Uncategorized

Daudar Gora Page 5 Hausa Novel By Bilyn Abdull

 𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨

      (𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)

 𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻

*_5_*

_________________

_*MAAB LUXURY HOME!!* Sabuwar duniyar hamshakan mata da ƴaƴan gata.💞_

_*GIDAN* ƙawa da ƙawata gidajen da suka cika gida._

_*SABUWAR DUNIYAR* Amare da uwargidan data amsa sunanta ƴar gaban goshi._

_*MAAB LUXURY HOME* wata duniya ce ta ƙawa da ƙawata gidajenmu da kayan ƙyale-kyale na burgewa da ɗaukar hankalin duk wani mai kallo_.

_*SUNYI FICE* Fice irin na ɗaya a cikin tsara, sune na farkon fari, a farin da za’a kira fari a kowace irin duniya._

_*A GAREMU* ba sitturu na alfarma da kawa ne kawai ke tabbatar da mu hamshakai ba. Sai mun haɗa da ƙawata gidajenmu da kayan MAAB LUXURY HOME zamu kasance cikakkun ƴan gata ababen kallo da nunawa sa’a koda a cikin dubun da sukafi dubu._

_*MAAB LUXURY HOME* sun takaita mana dukkan wahalar nema ko order a kasashen ketare ta hanyar wadatamu da galla-gallan kayayyakin adon gidajenmu_

_*MAAB LUXURY HOME.* Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini._

_*INA UWARGIDA INA AMARYA!!?* Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*._

*_Mai azama shi za’a kira dana farkon fari😉. Bara nai sauri nawa suzo hannuna kafin a kwashe😁⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️⛹🏼‍♀️._*

__________________

……..Kama hanun yaron da Iffah tai da nufin subar wajen duk da key ɗin motar mutanen har yanzu na’a hanunta yay dai-dai da isowar wani nutsatstsen taku mai tafiya da sassanyan ƙamshin turare tamkar shi kaɗai iska ke tsintowa tana busawa a hancinan mutane. Kamar wani magic wajen yay tsitt na wasu sakkani, tsirarun mutanen da suka taru a wajen tun furuwar abun duk suka zuba masa idanu. Ita kanta hajiya Iffah mai masifar ƙirjintane yay wata irin harbawa lokacin da mutumin ya sauke nasa lulu idanun cikin tsakkiyar nata. Da ƙyar ta iya fisgar su daga cikin nasa tana ɗan murguɗa baki da sauke niƙaf ɗinta cike da dakiya.
      Idanun nasa ya janye daga kanta shima da matsawa gaban yaron ya kai tsigunne dai-dai tsayinsa dan ya fara ɗauka yarinyar nan aljanace ma dai kawai. Cikin sassanyar muryarsa mai zurfi da nutsuwa ya motsa lips ɗinsa kaɗan tamkar an fisgo maganar.
     “Kana lafiya?”.
  Kai yaron ya gyaɗa masa.
    Ya ɗan ɗage gira da motsa bakinsa kamar zai taɓe. “Uhhm! minene sunanka?”.
         “Amjed”.
  Yaron ya faɗa cike da kwarin gwiwa.
       A hankali ya sake kaɗa fararen idanunsa tare da jinjina masa👍🏻 ya saki wani sassanyan murmushi a karon farko da jan kumatun yaron. “Oh my Friend! nice name. Kana sona da aboki?”.
   Da sauri yaron ya jinjina kai yana washe baki. Idanunsa ya ɗan sake fiddowa suka ƙara girma tare da ƙara sakin murmushi. Ya riƙo hannu yaron alamar suyi musabaha.
   Al’amarin ya birge mutane da yawa, duk da babu wanda yasan wanene shi, amma ko makaho ya kalla wannan mutumi yasan babban mutum ne. Suit ɗin dake jikinsa farare tas ma kawai abin kallone. Balle shi a karan kansa daya kasance ƙyaƙyƙyawan gasken fatarsa da gogewarta har ɗaukar idanun mai kallo take. Ga wani ƙamshi na musamman mai saka nutsuwa ga mai shaƙa, yanayin kamewarsa da cikakkiyar isa irin ta manyan mutane ke ƙara kawata kwarjininsa da cikar kamala ga duk mai kallonsa.
      A karo na biyu suka sake haɗa ido da Iffah dai-dai ya gama gaida kakar yaron nan da keta faman washe baki da jera masa godiya dan kuɗine dunkulallu sabbi ƙal ya damƙa a hanun Amjed. Harara ta balla masa da janye idanunta da sauri saboda wani abu mai tsananin sanyi taji yana tafiya daga ƙafafunta har saman kanta. Cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita shima ya juya ya bar wajen kai kace akan dole yake taka ƙasar saboda takun zaratan maza masu cikakkiyar isa da lafiya ce tattare da tafiyar tasa. Iffah ta jefama ɗaya daga cikin samarin nan biyu key ɗin motar, dan ɗayan ya tafi da hanzari ya buɗema ogansu ne. Dai-dai zai shiga ta ballama wanda ta jefama key ɗin harara da faɗin, “Daga yau ko daga nesa kuka hangoni to ku canja hanya koda a jirgi kuke kuwa”.
      Shigar maganar tata a cikin kunensa dai-dai zai shiga motar da aka buɗe masa ya ɗan ɗago idonsa, sai dai wadda ya ɗago da nufin kallar da mamakinta ke cin ransa tuni ta nufi barin wajen tamkar ba ita ta haɗa dabar wajen ba… Suna ƙoƙarin shan shataletalen titin idanunsa ya sake sauka a kanta ta miƙe titi tana tafiyarta a nutse, sai dai fuskarta a rufe take da niƙab data saki tun bayan haɗa idonsu na farko….

