Uncategorized

Matar Hariji Page 91-100 Hot Romantic Hausa Novel Complete

 

Zuciya ta aje tace “nidai ka kaini nagansu na roqi gafararsu wlh indai haka haihuwa take abban Fadwah bazan qaraba bazan sake haihuwa ba ni wannan ya isheni don Allah kada kacemin na qara haihuwa kaji?” 

Numfashi ya sauke yace “kin tsorata da yawa babe ki kwantar da hankalinki ke bakisha wahala bama a sadaka kika samu haihuwarki” saurin katseshi tayi da cewa “au ahakan?” Dariya ta bashi sosai yace “eh mana insha Allahu Ina dawowa zan baki wani babyn kiyi maza ke haifamin dozen guda kinji” qit ta kashe wayarta saboda kalamansa kawai bata Mata zuciya suke.

Shigowa Hajiya tayi ita da Alh Alh ya dauki yaron yayi murmushi yace “masha Allahu yaro me kama da babansa Allah ya albarkaceka Muhammad Nurraddeen….” Dagowa tayi da sauri ta kalli Alh yayi murmushi yace “tun kafin Lameer ya tafi yacemin idan kin haihu nayiwa yaron huduba da sunan mahaifinki”

Sunkuyar dakai tayi wasu hawayen farin ciki suka zubo Mata ta zame qasa tana hawaye cikin rawar murya tanayi musu gdy Hajiya ta dagata tace “bamu zakiyiwa gdy ba Hauwah tsakaninki da mijinki ne kunfi kusa kuma sakayyar halacci halacci insha Allahu idan ya dawo har dani zamuje mukaiki ki daidaita da mahaifanki aure dai damu da mukaqi dama wadanda sukaso babu wanda ya iya hanashi saboda Allah ya riga yayisa”

Suna wannan mgnr Aunty Zulaiha da Aunty Zainab suka shigo suka zauna Suma anata hira dasu itadai bata cewa komai saboda ciwon da cikinta yake danyi Mata ciwo basu ankara ba saida sukaji ta fara kakarin amai sukayo kanta duka.

Sabarta Alh yayi yasata a mota Hajiya ta shiga da jaririn sai asibiti suna zuwa sukayi Mata Allurai suka bata wasu magunguna sannan suka juyo gda, sunata zuba mata sannu suna zuwa dama isha tayi aka ciro gadon baby aka sanyashi a ciki aka kwantar dashi itama ta kwanta Hajiya me jika cewa tayi saidai su kwanta a dakinta bazaayi mata nesa da jikanta ba.

Fadwah ita ke kusan yini tanawa yaron wasa wata shaquwa ta shiga tsakaninta da jaririn ba kamar Muftahu ba da basa jituwa ko kadan ita kuwa Mubaraka ta koma dangin mahaifinta Jalingo inda Alh ya shiga ya fita Muneef da Hajiya ma basu sani ba aka qullah shirin aurenta da Muneef din.

Kwanan Hauwah uku da haihuwa Lameer ya diro cike da shauqi bai bari kowa ya ganshi ba ya shige dakin da lallaba ya sanya hannu zai dauke baben data rungume take feeding nashi tayi sauri qanqame abunta tare da bude idonta, murmushi yayi Mata yace “mata sunyi da rigima ta qare ohhhh Hauwah rikicin ki yawa gareshi kuka wiwi ke banasonki naqi baki baby to yaudai ga babenki dana baki a hannunki”

Sunkuyar dakai tayi cike da kunya tana wasa da sumar yaron ta fulanin na gaske wacce ya debo gurin uwarsa amma komansa har fatarsa na ubansa ne hannu yasa ya daukeshi yayi masa addu’a sosai sannan ya rungumeshi a jikinsa yanajin ninkin qaunar yaron da uwarsa na mamayar zuciyarsa.

Kwantar dashi yayi ya zuba masa ido kawai yana kallon buwaya ta ubangiji sumar yaronce kadai ta uwarsa amma hatta farcensa irin nasane a hankali yace “Allah daya”

Kwantawa yayi a jikinta ya sanya hannunsa ya shafo nononta yace “inason taya babyna shan madara sweet abani” turo baki tayi tace “ni ka tashi ka tafi saura kadan na mutu yaseen da nasan haka haihuwa take da babu abinda zaisa nasaka kayimin ciki”

Yanda take mgnr da qumajinta ya bashi nishadi yace “kuma gwarne nakeson kiyi kafin kiyi arba’in na baki wani ko?” Tureshi tayi ya koma gefe yana dariya Hajiya ta shigo yanayin data gansu ya bata kunya sosai har zatayi mgn taji tsoron amsar da lameer zai bata don yafita wauta.

