Uncategorized

Dalilan Rashin Sakin Shirin Labarina A Daren Jiya

 Tun bayan ficewar jarumi Nuhu Abdullahi da yake amsa sunan Mahmud a cikin shirin, to sai fa shirin ya fara walan keluwa. 

Shirin na labarina yana cikin wannan walankeluwarne kuma kwatsam sai itama mai gayya mai aiki wato jaruma Nafisat Abdullahi da take amsa sunan Sumayya a shirin ta bayyana ficewarta daga cikin shirin.

Related Articles

Bidiyon Sadiya Haruna Tana Taki Rawa Tabar Kasida Ta Koma Bin Safara’u Da 442

Matsayin da Na ba Mahaifina na Gida, Shi na bai Wa Adam Zango – Jaruma Tumba Gwaska

Kalli video Yadda Jarumin Adam A Zango Yake koyawa ‘Yarsa Waka

Yadda Rayuwar Jaruman Hauwa Waraka Ta Koma Bayan Daina Saka Ta Film

Masha Allah: Bidiyon Hafsat Idris (Barauniya) A Gidan Aureta

Haƙika ficewar Nafisat Abdullahi ba karamin nakasta fim ɗin yayi ba domin itace asali kuma gundarin labarin wanda dole sai da ita sannan fim ɗin zai ta fi yadda ake so.

Ga Cikakken Bidiyon dalilin da ya sa👇👇

Duk da cewa director Malam Aminu Saira da kuma marubucin shirin Nura Ngwangwazo sunyi ƙoƙarin riƙe masu kallo amman hakan bai hana jama’a fahimtar cewa Mashiryin shirin na labarina sun samu matsala da jaruman shirin ba.

Bayan sun samu da kyar an kammala shirin na labarina kashi Na 4 da kyar wanda gaba ɗaya bai yi wani armashi ba saboda tsaya a waje ɗaya da aka yi, duk a dalilin saɓanin da Mashiryin hirin ya samu da jaruman.

To kwatsam kuma bayan share kusan wata biyar ba tare da jin ɗuriyar shirin ba, sai kuma akaga wata sanarwa daga daraktan hirin wato Malam Aminu Saira inda ya wallafa kamar haka:

SANARWA! SANARWA! 
ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAH 🙏Muna Sanar da Ma’abota Kallon Wannan Shirin #LABARINA series cewa In sha Allah Zamu cigaba da daukar Season 5&6 . Muna kuma Sa ran Fara Haska muku shi a wata mai kamawa (JULY 2022) in sha Allah. Muna baku hakurin akan dogon Jira da kukai, muna Godiya ga ƙyaunar ku Gare mu 🙏 Allah yabar Zumunci 🙌❤️🌎 @sairamoviestv #LABARINA 5&6
Ko da ganin wannan posting ɗin a shafin daraktan ai sai mutane suka haƙiƙance kan cewar ai 1 ga wata za a dawo, amman haƙikanin gaskiya daraktan shirin abarina bai faɗi taƙamaiman ranar dawowa ba, kawai ya faɗa cewar a watan July za su dawo.
Bayan wannan kuma akwai wani labari da muka gani yana yawo shidai labarin da zamu kawo maku ance ɗayadaga cikin mashirya shirin Labarina ne ya wallafa shi ga labarin kamar haka:
Martani Zuwaga Nafisa Abdullahi” Bayan Fitar daga Shirin Labarina Inda Yanzu Haka An Cigaba da Daukar Wannan Shirin Na Labarina.
A Cikin Martanin da Akai mata” Shine Koda Nafisa Abdullahi Kuma Koda Babu Ita Za’a Cigaba da Shirin Labarina Wannan Shine.
Don Haka Yanzu Ma An Cigaba da Daukar Shirin Labarina Season 5 Inda Kuma Yanzu Aiki Yayi Nisa, Labarina Zai Ci Gabada Zuwar Muku Nan Bada Jimawa Ba.
Tabbas Wannan Shirin Na Labarina Shiri Ne dayake Matukar Burge Masoya Wato Masu Kallo, Na Tabbata Yanzu Haka Jama’a Masu Tarun Yawan Gaske Ne Suke Jiran Sa.
Ana sa ran dai daraktan zai maye gurbin Nafisat Abdullahi da jaruma Fati Washa wadda itama tauraruwa ce a masana’antar ta kannywood domin kuwa itama tana da masoya masu tarin yawa tamkar Nafisat ɗin sai dai wasu suna ganin cewar daraktan zai maye gurbin Nafisat Abdullahi da wata jaruma da ake kira da Ummi Alaqa wadda suke tsananin kama da Nafisat ɗin, To kuma  sauraro ko meye ra’ayinku game da wadannan jaruman guda biyu shin wacce kuka ga tafi dace wa a cikin su?

Back to top button