Uncategorized

Abdul Jalal Chapter 20 Book 2 Complete Novel

 

Jalal bai fita daga motar ba,  dayake motar tint glass ne, da mamakin Jalila motar data sha gaban tasu, Jeje ne a ciki da wasu manyan karti suka fito, suka tinkaro inda tasu motar take, knocking sukayi a side din direba, a hankali Jalal ya sauke glass sukayi ido hudu da Jeje, rikicewa Jeje yayi, cikin inda inda da mamaki yace

“J man kaine da kanka, huh ya gida amm… 

“shut up please” Jalal ya katseshi, “nasan za’ayi haka ai, shiyasa na shirya hakan, Jeje baka da amana, baka da mutunci, kobataci darajar kowaba taci darajar yayanta amininane, amma saboda baka da mutunci shine ka shirya cutar da ita, kuma duk abubuwan data fada akanka karyane? Ba karya bane ba, Jeje inaso in maka kashedi, koda makamancin wasa ba kai babu ita, idan nakuma fuskantar ka shirya wani abu akanta na cutarwa, you know what am capable of doing, ka kiyaye “

” haba Jalal kai ka dauki abun a haka amma ni banyi niyyar yimata wani abuba… “Enough malam, kayimin blocking way, ku janye motarku zan wuce” cike da bakinciki Jeje yasa aka janye motar, ya shirya ya dauke Jalila yaketa mata haddi, saboda abunda tayi masa, ya dauki fansa akan abubuwan datayi masa, ya akayi Jalal ya gane shirina haka, dukan motarsa yayi da karfi, yayiwa kartin umarnin su shiga mota. 

“kinga Abunda shishshiginki ya nemi ya janyomiki ko? Da kin bari kin taho ke kadai da wani zancen ake ba wannan ba” ya karasa maganar cikin fada, kallon Jalal tayi, ta dauke kanta

“waman yatawwakallu alallahi fahuwa hasbuh, dan haka be isa yayi min wani abu ba, kuma kaima baka isa ka kareni daga komai ba, ba gudu ba ja da baya wallahi koze kasheni seyayi nadamar niyyar dayayi akaina, kar ya fasa, zan nuna masa wacece ni duk Abunda nasa gaba Allah yana bani sa’a kansa, bana alwashi in kasa cikawa, duk wanda ya takaleni da sharri senaga bayansa, kodame yake takama, dan haka ba kaika kareni ba Allah ne, kuma ka gaya masa zamu gauraya dashi dan haka kadenamin tsawa” 

Jalal yakara jinjinawa Jalila akan taurin kai, betaba ganin mace me taurin kai kamanta ba, bata da tsoro bata son raini, kuma abun mamakin she has a luck, kota gangamo rigima se Allah ya kwaceta. Kallonta kawai yayi yai shiru bekuma cewa komai ba yacigaba da tukinsa, suna zuwa kofar gate yayi parking, “Fita” “aiko bakace in fitaba zan fita, komeye nayimin gadara aiba motarka bace, kuma bani nace ka kawoni ba dan haka karka kara yimin tsawa” harzata bude motar, setaga wannan lecturer da Sir Hafiz ya kaita gurinsa wato Sir sagir yazo wucewa, da sauri ta kalli Jalal 

“Yawwa kasan wancan mutumin?” 

Kallo daya yayiwa sagir yagane shi, cousin din baban Ilham ne, shikuma meye hadinsa da ita oho, amma yace “ban saniba kifita nace”  “to kayiwa kanka dama sako yabani in baka, tunda kace haka shikenan” ta fice abunta Jalal ya girgiza kai yatafi. 

Karfe tara na safe Ilham tana kofar gidansu Yaseera ta kirata awaya ta fito suka tafi gidan malamin nan. Suna zaune agabansa kaman masu neman gafara, ya kalli Ilham yace “kunyi sake gaskiya, saboda aikin baya tasiri akansa yanzu sosai kaman a baya, amma yanzu mekikeso ayi” Ilham kaman ta fashe da kuka tace “Malam har za’ayi maganar aure bawan Allah nan yaki yaita min wulakanci, amma katsam naganshi da wannan yarinyar da nake gayamaka rungume a kirjinsa, hankalina ya tashi matuka” “to aina gayamiki Asiri baze tasiri a jikinta ba, yarinyar bahaka take zaune ba tayiwa Al’qur’ani kyakyawan riko, tanada ibada danhaka sedai ayi Amfani da kissa, da dabarunku na mata akanta badai sihiri ba” ya dakko wata kwalba da ruwa a ciki ya mikawa Ilham, yace “gashi nan ki tabbatar kinzuba mai wannan ruwan a Abinci ko Abun sha kin bashi da hannunki yaci, daga nan kome za’ayi baze kuma yinkurin hana Aurenku ba” 