Miqewa yayi ya dauki Fadwah ya fita bai jima ba ya dawo dauke da wani babban akwati ya ajiye Mata a gabanta yace ki bude ki gani abinda baiyi miki ba ki ajiyeshi gobe saina canzo miki yanzu nidai kuyimin guri a dakinnan na kwanta bacci nakeji”

Hajiya dake fitowa daga bathroom tace “badai dakin nan ba kaje gurin maigadi ku kwana tare tunda ka manta hanyar gdanka, sosa qeyarsa yayi yace “aa ba haka bane Hajiya kawai so nakeyi mu kwanta tare Noor dinmu a tsakiya nasan baccin zaiyimin dadi sosai…” 

Daquwa tayi masa tare da jifansa da pillon hannunta tace “zaka tashi ka fice mana a daki ko saina Kira Alhajinka yazo ya fitar dakai” miqewa yayi yace “ya zanyi tunda baa qaunata” sunkuyawa yayi daidai fuskar Hauwah yayi kissing nata yace “kin samu daurin gindi lkcnki ne Allah ya kaimu lkcn da Zaki shigo hannuna saina…..”

Rufe masa baki tayi da sauri da nata yayi saurin tallafo kanta ita kuma tana qoqarin kwacewa Hajiya ta juyo saida gabanta ya fadi ganin yanda yake wani lumshe ido tayi saurin dauke kanta daga kansu ta fice da baya da baya.

Da sauri Hauwah ta tureshi ya kamota yana wani sauke numfashi yace “kinsan Allah kisan yanda zakiyi dani nazama fitinanne nima kullum sai nayi wanka a Texas saboda tunaninki” qwalqwal tayi zatayi masa kuka tace “sai kayi duk yanda zakayi dani kama kasheni ka huta ai dama nasan basona kakeyi ba…” 

Download>>> Yaro Ne Complete Document

Rufe mata baki yayi cikin dariyarsa yace “haba yarinya nikam ai kowa ma ya shaida Ina qaunarki tun kina qwailarki lkcn da kike tsoron bindira” duka ta fara kai masa ya kauce yana dariya yace “lkcn da akeyi miki adumbuli a bayan….” Toshe kunnenta tayi tace.

“Naji naji nace kaje kawai basai kayimin barbada ba” dariya yake sosai ya lakace Mata hanci yace “saida safe amarya ta ki kulamin da kanki kinji” daga masa kai tayi ya shafa kan babynsu yace “wannan shine raba gardama nasan yanzu idan kikaje garinku zasu qara yarda da cewa kowacce qwarya da abokin burminta wlh koda ban matsa nayi amfani da qarfin hukuma an bani keba idan lkcn zuwan Noor duniya yayi sai mun hadu kuma sai yazo kota wanne hali qila da sai anyi asarar rayuka ma akanshi shi daya tak sai a rasa rai sama da goma”

Juyawa yayi ya fice tabisa da kallo cikin sanyi jiki tare da zubawa yaron ido ita ba komai yake bata mamaki ba girman yaron amma wai ita ta haifesa a cikinta ya rayu harna watanni tara yanzu gashi yana rayuwa a duniyar da take rayuwa to wai ma ta Ina cikin ya shiga, a Ina yake zama a cikin nata?

Matsa cikinta ta farayi itadai bataji wani guri da yayi alamar wannan qaton yaron ya zauna ba, kuka ya fara ta murguda baki tace “yaro inma zakayi shiru gara kayi nagaji sai tsotse nono kakeyi bandama rainin hankali na ubanka Hajiya tace a baka madara yace aa saboda ba jikinsa kake jaba to Nima bazan bayar ba aiba dankai akayimin nonon ba lol Hauwah ananan da hali.