         
          🤔Wannan ƴa ta Babiy wataran sai ta saka an mata dukan sakwara a titi in har bata canja hali ba😬🚴🏼.

      ★★……★

  “Badai a ƙasa kika tahoba auta? Na ganki a gajiye tamkar an koroki”.
       Zubewa tai a taburmar da Ummu ke zaune, tare da ɗora kanta a cinyarta tana ƙara narke fuska. “ALLAH a ƙasa na taho Ummu. Haka kawai naji ina son na taho a ƙafan”.
     “Ai gashi nan duk kin gajiyar da kanki, dama keba wata isashshiyar lafiya ba. Tashi kiɗan watsa ruwa dan sai warin rana kikeyi”.
   “Kai Ummu warin rana fa?”. Tai maganar a shagwaɓe da kamo rigarta ta kai hancinta. Miƙewa tai tana tura baki gaba da faɗin, “ALLAH Ummu kinso dai yarfanine amma ƙamshin ma turare nakeyi”.
        Murmushi kawai Ummu tai da girgiza kanta, ita kuma ta shige ɗaki sai faman cika baki take da iska a dole taji haushi…..

          ★Da daddare suna zaune a tsakar gida cikin hasken farin wata daya raba Hanash na koyama Iffah aikin makaranta. Daga gefensu Ummu da Babiy ne zaune yana cin abinci. Hira suke jefi-jefi akan kayan lambunsa da zai fidda a ƙarshen satin nan ga ƴan kasuwa. Iffah tai karaf jin Babiy yace zuma batayi kirki ba wannan karon bazata wuce tulu biyu ba.
     “Babiy sai a bar mana mu shanye kawai a gida. Kaga dama Ummu zatamin alkakin saukar islamiyyarmu nan da wata biyu”.
          Murmushi Babiy yayi, “Zanso haka Ibnati, sai dai bazai yuwuba dan dukanta zan kaita masarauta ne”.
   Take murmushin fuskar Iffah ya ɗauke baki ɗaya. Kamar zatai magana sai kuma tai shiru ta maida kanta ga aikinta kamar bataji ba. Shima Babiy sai bai sake cewa komai ba akan zumar suka cigaba da maganarsu da Hanash da Ummu dake saka baki jefi-jefi…..

