Uncategorized

Abdul Jalal Chapter 6 Complete Hausa Novel

 

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un shine abinda Jalila ta fada jikinta a sanyaye

A hankali ta sauke wayar daga kunnenta ta kashe wayar

Takalli siyama

“Aminiya ya tafi”

Yasalam shine abinda siyama ta furta 

“Kwantar da hankalinki har yanzu da sauran lokaci ai”

“Kwanciyar hankalifa babu shi Aminiya dan bakiji yadda zuciyata take min bane 

Bari in tafi Gida uumi tace kar in dade kuma kinga nabata lokaci bari in tafi kawai”

Har gate Siyama ta rakota tana bata kwarin gwiwa, tare da bata shawarar cigaba da addu’oi 

Sannan ta mata alkawarin zatazo har gidan taji yadda akayi

Haka Jalila ta tafi Gida jikinta a mace 

Yanayin fuskar Ummi ya nuna mata tayi fushi da ita

Dan se basar da ita take Jalila ta rasa meyake mata dadi

Jeje ne a tare da wani mutum a cikin mota me tint glass yasaka wando three quarter da wata Yar Riga Mara hannu suman nan tayi tsage²

Kai daka ganshi ka ga dan iska

“Katabbatar kayi abinda yakamata in kukaje kasan abinda ya dace kayi shima wannan aikin naka akwai kaso me tsoka ka tabattar da aikin nan ya tafi dai² “

Mutumin yayiwa jeje maganar

“Considered it done my boss zan tabbatar da aikin nan ya tabbatat”

Jeje yafada yana dan risinar da kai

“Good”

mutumin yafada cikin Isa

Sannan jeje ya bude kofar motar ya fita ya dauki akwatinsa 

Inda sukayi zasu hadu da Jalal yaje ya tsaya ya kirashi a waya yan mintuna kadan sega Jalal ya karaso 

Shima 

“hmm yau kayi abun arziki ka cika alkawari”

Murmushi Jeje yayi

“ba dole ba my boss ina ciki farin ciki”

“Good yanzu se mu tafi ko”

Gaban Jalal ne yai mummunar faduwa 

Meyake damuna ne haka, menake shirin yine”

Jalal yake maganar a zuciyarta

Download>>> Ana Dara Ga… Complete Document

“Yanaga kana tafiya kuma a hankali yanzu ko akwai abunda yake damunka” Jeje ya tambayeshi 

Girgiza kai Jalal yayi 

Jeje ne yafara mika passport dinsa aka duba aka bashi ya danyi gaba yana jiran a duba na Jalal,

Jiki a sanyaye Jalal ya mika passport dinsa

(Karka kara kirana dan uwanka Jalal niba dan uwanka bane, tunda zaka iya manta soyayya da shakuwar dake tsakaninmu ka tsallake ka barni,

Tun tasowata bani da dan uwa namiji ban budi ido da kowa ba a matsayin aboki dan uwa sekai,!!!!!)

Maganganun Jawwad ne suke dawo masa dakuma tsantsar damuwa da hawaye da ya gani kwance a idon Jawwad su yake tunowa se yaji zuciyarsa ta cunkushe bakin ciki ya ziyarci zuciyarsa, gaskiya ba karamin kauna Jawwa yake masa ba in ya tafi beyiwa kansa adalci ba Jawwad wani bangarene me mahimmanci a rayuwarsa ga kuma mahaifinsa, anya inyayi tafiyar nan yayiwa kansa adalci

jikinsa ne yayi matukar yin sanyi, hannu yasa ya karbi passport dinsa ya juya dabaya yafara tafiya 

“Jalal ya haka lokaci fa inazaka jene”

Jeje ya tambayeshi 

Bebashi amsa ba yacigaba da tafiya da gudu Jeje ya taho ya sha gabansa 

“Man wai meyafaru ne ?

Ina zakaje yanzu fa jirginmu ze ta shi”

  “Zaka iya tafiya nikam na fasa”

Zaro ido Jeje yayi “why meyasa zaka fasa”

“Saboda haka naga dama nace in zaka ka tafi ni na fasa”

Ya bashi amsa

JALAL yayi maganar a tsawace

Wayarsa ya dakko ya kira Jawwad, amma be daga ba taita ringing

Jawwad yana kallon kiran yaki ya amsa seda takusa katsewa sannan ya daga wayar

“Kazo ka daukeni a airport”

“Kamar ya?”

Jawwad ya tambayeshi

“Ina airport nafasa tafiyar kazo ka daukeni”

“Bazan zo ba dacan ni na kaika”

“Idan bakazoba zan tafi u know I mean what I said”

“Ohh sorry gani nan zuwa”

Wai dagaske ya fasa tafiyar Jawwad ya tambayi kansa da sauri ya mike ya dau mota ya nufi airport

Ummice take lazimi akan dadduma gidan shiru kaman ba me rai a cikinsa

Jalila tana can dakinta tana duniyar tunani

Ummi ce ta dinga kiranta takirata ya kai sau uku sannan taji ta amsa

“Jalila zonan”

“To Ummi gani nan zuwa”

Mikewa tayi ta nufi dakin Ummi taje gabanta ta zauna

“Ummi gani”

“Naganki ai, Jalila wai meyake damunkine kwata² yan kwanakin nan kaman baki da lafiya baki da walwala Sam 

Meyake damunkune baki da Wanda zaki gayawa matsalar ki fiye dani baki da aiki se tunani 

My dear tell me what’s actually wrong with you bana jin dadin ganinki a haka”

Tausayin ummine yakamata taji kaman ta gayamata gaskiya amma seta fasa

“Ummina babu abunda yake damuna kawai surutan danake da daddare ne da mafarkai bana so”

“Eyyah sorry my dear kinji tunani baze hana faruwar komai ba addu’a zaki dingayi nima inayimiki Komene Allah zemiki maganinsa”

Haknan se Jalila taji hankalinta ya Dan kwanta 

Zame jikinta tayi a hankali ta kwanta akan cinyar ummi

Tanata ambaton Allah a zuciyarta domin tasamu zuciyarta ta rage bugun da take

Ba a dau dogon lokaci ba Jawwad ya karasa airport Jalal ya hango a zaune jeje yanata lallaba shi

“Tir da wannan dan iskan bawan, mtseeww”

Jawwad yafada a hankali

Jalal yana hango Jawwad ya mike 

“Dan uwa dagaske ka fasa tafiya”

“Nafasa Jawwad kona tafi bazan samu nutsuwa ba zuciyarta tana Nigeria tare da Dan uwana”

Rungume juna sukayi kaman zasu shige jikin juna

Wani mugun kallo Jeje yayiwa Jawwad

“Wai dagaske fasawar zakayi?”