Yakuma dakko wani turare, ya mika mata tasa hannu ta karba sannan yace “shikuma wannan ki tabbatar kinyi amfani da wannan turaren, kinshafa kafin kibashi Abinda kika zuba wannan maganin” Ilham ta gyda kai, yaseera tace “to amma malam kana ganin auren nasu ze yuwu kuwa?” “in har tayi yadda nace, komai zewuce ze aureta, kiyi a hankali, kikula da kyau muddin aka samu kuskure to komai ze iya lalacewa, danba karamin hadi nayi ba, karki bari wannan damar ta wuce” sukayi godiya Ilham ta bude jaka ta debo kudi fal ta bashi, sannan suka fito suka tafi, 

“Yaseera wallahi bansan ya zanyi inbashi Abu yaciba, haushina yakeji sosai, ko kallona bayayi balle yaci abun hannuna” “aikuwa haka zaki dage ki kokarta har bukatarmu ta biya, kiyi iya kokarinki kiga kin aiwatar, sannan yazakiyi da wannan yarinyar” “banni da shedaniya aini harnaga abunda zan mata kyaleta kawai” akazo inda yaseera zata sauka sukayi salkama. Ilham tana karasawa gida taga mota a bakin layinsu, rabawa tayi da niyyar ta wuce aka kuma biyota da motar, ta ja ta tsaya, Hannah ce tafito daga cikin motar, tasha gaban Ilham, kallo daya Ilham tayi mata ta ganeta, Ilham ta hade rai sosai, Hannah tacire glass din fuskarta tace “nasan kin ganeni, babu bukatar inmiki bayanin waceceni, kashedi ne nazo miki dashi, wanda sabawa kashedina daidai yake da rusa duk wani farincikin ki” “inajinki fadi abunda kikeso” 

“Naji labarin za’ayi miki baiko da Jalal, dan haka nazo miki da kashedin kiyi gaggawar janye batun ayimuku baiko, inbahakaba banki in salwantar da rai ba, dan haka kishiga hankalinki, kiyi tunani” mamakine yakama Ilham, wannan maganar kuma daga ina amma ta dake tace

“Kinyi kadan wallahi, sedai muyi asarar rayuwarmu gaba daya amma kome zakiyi, wallahi indai ina numfashi baki isaba, aurena da Jalal se anyi shi” “haka kikace ko?” “bakida kunne ne, dalla matsa ni kibani guri in wuce” Ilham ta bangaje Hanna ta wuce, Hanna tace “zaki gani kuwa” 

Ilham tai tafiyarta gida, Hannah ta shige motarta, itama ta bar gurin. 

Yausu Jalila suka kamalla first semester exams dinsu, su sameera se kuma bibiyan zahra suke akan su tabattar data amince da bukatansu, yayinda gefe daya suke tayiwa Jalila barazana kala kala. Da Jalila takoma gida ma sabgoginta ta shiga yi, Suleman ne yakirata, ita mutumin nan yafara isarta, ta daga wayar suka gaisa, yaita mata magiya tabarshi yazo gidansu, 

“dan Allah kayi hakuri babana ya bawa wani, inkazo gidanmu zega kaman ina kokarin bijirewa umarninsa ne” 

“subhanallah kiyi hakuri, baki gayamin da wuri ba, bazanso kisamu sabani da mahifinki ba, amma naso ace na sameki a matsayin matar aure ina sonki sosai, a tarayyata dake ya nunamin kinada nutsuwa da ilimi, dan haka ina son mudinga gaisawa kafin kiyi aure” murmushi Jalila tayi aranta tace “gaskiya mutumin nan akwai saukin kai” a fili tace “karka damu insha Allah zamu dinga gaisawa” sukayi hirarsu sannan sukayi sallama. Yana kashe wayar taga tests din Alhaji Kabiru akan wai tana wulakantashi tsawon lokaci yanzuma ya kirata wayarta busy tama waya da wani, in bazata yadda dashiba ze hakura” murmushi tayi sannan tace

“hmm kiris ya rage zaka gane baka da wayo” ta kirashi a waya ta dinga lallabashi tana bashi hakuri tayi masa alkawarin zasu hadu ranar juma’a, haka ya yadda yaita murna. Takira Zahrah a waya tace mata tacewa su sameera zatazo gurinsu ranar juma’a, zahra ta yadda. Jalila tace “Allah yasa abunda na shirya yatafi dai2”. 

A yammacin ranar ta shirya tasa nikabinta ta tafi hisba, taje takai report akan wannan gida da su sameera suke sheke ayarsu a ciki, sukayi mata alkawarin insha Allah zasu kaiwa gurin sumame, Jalila tace tanason ganin mataimakin commnder personally, yace bakomai sukaje wani office din Jalila tace “ranka ya dade gurin nan sonake kuje ranar juma’a misalin karfe hudu na yamma”

“Amma meyasa?” “saboda a lokacinne manyan lalatattun suke zuwa, abun haushin hada manyan mutane” “karki damu Insha Allah zamuje” “to shikenan nagode sosai ranka ya dade” Jalila ta taho gida cike da farinciki tareda fatan Allah yasa su afka tarkonta, sesun kunyata tun a duniya, daga nan ta taho gida, tana zuwa gida Jalila tasamu Nana tace “Nana kece me sauraran radio, dan Allah inaso kibani lambar wani gidan radio inkina da ita wanda kikasan in Labari yajemusu se duniya taji” 

Nana tace “ikon Allah yaukuma me za’ayi da lambar radio, Allah yasa dai ba wata rigimar kika kwaso mana ba” “ke haba dai, nima sonake indinga jin radio yadda nima zan dinga kira inji muryata a radio” Nana tai murmushi “to shikenan na dauka wata rigimar za’a kwaso mana ne” Jalila Allah 2 take asabar tazo taga yazata kaya. Ta kaiwa daddy Jalal list din abunda take bukata na girkim da zatayiwa bakinsu.