KARANTA ZAFAFA 2023

*IDON NERA By Mamuh ghee*

        Tun wannan magana babu wanda ya sake tada zancen zumar nan. Babiy da Hanash suka duƙufa tattare kayan lambu da za’a fitar. Yayinda Iffah ta cigaba da zuwa makarantarta a zahiri kamar babu wata damuwa tattare da ita. Sai dai kuma a baɗini tun randa akai maganar kai zuma daular ruman zuciyarta sam bata huta ba. A duk motsinta cikin ƙullawa da kwancewa take game da babban burinta na ɗaukar fansa. Wanda tasan bata da wata hanyar yin hakan sai ta wannan zuma da Babiy ke kaiwa masarauta. Kuma tasha jin cewa Tajwar ne ke shanta kawai.  
        Har ana saura kwana biyu bata samu wata mafitaba akan ƙudirinta, dan haka tana zuwa makaranta taja wata ƙawarta da kafin yanzu da ta canja suke sabgarsu da rashinji tare gefe. Ikram da taji farin cikin ƙawarta ta fara dawowa yanda take babu musu ta bita suka koma can ƙarƙashin wata bishiya suka zauna.
    “Ko kefa Iffah, ALLAH bana jin daɗin yanda kike shareni yanzu sam. Dan ALLAH ki manta da komai mu cigaba da yima su Akia Arfa addu’a”.
         “Humm”. kawai Iffah tace da ɗan laɓe fuska. “Kinga ni ba wannan yasa na kiraki ba, tambayarki nake so nayi?”.
     “To ALLAH yasa na sani”. Cewar Ikram tana gyara zama.
  “Kinma sani, kwanaki bakin bani labarin sister ɗin mamanku tasha zuma taita ciwon ciki ba, kafin aje asibiti har hanjinta ya kakkatse?”.
           “Yes anyi haka, bayan kwana huɗu ma ta rasu ai. Sai daga baya aka gane ashe saurayintane ya zuba mata wani magani a ciki. Sai dai har yanzu ma ana shari’an, dan a binciken likitoci sudai sunce basuga komai ba, abokinsa kuma da suka ƙulla tare ne ya tona masa asiri, ya kuma rantse sun zuba ɗin dan tare suka sayo maganin”.
       Iffah dake saurarenta tace, “Anya kuwa ba abokin na masa sharri bane?”.
    “To mudai bamu san dai-daiba sai ALLAH. Grand mother ɗinmu ma ita tace dan ALLAH abar shari’ar tunda UBANGIJI mafi sani ne. Idan anje garesa shi ya rarrabe ƙarya da gaskiya”.
          “Uhm gaskiya kam tayi magana mai ƙyau. To amma ni abinda ya bani mamaki, shiko wannan wane kalar maganine haka da har za’ace likitoci sun kasa ganewa, bayan kuma gashi sunce ya kakkatsa mata hanjinta da kansu.”
     “K nifa abinda na fahimta kamar an sayesu ne likitocin, kin sanfa ɗan manyan mutanene yaron. Amma abokin nasa ya faɗi sunan maganin sai dai na manta”.
           “Komaima zai iya faruwa indai shegun manyan ƙasar nannne, kansu kawai suka sani azzalumai. Amma ina son nasan sunan maganin dan ina son nai bincike a kansa ma ni wlhy.”
     “Kedai kawai wani abun adai rufesa kawai. Uhm kina nan da shegen son bincike-binciken nan naki, anya Iffah idan ALLAH ya cika miki burinki na zama ƴar jarida bazaki addabemuba? Dan na kula har hurumin aikin jami’an tsaro zaki dinga shiga tsabar bin kwaf-kwaf ɗinki”.
              “Ƴar sa ido naji, nidai kafin a tashi ki tuno sunan maganin inba hakaba zanta addabarkine”.
   Ikram tai dariya tana miƙewa. “Indai wannan ne zanyi ƙoƙari. Maganin ma fa ba wani na kirki bane ba ance ana zubama ƙananun ƙwari ne dakan damu mutane a cikin gida a ruwa haka ko abinci, dan basajin warinsa sam ko ami aka zuba sai kiga sunsha ruwa da shi ko abinci.”
      “To kinga koda ba bincikeba ai zai mana amfani, dama mu da muke cikin lambu kullum cikin ganin macizai dama halittu masu cutarwa iri-iri dake iya zama a cikin gida haka.”
   “Eh gaskiya kuma hakane, zai ko taimaka muku insha ALLAHU”.