Komawa tayi tayi kwanciyarta ta juyawa yaron baya yanata kuka yana neman abinci, Hajiyace taji kukan yayi yawa ta shigo da sauri taga yanda yaron yake neman abinci ta matsa ta daukeshi tace “ni narasa wacce irin yarinya ce ke Hauwah waike yaushe gidadanci zai barki ne yaro sai kuka yakeyi yana neman abinci amma kinajinsa”

Turo baki tayi tace “toni Hajiya zafi nakeji wlh idan yanasha kamar lkcn da babansa ya farasha harma yafi haka zafi shifa jaririn nan har cizona yakeyi shikuwa Dadynsu baya cizona”

Wani takaici Hajiya ta hadiya tace “to yanzu akira miki mijin naki ki bashi kenan ko?” Sai yanzu ta fahimci wautarta tace “am imm nifa ba haka nake nufi ba Hajiya kawai dai kice ya daina cizona dan yaseen ya qara cizona saina mareshi”

Abin dariya yabawa Hajiya yau tana ganin ikon Allah daqyar ma aka samu ta yarda tabawa babyn nono wai ita kunya takeji yana namiji bazai gane Mata nononta ba saida taga ran Alh ya baci sannan ta karba ta bashi tana kuka wai an cuceta tasan sai babe yayi mata fada🤔

Itako Hajiya dama ta zama kakarta kowanne shirme ita ake dorawa, cikin kwanaki hudun da suka rage mata tayi kyau sosai binjintar da Lameer yakeyi abin har mamaki yake bawa kowa hatta ankon suna shine yayiwa kowa hadda yan uwanta da yaje ya fada musu haihuwar sukace zasuzo suna.

Bai fada Mata ba saboda sanin haukanta hana kowa sakat zatayi musamman yanzu da take a fusace saboda ance saita rinqa bawa danta nono har cewa tayi ai an tsaneta ne don anga bata da kowa.

Ana gobe suna da kansa ya tura da mota cikin saa kuwa Baffa bayanan ya  maqarfi yakai shanu kasuwa kuma yanayin sati bai dawo ba aikuwa su Inna Jumme su lantana da babbar yayar Hauwah ladiyo da qawarta Lahira suka dungumo suna birni.

Wayyohh murna gurin Hauwah taga na gda tama manta da rakinta da takewa mutanen gidan da ance tazo parlour tayi baqi yan barka sai tace ai dinki akayi Mata tana miqewa farkewa zaiyi,

Tuni ta take ta rugo a guje ta rungume Inna Jumme tanata dariya sai kuma kuka tana dube dube ganin bata hango kowa ba tace “Inna Ina Goggo da Baffa” 

Shafa fuskarta Inna tayi tace “yaushe Ina aka tabayin haka autar wuro goggonki bata zuwa sunan danki ai Baffa kuwa baya gari yana Maqarfi” gefe tayi ta riqe qugu ta zube a qasa ta kama kuka rarrashin duniya taqi yin shiru saida aka Kira Lameer yana yan awaki ya tafi siyan abin hakika aka fada masa sarqa me rikicin gangan ta rikice fah.

Babu shiri ya basu kudin ragunan daya siya aka sanya masa a mota suka tafi Salees yanata yimasa tsiya yayi murmushi yace “bakasan yanda nakeji bane nasan tabata akayi kuma bari muje kaji yanzu idan bani dinba ko waye zaizo bazatayi shiru ba yini zatayi tana kuka”

Dariya sosai Salees yayi yace “wannan raino naka bansan yaushe zai qare ba kayi rainon yaya kayi rainon uwar yaya” shidai bai qara cewa komai ba har suka isa gdan ya qyale Salees da sauke ragunan ya shige ciki ya hangota can qarshen dakin ta hade kai da gwiwa tanata kukanta.

Matsawa yayi ya riqota tanajinsa ta sake rushewa da kuka tace “ni ka daina tabani nama daina sonka na daina kulaka kullum kai babu ruwanka da damuwata to wlh babu ruwana da danka nima Gwaggona da Baffana nakeson gani shine kace kada a tahomin dasu ko?” 

Ta fada tare da kafesa da jajayen idanunta fuskarta harta tasa abinka da farar fata yayi murmushi kawai ya sanya hanunsa ya dagata cak ya nufi dakinta da ita tana zamewa tana cewa ka sakeni banaso ni banaso kowama ya tafi banason ganinsa Gwaggona nakeson gani”

Bai direta ba saida yakaita har dakin ya sauketa a gadon ta miqe zata fice yayi saurin cafkota ya kulle qofar ya mayar da ita ya kwantar ya kwanta a jikinta yayi qasa da muryarsa yace “ke bansan yaushe zakiyi hankali ba kema fa uwace yanzu haka Zaki rinqa yimin idan natafi dake American?” 