Jeje ya tambayeshi a fusace

“Jeje nafasa tafiya bazan juri ganin kwalla da bacin rai a idon Jawwad kamar yadda nafada maka kona tafi dubai zuciyata tana Nigeria”

Jawwad ne yaja trolley Jalal yasaka a boot, ya bude masa motar ya shiga

Jeje ne ya zagayo gaban Jawwad yai masa magana kasa²

“Yadda ka bakantamin yau ka rubuta ka ajiye komai Daren dadewa se na bakanta maka fiye da yadda kayimin”

“Allah ya fika”

Shine amsar da Jawwad ya bashi

Ya shiga ya kunna mortar suka tafi Jeje kaman yayi hauka gaba daya shirunsu ya rushe shi beasan meze gayawa boss dinsa ba

Naushi ya kai cikin iska kamar mahaukaci

“Fuck you Jawwad, indai muna raye sena kuntata maka kamar yadda kayimin “

Download>>> Matar Hariji Complete Document

A hankali wani bacci me dadi ya dauke Jalila akan cinyar Ummi se ajiyar zuciya take kaman wadda ta wuni tana kuka

A hankali Ummi ta shafa kanta Allah yayi miki maganin abunda yake damunki baby na

Duk da yamma tayi Ummi bata tashe ta ba ta kyaleta saboda in tayi wannan farkawar cikin dare bata komawa bacci

Se gefin magariba Jalila ta farka tana farkawa da bugun zuciyar nan ta farka 

“Ya salam”

ta fada a hankali

“To dagani tunda kin tashi”

“Ummi ki Dan kyaleni mana in gama hutawa ni dama xaki goyani”

Ture kanta Ummi tayi ta mike ta tafi dauro alwala 

A hankali taji bugun zuciyarta tana komawa normal

Ringing din wayarta ta jiyo a dakin ta da sauri ta mike ta tafi ta daga wayar lambar siyama CE

“Aminiya ya ake ciki kuwa ?”

“Oho”

“Kaman ya oho ya tafin ne? Kinkuma tambayar Yaya Jawwad?”

“Aminiya mezan tambayeshi ne ?ya rigada yacemin ya tafi se dai kuma addu’a kawai”

” banji dadi ba aminiya 

Allah ya kiyaye ya tsare se mucigaba da addu’a amma ina ji a jikina kaman betafi ba”

“Tab wannan uban taurin kan to Allah yasa amma tunda ya furta seya tafi”

“Insha Allah be tafiba gobe in Allah ya kaimu ki shirya da wuri mutafi islamiyya karki jamana dukan makara”

“Insha Allah aminiya”

“Wani irin sha³ ne kai jeje why do you failed this mission, after all u know na Dora burina akan wannan tafiyar dazukuyi meyasa?’

a wannan tafiyar naso dawwamar da bakin ciki a zukatan ahalinsa na har abada”?

Mutumin dazune da ya kai jeje airport a motarsa yake maganar cikin fada

“Am sorry sir amma ba laifina bane wannan abokinnasa ne ya hana shi”

“Wa kenan”

Mutumin ya fada cikin fada

“Wannan mayen nasa Jawwad, saboda shi ya fasa tafiyar”

“Jawwad ko? Yayi kyau zan tabbatar masa da ba a shiga hanyata semun bar masa mummunan tabo a cikin zuciyarsa Wanda har gaban abada baze goge ba, dama shine yakemana karan katsaye a al’amuranmu zamuyi maganinsa”

“Hakan shine mafita ayi maganinsa kawai”

Jeje yayi maganar da sauri

Har cikin Gida Jawwad Yakama hannun Jalal yashiga dashi yan gidan duk suna parlour ILHAM.tana zaune  tayi shiru tana tunani

Yayinda mummy keta rusa kuka daddy yana rarrashinta

Jawwad ne yayi sallama gaba daya suka daga kai domin amsa sallamar 

Kawai sesuka ga Jawwad tare da Jalal

Jawwad ya janyo hannunsa zuwa cikin palour

“Gashi nan ya fasa tafiyar hankalinku ya kwanta, mummy kukan ya isa gashi ya dawo”

Jawwad ya fada yana kallon mummy 

To Alhamdilillah nima ba a son raina ya tafi ba, ba yadda zanyi ne tunda ya dawo se muyiwa Allah godiya

Ita kam Ilham bakinta ne yaki rufuwa

Mummy da gudu ta mike taje ta rungume Jalal tana cigaba da kuka hada sheshsheka

Kunsan d’a da uwa karo na farko bayan lalacewar Jalal da yaji kukanta ba dadi a zuciyarsa

“Kukan ya isa ai tunda gani na dawo

Ki godewa Allah ki godewa Jawwad Bazan iya tafiya in barshi da kewata ba”

Jalal yai maganr yana kallon Jawwad

Mummy kasa magana tayi se daddy da yake kokarin godewa Jawwad

“Haba daddy kar kasa inji kunya mana bakomai “

Nima Jalila ce takara fargar dani abu me mahimmanci Dana kusa mantawa thank you sweetheart Yayi maganar a zuciyarsa

Sannan ya mike yai musu sallama ya tafi Gida 

yana zuwa ya dau wayarsa Layin Jalila ya kira domin ya gaya mata Jalal ya fasa tafiyar amma bata dauka ba

ILHAM tana Shiga daki tayi wani tsalle tare da jefa hannunta sama tace yes key tasaka wa kofar dakin ta sannan ta dawo ta dauki wayarta ta kira layin mahaifiyarta

“Hello Mami”

“Na’am ya ake cikine?”

“Albishirinki”

“Goro”

“Yafasa tafiyar nan dazu Jawwad ya kawo shi Gida yafasa”

“Ke dan Allah dagaske koda wasa”

“Wallahi mami ya dawo”

“Kai amma Jawwad din nan ya kyauta, ya saukaka mana aiki”

“Wallahi kuwa mami”

“To yanxu dai ba sanya zamuyi ba, ki kara dagewa Ilham duk randa burinmu ya cika sekin fini amfana”

“Insha Allah mami zan dage”

“Yawwa yarinyar kirki se na jiki”

“To mami ki gaida mutan gidan”

“Yawwa zasuji”

Download>>> Ingarman Namiji Complete Document

“Jalila kinga gidan Maman annur ta haihu ban samu na shiga naga babynba zo muje,

Muyi mata barka”

“Ummi wai ita barkan nan dole ce tunda dai bata mutu ba da ranta”

“Ohh ni maryam Jalila mutum ya dau ciki wata Tara ya sauke lafiya tsakanin mutuwa da rayuwa ai aje acemasa barka”

“Ummi naje gobe in Allah ya kaimu yanzu bana jin dadin jikina”

“To Allah ya sawwake miki zo ki rufe kofar gidan”

Jalila tabi Ummi ta rufe gidan sannan dawo cikin Gida ta dakko wayarta ta dawo palour ta Missed call din Jawwad ta gani

“Yasalam yaushe Yaya Jawwad ya kirani ban Sani ba”

Kiransa tayi ya katse kiran sannan ya kirata

“Abunda zan gaya miki ya Riga ya wuceki tunda baki daga wayar ba, se yanzu”

Cike da shagwaba Jalila ta fara magana

“Haba yayana na kaina bangani ba ne se yanzu amma tuba nake ranka ya Dade”

Murmushi yayi 

“Sisyna ta wa ni kadai”

“Nanan fa?”

