washe gari Kamar kullum bayan Al’ameen ya dawo sallan asuba, sunnah TV Sumayya ta kunna musu daga ita harshi in suna kwance suna sauraron wa’azi.

Sai wajen 7:3pm Sumayya ta mike shara tayi yayan Khadija ya Mata wanke wanke, ruwan zafi ta jona abuta,Yana tafasa ta juye a boker tasawa yayan Khadija nasa, ta shiga ban dakin

 tana fita yayan Khadija ma wanka ya Shiga.

Vayan sun Gama shiryawa kudi ta mika masa 1k”ka sai Mana egg’s guda biyar sai bread na 500 Mai kyau ka hada Mana da butter “

Karban kudin yayi,ya fita.

Bayan ya sayo k’wai da bread, soya k’wai in Sumayya tayi ta hada musu cornflakes ga tie,jira musu tayi a kasan cafet,kamo hannunsa tayi suka zauna a kasa, bubude abincin tayi”karbi shukalinka”

Toh yace Ya karba shukalin ,tattaba plates in yayi Jin plate biyu ne ga bowl d’aya ga cups biyu,wannene abincin nawa Naga Kwanukan da yawa?

Duka zakaci d’ayan soyayyen k’wai ne d’ayan bread ne da butter a jikinsa sai Kuma bowl na cornflakes,sai cups na tie”nace Ina tura Masa plate in k’wai a gabansa”kaci kwai sai kana Had’awa da tie ga bread”

Shikam Al’ameen ya kasa magana Wai karyawane da abinci Kala uku shi Al’ameen,ganin Al’ameen bai fara ci ba ita har tayi Rabin cup na tie inta yasa ta aje kofin,hannu tasa a cikin k’wai in ta yagi babba ta tura Masa a baki

Shikam Jin abinci a bakinsa da Kuma yatsarta sai faman tura Masa take yasa sa cizon yasan kad’an,

Ai Kara ta sake hade da yarfa hannun nata”wayyo yatsana jini jini yake na bunu tace tana duba hannun”.

Da mamaki Al’ameen yace jinii ma Sumayya?

“Eh gashi shikinan ya gusuramin yatsa”

Mu gani

“Bazaka gani ba sai kace idone da kai”

Toh muji.

Bazakaji ba din,tace tana daukar kofin shayen ta

Jin tayi Shuru yasa sa gutsurar bread Mai butter,Wai zai Bata itama d’ayar hannun nasa yasa ya lalubo fuskarta,Jin fuskar Tata yasa ya fara lalubar bakinta da hannunsa

“Kasan Allah Inka samin hannun hagunka a bakina ba”tace ganin Yana ta tattaba Mata baki da hannun nasa

Kayya abinci Zan baki,yafada Yana Mika Mata gutsuren bread inda ke hannun damansa a baki,

Rufe bakin tayi Taki budewa.

Shikam sai goga Mata bread in yake a lebe gashi duk butter ya Bata Mata fuska

“Kanata Bata mini fuska da butter”tace bayan ta rike hannunsa

Toh ba kinki bude bakin ba sai kokari nake,

Kaga kaci abincin kan, ka barni naci nawa,tace Masa tana goge fuskar ta 

Toh ki bare na baki wanann kawai kinji

Ganin yanda ya nace Mata yasa ta bude bakin Yana saka Mata bread in da sauri ta datse hakorin ta,Wai don ta cije yatsarsa shima abin mamaki da sauri taga ya cire hannunsa kafun ma hakorinta ya Sauka akan yatsar,Yana dariya

Ai Daman nasan saikince Zaki Rama shiyasa Nima nayi taka tsamtsam da yatsana.

Shuru ta Masa Bata tanka masa ba.

Haushi ya shigane bakutuwa?

Kara ta sake tayi kansa “nice bakutuwa”

Jin ta hafto, yasashi Kare kansa, hannu yasa ya tare fuskarsa.

Ganin haka sai abin yayi mugun Bata dariya waishi harga Allah tunani yake wani abin zata Masa haryana tare fuska.

Jin shuru baiji tayi Masa kome ba yasashi fara laluben ta Aiko ya jita a kusa dashi,da sauri ya rikota, sorry kinji

“Ni……shuru tayi Bata karasa ba Jin sallama a kofarsu amsawa tayi ta mike kaci abincin kafun na dawo”

Toh yace Yana saka hannunsa ya d’auki cup inda ta aje masa…

Sumayya tana fita taga wata budurwa irin classic innan zata Kai kusan sa’ar ta kyakkyawace Amma baka Tasha kwalliya tana rataye da school back “sannuki da zuwa”tace Mata tana shimfid’a musu darduma”Bismillah ki zauna”

Yauwa Ina kwana?bakuwar tace tana zama akan sallayar

“Lafiya ykk ya gida”?

Lafiya Alhamdulillah,ya aiki?

Lafiya klau,Ina zuwa Sumayya tace tana mikewa d’akin ta shiga ta hada cornflakes da ruwa  Daya a fijrij ta hada a tire ta kawowa bakuwarBismillalahih ka  abin Kari ba nauye Kam”tace tana ajemata a gaba

La d’awainiyane haka Allah dakin barsa yanzun na fitoh gida zanje school ne ma nace bara na biyu dai ta gidanki

“Allah sarki Amma dai ki saka Koh albarkane yafi dai kikici bazanji Dadi ba”

Shikenan bara dai NASA albarkan tunda kin Masa tace tana iban cornflakes in da shukali uku tayi tace Alhamdulillah

“Badai harkin koshi ba”?

Alhamdulillah wallahih ya isheni,suna na kamila Ina zaune a unguwan gadi,Daman nazone wajen ki in Babu damuwa inason zan fara Training in make-up,Naga wanda kika ma kanwata a auren Asma’u shine nace tamin kwatancen gidanki  inyaso sai nazo inji.