Ajiyar zuciya tayi tace “ni bazani ba Gwaggona kawai nakeson gani” kwantar da kansa yayi a kafadarta yace “yanzu kuma shine saikin tashi hankalin kowa a gidannan kina gani su Inna ko ruwa sun kasa shs daga zuwansu kin fara nuna musu halinki wato kinaso suje suce har yanzu bakiyi wayo ba a birnin ko?” 

Shiru tayi batace masa komai ba yayi murmushi yace “banason shirmenki wannan ni dakene zan kaiki kije kiyi sati a gurin Gwaggonki kafin mu tafi amma sai kinyi hankali idan bakiyi hankali ba bazakije ba” 

Saurin qaqalo dariya tayi tace “namayi daga yau bazan qara ba” kissing dinta yayi yace “yawwa kin bawa Noor abincinsa kuwa?” Qasa tayi da kanta yayi murmushi yace “baki basa ba ko?” Daga Kai tayi yayi murmushi ya fita ya karbo yaron ya miqa mata ya saita mata kansa ta kalleshi ta kalli yaron tace “kamarku daya dashi”

Murmushi yayi yace “ba abinda na tambayeki ba kenan ki bawa dana nono nagani” noqe kafada tayi tace “kaje zan bashi ni basai ka….” Wani kallo da yake mata yasata hadiye mgnr ya sanya hannunsa ya zuge zip din rigar ya sanyawa yaron nono ya kama da sauri.

Qara tayi saboda zafin da taji, yayi murmushi yace “kokefa amma danki na cikinki ki rinqa yimasa horon yunwa” hawaye takeyi tace “ni kaje banason surutu” miqewa yayi yace “babu komai na gode” ficewa yayi yaci gaba da harkokinsa bai samu zama ba sai da gama da baqinsa sannan ya wucce gdansu yayi wanka ya kwanta.

Wayarta ya kira tana gani taqi dagawa yayi dariya itafa a dole laifi yayi mata yasata ta bawa danta nono, yananan kwance yanata tunanin wautarta da rikicinta yanata dariya har bacci ya daukeshi.

Tun asuba daya fita bai dawo gdanba gidansu ya tafi ya shiga gurin mahaifinsa suka gaisa yayi masa addu’ar Allah ya raya musu Muhammad Nuraddeen  sai lkcn su Inna sukaji ashe Ardo akayiwa takwara sukayita murna kuwa basu taba zataba.

Shagalin suna sosai akayi ranar su Inna sunga ikon Allah yanda aka rinqa girmamasu a gidan abin ya tsaya musu a rai musamman Hajiya data rasa inda zata ajiyesu  komai nasu na dabanne me jego ta shiga ta fita an kece raini anyi hotuna na uban ubansu.

Washegarin suna su Inna sukace sufa tafiya zasuyi sosai Lameer da Hajiya sukaso su bari su qara kwana biyu amma sukaqi hakanan suka hada musu goma ta arziqi Hauwah na kuka suka tafi suka barta kan cewa sai tazo kawo musu Baffa.

Sake bada mota yayi da kudi me yawa da kayan sawa atamfofi da lasina yace akaisu har gda, aikuwa yasha ruwan albarka suna tafiya a gaban Hajiya ya sunkuceta yana juyawa da ita itakam Hajiya ta gaji da ganin rashin kunyar Lameer saboda haka ta nufi cikin gda ta barsa da ita tasan indai Hauwah ce ba qarewa zasuyi qlau ba balle yanzu da take ganin yan uwanta sun tafi sun barta……………

Direta yayi ya Kama hannunta suka shiga ciki ya zaunar da ita a kujera yace “meye na damuwar nan da yan kwanaki kema zakije kiyi sati guda”murmushi tayi ta saki ranta suka fara hirarsu kafin ya tashi ya fice.

Haka kwanaki sukayita tafiya Noor yanata girmansa gwanin sha’awa kyakkyawa dashi son kowa Lameer yana bata kulawa sosai lkcn da tayi arba’in kamar zai saceta haka yakeji saboda qauna a ranar yazo wai yazo ya dauketa ita kuma Hajiya ta kafe akan bazai dauketa ba sai sunje Rugar Sambajo sun dawo, dolece kawai tasa ya hqr saboda bayason tsayawa yana jayayya da Hajiyan amma a matse yake da iyalinsa.

Kwananta biyu da arba’in ya shirya musu tafiya hardashi akayi tafiyar zuwa rugar Sambajo itadai Hauwah har sukaje bata iya gane qauyen nasu ba saboda cigaba da qauyen ya samu an zuba musu kwalta har gaban gidansu an dasa musu turakun lantarki gashi memakon taga bukkoki sai taga gidaje ginin zamani duk an zagayesu da bulo, mamaki yasata sakin baki tana kallon ikon Allah Saida taji ana qoqarin karbe mata da sannan ta dawo nutsuwarta ta juyo kadai sai taga baffanta aikuwa tayi wani ihu ta rungushi.