“A’a banda ita”

“Sena gaya mata”

Dariya sukayi gaba daya

“Yayana me yasaka farinciki hakane labarta min”

“Kece Jalila”

“Nikuma” 

“Eh mana”

“Ya akayi nasaka farincki”

“Saboda kin tunatar dani abu me mahimmanci

Jalal wani abokinsa ne ya zigashi yayi tafiyar nan Wanda ni da Sam banyi tunanin hakan ba kuma nasan da wata manufar ya zigashi, kuma wai tare zasu tafi

Yanzu dai zancen danake miki Jalal yana Gida yafasa tafiyar ya dawo”

Wata nannauyar ajiyar zuciya Jalila tayi

“Alhamdilillah am glad to hear this from you Allah yakara kiyayewa ya shiryeshi”

“Ameen sisyna muna godiya da gudunmuwarki 

Allah yasaka da mafificin Alkhairi ya jikan Abeenmu”

“Ameen dan uwan da babu irinsa”

“Ki gaida ummina”

“Zataji insha Allah na gaida maama,”

Sukayi sallamaa Jalila tace Alhamdilillah

Siyama ta kira ta labarta mata sukayi ta murna tare bakin Jalila yaki rufuwa

Bayan Ummi ta dawo ne ta lura da farin cikin da Jalila take sewani walwala take

“Waime ya farune naga kinata wannan farincikin haka baby gayamin mana”

Dariya Jalila tayi

“Hajiya Ummi ba komai kawai tsintar kaina  nayi cikin farin ciki Mara misaltuwa”

“To Allah yasa alkhairine”

“Ameen ummina”

Haka Jalila tayi kwanan farin ciki Allah ya temaketa yau batayi mafarkan ba balle a tsorata ta 

Lokacin tafiya islamiyya yayi yan matan sun dau guga a cikin dogayen hijjaban makaranta suna tafe suna hira yau fuskar Jalila fes ba wata damuwa Dan haka yau ajinsu suka tabbatar ta dawo banda hira da surutu ba abinda sukeyi ana hirar yaushe gamo wasu na mata tambayar meyasa randa tazo bata walwala kwanakin nan sunyi missing dinta

Hayaniyar ce ta ishi malam Naziru ya fito Dan ya tsawatar musu 

Yana zuwa Jalila yayiwa kashedi

“Yau malam baya nan balle ya ceceki wallahi naji surutu a ajin nan babu ruwana ke zan zanewa jikinki”

Befi yan mintuna da tafiya ba Jalila tabasu sabon topic suka barke da hira hada shewa itakuma ta silale ta gudu ta bar ajin ta nufi babban aji

Malam Naxeeru ne yakuma komawa domin casa yan ajin kuma ya kudiri takan Jalila ze fara 

Yana zuwa ajin ya nemeta yarasa ya tambayi tana ina sukace basu saniba aikuwa suka sha jibga yayinda uwar gayya ta fece sun daku ragwaye na kuka, yayinda masu karfin hali kena zuci Dan malam Naziru ya iya bulala,

“Tsinanniyar yarinya ta jamana duka ta gudu shegiya azzaluma wallahi ban yafe ba”

Cewar wata daliba aikuwa a fusace siyama ta juyo

“Allah ya isanki ta biki haba lubabatu ai ba matsa bakinki tayi tace kiyi magana ba kuma Jalila ba shegiya bace”

Download>>> Kwarata Complete Document

“Nafada wallahi ban yafe ba”

Lubabatu ta maimaita

“Ke nima ba yafewar nayi ba wallahi wannan azabar dukaa itakuma ta gudu”

Wata dalibar tayi magana Siyama na kokarin tarewa Jalila wasu suka hayayyako mata ana haka Sega Jalila ta dawo gaba daya sukayi tsit saboda sunsan hali indai bakine Jalila akwai baki 

Ba’a kada ita a fanni surutu

“Yanaji ana surutu amma ina shigowa naji anyi tsit”

“Aminiya ba komai hira kawai mukeyi, 

Amma fa malam Naziru yace yau in yakamaki kashinkj ya bushe”

Siyama ta fada tana dariya

“Hh base ya ganni ba ai bazan bari mu haduba indai yaune”

Ilham ce ta sha kwalliya kaman ka saceta ka gudu se karairaya take ta shirya abinci a Warmer’s ta nufi part din 

Jalal ba kowa a parlour dan haka ta aje a parlour ta karasa bedroom dinsa 

Dogon wando ne ajikinsa se vest ya na gefen gadonsa yana ta busa shisha

Sallama tayi da mamakinta taji ya amsa, a hankali ta tako gabansa cikin iyayi tafara magana

“Yaya dama mummy ce tayi girki tace in kawo maka”

“Ina abincin”?

Yai maganar kaman ba yaso 

“Yana parlour”

Gyada kai yayi

“Thank you”

“Amma zakaci ko?”

“Maybe”

Shine kawai abinda yace seda ta juya zata tafi ya daga kai ya kalleta 

Ganinta yayi kamar wata balbela, gashi se wani kariraya takeyi sam bata da wani shape se tsawo amma fara ce tas

Murmushi yayi a ransa yarinya Karama amma ta iya wannan shirmen ya Dan ja tsaki

Itakam fita tayi tana addu’ar Allah yasa yaci abincin nan

Kamar yadda Jalila tafada har aka tashi bata hadu da malam Naziru ba sunyo ayari guda yan ajin su daba yan ajinsu ba kowa na kokarin bin hanyar gidansu,

Anzo layinsu lubabatu suka tarar da yayan lubabatu a bakin hanya da abokansa se shan sigari suke ga tarin karnuka a gabansu kaida kagansu kaga yan daba

Jalila tare suke tafiya da su lubabatu seda sukazo dai² inda matasan nan suke Jalila secewa tayi

“Tab Siyama kinsan wani abu 

ga irinsu Jalal da gayyar abokanan Sa baki kullum cikin hayaki, kalli yadda bakin yayan lubaba yayi saboda zukar taba lebensa duk ya zazzage,

Ni bansan ya akayi bakin Jalal bezama haka ba wai shantu”

Wata ashar yayan lubaba yasaki yayo kan su shida abokanansa tareda karnukan kankace meye wannan ayarin yan makaranta sun watse ba kowa a hanyar

Jalila ta dinga dariya yan mata manya da kanana sun zage sun kwashi gudu

Sukace gaskiya gobe insha Allah se mun kai karar yarinyar nan gurin malam aja mata kunne

“Jalila lafiya kike ta haki haka ?”