“Toh gaskiya ni bana koyarda make-up saboda bani da shago sai gidana Kinga Kuma Ina da ayyuka yau da gobe”tace Mata tana tunanin ta yarda ne Koh karna yarda

Ba damuwa sister Nima Ina zuwa school Kinga saiki bani time inda zanna zuwa Koh ki ban number ki duk lokacin da kike free sai ki kirani Koh Kika samu Yan make-up.

“Shikenan yanzun dai ki bare Inna ma mijina magaa in ya Amince xakiji daga gareni”

Ok ba damuwa saiki bani contact naki Koh in ba damuwa sannan nawane kudin da Zan biyaki Kinga Inna koma Koh yaushe Kika kirani saina tawo dasu

Toh, make-up dai kashi kashine sanann yanayin kwakwalwar mutum wata a wata D’aya zata koye make-up wata biyu wata fiye da uku ma Bata iyya ba so ni bansan ya yanayin d’aukar kwalliyarki ba Amma dai inso samune wata uku kina koya”

Ok yanzun wata ukun nawa ne kudina

“50k Koh wani wata kudinki na wata uku 150k kenan”

Wai habba sister kudin nan yayi yawa Mana dubu dari da hamsin,

Gaskiya kenan Kinga a cikin kudin Zan Saya make-up kit sabo duka,saboda bazaiyu Ina baki na aikina kina koya dashi ba, sanan infa kika iyya a kwana uku Zaki iyya samun sama da kudinda Kika biya na koyo”

Hakane Kam Amma dai ki duba ki rage mini kinsan baban mu yace in zaiyu nida kanwata zai biyawa.

“Shikenan Zan rage dubu goma”

ok shikenan an gode saina jiki

Shikenan bara na baki number,daidai lokacin Al’ameen ya fito d’akin hannunsa rike da cup inda yasha shaye

What?? wa nake ganin nan Kamar  Muhammad Al’ameen Yusuf bakuwar tace tana zare ido

A matukar razane har bakin sa na rawa yace kamilaaaaa………..

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincenseIG @umsadincense *IG πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa πŸ‘Œ

free book 🀧     

Page 3️⃣6️⃣&3️⃣7️⃣

Kamila kice Koh dai Mai irin muryar tane, Al’ameen yace cikin d’unbin mamaki

Ikon Allah Ashe da rabon za’a sake ganin juna Muhammad,kamila tace tana me Kara kallon Al’ameen

Wallahih fa kamila yace Yana isowa kusa dasu sumayyar

Oh duniya Muhammad Daman a unguwan nan kake?

Anan nake kamila,ya bayan rabuwa ya maigidan ki da yara?

Jiki a sanyaye kamila tace,hmm muhammad mijikam aure ya kare, yara Kuma Allah Bai kawo ba tukum.

Allah ya kawo masu albarka

Ameen Muhammad,Amma nayi mamaki wallahih wannan ce matar ka,ta fad’a jikinta na Kara sanyi tunawa da abinda ya faru a shikarun baya da suka wuce

Eh kamila matatace sunanta Sumayya

Masha Allah gaskiya matakam tabar kalla Masha Allah wallahih gata kyakkyawa son kowa kin Wanda ya rasa,tace tana kallon Sumayya har lokacin

Haka Allah yake abinsa sai ya baka abinda baka taba tunani Koh tsammani ba, shiyasa duk abinda bawa ya samu a rayuwa rabonsa ne ba Mai hanasa muddin Allah ya basa

Gaskiya ne muhammad,Aiko shikenan Daman kwalliya nazo tambaya Allah dai yasa madam in zaka barta ta koya mini,tace tana Mai Al’ajabin Rayuwa

su kamila kenan yaushe Kika dawo Jala ne?

Shap aini na jima a Jala, Amma Dad nawa transfer mun dawo nan

Allah sarki toh ya gidan naku da aiki?

Gida Alhamdulillah aiki Kam Babu sai karatu.

Karatu Kuma,kamila?

Eh Mana ai kasan bayan rabuwar mu aure nayi sai karatun ya tsaya sai yanzun na samu na Shiga TSU 

Gaskiya ne Allah ya bada sa’a..

Ameen, muhammad Kai ya lbrn karatun?

Kai kamila wani karatu Kuma makaho talaka zaiyi ba kudi ba ido ya fad’a Mata maganar cikin murmushi

Sosai taji wani abu ya Tukare Mata makoshi Jin kalaman da ya fad’a ya tuna Mata da kuskuren da ta tafka a rayuwar ta tabbas Al’ameen Mai hakuri ne da wanine haduwarsu yanzun bazai ma saurare taba

Cikin sanyin jiki tace,toh nikam Zan tafi Sumayya saina jiki Koh,ta fad’a tana kallon Sumayya dake zaune a Kan darduma

Sumayya Kam ba karamin haushi taji ba Kamar ta tashi ta Basu waje, Amma saita maze gudun karta bada kanta agun kamila,”yauwa”kawai tace tana kallon kamila dake Shirin fita a kofar

Sumayya! Al’ameen ya Kira sunan ta

Kin amsawa tayi Tamar kunnen uwar shegu

Sumayya Koh kin tashi a wajen ne?

Nan ma Sumayya kin amsa Masa tayi.

D’aki ya shiga a zatonsa ta koma d’akin ne Amma ya Gama laluben ta bai jita ba

Sumayya Kam na zaune duk haushi ya Gama kasheta Jin yanda Al’ameen ke wani sake baki Yana Hira da Yar banzar bazawaran (Kai Sumayya harda zagi)

Ji kawai tayi Al’ameen ya rungume ta a zaune da take

“Menene”tace tana zame jikinta a nasa

“Me yasa kika ki amsa mini bayan kinji Ina kiranki,yace Yana Kara lafewa a bayanta

“Oho Kuma ka sakeni”

Meye Kuma nayi Miki haka hajiya

“Bansani ba nika sakeni nace maka”

Habba bakutuwa

“Ka sakeni fa”

Green sum……

Sumayya Bata bari ya karasa ba kawai ta dasa Masa hakoranta a hannunsa D’aya zagayo dashi Kan kirjinta

Washhhh Allah na yatsata,yace Yana yarfa yatsar don harga Allah da gaske Sumayya ta cijesa,ni Kika ciza?