Dukka gurin suka kamayi Mata dariya ya tureta yace “kaji yar qaniya da bazatayi hankali ba zata karyani kinje kinci cimar birni kin zama bukekiya dake kauce ki bani guri ni takwarana nakeson gani”

Turo baki tayi tace “aidai saida aka sameni sannan aka samu takwaran badanni ba bazaa sameshi ba” sanda Ardo ya wawuro yace “aifa dama nace duk ranar da kikazomin nan saina rade miki qafafu” nan fa suka fara zagaye gurin har Allah ya bata saa ta dafe bayan Lameer Baffa yace “ai shima me laifine ya sacemin autata ya tafi da ita birni ta manta damu lamuni daya zanyi muku da kukayimin takwara”

Sauke Hauwah yayi sunata dariya wasan dake tsakanin Hauwah da mahaifinta yafi komai birgesu Hajiya suna shiga dakin Gwaggonta tayi tsalle ta fada gadon Gwaggo tana dariya tace “shekara biyu da rabi ban hau gadon nan ba tun Ina yar qwailata yau gani hard….” 

Gwabe Mata baki Gwaggo tayi tace “bantaba ganin mara kunyar yarinya irinki ba a gaban mijinki da surukarki zakice danki ko?” Rufe idonta tayi tana dariya Hajiya tace.

“Ai rainon Lameer ce abinda yafi hakama zatayi nikam na sabada da rashin kunyarsu kune dai zakusha fama”

Kunyace ta lullube Lameer ya kalli hauwa da taketa lalube lalubenta tayi masa gwalo yace “ni kikewa gwalo ko?” Dagowa tayi tace “lahhhh Allah sarki ni baiwar Allah ni ko kallonsa ma banyi ba kiji wai Hajiya nice nakeyi masa gwalo”

Inna ce tace “hajiya kina kallon tabara” murmushi tayi tace ai sababbune wadannan yayanma nakeji” 

Haka suka yini yana manne da ita shammatarsa Hajiya yayi yajata yace “zo ki rakani gdan gonata mugani nakwana biyu banje ba” da haka suka fice yaja motar sukabar qofar gdan dama Noor yana gurin Ardo suna zuwa ya shiga dasu yayi parking suka rinqa zagayawa.

Tanata santin gurin yayi murmushi yace “nakine wannan halak malak” juyowa tayi a sukwane tace “ni kuma Abban Noor?” Daga Mata kai yayi yace tukuicin kyautar da da kikayimin kenan, inasonki Hauwah ji nakeyi kamar bazan iya rayuwa babuke ba” 

Wasu hawayene masu zafi suka zubo Mata ta rungumeshi tana kuka tace “bansan dame zan saka maka ba Abban Noor bansan me zanyi maka ya zama tukuicin halaccinka gareni ba wanne irinso kakeyimin da baya baka damar ganin laifina?”

Dagata yayi cak ya nufi wata qofa da ita ya bude ya shiga dakine babba a gyare tsaf katifar ya dauketa ya janye mayafinta ya kwantar da ita yasa hannu zai zuge mata zip ta riqeshi ya dago idanunsa da suka kada sukayi jajir ya kada Mata kai.

Hawayene ya zubo Mata yace “ba zanyi miki komai ba Amma idan kin bani hadin kai” bazata iyayi masa musu ba tabbas sunyi qoqari daga ita har shi watansu na hudu kenan wani abu bai shiga tsakaninsu ba sosai suka tsotsi albarkar jikin junansu.

Koda Lameer yakai qarshe yaso shigarta Amma taqi ta ma sanya masa kuka iyakar rarrashinsa taqi yimasa Shiru dolensa yayi yan dabaru ya samu yayi release ya miqe ya shiga yayi wanka ya fito yace.

“Ai saiki tashi kije kiyi wanka mu tafi” turo baki tayi tace “ni bazanyi wanka anan ba kawai mu tafi” bai kulata ba ya dauki key dinsa yayi waje itama ta miqe ta mayar da kayanta suka fita yaja motar suka tafi bata taba bata masa raiba irin yau.