“Bakomai Ummi karnukan bakin anguwane suka biyomu”

Jalal ya bude Warmer’s dinda Ilham ta kawo yaga cous² tsaki ya ja lallai ma yarinyar nan tasan bayacin wannan abun amma shine aka kawo masa rufewa yayi ya tafi gidansu Jawwad Dan samun abinda zeci a can

Ya tarar Jawwad yatafi masallaci dan haka ya nemi guri ya zauna yana jiran dawowarsa

Wayar Jawwad ce ta dinga ringing ta cikawa Jalal kunne Dan haka yaje ya dauka da nufin fadawa me kiran me wayar baya nan 

Ya daga wayar yasaka a kunnensa

“Hello yayana “

Shiru yayi be amsa ba

“Yaya Jawwad yanaji kayi shiru bakajine?”

“Bashi bane”

Ya bata amsa a takaice

“Au Ashe Kaine ya akayi kafasa tafiyar,

Kacigaba da rashin ji kana biyewa abokan banza wataran se sun jaka inda zasu kasheka”

“Da kasake ka tafi da yanzu ka gane illar hawayen iyaye”

“Kinmanta kashedin danayi miki game dani ko? Har yanzu baki fasa min shishigi ba ki ji da rayuwarki, ba ruwanki da rayuwata”

Ya katse wayar ya aje tare da fadin

“Jarababbiya kawai, ko ina ruwanta dani oho, zan sauke mata wannan taurin kan”

Jawwad ne ya dawo ya tarar dashi 

“Yunwa fa nakeji, find something for me to eat”

“Kamar me kake so”

“Komeye ma amma banda tuwo

Yarinyar nan ta kaimin abinci nazata wani abun kirkin ne ashe wannan abinne dabana ci saboda tsabar ta rainani aikuwa zan koyamata hankali”

“Ai kai abunda baka ci dayawa wanne daga ciki”

“Kaga ni abar wannan maganar me kukayi yau”

“Nima banci abincin ba alala sukayi yau”

“What alala kuma,”

Ya Dan girgiza kai 

“Kasan itama bana ci”

“Anyway bari in canza kaya muje restaurant se muci”

“Kar ka kaini inda za abani abunda za bata min ciki kasan bana son jagwal gwalo”

Murmushi Jawwad yayi

“Jalal kaima yakamata ka canza kayan nan kasaka manyan kaya”

“Nifa bana son wannan kayan nauyin isa ta suke da zafi”

“Please dan Allah kasa manyan kaya”

Jawwad ya fada yana Ciro masa wata hadaddiyar Shadda coffee colour yaita lallaba shi har ya yadda ya karba ya canza kayan yasaka shaddar nan,

Ba karamin kyau Jalal yayi a cikin kayan nan ba manyan kaya ba karamin fito da kamalar namiji yake ba Jawwad yaita koda shi, yana masa hotuna yana yaba masa yayi kyau,

Haka suka shirya suka tafi restaurant cin abinci

Download>>> Tayi Min Kankanta Complete Document

Jalila ce a office din malamai ta inda suka shiga ba ta nan suke fita ba suna mata fada akan rashin ji 

Saboda ankawo kararta akan jiya ta tsokanowa yan uwanta dalibai yan daba, masu zaginta sunayi irinsu malam Naziru, masuyi mata nasiha sunayi ita dai Jalila shiru tayi batace komai ba  suka gama ta tashi ta koma aji tanata cika tana batsewa

  Ba a jima ba malam Naziru ya shigo ajinsu da hanzari yana kiranta

“Jalila zancen musabakar nan ne ya taso wadda za ayi a Abuja  sati me zuwa insha Allah”

Wani irin mugun kallo Jalila tayi masa tai masa banza

  “Jalila da ke nake fa kije ki jadadda hadda abun yazo mana a bazata dukda nasan bani da damuwa akanki”

“Ba inda zani kunemi me zuwa karkuje inja muku magana, yaza ayi kamata taje musabaka “

Tafada tana hade rai

Sekuma ya Dan sha jinin jikinsa 

“Wai meye hakane Jalila ana magana kina wani zance daban ina miki magana”

Mikewa tsaye tayi tare da kara hade rai

“Nace fa bazani ba anemi wasu suyi ni bazani ba,”

Ta dau Jakarta ta bar ajin

Office malam Naziru yakoma yana mita 

“Kajimin ja’irar yarinya nizata cewa bazata je musbaka ba wai anemi me zuwa”

Malam Yusuf ne yace

“Banga laifinta ba nan kuka sata a gaba da fada bama kai se yanzu kuma bukatarku ta taso kuce tazo tayi muku,

irin wannan yaran nasiha ake musu ba zagi ba duk abu suna da irin baiwarsu”

“Hmm ni ba wannan ba tunanin mafita nake kasan ta da taurin kai abune me wahala taja ga malam baya nan”

Jawwad ne ya tashi ya tafi amsa waya yayinda Jalal ya dukufa yana cin abinci saboda yunwar dayake Ji

“Masha Allah”

Wata budurwa ta fada, mikewa tayi daga inda take tazo kujerar gaban Jalal ta janyo ta zauna

“Sannu dai barka da wannan lokacin”

Dan dagowa yayi ya kalleta, ya maida kai ya cigaba da cin abincinsa

“Ehmm nace ba Dan Allah magana nakeso muyi da kai”

Still shiru yayi mata yaki magana haka tacigaba da surutun ta ko kallonta yakiyi

Jawwad ne ya dawo yasamu guri ya zauna

“Sannunku da fatan ban takura muku ba”

Jawwad yafada yana murmushi

“Mtseww kaga ci abunda zakaci mutashi mu tafi ni nagama kasan bana son kallo”

Jalal yayi maganar a fusace 

“Dama yana magana?”