“Eh din kuma,ka sakeni nikam”

Wai menene Kam?

“Bansani ba”

Karki sani Kuma kamila zata fara zuwa make-up gobe nace Mata na, Amince kamar yanda Kika Bata umurni,yace ya na son gane dalilin fushin nata Koh saboda kamilane, don shidai lfy suka rabu kafun ta fitoh waje

“Bazan Yi ba ai ba’a dole karta kuskura tazo mini gida don kurinta zanyi”

Kishi kike da ita?

“Akan me zanyi kishi da ita kuma” samayya tace tana Jin bugun zuciyarta na karuwa

Akan mijinki,Mana

“Ina mijin yake”

Au bakisan inda yake ba?

“Eh ban sani ba saika sanar dani”

Jin abinda Sumayya tace yasa Al’ameen zabura da karfi ya fizgota jikinsa ya juyarda ita suna fuskantar juna,kikace in sanar dake Ina mijin yake? Sumayya ni kike fadawa wannan magana saboda Ina miskini Kuma kina ciyar dani,ya fada ransa a matukar bace

Sosai Sumayya ta razana harga Allah batasan maganar ta fita ba Sam ita Karan kanta bazatace ga abinda ya harzukata ba yanzun yanzun nan

Tambayar ki nake Sumayya saboda kina ciyardani? Koh saboda bana gani shine kike wulakantamin aure?

Sosai ta Shiga rud’ani Bata d’auka Al’ameen da ta sani yanada irin wannan fuskar ba”Kayi hakuri”tace tana zame damtsen ta a hannunsa D’aya damke

Kala baice ba mikewa kawai yayi ya d’auke sandarsa da ciny’ayyen takalmin sa yafita

Bayan fitar Al’ameen sosai Sumayya ta Shiga Dana sani,tabbas magana zarar budu inta fitoh Bata komawa,da tasan haka zai Bata Masa Rai da Bata fara ba

Mikewa tayi ta Shiga d’aki ta kwanta sosai zuciyarta ke Mata zafi 

Bangaren Al’ameen Kam bayan fitarsa gida Tashan kayan marmari ya nufa, duk yanda yaso ya samu bashin Kaya abin ya gagara haka yayita yawo Amma shuru Bai samu kome ba ,tabbas irin wannan yake gudu Sam bayason mace  ace ita ke ciyar da miji,Sam maganar Sumayya Ada Baya Masa ciwo Amma yanzun yaji wani irin ciwo akan maganar sosai,sanann ya Mata hakan ne don ta kiyaye gaba in zata Masa magana ta ringa taunawa,ya fahimci kishine kawai ke d’awainiya da ita 

Jin ana Kiran azahar yasa Sumayya mikewa sallah tayi ta d’aura shinkafa da wake,zubawa tayi a flasks don itakam Sam bazata iyyacin kome ba yanda take Jin tsananin damuwan nan,gashi batasan Ina Al’ameen ya Shiga ba,har yanzun Bai dawo ba 

Har yamma Al’ameen shuru Bai dawo ba duk inda hankali Sumayya yake ya Tashi sosai ta Shiga damuwa matar Bashir data ma alkawarin lalle day uku tana Aiko yaro karshe ma Sumayya tace yaron yace Mata bazata samu zuwa ba

“ya Allah ka dawo mini dashi lfy”tace tana zabga tagumi

Sai bayan Isha’i Daya idar da Sallah Aljuhunsa ba kome yanda ya fita haka ya dawo Koh abinci Bai Karaci ba bayan na karyawa,da sallama ya shigo d’aki

Sumayya dake cikin dogon tunani tana zaune akan sallaya Koh hijab Bata cireba , da sauri ta amsa”waalaikumu salam yayan khadija lfy kuwa baka dawo ba sai yanzun”tace tana isowa garesa

Uhmm sai yanzun, kawai yace Mata Yana k’wabe rigansa,jallabiya ya d’auko a cikin kayansa ya fitoh waje Bai Kara Mata magana ba

Baki a sake Sumayya ta Bisa da kallon mamaki harya fita,ta koma ta zube a jikin kujera hawaye na cika Mata ido,ta Shiga uku sauran hope natan Daya saura shine shima yake kokarin juya Mata baya Wai meke faruwa da itane me yasa duk Wanda zai sota daga baya sai ya kaurace Mata,kuka kawai ta sake “nikam na Shiga uku”tace tana cigaba da kukanta, Al’ameen Bai taba fushi da itaba sai yau menene Bata Masa ba Abaya Bai taba fushi ba sai yau daya ga kamila.

Al’ameen Kam wanka ya Shiga Yana fita yaji muryar Sumayya kasa kasa tana kuka da sauri ya aje kayanda ya cire,Wanda yaso wankewa Amma baida omo.

D’akin ya shiga Amma saiya maze ya kwanta akan kujera Bai kulata ba 

Sumayya Kam Jin yanda Koh damuwa baiyi da kukan da yaji take ba yasa a hankali cikin muryar kuka tace”yayan khadija ga abincin ka”ta fada tana mikewa ta dauko a saman freezer

Na gode Amma bazanci ba yace, ba tare da ya Koh motsa a inda yake ba

Kuka kawai Sumayya ta sake kamar ana yankata”nikam na shiga uku tunfa safe banci kome ba bayan karyawa saboda Ina jiranka ka dawo Amma shine ka dawo kace bazaka ci ba”

Na hanaki cine ai ban hanaki ba kici Mana ni indai nace bazanci ba

“Wayyo Allah na ni Sumayya Yaya zanyi da Raina ne”

Da na Miki me?

