Uncategorized

Macijine Shi Page 53-54 Hausa Novel

Na mammy kabeer

Elegant online writers📚📚

Free book 

Page 53/54

________________Gaba ɗaya Rashad ya zama kamar wani mahaukaci,ba abinda ke gabansa face biyan buƙatarsa.

Gaban rigar  fattu ya kama da karfin tsiya ya tsargeta ,tun daga sama har ƙasa.

Nan da nan farar best ɗin fattu da baƙin skin tite ɗin ta suka bayya, Allah ma yasa wandon har ƙasa yake.

” Wllh yau ko da zaki mutu ,saina ida nufina akanki,banga wanda zai iya karbarki daga hannuna ba” Rashad ya faɗa cikin wata irin murya ta azzalumai,waɗanda suka manta da cewar Allah yana kallonsu duk abinda suke aikatawa.

Da gyar fattu ta iya buɗe rinannun idanunta ,wanda tsabar mari da kuka suka sanya idanun kumbura sosai.

Ahankali take daga lips ɗin ta magana take amma saiƙa kura mata ido zaka fahimci me take cewa.”wallahu galibun ala amrina” shine abinda take ta maimaitawa abakinta.

Ƙoƙarin zare skin tite ɗin Rashad keyi amma sam ya kasa,jikinsa sai rawa yake,yana jin kamar wanda ake jona masa  shocking,Amma tsabar masifa da jaraba ,yaki fasa abinda yakeyi, 

Cikin haushi,ya ƙara kaiwa kumatun fattu mari mai zafi da shiga jiki.”Dan ubanki me kikasa ajikinki?idan na taɓaki nakejin kamar ana zuƙemin  jini?”Rashad ya faɗa yana mai kai fuskarsa saitin Tata,bakinsa ya ɗora akan na fattu,aikuwa ba wata wata fattu ta gartsa masa cizo alips ɗinsa.kara ya kwalla yana mai komawa gefe dafe da lips ɗin sa na ƙasa “kai -kai -kai Ni kika ciza Dan uwarki?zaki gane kurenki ,wllh yau saina kusan kasheki Shegiyar yarinya mai taurin kai”Rashad ya faɗa yana mai danƙo gashin fattu ,wanda yayi buju-buju.

Fattu fa ko motsin kirki bata iyayi,gaba ɗaya jikinta ya saki,tunda take a rayuwarta,bata taɓa shiga tashin hankali da azaba irin na yauba.

Sunan Allah kawai take ambata cikin ranta.

Adeeb kuwa cikin gaggawa yayi jawabinsa tare da godiya ga baƙin da suka zo dan tayashi murnar dawowa gida cikin ƙoshin lafiya.sosai ƙirjinsa ke mugun bugawa zuciyarsa  kamar zata fito waje,idanunsa sunyi jajur dasu,wani irin ɗaci yakeji cikin zuciyarsa,sannan ko dana second ɗaya ne fattu taƙi barin tunaninsa.

Gefen da Rashad ke zaune Adeeb ya ƙara kai dubansa, baya gurin har zuwa yanzu,kai gaskiya akwai Abinda ke faruwa ,dole yaje ya duba Hulwa.

Karanta Littafin >>> Macizai ne Page 1-10 Hausa Novel 

Dan haka cikin hanzari ya mike tsaye ,kallonsa abie yayi tare da tambayar ina zashi haka ?ya mike cikin hanzari,sanar da abie yayi cewar kansa ke ciwo yana son yaje ya kwanta.

Sanin da abie yayi cewar ,sam Adeeb yana son hayaniyane,yasa shi cewa yaje ya kwanta sannan yasha magani,akwai maganar da zasu yi zuwa dare.

Cikin sauri da sassarfa Adeeb ya nufi ƙofar barin hall ɗin,yana ɗan kallon gefen da tareeƙ ke zaune,saidai baiga tareeƙ agurin ba.dan haka ficewa yayi daga hall ɗin yana mai  takawa da sauri sosai.

 

Bangaren nanny ya nufa kai tsaye,yana shiga ya tarar da tareeƙ da nanny atsaye cirko -cirko,gabansa ne ya ƙara faɗuwa ,da sauri ya karasa gurin nanny yana kallonta,”nanny Ina Hulwa?”ya faɗa cikin muryar damuwa.

Kallonsa nanny tayi itama da alamun  damuwa akan fuskarta tace ” to magajin fada,nan da ka ganmu wllh ita muke nema,naje gurin taron can kenan,na barta tana barci,kuma ina dawowa naga bata ɗakin,na duba ko ina cikin bangaren nan banganta ba,saiga tareeƙ kuma yana tambayar ko Rashad ya shigo nan” 

Da sauri Adeeb ya nufi ɗakin da fattu ke zaune gabansa naci gaba da bugawa da ƙarfi.