Budurwar ta tambaya

Dariya Jawwad yayi 

“yanayi mana, gashi kuwa kinji”

“Amma nayi masa magana ya shareni”

Se Jawwad yai niyyar tsokanar Jalal

“Au be kulaki ba, aikuwa yana magana, haba bros ya zata na maka magana ka shareta”

Wani takaici ne ya tokare wa Jalal shi Sam baya San sabga da mata dan haka banza yai musu

“Au bazakayi maganar ba kuwa”

“Inaga nidin ce baze kulaba, ba komai nagode”

Ta mike zata tafi

“Kiyi hakuri fa Dan uwan nawane se a hankali”

Murmushi tayiwa Jawwad sannan ta mike ta bar gurin 

Wani uban tsaki Jalal yayi yana hararar Jawwad

Sunkuyar da kai Jawwad yayi yana dariya Jalal ji yayi kamar ya naushi Jawwad 

Haka Jawwad yagama cin abincin suka nufi Gida

Tunda Jalila ta koma gida sedata shafe kwana uku bata zuwa makaranta 

Ummi tayi² tagaya mata meyasa bata zuwa makaranta amma taki, kullum seta ce mata bata da lafiya,

Seda malam Naziru da wasu malamai suka biyo Jalila har Gida akan takoma makaranta saboda batun musabaka 

Ummi tace musu ba komai indai Jalila ce zataje musabakar insha Allah sukayi mata godiya suka tafi

Ta dawo Gida taitama Jalila fada meyasa zatace bazatayi musabaka ba har malamanta su biyota Gida suna lallabaki

Dan tsuke fuska Jalila tayi

“Ummi bakiga abunda sukayimin ba suka dinga min masifa kuma se yanzu yawani zo wai inje musabaka wallahi Dan kinsa bakine kuma Dan malam babba zani wallahi da bazanje ba”

“To yanzun ma kice bazakiba mana in dai za a biyewa halinki ai kullum se an zanekima ba fada ba”

Kayan da Jawwad yabashi yasaka ne duk suka isheshi da zafi Dan haka suna dawowa gidan su ya wuce domin ya canza wasu kayan zuwa kananan kayan daya saba sawa

Yana bedroom dinsa yana kokarin canza kaya yaji motsin Ilham a palour zata kwashe Warmer’s din data kawo masa abinci, bubbudewa tayi taga baici ba

Fitowa parlour yayi ya tsaya a bakin kofa Dan dago kai tayi ta kalleshi masha Allah wani irin kyau taga yayi me daukar hankali kayan sun masa kyau sosai ta Dan kura masa ido

“Ke me ye haka uban me kike kallo, saboda tsabar kin rainamin hankali kika kawomin wannan abincin, kuma kinsan banacin wannan abun amma kika dakko kika kawomin yaushe nafara wasa dake dazaki min wannan rashin mutuncin”

Yasalam ta manta baya cin cous²

“Am…am wallahi Yaya namanta…..”

“Shut up kwashe su kibarmin daki sokuwa kawai komai kin manta shiyasa kike dakikiya both islamiyya da boko kanki Sam baya Ja fita ni”

Ai garani ina zuwa kaifa

Ta fada a zuciyarta ta kwashe kayan tana zumbura baki tana kunkuni 

“Ke ni kikewa kunkuni na tattakaki wallahi kinsan halina sha³ kawai”

Sum² ta bar dakin

“Indai zaka biyewa mata se Jininka ya hau”

Yai maganar a fili tare da yin tsaki

Jalila ta dage da tilawar haddarta malam Naziru se kuma lallaba Jalila yake saboda yana son taje musu musabaka Abuja

Kullum dare se tayi waya da Jawwad se suyi kwanaki basuyi waya da Nana a wayaba, amma kullum suna manne da Jawwad a waya 

Yauma yana dakin Jalal suna hira Jalila ta kira waya in suna wayar nan Jalal bata masa rai sukeyi  Jawwad kuma yaita biye mata

“Yayana saura kwana uku insha Allah zamuje Abuja musabaka”

Download>>> Matan Asokoro Complete Document

“Masha Allah, badaban inada lectures ba ranar dase nazo garin Abuja naga yadda kanawata zatayi musabaka in bata kwarin gwiwa”

“Koba ka nan kalamanka zasu bani karfin gwiwa, kasani a addu’arka Dan Allah”

  “Addu’a kullum cikin yimiki nake Insha Allah zakiyi nasara”

“Godiya nake yayana ka gaida mutan gidan”

“Zasuji insha Allah, muna tare da yayanki Jalal zan gaya masa shima ya yi miki aduu’a”

Jalila dariya ta kwashe da ita tare da kashe wayar

“Jalal kanwarka zataje musabaka Abuja ranar Juma a insha Allah kasata a addu ‘a”

Jawwad yafada yana kallonsa

  “Kanwarka dai kasan ni bana kalen dangi”

“Kanwa tawace kalen dangi Jalal? kaima kanwarka ce Jalila ce fa”

Shiru Jalal yai be kuma cewa komai ba

Dama wannan yarinyar har wani karatu ta iya zata je musabaka kil ma karya take dama dai Neman magana ne ko Shiga abunda ba ruwanta ne yai maganar a zuciyar sa

Yarinyar dasuka hadu dasu Jalal a restaurant ce zaune akan gado Jeje na gabanta a tsaye yana rarrashinta

“Gaskiya Jeje ni bazan iya ba gaskiya zeyi taurin kai ko kallona fa be yiba har na gama surutuna na tashi be kulani ba se abokinsa ne yamin magana”

  Tai maganar tana yatsina fuska 

Jeje ne ya Dan gyara tsayuwarsa

“Hanna kiyi hakuri, dama tun farko seda nagaya miki, mugun Dan wulakancine baya saurarar mata Sam amma kicigaba da bibiyarsa kidage Hanna zaki iya”

  “Amma dai kasan bana son wulakanci ko nida maza ke min layi, amma ace ana wulakantani Dan ma dai ya hadune gayen da bazanyi aikin nan ba”

“Kiyi hakuri Hanna seda na duba naga babu me iya min wannan aikin se ke,

Hanna ki dage tunda naga gayen yayi miki”

“Anyway I will try my best ka barni dashi da Hanna yake zancen zan sauke masa wannan taurin kan bani lambarsa”

“That’s good Hannah shiyasa nake ji dake”

Jeje yafada yana jin jinamata

Jalila ce tayi sallama da Ummi 

Ummi tayimata nasiha da fatan samun nasara

Haka taje islamiyya sukayi sallama da kawayenta da sauran malaman daba dasu za a tafi ba sunata musu fatan alkhairi da fatan samun nasara

Daga nan suka kama hanyar Abuja da sauran dalibai dazasu tafi tare,

Sun sauka lafiya aka basu masauki su huta da la’asar guri ya cika da manyan mutane daga gurare daban² aka fara gudanar da musabaka

Ilham suna parlour da mummy suna hira, mamanta tayi mata waya ta mike tace wa mummy tana zuwa

Daki ta nufa taje ta daga wayar

“Hello Mami ina wuni”

“Ke bar batun gaisuwar nan

Ya akayi yaci abincin”

“Ina fa yaci abincin na kai masa kaman zeci namanta bayacin cous² da ba shi na girka ba da tuni yaci”

“Ke ni yimin shiru tunda beci ba, kina wani shirmen kika dafa abinda baya ci

Yanzu yana ina”

“Yana part dinsa mana”

“To ke kina me ki tashi ki bar abinda kikeyi kije ki tayashi hira mana”

“Maami dan baki san halinsa bane mugun Dan rainin hankaline”

“Kiyi hakuri Ilham, ribarki CE fa da kin aureshi burinmu yacika zan dau fansar abinda uwarsa tayimin, a wuce gurin, in kina yawan zama a inda yake dahaka zaku shaku, in Allah ya kaimiu weekends kizo akwai turaren Dana karbo miki sannan yanzuma ki shafa wancan turaren Dana baki malam yacemin yayi aiki sosai a cikin turaren”