         Kafin a tashi kuwa Ikram ta cika alƙawarin samowa Iffah sunan magani. Takoyi farin ciki har haƙwaranta na bayyana wajen murmushi irin wanda ta jima batayiba a rayuwarta. Iya kuɗin motarta ne kawai a jikinta. Dan haka ta gama tsara ƙaryar da zatai ta samu kuɗin sayen maganin idan ta koma gida. Koda ta koma gida tun kafin takai zaune ta sanarma Ummu ai an basu wani Assignment mai wahalar gaske. Gashi bata da littafin dazai taimaka mata tayi har sai ta saya. Ganin yanda tai maganar a serious yasa Ummu yimata murmushin kwantar da hankali.
       “Karki damu in har ana saidawa anjima sai Hanash ya fita ya saya miki kema, ko kuma ki bincika a kayan karatun su Arfa ƙila ki samu ai”.
   “Ummu basu dashi sam, dan kwanaki ma da malaminmu yay maganarsa sannan suna nan ai. Kinga da suna dashi ai da sun bani”.
         “Uhm hakane kuma kam. To ki bari Hanash ɗin ya dawo sai ya dubo miki”.
      “Ummu ni kawai ki bani yanzu da nayi wanka sai naje da kaina na dubo. Ƙilama daga nan na ƙara ilimi”.
            “Kai Iffah kin cika fitina, kin dai san ba son yawan fitarnan taki muke ba ai”.
     “Na sani Ummu, insha ALLAHU babu abinda zai faru addu’arku na biye dani, kuma ina suturce jikina idan zan fita”.