Ko ina ya duba amma bata nan,to ina taje?yasan dai ba yawo takeyi ba ,ba inda ta sani cikin fadar nan,ko part ɗin sa ma sau ɗaya ya kaita,da sauri ya juyo yana kallon tareeƙ,” Ina Rashad yayi?”ya tambayi tareeƙ cikin wata irin murya mai kama da ta basawa.

“Yallaɓai ina zaune naga lokacin da Rashad  ke waya,kuma saiya fito waje,hankalina bai kwanta da fitowar sa ba,dan haka saina biyoshi,ina fitowa na hangesu shida Zulaihat,dan haka na buya ina sauraron me zasuce,yallaɓai amma banji me suke tattaunawa ba,saidai ga dukkan alamu akwai abunda suka ƙulla tare, sai dai kuma basu sami jituwa ba,dan kuwa cikin fushi suka rabu.

Nayi ƙoƙarin bin Rashad Dan ganin inda ya nufa amma ban ganshi ba” tareeƙ ya faɗa yana kallon Adeeb cikin damuwa.

Dafe kai Adeeb yayi zuciyarsa na masa zafi,lallai idan har wani abu Rashad ke ƙoƙarin aikatawa akan Hulwa ,to zai gane kurensa wllh azeem,saiya ɗanɗani kudarsa.

Cikin sauri Adeeb ya nufi ƙofar fita daga part ɗin,tareeƙ ya na biye dashi,ganin zasu fice yasa nanny tayi saurin bin bayansu dan bazata iya zama ba.

Suna fita daga part din,  kai tsaye Adeeb part din ammi ya nufa,ko fattu can ta tafi,saidai suna gab da shiga ya tsinkayi Muryar ammi na kiran sa,tsayawa yayi harta ƙaraso,”lafiya na ganku haka afujajan?gashi ka bar gurin taro ba’atashi ba?”ammi ta faɗa tana karantar yanayin Adeeb.

Karanta Littafin>>> YEL Hausa Novel Document

Ahankali Adeeb ya sauke wata ajiyar zuciya mai zafi,tare da lumshe idanu kana yace “ammi mun rasa inda yarinyar nan tayi ne ,shine zamu duba ko tana party ɗinki” Adeeb ya faɗa cikin yamutsar fuska kamar zaiyi kuka.

“Hmmmmm ji dan Allah wai akan wannan Shegiyar yarinyar suka tada hankalinsu haka,dan kawai basu ganta ba.

Tukunnama wllh sai kunga yadda rayuwarta ta koma yanzu,dan nasan Rashad ya kammala aikinsa”ammi ta faɗa cikin zuciyarta,amma azahiri,

Cikin hanzari ta riƙo hannun Adeeb tana mai zaro ido.” Ikon Allah ina kuma ta nufa?dan gaskiya  bata part ɗina, sai dai kuma ɗazu naga Rashad yana shawagi tsakanin part ɗina Dana nanny,Allah yasa bashine yayi mata wani abu ba” cewar ammi tana mai dafe kai cikin nuna tsantsar tashin hankali.

Gaban Adeeb ne ya fadi ,shikenan dama yasan hakan zata  iya kasancewa, dan kuwa sam yau bai yarda da Rashad ba dama ,”innalillahi “Adeeb ya faɗa cikin ruɗu da tashin hankali.

Da sauri ya kunna kansa cikin part ɗin na ammi,suka rufa masa baya.

Saidai nan ma sunyi iya bincike su amma bata nan,wasa -wasa fa sune har part ɗin Rashad Amma bashi ba Hulwa,zuwa wannan lokacin Adeeb ya shiga tsantsar tashin hankalin da bazai misaltuba,gaba ɗaya fuskarsa tayi jaaa kamar manja, idanunsa sun koma kala kalan nan,idan ya buɗe baki har wani turiri zakaga yana fitowa daga bakin nasa.

Hankali kowa ya tashi,tsakanin ammi ,tareeƙ ,nanny dakuma amma ,wacce ta tsincesu abangaren Rashad,Dan itama  nemansa tayi ta rasa agurin taron,shine tazo dubawa ko part ɗin sa ya dawo.

Sai kuma ta riskesu suna dubansa.sosai tashiga tashin hankali,karfa Rashad ya janyo mata wata sabuwar matsalar,amma tasan ma bai zama lallai abinda suke zargi ya kasance ba.

Cikin wani irin voice Adeeb ya juyo yana kallon amma tare da fara magana ” wllh !wllh!!wllh!!! idan wani abu ya sami hulwa ta silar ɗank,i nayi alƙawarin saina  illatashi,ta yadda ke kanki bazaki so ganinsa ba” Adeeb ya faɗa yana mai nuna amma da ɗan yatsanshi, tsabar masifa da bala’i kumatunsa har rawa suke.

Cikin tsoro amma ta ja baya tana mai dafe ƙirjinta ,dan kuwa ta tsorata da yanayin na Adeeb,tana kuma fatan Allah yasa ba hannun Rashad aɓatan fattu.