“To maami bari inje “

“Yawwa Ilham koke fa”

Mikewa ILHAM tayi tafara shiryawa tasaka wata doguwar Riga Ja me kama Jiki, ta shafa turare ta Dan Dora siririn mayafi akanta ta fito parlour bakowa a palour mummy ta tashi, Dan haka ta fito ta nufi part din Jalal

Yana kwance da gashi se dogon wando da vest ya kwanta ya lumshe Ido jinsa yake jikinsa Sam ba kwari kaman anyi masa duka

Ilham ce ta shigo parlour ta sameshi a kwance akan three seater yanajin shigowarta amma be motsaba kan kujerar dayake taje ta zauna daga karshen kafafuwansa ji yayi jikinsa ya kuma mutuwa

A hankali ta kai hannu ta dan matsa yatsunsa na kafa taji yayi shiru bece mata komai ba Dan haka ta cigaba da matsa yatsun kafarsa a hankali

“ILHAM”

Taji ya kira sunanta a hankali

“Na’am Yaya Jalal”

Ta amsa masa

“Wane irin turare ne wannan kikasa?”

“Me turaren yayi?”

Ta tambayeshi

“Ji nayi ya kashemin Jiki, kamar ya karamin ciwon kai”

Abun yabata mamaki dataga be hantareta bako ya koreta

Kashe murya tayi cikin shagwaba da iyayi ta fara magana

  “Haba Yaya Jalal turaren da kasanni dashine fa”

Mikewa yai zaune tare da fadin

“No ILHAM this one smells different”

Kusa dashi ta matsa ta kwanta akan kafadarsa 

“Kaine dai kaji haka amma ni ban canza perfume ba”

Dan tureta yayi kadan ya Dan kalleta “

dakkomin Wayne a fridge ki hadon da cup”

“OK angama my J”

Ta mike tanata karairaya, tare da mamakin wannan sakin Jiki da Jalal yai da ita haka

Shikam da ido yabita yanajin kaman ba shiba

Wayne din takawo masa ta bude ta zuba a cup ta mika masa ya Sa hannu ya karba itakuma ta dawo kusa dashi ta kwanta a jikinsa

Hannu ya mika ya dakko remote ya kunna Tv

Yana kunnawa yaci karo da fuskar Jalila

Tana murmushi tasha hijjabi blue ga farin glass tasaka ga sufiku a gabanta na karatu gani yayi kamar shitake kallo

Gabansa ne yafadi yaji tsigar Jikinsa ta tashi.

Malamai ne suka jeru suna shirin janyowa Jalila inda zata karanta

Itakam tayi shiru ta kurawa camera ido haka nan taji gabanta na faduwa dukda tasaba zuwa musabuka amma takejinta wani iri

Jalal ne ya kurawa TV ido gani yake kaman shi Jalila take kallo so yake ya tabbatar itace kuwa a jikin allon TV kokuwa kamrun dayasha ce tafara gaya masa karya(giya)

Ita kam Ilham kara shige masa take tana kuma zuba masa Wayne tana mika masa

“Ilham ki kyaleni please”

“Yaya J why?”

Download>>> Asad (The Arrogant) Complete Document

Tayi maganar tana kuma kwanciya a jikinsa

Shikam yakoma kaman wani karamin yaro

“Bana so Ilham ki kyaleni kwanciya zanyi kaina ciwo yake”

Dan dagashi tayi ya koma ya kwanta akan kujerar yana kallon TV kasa²

A hankali Ilaham ta mika hannunta tana shafa sajensa 

“Sannu Yaya J”

Gyada mata kai yayi

“Ilham karki kuma saka turaren nan inzakizo inda nake banaso”

Yai maganar a hankali

“To na dena”

Tv ya kuma kalla Jalilan ce dai sedai wannan karon annurin fuskarta ya gushe ta dai²ta nutsuwarta aka janyomata inda zata biya

A hankali tayi bismillah tafara karanto Qur’ani cikin sauti me dadi 

Ture Ilham yayi daga Jikinsa ya lumshe idonsa jin sautin karatun nata yake yana ratsa ko ina na jikinsa yana saukar masa da nutsuwa Ji yayi kasalar tana sakinsa duk yayinda ya bude Ido seyaga kaman Jalila shi take kallo jinsa yake kaman ba Shiva

Ilham hannu ta kuma mikawa zata taba shi ya daka mata tsawa 

“Ke wace irin banzar yarinya ce waima tukuna me kikemin anan gurin ne tashi kibar min daki kafin in zaneki banza kawai”

“Haba Yaya amma

” bazaki fitan ba kenan kalli Tv duk rawar kanta kalli yadda take karatun Qur’ani gwanin burgewa keko sha³ baki iya komaiba se hauka get out from my room”

Idonta ta kai duba kan Tv Jalila tagani tana zuba kira’a kaman ba itace me shegen surutu da Neman magana ba, wani abu taji yazo ya tokaremata zuciya wato tun dazu da ya kurawa Tv ido ita yake kallo kenan

Wani mugun kallo taimasa

“To ai gara ni inazuwa Islamiyyar kai………..

Bata rufe bakiba yasaka kafafuwansa ya take nata kafar wani irin ihu tayi da karfi kuma yaki dagawa

” Dan girman Allah kayi hakuri, wallahi bazan kuma ba”

Kara takesu yayi 

“Dan ina daga miki kafa ina nan a Jalal dina da kikasani, yanzuma Sa a kikaci da wallahi sena zaneki da belt, tashi kifita wawiya kalli rigar jikinki sokuwa kawai”

Da kyar taja kafa ta fita kafarta se zugi takeyi ta koma dakinta ta hau gado ta kama kuka

Wani uban tsaki ya ja yanemi guri ya zauna 

Tashar da suke haska musabakar su Jalika sun tafi talla dan haka

ya dauki cup din giyarsa ya cigaba da sha yakuma zubawa ze sha aka kuma hasko Jalila haka nan se ya aje giyar hannunsa shima ya kuramata ido, yanayin Jalila ne ya nuna kaman bata da nutsuwa 

Aka kuma janyomata karatu amma tayi shiru ta tafi tunani kowa ita yake kallo 

Jikinta ne yayi sanyi jitake kaman wani abune ke shirin faruwa, mafarkanta datakeyi yan kwanakin nan ne suke fado mata a rai taji gabanta yacigaba da faduwa.

a hankali tayi ajiyar zuciya ta Dora inda aka janyomata da karatun ta cikin birgewa 

Bacci ne yafara fusgar Jalal dan haka anan gurin ya zube ya lumshe ido yana sauraren karatun Jalila har bacci yayi awon gaba da shi