        Badan hankalin Ummu ya kwanta ba ta yarda tabar Iffah ta fita. dan ta dage akan gobe ake buƙatar sukai Assignment ɗin, idan tace zata jira sai Hanash ya dawo dare zaiyi tunta sunje babbar kasuwar cinikayyar ƙarshen watane ta daular ruman kai kayan lambu. Kamar kullum tai shirinta tsaf tare da rufe duk jikinta sai idanunta kawai da ake gani. Sosai ash color na abayar jikin nata mai adon duwatsu blue masu sheƙi sukai mata ƙyau duk da ba’a iya ganin fuskarta. Cikin nutsuwarta take takunta tamkar wata tarwaɗa. Dan Iffah tun tana yarinya irin yaran nanne masu shegen iyayi da kauɗi. Tun a shekarun baya mutane kance za’ai kallon ƴammata a wajen nan, dan tafi yayunta son kyale-ƙyale da tsantseni irin na ƴan gayun mata masu ji da kansu. Da ƙafa tazo har titi duk da akwai ɗan tafiya a tsakaninsu. Ta tare abin hawa tare da sanar masa inda zai kaita.    
       A ƙofar katon kantin da ake saida duk wani nau’in magani daya shafi gona dana kauda mugayen halittu masu cutarwa ga mutane dakan shiga cikin gida ya sauketa. Ta biyashi kuɗinsa sannan ta shige. Kanta tsaye ta miƙa takardar data riga ta rubuta sunan maganin dan karta manta. Aka faɗa mata kuɗin ta biya suka bata. Wani irin farin ciki takeji a ranta, tunin karta koma gida babu littafi ta zama abar tuhuma ya sata cema mai abin hawan data hawo ya kaita babban shagon littatafai. Koda suka isa cewa tai ya jirata yanzu zata fito su wuce. Gargaɗi ya mata akan kuɗintafa ya ƙaru, tace babu damuwa tana shigewa.
          Ganin babu yawan mutane a shagon duk da ƙatone sosai ba kuma wajen da za’ai hayaniyar da zaka san adadin mutanen wajen bane yasata ɗage niƙab ɗinta yanda zataga komai da ƙyau. Kowanne littatafai da sashensu a rubuce kuma yanda bazakasha wahalar nema ba, maimakon ta nufi inda zataga irin nata kai tsaye saita fara zagaye. Sai da ta gama kewaye-kewayenta tamkar ta manta da wanda ta ajiye a waje kafin ta tsaida hankalinta ga inda zataga littafin daya dace ta ɗauka. Surutun yara takeji kaɗan-kaɗan ta bayan inda take, ta ɗan dudduba taga babu ta inda zata leƙasu sai ta haƙura cikin taɓe baki takai hannu kan wani littafi zata ɗauka. Daga can ɓangaren ma dai-dai an kai hannu akan littafin za’a ɗauka dan duk kanta ɗaya ce, littatafan ne kawai suka rufe wanda ke can baya ganin na nan. Iffah taja, daga can ma aka ja, jin za’a fisge saboda an fita ƙarfi dama tsaho dan ita harda su ɗiɗɗishe saita fisga itama a ɗan fusace saboda gani take wani keson raina mata hankali. Ta cikin ɗan space ɗin data cire littafin ita da shi suka zubama juna idanu, haka kawai taji tsigar jikinta ta tashi duk da ita bama wani ganesa tai da ƙyau ba saboda space ɗin bawai ya buɗe da ƙyau bane. Kamilalliyar fuskarsa da dama babu wani walwala a cikinta ya ƙara tsukewa dan shiko sarai ya ganeta………..✍

       
        
★ Shin wanene wai wannan dake neman zamema Iffah ɗan kaɗafi?.
★To wai mima zatayi da maganin data saya ne?.
★ Ko Iffah zataci nasarar cika ƙudirinta?.
★Idan taci nasarar minene zai biyo baya?.
★Mike kashe matan Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdull-majeed ne?.
★Shi kansa Tajwar Eshaan ɗin wanene shi?.
★Yaya yake? Taya zamu san ainahinsa?.

     *_Duka amsoshin nan na’a cikin gundarin labarin littafin DAUƊAR GORA. Masu iya magana kance (CIKI KA SHATA). To waima miye ma’anar kalmar Dauɗar gora ciki ka shatan ne?🤗. Kumuje zuwa kudai, karku bari a baku labari masoya🤸🏼, dan cakwakiya iya cakwakiya. Kundai san minene gidan sarauta, balle irin wannan na DAULAR RUMAN da Tajwar ɗinta ke amsa suna Shahan-shan. Ma’ana (King of Kings🤴🏻). Bafa cakwakiyar kawai bace, akwai tsumammiyar soyayya mai fasa zuciya😋._*
            Dawa?.
       A ina?.
   Taya?.
_Duk amsar na cikin *DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA🤗* dake a ɗaya daga cikin littatafai biyar na *ZAFAFANKU* abin alfaharinku. Kundai sansu kun san aikinsu babu wasa babu jan rai a cikinsa balle shiririta. Zamu gamsar da ku da salon labaranmu a wannan karon fiye dana baya insha ALLAHU. Kudai kawai ku kasance da zafafan naku biyar zakuce nina faɗa muku😋😁._

Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K’AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*

_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+22799643131

Books biyar  1250CFA
Books hudu  1050CFA
Books uku  850CFA
Books biyu  650CFA
Bookk daya  450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

Back to top button