Qiri² yaga samu yaga rashi data barshi da yasamu nutsuwa amma yanzu banda sha’awa babu abinda ta qara masa murmushi yayi na qeta ya kalleta yace “jibi zaki dawo ko?” Wani kallo tayi masa yayi murmushi yace “bazaki wucce hakan ba idan kuma kikayimin wata mgn wlh ranki baci zaiyi kuma a yau sai mun koma dake” 

Mirgina kai kawai tayi ta rinqa hadiye kukanta suna zuwa ta bude motar ta fice ya tabe baki shima ya fita gurin su Baffa ya tsaya suka qara gaisawa sosai Baffa yakejin kunyar Lameer saboda irin abubuwan da yakeyi musu bazasu qirguba shine ya shige gaba wajen kawo musu titin kwalta da wutar lantarki qauyen nasu shine ya gine musu qauyen yayi musu gidaje na zamani musamman gidan baffan sannan duk watan duniya saiya kawo musu kayan abinci da kudin cefane tun baffa baya karba har ya fara karba.

Yanzu gashi yayi masa takwara kuma fada tsakanin manoma da makiyaya ya qare ya shiga ya fita ya sasanta dangin mahaifinsa gidan sarkin Alqalawa da gdan Moddibo Durange kakan Hauwah har an fara hada surukuta bayan tashi da Ardo.

Har bakin mota Hauwah ta rako Hajiya tace Mata “saimun taho Hajiya agaida Alhaji har ta juya zata tafi ya cafkota bai wani damu da yawan mutanen dake gurin ba ya hadeta da jikinsa ya dago kanta ya dora bakinsa saman nata ya sauke Mata wani hot kiss.

Numfashi yaja da qarfi da saida kowa yajishi ya saketa cikin sarqewar murya yace “ki shirya da wuri zanzo na daukeki” itadai kunya bata bata damar bashi amsa ba ya zaro kudi masu yawa ya tura Mata a hannunta yayi mata bye bye ya wucce ya shige yaja motar suka tafi Hajiya na daga Mata hannu.

Cikin kwanaki biyun Hauwah tayi zagayen danginta wayyohhhh hauwa taga gata saboda mijinta ya siye rugarsu da danginta ya gama musu komai burinsu na shekara da shekaru ruwa hanya wutar lantarki duk sanadin aurensa da Jiddoh sun samu.

Aikuwa daga masu yiwa Baffaji wato Noor kyautar akuya tunkiya rago kai harda masu yimasa kyautar shanuwa abin gwanin birgewa.

Itadai badon taso ba suka gama kwanakinsu a Rugar Sambajo ranar da kwana biyun ta cika kuwa 4 na yamma sai gashi anan yake fada musu aikinsa ya mayar dashi America saboda haka zai tafi da Hauwah.

Shidai Baffa babu bakin mgn saboda yanzu qaunar Lameer yakeyi kamar shine dan nasa saida ta gama shirinta tana kuka take fada musu kyautar gdan gonar da yayi mata nanfa suka rinqa godiya Baffa harda hawayensa.

Kyauta taban mamaki jiddah tayiwa Mahaifinta kudade ba qananu ba Gwaggonta kuwa kyautar wata qaramar sarqarta da dankunne tayi mata qaramin kudinsu 1.5 Gwaggo tace siyarwa zatayi tasai shanu.

Itama Inna ta kwashi ganima itama tayi Mata kyauta taban mamaki yan uwanta ma haka tabisu da dubu biyar biyar da atamfofi maza kuma dubu goma da shaddodi masu tsadar gaske.

Lameer ya dauke matarsa suka tafi tunda suka taho ake take kuka yariga yasan laifinsa ne shiyasa bai wani damu da bata hqr ba har suka shiga Kano kalma daya bata shiga tsakaninsu ba, ba asalin gdansu ya nufaba wata unguwarce taga ya nufi wani katafaren gida yayi horn aka bude masa yasa kan motar yayi parking ya bude mata kamar bazata fitoba saida ya daka mata tsawa sannan ta fito.

Bude Mata qofa yayi ta shiga ya mayar ya rufe ya qwallawa Laraba Kira ta fito yace “kiyiwa Noor wanka ki kula dashi kafin mu sauko” karbarshi tayi a hannunsa ta shiga bangarenta shikuma ya sunkuci hajiyar tasa yayi sama da ita, kayan jikinsa ya rage ya kalleta fuskarsa babu rahma yace “ki cire kayanki nicked nakeson ganinki” 

Zaro ido tayi idanunta suka fada cikin nasa yace “ko bazakiyi ba?” Saurin zare mayafinta tayi tana kuka tana karkarwar haqori ta zuge zip din rigar ta fadi ya zagayo bayanta ya rungumeta ya zare Mata under siket din ya balle Mata bra din ta rintse idonta ya sanya hanunsa ya kama boobs dinta tare da sauke ajiyar zuciya.