“Kaci abincin toh kaji”

Ah ah naci ai 

“Waya baka kudi ka saya”

Ai Ina da sana’a Koh?

“Nidai don Allah Kayi hakuri kaci kaji”

A matsayina nawa Kika damu da sai naci abincin ki?ya tambaye ta

“A matsayinka na”……

Sai Kuma tayi shuru tana kallonsa

Uhmm ,kawai yace Yana lumshe idanunsa so yake ya kitsema wannan baiwar Allah Koh Amafarkine Yana son kallonta, tunda ya makance Bai tanajin yanason kallo ba irin haduwarsa da Sumayya sosai yakeson ganinta da idanunsa 

“Wa…..i mi…jin..a..”tace cikin eeii eiiina

Waine ma kenan?

“Mi..ji…na”

Sumayya!ya Kira sunanta

“Na’am”

Meya Bata Miki Rai d’azun?

“Babu”

Akwai Kam?

“Babu”tace hawaye nabin kumatunta

Nine Koh kamila?ya Kara tambayarta

“Koh D’aya”

Ki fadamin gaskiya wannan shine kad’ai zaisa na hakuri.

“Kaine”

Me nayi Miki har zakina fad’amin magana irin Wannan

“Toh ba Kaine ba”

Nine me?

Kaketa Mata dariya harda wani…..sai kuma tayi shuru Jin subutar baki da tayi

Shikam murmushi ne ya subuce Masa hade da wani irin farin ciki tunda Sumayya na kishinsa,Kuma duk inda akwai kishi akwai alamun so,

sai Kuma akace ki gaggaya min magana?

“Kaye hakuri don Allah”tace tana mikewa a hankali ta matso garesa fadawa tayi kansa da karfi ta sake kuka

Rumtsa idanunsa yayi Jin saukan hawayen ta a kirjinsa tamkar ruwan guduma haka yajisu, Sumayya!ya Kira sunan ta Yana Mai Kara matseta a jikinsa

“Na’am”ta amsa Masa hade da cusa kanta a kirjinsa ji take Kamar numfashin ta zai d’auke

Sumayya na hakura Amma karki sake mini Wasa da aure kinji banaso.

“Wallahih bazan sake ba”

Allah yasa,yace Yana shafa rigan jikinta

Sumayya wannan ba kayanda kikasa da safe ba?

“Shine” Ta basa Amsa

Miya hanaki wanka? sai tsami kike ma,ya fada hade da shafa Mata baya

“Damuwa ne ya hanani,Kuma ni bana tsami”

Bagashi  ba sai tsami kike, yace Yan sunsunar wuyanta,dake tsananin kamshin Turaren ta

“Zakaci abincin na baka”?ta tambaye sa cikin damuwa

A koshe nake ki bare sai da safe sai naci.

“Nidai ban yarda ba wallahih Koh kaci saikaci nawa”

Toh zanci,kije kiye wanka ki wanke tsami kisa Kaya 

“Bayan na Gama sai muyi me”?

Saina karbi hakkina,ya Bata Amsa shima

“Niii….. niii.. Babu ruwana,abinci nake nufi”

Ai kema abinci ne,ya Bata Amsa

“Wacece kamila”?

Uhmmm abinda ya hanaki sukuni kenan?

“Nidai ka fad’amin kawai malam”

Toh malama bakutuwa kije kiyi wanka sai kizo kici abinci sai mu k’wanta da safe saina fad’a miki,.

“Har gobe kuma”tace tana hada fuska

Eh na gaji bacci nakeji yanzun yace Yana cire Mata riga

“Bacci Kuma kake kwabeni”?

wanka zakiy i,ya Bata Amsa hade da karasa cire Mata rigan

 

Wanka Sumayya ta Shiga tana fitowa lokacin karfe 8:00 dai dai, shiga d’akin tayi Kaya tasa,tana Gamawa ta jawo abincin “yayan khadija muci abinci”

Sumayya kici nikam na koshi saiki  dumamin da safe.

“Ni wallahih ban yarda ba,toh bakace ka hakura ba Koh baka hakuran bane” tace tana hawaye

Tabbas ko yaki Koh yaso Sumayya ce rufin asirin sa inba itaba bashida wajen da zaici abinci tunda ba kudi Koh sana’a bane dashi,sauka yayi ya matso Yana lalube ya zauna shukali Sumayya ta Mika masa,ya karba suka faracin abincin

Koh minutes uku basuyi ba sukaji sallaman yaro a kofarsu,

“Kai wallahih nifa na gaji habba matan nan bazata samu lallen nan ba”

Wace Mata Sumayya kardai kice min matar Bashir baki je kin Mata lallen ba?da mamaki yake tambayar ta

“Nikam banje ba”

Saboda me?

“Saboda baka dawo ba,Kuma ni yanzun dare yayi”

Amma sumy gobe nefa sunan Kuma baki je kin Mata ba,sannan yanzun Kuma kice kin fasa,baxataji d’adi ba in Kama mutum Alkawari Yana da kyau ka cika Kinga na riga nace wa Bashir zakizo kima matar sa lalle bazaiji Dadi ba in Kika ke zuwa Kuma gobe suna.

Hakane kam, Sumayya tace tana fitowa waje

Ina wuni Aunty?yaron ke gaida Sumayya

“Lafiya ya mamarka”?

Lafiya aunty Wai inji mamana inzo in fada Miki Wai don Allah kiye hakuri kizo ki Mata lalle ta nemi me lalle Bata samu ba

Toh shikenan bara na d’auko hijabina, Sumayya tace tana shiga d’akin

“Yayan khadija zanje lallen saina dawo ga abincin ka karasa ci”tace tana d’aukar hijab nata da jakan lalle   purse ta bude 50k ta d’auka,zata fita a d’akin

Toh baki karasa cin abincin ba?