Can kuwa wajen taro ,anyi addu’oi,kuma anci  ansha taro ya tashi lafita,abie yana ta tunanin ina iyalin nashi suka nufa ,dan baiga kowa agurin taron ba,zuciyarsa na raya masa akwai Abinda ke faruwa ,dan haka kai tsaye bayan ya sallami baƙinsa ya nufi bangaren sa ,jakadiyarsa ya tura cikin gida dan ta gano masa ko lafiya.

Adeeb yana gama korawa ammi warning yayi waje cikin zazzafar zuciya da jin jikinsa yana masa wani irin rawa,idanunsa gaba ɗaya ya rine zuwa kalar na macizai.tsoro sosai ya kama su ammi da nanny,hatta tareeƙ atsorace yake,dan bai taba ganin yallaɓan nashi cikin wannan yanayin ba.

Part ɗin sa ya nufa kai tsaye,saidai yana zuwa saitin ɗaya part ɗin  na ,ammi yaji zuciyarsa ta tsananta da  bugawa ,cak yaja ya tsaya tare da ƙure ƙofar part ɗin da idanunsa.zuciyarsa na raya masa ya shiga ya duba,saidai yana tunanin ammi bata fiye amfani da bangaren nan ba ,kuma me zai kawo Rashad nan ma ?

Idan kuma yazo nan ɗin da Hulwa dan kawar da tunaninka fa ?ɗayar zuciyar ta bashi amsa.dan haka ba bata lokaci ya kama handle ɗin kofar ya murza da zummar shiga,saidai kuma akulle yaji ƙofar ,hakan ya matukar bashi mamaki,dan kuwa kullum part din nan abuɗe yake ,koda ammi bata ciki akwai hadimai acikinsa.amma how comes yau zai kasance akulle haka.nan take zuciyarsa ta bashi lallai Hulwa na cikin part ɗin nan.daidai lokacin su ammi suka ƙara so gurin.kallon tareeƙ yayi cikin wata irin murya yace ” na tabbata Hulwa na cikin nan,saidai ina mamakin yadda part ɗin ya kasance akulle karon farko” ya faɗa yana kallon ammi,wacce tayi wiƙi -wiƙi tsoro ya ɗan bayyana akan fuskarta.

Dan kuwa Adeeb ya kafeta da mayun idanunsa.sam ba zargin ta yake ba,kawai yana tunanin yadda aka yaudareta ne itama har akayi amfani da part ɗinta.dan baya raba ɗaya biyu cewar Rashad na cikin part ɗin.

Cikin in-ina ammi tace “habeebe a.a.a…k.wai spy ..kk…eyy ” ta faɗa cikin jan numfashi.

Kallonta tareeƙ yayi cike da zargi,dan shikam harga Allah tun farko ita ya zarga dan yasan bakin nufin ta akan  abun daya shafi Adeeb sarai.

Amma ma kallon ammi take cike da tuhuma,karfa tuggu ta haɗawa Rashad Dan kawai tana son ganin bayanta?

” Wai wannan wane irin wandone kika sa ?kusan minti nawa ina ƙoƙarin cirewa amma na kasa?wllh idan ma wani siddabarun kikayiwa wandon nan yaƙi fita,to zanyi abuna ahaka, dan ubanki yau ɗin nan nayi alƙawarin ,sai Adeeb yayi kwanan baƙin ciki “Rashad ya faɗa yana hankaɗa fattu kan wani ƙaton tebur dake ajiye gefen gado ,da alama an ajiyeshine ɗan ɗora kofuna ko abinci idan bukatar hakan ta taso.

Aikuwa tana fadawa ta fada kan wani glass cup, nan da nan  ya tarwatse gaba ɗaya ya sossoketa aƙirjinta da wuyanta.wani marayan ƙara fattu ta sanya ,wanda koshi Rashad baiji sautin ƙaranba, dan kuwa muryarta tayi mugun dashewa.ahankali idanunta ke lumshewa yana budewa,gaba ɗaya jini ya bata farar best ɗin dake jikinta.amma bako imani bare tausayi haka Rashad yake ƙoƙarin keta mata haddi, ba tare da ya cire koda wannan skin tite ɗin ba.

Wata irin zabura Rashad yayi sakamakon ƙaran da fattu ta kwalla,wanda yayi daidai da ƙarar  faduwar kofar dakin .

”RASHAD!!!!!!…………”

Aka kwallah kiran sunan Rashad Wanda saida Rashad ɗin ya buge kansa ajikin tebur ɗin nan tsabar razana da yayi da wannan kiran sunan nashi da akayi……

Hmmmmm masu karatu,nima tsabar tsoro bansan sanda wayar hannuna ta fadi kasa ba,mutara zuwa gobe idan na ɗauki wayar .fatana dai wayata bata fashe ba.

Mrs babi ce💘💘

Share and comment fisabilillah

More comment

More typing.

Back to top button