Yace “na azabtu da yawa Babe bansan haka akeji ba sai yanzu bantaba shiga damuwa da tashin hankali irin Wanda na shigaba a tsakanin wata biyu zuwa yau kullum sex nakeso ashe gskyr Salees da yake cemin nayi hqr na daina kuka babu ciwon da basa da magani saidai idan baa daceba, baffanki shine ya bani maganin matsalata wani zuwa da nayi muna hira da Hamma Lawal ashe yanajina shine ya shiga ya fita ya karbomin magani gashi yanzu nima na zama cikakken namiji zan moreki son Raina”

Yana fadin haka ya sanya Mata dick dinsa a bayanta yana goga mata ruwan maziy dinsa dake fita yana sauke numfashi, a haka ya saukar Mata da kasala ya zagayo ya sanya bakinsa ya kama nipples dinta ya fara sha ta qanqameshi ta saki ajiyar zuciya ya turata gadon suka fada,  ya rinqa kewayeta da salonsa har yakai ga cimma gaci ya ratsata daqyar tana kuka tana qanqameshi ya dago ya zuba Mata ido yana pompim dinta.

Ya dauki kusan 1 hour da romance da sex sannan ya samu yayi release ya rungumeta ita kuma saboda rashin sabo sosai taji a jikinta.

Hqr ya rinqa bata hardai ya samu tayi shiru sukayi wanka sukayi sallar magrib da Isha ta koma ta kwanta zazzabi yana neman rufeta ya fita na nemo mata abinci ya dawo ya lallabata taci yabata fresh milk din da suka taho dashi Tasha tayi brush ya karbo Mata Noor suka kwanta tasa masa nono yaron da dan banzan wayo sai qare mata kallo yakeyi.

A wannan dare Hauwah taga ruwan jaraba gurin Lameer ya hanata sakat kuma ci yake Mata slow motion me fitar da hayyaci itakam har saida tace dama be samu maganin ba suyita zamansu a yanda suke.

Shikuwa wani mahaukacin dadi yakeji Hajiya ba qaramin gyara tayiwa surukar tataba sannan take a kwana biyun nan baffa da yasan tsiyar daya qullah ya sanya Inna ta rinqa tsumata ruwanta tsumi ruwan tsarkinta tsumi da dare kuma a bata wani baqin hadi da aka kwaba da man shanu ace ta tura a gabanta haka take turashi daqyar.

Ashe wani hadine nasu na fulani na mallaka sadidan aikuwa Lameer ya zama nama sai yanda sukayi dashi tunda kwadayi yakaishi ya shiga wannan guri.

Kwana bakwai suka qara ya debesu ita da Fadwah da Noor suka daga zuwa Texas, bayan tafiyarsu da sati biyu wani mummunan al’amari ya faru lfyr Allah muneef ya dawo sun fita sharholiyarsu shida abokansa yaje yasha wata qwaya ya fada ruwa suka tafi suka barshi baasan dashi ba sai bayan kwana biyu da sukaji shiru din tayi yawa.

Sosai mutuwar ta taba Hauwah shikuwa Lameer kamar ma abin bai dameshi ba saboda shi dama ya dade da cireshi a ransa cewama yayi mugun iri aka rage, ita kuwa Mubaraka tanacan data koma Jalingo ta fara iskancinta abin yaqi saboda bullet yayi Mata illah sosai ta dawo ta zauna tana jinya.

Dole badon Allah ba ta koma ga ubangiji ta kama addu’a har Allah ya fito Mata da wani dattijo ta aura kusan saan babanta ne sauqinta ma daya baya haihuwa sai kishi na hauka da matansa sukeyi gashi jarabbe duk da yasan matsalarta yaqi daga Mata qafa wasa wasa har saida aka kumayi Mata aiki likita yace ya rinqa daga Mata qafa.

Sannan ne ta samu sauqi amma fah tanashan jifa gurin kishiyoyinta ga gori cewa sukeyi garin neman maza haqqin mijinta yasa ta nakasa harsashi a gindi, idan sukayi Mata wannan gorin har kuka takeyi gashi shekara biyar babu haihuwa garama Muftahu tana ganin hotonsa ita kuwa Fadwah tama manta kalarta Lameer ya dauke yarsa sun tsallake boorder.