“Ah Ah Alhamdulillah kaci kaikam nikam sai nadawo”

Sumayya muje na rakaki kinji?yace Yana mikewa

“Ah ah ga yaro zamu tafi tare,sai dai kazo ka d’auke ni anjima”

Kamar karfe nawa?

“Kana da agogone”?

Oho,nikam ki fad’amin.

“Yanzun 8:12 zuwa 10:00 sai kazo ka d’auke ni”

Toh shikenan yace Yana zama,d’aukar abincin yayi ya cigaba da ci

Sumayya Kam fita tayi da yaron,sai da sukazo kusa da titin first bank taga shagunan a bude kamar Rana ga wuta ako ina,”tsaya Kai mu Shiga shagon nan”  tace ma yaron tana Kama hannunsa suka tsallaka titi,shagon ta shiga”excuse me”tace ganin Mai shagon inyamurine

Yes ma barka da zuwa shigo ciki customer ki duba Kaya

Da mamaki sumayya ke kallonsa Ashe ya iyya hausa,yauwa “sannunka,Kaya nake so”

Ok wani iri?

“Jallabiyoyi”

Ok ki shigo gasunan kizo ki zaba Wanda ya miki,yace Yana zazzaro Mata jallabiyoyi sunfi kala goma

Guda uku sumayyaa ta zaba masu masifan kyau fari da baki Mai maiko sosai da hula sai Kuma Mai aiki ruwan sararen samaniya,takalmi ta sai Masa Mai kyau na tambarin Adidas silifas ne,sai t-shirt da 3quiter sai Jean’s,sosai Sumayya Tama Al’ameen sayayya harda Turare na maza ta sai Masa da abin haske Kai da gemu,sai kusan 9:26 suka je gidan Matan da zatama lalle 

Lalle Sumayya ta Mata baki da ja, Al’ameen tun 10 yazo Amma Basu Gama ba,ya zauna Yana jiranta a kofar gidan

Suna Gama lallen Sumayya ta karbi kudinta laidan da ta aje a kulle a gefe na kayan da ta saima Al’ameen ta saba,waje ta nufa

Tana fita taga yayan khadija a zaune

“Yayan khadija mu tafi Koh”tace Masa

Kun gama?

“Eh mun Gama”

Ok yace Yana mikewa tafiya suke shuru,can dai Al’ameen ya kasa hakuri Jin yanda yakejin motsen laida a hannun Sumayya

Sumayya nikam laidan menene a hannunki Kato haka don nasan dai laida kananu basa Kara haka?

“Abu na saya”ta basa amsa

Kala baice ba suka cigaba da tafiya har suka Isa gida,Dayake sunyi wanka dazun yasa Kaya kawai suka chanja 

Yauma kwanciya sukayi tare bayan Al’ameen ya Gama kwsan rabonsa

Washe gari da safe bayan Al’ameen ya tafi masallaci, Ghana must go nasa ta bude Daman jiya ta kirga kayan jallabiya ukune sai wando da riga D’aya sai 3quiter D’aya sai armless D’aya sai gajeren wando biyu vest D’aya, kwasosu tayi ta juye a basket na dattin kayanta,sabbin kayanda ta suyo jiya ta mayar cikin bakkon ta shirye Kamar yanda kayan suke a kirge sauran Kuma ta aje sai Randa ya wanke kayansa biyu masu dattin saita musanya Masa,

 Vaseline insa da ya kusa karewa ta juye a laida daukar manda ta siyo Masa tayi ta diga a cikin gongomin kamar yanda baseline insa yake, Haka ma tamasa da sabulu

Sai 6:30 Al’ameen ya shigo gidan

Sumayya Kam ganin ya shigo d’akin da sauri ta d’auki takalmin sa ciny’ayyen ta saka Masa sabo,ta dawo d’akin,kudi  ta basa 2k yasai musu dankalin turawa boket D’aya sai k’wai guda biyar,

Fita yayi a d’akin bayan ya karbi kudin yazo ya zura takalminsa,sai Kuma ya cire da sauri,ya ringa laluben bakin dakalin Amma wayam baiji takalminsa ba

Sumayya!!ya k’wala Mata Kira

“Na’am”Sumayya ta amsa tana fita a d’akin itama

Sumayya Banga takalmina ba pls ki duba mini Mana?

“Ba gashinan a gefenka ba” tace tana kallonsa

Wannan ba nawa bane

“Nawa kenan?kadaisan banda takalmi irin wannan soson”?

Amma ni sai inaji Kamar ba nawa bane,nawa fa da laushi sosai ya kode

“Toh wannan in fa”,ta tambaye sa tana mamakin fahimta irin nasa

Kamar sabo sabo,

“Hhhh lalle zaka tafi da kafa kenan tunda dai ga takalminka kace Wai ba naka ba”

Sumayya bafa Wasa nake ba Wannan ba takalmina bane 

“Nidai naka na gani atoh”tace tana komawa d’akin

Al’ameen Kam ba yanda ya iya Haka ya saka takalmin Amma har ransa yanaji ba nasa bane.

Bayan fitar Al’ameen Sumayya aikace aikacen ta na gida ta Gama ta d’aura ruwan zafi a kittle.

Al’ameen Kam bakin kasuwa  yaje ya musu sayaya ya kamo hanyar gida

Bayan Al’ameen ya dawo Sumayya ta soya dankali da k’wai sai ta hada musu tie, rufewa tayi ganin Al’ameen ya Shiga wanka

Al’ameen aban d’aki mamakine ya kamasa Jin sabulunsa na kamshi ,Amma baiyi magana ba bayan ya fitoh, d’aki ya Shiga a hankali ya bude bakkon sa jallabiya D’aya ya zare a ciki ya zaro gajeren wando da vest.

Sumayya na zaune akan kujeran tana kallonsa saka wando yayi da vest sai Kuma taga ya tsaya Yana tattaba vest in,Amma baiyi magana ba ya d’auki jallabiyar yasa,sai Kuma ya juye kayan bakkon duka a cafet Yana tattabasu.