Da safe Jawwad ne yazo ya tarar dashi yana bacci a parlour a kasa kan carpet ga kwalbar giyarsa yasha fiye da rabi

Girgiza kai Jawwad yayi 

“Allah ya shiryeka Jalal”

Yasa hannu ya kwashe kwalbar da kofin ya fita dasu ya dawo ya tashi Jalal don yasan be salla ba balle ya karya 

Hannu ya kai ze tasheshi yaji kansa yayi zafi, bayansa ya Dan bubbuga a hankali Jalal ya bude ido ya mayar ya lumshe

“Ka tashifa gari yayi haske kayi salla kazo mu karya”

Jalal ne yake tunano abubuwan dasuka faru jiya da daddare gaskene kokuma mafarki yayi ji yai kansa yakuma sarawa

“Kaina ne yakemin ciwo sosai Jawwad”

“Sannu ka tashi in muka karya seka sha magani”

Da kyar ya lallabashi yaje yayi wanka yai sallar asuba, Jawwad ya dakko musu Abinci

Ilham CE ta fito tana taka kafa da kyar mummy ta kalleta

“Meyasameki kike taka kafa da kyar”

“Dutse na taka jiya a garden”

“Subhanallah bakiji ciwo ba dai ko?”

“A a banjiba kafar ce dai kawai take ciwo”

“To ko asibiti za a kaiki a duba kafar”

“A’a mummy zata dena ne Insha Allah”

“To shikenan ni zan fita ne zanje ganin likitan Ido, ga breakfast can na gama in wancan Dan zeci yazo ya dauka kema kije ki dau naki”

“To mummy adawo lafiya”

“Allah yasa”

Mummy ta fita

Jalal ne ya dakko wayarsa ze kira daddy yaga message ya shigo wayarsa Dan haka ya bude message din bakuwar lambs ce

      “Barka da safiya jarumin      

        maza fatan kana lafiya        

       Zanso ace a halin yanzu 

       Muna tare ina kallon                  wanna kyakykyawar fuskar

      Amma lokaci na nan zuwa

       Dazamu kasance tare kaji          Dadinka masoyina 

             From ur lovely bae”

Wani uban tsaki Jalal yayi

“Nasan Ilham ce zataci kaniyarta zata gane innin sa,’anta ne”

“Ya dai meyafaru ne kake surutai haka”?

Jawwad ya tambaheshi

“ba komai ci abincinka kawai”

Ya mike ya nufi cikin Gida tundaga parlour yake kiran sunan Ilham amma bata nan dakinta ya nufa yana zuwa ya tarar tana dakinta tana karyawa

A firgice ta dago tana kallonsa

“Uban meye wannan kika turomin a waya wai meyasa ba kyajine Ilham”

Kallonsa tayi cikin rashin fahimta 

“Wane sako kuma ni ban turomaka komai ba”

Ransa ne ya kuma baci wato raina masa hankali zatayi gadan² ya nufi inda take da niyyar ya ci kaniyarta 

Ta mike tsaye tafara kuka tana 

“Wallahi Yaya bansan laifin danayiba”

Yana karasowa Inda take yaji tana warin wannan turaren na jiya kansa ne ya Sara yaji yana Neman ya fadi, da sauri ta taho inda yake

“Yaya menene?”

“Dalla tsaya karki karaso inda nake”

Bango ya daddafa yabi kofa ya fice da kyar ya koma part dinsa Jawwad ne ya ganshi ya rike kai yana dafa bango

“Subhanallah Jalal kanne dai”

Jawwad yafada yana riko JALAL

“Jawwad kaina kaman ze fashe”

“Bari mu tafi asibiti ina key din motarka?”

“Kaga kyaleni bazani wani asibiti ba”

“Meyasa meye amfanin ka zauna a Gida baka da lafiya”

Guri Jalal yanema ya kwanta ji yake duniyar tanata jujjuyawa

  Kai tsaye cikin gidan Jawwad ya tafi ya nufi part din daddyn Jalal yasameshi a parlour yana breakfast

Suka gaisa Jawwad yagaya masa halin da Jalal yake ciki, tare da daddy suka taho gaba  daya part din Jalal

Suka tarar dashi a kwance yanata juyi akan gado ya rike kai Juyin duniya ya tashi su tafi Asibiti yace baza shi ba kunsan mutumin da taurin kai

Se wani likita aka kirawo yaimasa allura se yasamu yayi bacci

Alhamdilillah Jalila ita tazo na biyu a gasar musabaka da akayi tasamu kyautuka da dama kuma an karrama malamanta 

Ita Jalila duk ba haka taso ba na daya taso tazo

“Duk wannan sakaran ne yajamin haka kawai naita mafarkinsa nazo musabaka ya hanani sukuni”

Haka taita mita suka kamo hanyar dawowa Kaduna suna murna amma ita haushi duk ya isheta

Har Gida motar makaranta takai Jalila, siyama tana gidan tana Jiran isowar Jalila

Ummi tana ganinta ta rungumeta tana murna, amma Jalila tai kicin² da fuska 

“Lafiya kuwa babyna?”

“Ummi ta biyu fa Nazo”

Tafada kaman zatayi kuka

“Haba baby Wanda yazo na karshe kuma yace me? Daga na daya fa seke haba babyna”

“Gaskiya aminiya inkakiyi haka baki kyauta ba kullum zakiyita zuwa na dayan, hakan ma mu munyi murna”

“Yawwa ai gara kigayamata siyama, adinga godewa Allah Baby”

Ummi tayi maganar tana dungurewa Jalila kai Dan turo Baki JALILA tayi 

Taje tayi wanka suka kule dakii itada siyama suna hira

“Kinsam wani Abu aminiya”

JALILA tai maganar tana kallon Siyama

“A’a sekin fada”

Siyama ta bata amsa

“Wallahi Jiya agurin musabaka naji gabana yanata faduwa ina tuna mafarkin nan danake”

“Kai Aminiya meye kuma na tunawa ABU ya Riga ya wuce kimanta kawai

Bari inbarki ki huta kishirya ranar Monday insha Allah za a koma school”

“Can ta matsemusu bazan komaba senagama hutawa ki gaida umma”

“Aminiya halinki seke tararki za aci fa in baki koma ran Monday ba”

“Hhh tab Tara sedai a ci wasu Tara ba dai niba”

Sukai sallama ta Raka Siyama kofar Gida ta dawo dakinta ta kwanta akan katifa domin huce gajiya

Mummy ce ta dawo Ilham tagaya mata ai Jalal ba lafiya suka tafi part dinsa, yana kwance akan gadonsa yana bacci jijiyoyin kansa duk sun daga dagani baccin ba dadi yakemasa ba, warin turaren Ilham yakuma shaka dukda bacci yake seda ya yamutsa fuska ya juya wani bangaren

A hankali mummy ta kai hannu ta shafa sumarsa tana fadi

“Allah yabaka lafiya son”