Cikin shekaru biyar din Hauwah ta goge ta zama babbar mace yaransu uku Noor Ma’eesha Mufeed sai babbarsu Fadwah yaranta kyawawa sosai sun saje da yayan turawa idan suna turanci kamar wadanda suka hadiyi dictionary idan suka juya larabci ma baa cewa komai ga uwa uba fullanci shi dama wannan kamar yaren ubansu kasancewar shima Lameer ya iya sosai ko 9ja sukazo basa hausa sosai sai kakanninta sunyi da gaske shikuwa Mufeed da yaji sun fara hausa zaisa kuka yace zaginsa sukeyi dan sunga be iyaba.

Wannan zuwan basuyi niyyar dadewa ba saboda exams din da Hauwah zasu fara kasancewar tana deegre dinta a can American, ana gobe zasu tafi da yamma sunata tserensu sukaji ana taba belt din parlourn lameer yayi dariya yace “fadwah bude zakuyi bayani Momynku ta wucceni shine kukemin dariya ko?….” 

Mgnar ce ta maqale saboda ganin me shigowar yayi saurin miqewa ita kuma ta zube ta rushe da kuka tace “kullum cikin kuka nake Ina fadawa Allah ya nunamin ranar da zanzo na gurfana gabanka na nemi qafararka” 

Hauwah ce ta fito daga kitchen ta saki tire din tare da cewa wace wannan Babe” matsowa tayi ta kama qafarta tace “dama an fadamin hqr ya baki babban matsayi a gdanki sai kinso mijinki yakeyin komai Hauwah kiyimin alfarma daya ta qarshe a rayuwata ki roqamin mijinki ya yafemin ko haqqinsa zai barni haka kishiyoyi sun sani a gaba da gori na rasa Ina zansa rayuwata”

Numfashi Hauwah ta sauke ta dagota tace “wlh ya dade da yafe miki Mmn Fadwah dama wannan zuwan nakeson na lallabashi mu kawo miki ita kiganta” juyawa tayi ta yafito Fadwah tace “fadwah Ina qannenki” tabe baki tayi tace “tunda mahaukaciyarnan ta shigo sukabi dady sama kinjisu canma ball sukeyi nima bari naje” 

Kamota tayi tace “kada na qaraji tsugguna ki gaisheta ki bata hqr mahaifiyarki ce” zaro ido yarinyar tayi tayi saurin daga Mata hannu tace “kiyi abinda nace kadai” sunkuyawa tayi ta gaisheta ta kamota ta rungumeta daidai lkcn da Lameer da yaransa biyu suka sauko ya tsugunna ya janye Fadwah yace “kada ki damu mubaraka kije kinci albarkaceka Hauwah da Fadwah na yafe miki amma ki kiyayi yata kima qaddara baki taba haihuwarta ba baa canzawa tuwo suna to Amma idan yayi ruwa saidai a kirashi talge sabida haka ni na canzawa Fadwah uwa wacce ko a lahira inada tabbacin bazanji kunya ba”

Ba itaba hatta Hauwah saida kalamansa suka sanyata hawaye ya dauke Mufeed ya kama hannun Noor zasu fita Hauwah tayi saurin tarar gabansa tace “don Allah kayi hqr kayi Mata wani Abu” kaucewa yayi yace “kiyi Mata transfer ta 2 millions ta account dinki sai ki dauki wayata ki mayar da abinki”

Tasan ba sake sauraronta zaiyi ba saboda haka itama bata sake cewa komai ba ta shiga kitchen ta dauko Mata abinci ta dawo ta dauki wayarta ta tambayeta account ta bata ta sanya Mata 3 millions ta haura sama ta hado mata akwati guda ta kayanta ta bata gdy rasa irin wacce zatayi tayi mubaraka sai kuka abinda tafi qarfi yanzu yafi qarfinta hakanan ta tafi tanata kuka tana kallon Fadwah amma taqi zuwa inda take.

Haka komai ya wucce suka tarkata suka koma Texas rayuwa taci gaba da tafiyar musu cikin farin ciki Lameer ya zama cikakken namiji Hauwah tana ciyuwa babu daga qafa idan tayi masa mgn yace qara’in rayuwa yakeyi……………

_Tammat bih hamdullah_

_Nan wannan lbr yazo qarshe kurakuran ciki Allah ya yafe mana baki daya_

Back to top button