 Sumayya!ya kirata

“Na’am”tace tana kallonsa

Sumayya wa’innan ba Kayana bane?

“Akan me zakace haka”

Sumayya wa’innan Sabine kijifa kayan kamshin sabbin Kaya suke bama Turare ba kiji da karfi fa kayan ba masu laushi irin nawa  bane?

“Nidai naka na gani”

Sumayya me Kika sayo jiya da naji laida na kayo kayo a hannunki?

“Ina ruwanka”ta basa Amsa

Indai baki fad’amin gaskiya ba toh bazan fad’a Miki wacece kamila, menene hadin mu da ita ba

Tabe fuska Sumayya tayi “Gaskiya n…………….

                  

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense@umsadincense*@umsadincense@umsadincense08084453785kyauna

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€

 πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―      

               ~ Na ~

 

 πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

  

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ

free book 🀧 

Page 3️⃣8️⃣&3️⃣9️⃣  

“Ni Kaya na saya” ta basa amsa

Wani irin Kaya kenan?

sannan Ina Kayana?

“Nina yarda kayayyakin ka duka sabo na sai maka Naga nakan sun kode,Amma kayi hakuri bazan sake ba” tace tana Kama hannunsa dake kokarin zare jallabiyan jikinsa

Sumayya akan me Zaki sayamin Kaya bazaki fad’a mini ba saboda bani da ido saiki zo ki musanya mini,kamar wani yaro.

“Kayi hakuri kaga yanda jallabiyar nan ta karbe ka kuwa yayan khadija” tace ta ja maza zip in gaban jallabiyar,hade da d’aukar Turare ta fisa Masa,vayan ya shafa Mai 

Nagode Allah ya miki albarka ya hanani Miki butulci a rayuwa Sumayya

“Ameen” tace tana jera abincin karyawan, Bismillah ta Masa suka fara ci cikin kwanciyar hankali

Bayan sun  Gama cin abinci  tattara Kwanukan yayi yakai waje,bayan ya ajeye, d’akin yadawo 

“Toh yayan khadija wacece kamila”Sumayya ta tambaye sa 

Nifa nayi Miki Alkawari ,ai basai kin Kara tambaya taba nida kaina Zan fad’a Miki kome Daya shafe kamila.

“Uhmm ba Dole na tambaya ba tunda sai jamin Rai kake yaufa da wure na Gama aiki Amma sai wani sham kamshi kake”

Nasha kamshin, kema saiki Rama.

“Wallahih ka Gama iyya jarabanka bazan biye maka ba sai naji lbrn nan ehen”

Toh zoki zauna a kusa Dani samun lbrn yafi Dadi,yace Yana zama akan kujera

Saboda tsabar sonjin lbr yasa Sumayya mikewa da sauri tazo Kan kujeran ta xauna kusa dashi

Hannu yasa ya matsota jikinsa a hankali ya rungume ta a jikinsa cikin sanyin hallintarsa murya a sanyaye yace Sumayya!

“Na’am yayan khadija”

Yau Zan baki labarin kamila Amma saikin ji labarina Nima kafun ki gane lbrn kamila dakyau.

“Yauwa Aiko Ina sonjin lbrn ka da dangan takarka da gidan ADARA duk da Ina tunanin dangin mahaifinkane Amma halayenku sun banbanta,hakan matsayinka da khadija a gidan nan na fahimci a kaskance kuke ba Kamar sauran Yan gidan ba”

Duk xakiji insha Allah Koh Nima Zan samu amsar dalilin auren mu Wanda har yau bansan dalili ba.

“Wai kana nufin ba Kaine kace kana Sona ba,aka aura maka ni “?ta tambaye sa cikin zare ido. 

Nima ban sani ba Sumayya bansan dalilin auren muba Amma koma menene inaji a jikina insha Allah haduwar mu dake alkhari ce

 

“Insha Allah insha Allah yayan khadija” tace tana share  hawaye Daya gangaro mata

Gyara zama Al’ameen Yayi a hankali ya fara magana…………….

 *Shikaru Talatin da biyar da suka wuce baya* πŸ•’

Malam Yusuf sumul, shine cikekken sunansa da aka Sansa dashi matashine Dan shikara 35,Yusuf mutum ne Mai Hakuri addini ga kawaici baid’auki duniya da zafi ba,Yana da tsananin zurfin ciki duk yanda zaka zauna dashi bazaka taba fahimtar wani abu a tattare dashi ba shiyasa ba Wanda yasan shid’an inane Koh daga Ina yake, duk da kowa ya gansa Kuma yaji yanayin hausar sa da maganar sa Dole yasan cewa ba D’an kasa bane .

Alhaji Rabi’u ubangari. Wanda akafi sani da ubangari,maikacin gonnati ne Kuma Mai rufin asiri sosai,Yana da Mata biyu.

shine Mai gidan Yusuf, saboda tsananin hankali da nitsuwar yusuf yasa ya d’aukesa Kamar D’an gida ya basa d’aki a cikin gidansa,Yusuf na Masa aikace aikace kamar zuwa kasuwa wanki da gugan kayan yaransa da NASA na kansa Yana Kai kananun yaransa makaranta ya dawo dasu,

Yaran ubangari guda biyar ne sai yaran Yan uwansa maza biyu Mata hudu,kenan yara goma Sha D’aya ne a gidan ubangari

Zainab Fatima Auwalu lukman Nasir,sune yaran ubangari na cikinsa

Haidar Umar khairat munira safara’u murja sune yaran Yan uwansa Dayake rikewa

Yusuf da ubangari akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu duk da baisan Yusuf ba Amma da zuciya d’aya yake zaune dashi ganin tsawon shikaru Bai taba nuna wani mugun halinsa Wanda mutane zasuye Allah wadai dashi ba.