ILHAM ta amsa mata da “Ameen”

Se bayan azahar ya farka Jawwad ya shiga cikin gida yace Ilham ta hado tea ta kawowa Jalal, 

Jawwad ne gefen Jalal yana masa sannu

“Ya kakejin jikin naka yanzu”?Jawwad ya tambayi Jalal

“nifa har yanzu yanamin ciwo, amma bakaman dazu ba”

“To ai kaima ance muje asibiti kaki ka manne a Gida”

“Ni ba wani asibiti da zanje”

Sakone ya shigo Wayar Jalal, Jawwad ya miko masa wayar

Download>>> Yaro Ne Complete Document

         “Barka da wannan lokaci 

           Lovely am missing ur 

           Handsome face wish to

           See u soon 

           Love u so much

           From ur lovely bae”

“Mtseww wannan wace irin jaraba ce”

Yana aje wayar tafara ringing an kira yafi sau uku yaki dagawa

“Jalal wayarkace fa ke ringing

Ka daga mana”

“Bazan daga ba in ka gaji da karar kai ka daga”

Girgiza kai Jawwad yayi halin JALAL se hakuri

Hannu yasa ya daga wayar se yaga unknown number muryar mace yaji

“Hello babyna fatan kana lafiya”

“Sorry ba me wayar bane, me wayar baya jin dadi amma wa za ace masa”

“Eyyah shiyasa naji ni bani da lafiya nima ko abokinsa ne JAWWAD”

“Dan uwansa dai”

“To amin afuwa Dan uwansa”

“Eh nine”

“Hannah ce ai masa sannu, ko zaka bani address din inzo in dubashi”

“Ohh no daga nan ma kiyi masa addu’a mungode”

“Anyway Allah yabashi lafiya amma banajin zan iya komai bayan mallakin zuciyata ba lafiya,

Ka gaisheshi please”

“Zeji insha Allah”

Jawwad ya katse kiran ya kalli Jalal

“Mutumin yaushe kafara soyayya ba labari wace kuma Hannah”

“Mtsewww soyayyar banza kai kasanta”

“Easy mutumina adena cika baki wadda takiraka din nan bakaji kalaman data fada tace agaya maka ba”

“Dan Allah ka kyaleni inji da kaina”

“Ohh sorry nadena sannu,

Yanzu za a kawo maka tea”

ILHAM kam wani tunani tayi this is another opportunity for her to use that medicine again

Tunda wancan lokacin be Ciba a abinci yanzu tasan zesha a tea

da rawar jiki Ilham ta mike taje ta nufi kitchen ta hada tea ta zuba wani maganin a ciki ta juye tea din a flask ta doro cups akan plate ta nufi sashin Jalal

A cikin bacci Jalila taji kirjinta ya tsanan ta bugawa Ilham kawai take gani a mafarkinta a hankali ta bude ido gabanta ne yacigaba da faduwa meke Ilham ke shirin yine nake ganinta a bacci na

“Laila ha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin”

Shine abinda Jalila taita maimaitawa kamar wadda aka tsikara tayi zumbur ta  mike zaune ta dakko wayarta

Sallama Ilham tayi tana kokarin shigowa

Jalal ne ya Daka mata tsawa 

“Tsaya a nan malama karki karaso inda nake”

“Haba Jalal wai meyasa kai ba a maka gwaninta ne”

Saroro Ilham ta tsaya tana kallonsu

“Eh naji ba amin gwaninta amma karta shigomin nan”

Mikewa Jawwad yayi ya karbo tray din hannunta 

“Kiyi hakuri ILHAM kinji zedena ne nasan ba kyajin dadin abunda yake miki, nan gaba in ance yayi koda kudi baze miki ba”

Gyada masa kai kawai Ilham tayi tabashi tray din kayan tea ta koma

Gaban Jalal ya dawo ya zauna

“Bross Ilham kanwarka ce yadda kake treating dinta Sam be dace ba”

“To mekakeso in mata indinga goyata ko kuma in zauna ina mata dariya a hakanma kana ganin rashin kunyar da takemin har ta kalleni tace ni take so sa’anta ne ni?”

“Jalal Ilham itama yarinya ce, kuma so ba karya ne ba bazaka gane hakan ba se ranar da yai maka kamun kazar kuku”

“Naji labarin ya isheni haka, hadamin tea in sha”

Jawwad na cikin hada masa tea dinne Jalila takira wayar Jawwad 

Murmushi yayi sannan ya daga wayar

“Sisyna am sorry nayi laifi ban kiraki naji yakike ba yau hankalina ne ba a kwance baya musabakar?”

Seda ta tura baki kaman tana gabansa 

“Yaya Jawwad ta biyu fa nazo”

“Kai amma nayi murna, dole inzo Kaduna muyi celebrating”

“Wani celebrating bafa ta daya Nazo ba wai ta biyu”

“To ai kinyi kokari baby meye kuma na bata rai? Aini a hakan ma kinfiyemin Wanda yazo na daya”

  “Dan Allah ka aje wayar nan, ko kabani tea din in hada da kaina”

Jalal yai maganar a fusace 

“Ohhh sorry bari in hada maka”

Jawwad yai maganar yana kashewa Jalal ido

  “Yayana kaida waye ne?”

Jalila ta tambaya

“Nida yayanki ne bashi da lafiya tun jiya yake fama da ciwon kai an masa allurai amma har yanzu kan bedena ciwo ba, shine zan hada masa tea yakemin masifa”

Dan tabe baki Jalila tayi

“Dama yana salla ne se ince ko beyi Azkar ba, to Wanda be salla ba ya za a tambayeshi yayi Azkar ma, kasan in mutum ya nisanta kanshi da Allah komai ma seya sameshi”

Dan kallon Jalal Jawwad yayi yaga idonsa a lumshe se yayi tunanin ko bayajin me Jalila take fada, amma tsaf yaji me tace

“Hmm Adduar ki kawai muke bukata baby”

“To Allah ya shirya ya bashi lafiya, ka kama kansa ka karanta mai bismillah kafa sha Tara se ka biya masa ma tayassara minal Qur’an”

“Godiya muke ya sayyada, Allah yakara hasken makaranta

Brother tashi ka karbi tea din”

Yafada yana Dan jijjiga Jalal

Tashi zaune Jalal yayi ya karbi tea din ya kai bakinsa ya Dan fara sha

“What!! tea naji kace”

“Eh tea zan bashi ya sha kinga yana da dumi”

“Waye ya hada tea din?”

“Ilham ce ta hada masa mana”

Jawwad yabata amsa

Dan tunani Jalila tayi

Meye yasa ta dinga faduwar gaba tun agurin musabaka har yanzu bashi taita ganin Ilham da sauri tace

“What Ilaham kuma? Karya sha tea din nan Yaya Jawwad ka karbe tea din nan”

Tafada cikin karaji.

Back to top button