Yaran gidan na basa girmansa kasancewar duk yaran gidan ya fisu a shikaru,yanajin dadin zaman gidan sosai don tun kafun Alhaji yayi aure suke tare har Allah yasa yayi aure 

Yaran suna ganin girman Yusuf saboda yanda mahaifin su ke tare tashi hakan yasa suke kiransa da bappa yusufa

Zaman Yusuf a gidan ya fara gunduran sane bayan girman Yar Alhaji Rabi’u ubangari zainab,wance Allah ya diga Mata son yusuf Mai tsanani duk da a lokacin tana da shikaru 14 yayin da Yusuf keda shikara 35    

Tun tana boyewa har abin ya gagara ta tinkare Yusuf da maganar.

Sosai Yusuf ya ja Mata kunne akan zancen kuma ya tabbatar Mata shi bazai aureta ba donshi a matsayin diyarsa,ya d’auketa duk yanda tayi kokarin ganin tashawo Kan Yusuf abin ya gagara,taso fad’awa  mahaifyarta zancen tanason Yusuf Amma khairat Yar bappanta ta hanata saboda tasan mundin maman zainab tasan zancen daker zainab ta aure Yusuf.

 ADARA FAMILY HOUSE haifafun jalingo ne tun iyaye da kakanni anan gidan Adara suka tashi don duk fad’in sintali ba gida Mai dumbin tarihi da shikarun mazauna ciki irin family ADARA tun husul sai chanje chanjen gini da ake in zamani ya shude,

Tun husul ma haka suke mutane ne masu masifan tsiya ga fad’a kamar ahlin dambe shiyasa aka musu lakabi da ADARA  

Aishan ADARA  d’aya ce daga cikin yaran gidan adara ,macece Mai matsifa na bugawa a jarida duk yanda kaga mala’in yaran gidan ADARA Aisha ta damasu ta shanye saboda tsananin masifarta yasa Koh saurayi Bata dashi don a lokacin abin kunyane mace takai shikara 20 batayi aure ba Amma Aisha shikarunta 20 Koh saurayi Bata dashi saboda tsananin tsoronta da maza keye 

Gidan ADARA tun asali haka yake har wa yanzun.

Aishan ADARA na Saida Dan wake a bakin kasuwan main market na jalingo

Sun hadu da Yusuf ne lokacin da yaje kasuwa sayayyan kayan Miyan gidan ubangidansa,ya saye danwaken ta by mistake robanta ya fashe a hannunsa,

Ba karamin bala’i Aishan ADARA ta sauke Masa ma kwando kwando da Kuma uzzurawa saiya biyata robanta 

Yusuf Kam ba karamin mamaki yasha ba ganin irin bala’in da Mai danwake ke Masa akan robanda Bai wuce sule biyar ba sai bala’i take Masa Kamar ya Mata Satan jari

Sosai Yusuf yaji haushi kala baice Mata ba ya Kama hanya Yana tafiya itakam sai binsa take sayya Biya robanta

Yusuf kam yasha Alwashin bazai biya ba ganin jarabanda take Masa haka tayita binsa harya Gama cefenen ya Kama hanyar gida bayan ya tare machine.

Duk jaraban Aishan ADARA yau taga iyyakarta don ba zagi ba duka da Mannin hauka Yusuf ya rabu da ita

Bayan dawowar Yusuf gida Sam ya rasa sukuni,tunanin Mai danwake Kam ya hanasa sukuni Sam

Ta bangaren Aishan ADARA ma hakane Sam bayan tafiyar kyakkyawar mutumin da Bata Sansa ba  gabaki daya ya hanata sakat a tsawon shikarun ta Bata taba bi takan soyayya ba Amma wannan Karo tayi tuntuben so a bakin titi Wanda Bata San inda zata sake ganinsa ba

Bayan sati biyu Sam Yusuf ya kasa sukuni ya kasa hakuri sosai Y’an kwanakin nan ya gane meke d’awainiya dashi,sai a lokacin yaji tausayin zainab Ashe haka takeji yake wulakanta ta,

Farga bansa d’ayane kar yaje gareta da soyayya ta tsigalesa don Tabbas daga ganinta Yar bala’i ce sosai Abu na biyu Kuma asalinsa kar rashin sanin danginsa yasa a hanasa auren ta.

A hankali Yusuf ya fara zuwa gun Aishan ADARA cin danwake Wasa Wasa harya kasance ba ranan da baya zuwa ci haka ba ranan da basa fad’a a tsakaninsu kafun su rabu ,har shakuwa yazo ya shiga tsakaninsu Mai tsanani Wanda a zahiri kowa son junane ke d’awainiya dashi,Amma ya kasa sanar da D’an uwansa

A hankali Yusuf ya fahimci masifar Aisha a tarbiyan gidansu  yake a Hankali ya Soma nutsar da ita sosai yake nuna Mata abin Bai dace ma Abu kamar Wasa Aishan ADARA ta nutsu sosai sai dai fa har lokacin in ka tabota zaka Sha bala’i sai dai in abinda ba ruwantane Bata Shiga haka zalika ta daina dambe da kowa,abin harya fara bawa jama’a mamaki sauyawan ta

Lokaci da Yusuf ya bayyana ma Aisha soyayyarsa gareta Babu wani jinkiri ta amsa sosai  suke zuba love

Yusuf ya samu Alhaji akan maganar Aisha ba karamin murna alhajin yayi ba dayaji Yusuf ya samu wance yake so don burinsa kenan,ya tambaye Yusuf danginsa don maganar aure Dole ana bukatan dangi na jini

Hankalin Yusuf ya Tashi matuka don har kwanciya yayi a gadon asibiti Akan zancen danginsa da Alhaji ya matsa Masa akai

Karshe dai fa ubangari yaga abin fa nayine yasa sa hakura da tambayar Yusuf shi yashiga maganar auren Yusuf

Da yake ubangari ya jima tare da Yusuf kowa gani yake kamar Yan uwane hakan yasa ba dogon zance aka basa auren Aisha don Suma sun Matsu tayi aure ganin ta girma a gida

Ta bangaren zainab Yar ubangari Kam in hankalin ta yayi dubu ya Tashi tayi kuka tayi kuka Kamar zatayi hauka Amma khairat ta taka Mata birki tare da Mata alkawarin sai Yusuf ya aureta amma tabare ayi auren taga matakin da zata d’aukar Mata

Bayan auren Yusuf sumul da Aishan ADARA, Alhaji yaki yarda Yusuf ya Kama gidan haya a gidansa sukaci gaba da zama, soyayya suke shimfid’a wa Mai tsafta sosai Aisha ta nutsu suna zaune da yaran ubangari da matansa  lfy Sam bata nuna musu Yar Hali  sai daifa basa shiri da zainab ganin kallon banza da take mata

Sai Bayan shikara uku da auren Aishan ADARA da Yusuf kafun Allah ya baiwa Aisha ciki sosai sukayi farinciki da wannan cikin da Allah ya azurtasu,sukaci gaba da rainon cikin cikin farin ciki

Bayan Aisha ta haihuwa sun samu d’a namiji Mai matukar Kama da mahaifinsa Kamar an tsaga Kara,  mahaifinsa yasa Masa suna muhammad.

Mahaifiyarsa na kiransa Al’ameen.

Da sauri Sumayya ta d’aga ido tana kallon Al’ameen dake Bata lbr”kana nufin kace mini gidan n……..”

Bai bare ta karasa ba ya girgiza Mata Kai Yana Kara kwantar ta ita a jikinsa,ki aje tambayoyin ki Inna Gama saiki tambaya

Kai kawai ta gyad’a Masa 

Ya cigaba…..har lokacin zainab Bata saduda da soyayyar Yusuf ba don a lokacin ta kammala secondary school nata,Amma Taki aure Dole yasa babanta nema Mata wani makarantan gaba da secondary taci gaba 

Bayan haihuwa Al’ameen da shikara uku Aisha ta Kara haihuwar wani da namiji yaci sunan Salim, tun daga lokacin Aisha Bata sake samun ciki ba,sukaci gaba da kula da yaransu don a lokacin Alhaji ya budewa Yusuf shago yabar aikace aikacen gida basuda wata matsala sai na d’ansu Salim Wanda ke fama da mummunan ciwon zuciya,duk bayan wata D’aya sai sunga likita Kuma sai anci kudi.

A hakan rayuwa tayita tafiya yau Dadi gobe akasinsa Al’ameen da Salim suna matukar samun kula daga iyayen su suna Isa shiga makaranta aka sakasu yarane da suka shagu da junansu matika Kamar wasu tagwaye Dayake Salim nada gaban girma tuni ya tsara da yayansa har lokacin Aisha Bata San cewa Yusuf ba Dan uwan Alhaji bane duk da tana yawan tambayan sa labarin Yan uwansa Amma Yusuf daga tayi tambar saiya hau hada Mata fuska

Bayan wasu shikaru lokacin Al’ameen nada shikara 11 Salim nada shikara 8 a duniya. Aisha na d’auke da karamin ciki.

wata ranan juma’a da zuriyan yusuf bazasu taba mantawa da ranan b a tsawon rayuwansu ba har Abada ciwon bazaibar  zukatan su ba

Da misalin karfe bakwai na dare yusuf ya dawo gida,Yana kokarin shiga shashen su sai ga khairat taresa tayi cikin kuka Wai zainab ba lfy  tana dakinta Alhaji yace yaje su kaita asibiti

Da gudu yusuf ya bi bayan kairan zuwa shashen Yan matan gidan,shiya fara Shiga d’akin Yana shiga khairat taja kofar ta rufe kofar ta waje da makulli.

Yusuf na shiga d’akin ya ware ido ganin zainab ba Kaya daga ita sai d’aurin kirji a zaune akan gado

Tambayar ta yusuf ya farayi, zainab menene haka Kuma ki nemi riga ki saka yace Yana Mai kokarin bude kofar

Dariya zainab ta sake hade da furta wallahih kaji na rantse maka Yusuf tunda ka hofantar da soyayya ta kasa kafa ka shureta Nima saina jazamaka bala’i inda zaisa ka aureni Dole wannan itace kad’ai abinda zanyi na mallakeka,ka ‘dauka Koh shurun da nayi na hakurane?

Ah ah wallahih ban hakura ba tanadi nake maka.

Subhanallah shine abinda yusuf ya furta cikin gigita, zainab Ashe bakida hankali wani irin shirmene haka

Hauka zakace ba shirme ba tabasa amsa tana matsowa garesa hade da fizgo kwalar rigansa ta yaga sosai tana ihu

Sosai yusuf ya razana ya Shiga kokarin k’wace kansa

Khairat Kam tana rufe d’akin ta tsaya kamar minutes biyu kafun ta fara rafka salati a tsakar gidan wayyo jama’a wani zaima zainab fyade a d’akinta yanzun nazo shiga kawai naji kofa a rufe zainab nata kuka ku kawo d’auki

Da gudu Yan gidan harda Aisha  da makwanta Dayake darene ga madalisa a kofar gidan  suka ruga da gudu zuwa d’akin zainab da suke Jin kukanta na tashi har lokacin

Jin kofar a rufe yasa matasan samarin unguwan suka dauko katon itace suka bugawa kofar take kofar ta balle,cikin mamaki tsoro Al’ajabi suka zubawa d’akin ido ganin abinda ke faruwa kamar a mafarki y…………….

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d’ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa* 

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da*  *gyara* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE* 

πŸ€ *Na tsunguno(habil)* 

πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,

πŸ€ *Na d’aki(halud Al’oud)* 

 

 *UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d’aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa* 

πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria* 

Contact them vie

πŸͺ€08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense

Back to top button