Jalila tagayawa zahra cewar tacewa su Sameera karfe hudu na yamma zatazo gidansu.

Ilham duk wata hanya data san zatabi domin janyo hankalin Jalal hartasamu damar bashi wannan maganin amma yaki, dan wani mugun kwarjini ya kema ta gashi ko san ganinta bayayi, gefe guda tsanar Jalila na karuwa a zuciyarta, kiris take jira tasamu damar dazata yiwa Jalila abunda se kowa ya tsaneta. 

Haka nan Jawwad yakejin tausayin hanan a ransa, yana ganin kaman be kyauta ba, amma duk yadda za’ayi shi Jalila yakeso, kuma yana fatan ze aureta. Yayinda bangare  Jalila tana kokarin yin baya2 da Jawwad musamman idan Maama tana nan, sabida batason tashin hankali sam, dan zuciyarta na rayamata yiwa Maama rashin mutunci wataran, shiyasa ko Abinci ta dena kai masa sedai halima ta kaimusu, iyakacinta da shi ta waya, sekuma in anyi sa’a ya shigo cikin gida kokuma sun hadu a harabar gidan. 

Ranar Alhamis Jalila taje gidansu zahra, Zahra tayi murna sosai da ganin Jalila, tayi wa ummanta introducing din Jalila suka gaisa daga nan suka wuce daki, Jalila tace “ke ba zama nazo yiba, ya ake ciki kingaya musu gobe in Allah ya kaimu zakije?” 

“Eh nagaya musu, zanzo karfe hudu” 

“yawwa zahra to yanzuma wani abu nakeso kiyimin” “me kenan?” Jalila ta dakko wayarta tasaka wani sim din a ciki, sannan ta kalli zahra, lamba zankira yanzu, inason kicewa mutumin nan kinaso ku hadu a wannan gidan ranar juma’a, kinuna masa kaman kinsanshi a baya amma bazaki gaya masa wacece ba” Jalila taima zahra bayanin abunda takeso tayi, zahra tace “Amma Jalila…” kinga babu batun amma kawai kiyi hakan” “to shikenan” Jalila tai hiding lamba takira Alhaji kabiru tabawa Zahra, bugu biyu ya dauka sannaan yace

“Hello wake magana” zahra tace wata baiwar Allah ce, kadai kacemin baka dau murya ba”

“gaskiya bangane ba, wacece dan Allah?” “nikuma kaga naganeka ba amma in duniya da gaskiya be kamata ka kasa gane wace ba, a cikin yan matanka ne” “to aikinsan abunne dayawa” “hakane kam, amma in ka ganni zakaji kunya akan cewar baka ganeniba” “ko? To nidai ki gayamin” “bazan gayamaka ba sedai in munhadu a gidana zaka gane” washe baki yayi, “gidanki wanne kenan” ta kwatanta masa gidan dasu Sameera suke zuwa, “kazo ranar juma’a karfe hudu, semu hadu ko?” “aikuwa zaki ganni dan zanso sanin wacece?” zahra tai murmushi “to shikenan nagode se anjima” zahra ta kashe wayar, ta kalli Jalila, Jalila ta jinjina mata “weldone dear kinyi yadda nakeso, zan barmiki sim din nan a gurinki, kucigaba da waya har Allah ya kaimu gobe juma’a, komai yazo karshe” 

“Amma Jalila shi waye wannan?” “ba ruwanki kedai kawai kiyi abunda nace inkuma akasamu kuskure kece a ruwa baniba” Jalila taimata sallama tai tafiyarta. 

Yau juma’a shine ranar da Jalila take sa ran su Sameera su fada trap dinta, kuma gobe ranar asabar bakinsu Jalal zasuzo dan haka ta rarraba hankalin ta kashi2, tun sassafe take up and down, taje kasuwa tayo siyayyar abubuwan dazata bukata na aikace2 da zatayi, karfe uku da rabi ta shirya tasa hijjabinta da nikab ta dau jakarta, Nana ta kalleta “Jalila ina zaki hakane kiketa sauri?” 

“banisa zanyiba yanzu zan dawo” amsar da Jalila tabata kenan tafito, tanata sauri a harabar gidan taci karo da Jawwad, “Baby ina zuwa haka da ranar nan? ” “Yaya zan dan fitane gidansu wata kawata” 

“in hanya ne muje se in kaiki” “Aa kayi tafiyarka kawai, yanzu znadawo bazan bata ba kaji sweetheart” ta kashe masa ido tai waje murmushi yayi ya girgiza kai, 

Jalila ta tafi layin gidan, can karshe tasamu guri ta zauna, tana nan zaune motarsu Sameera tazo suka shiga itada Saleema, sunyi wata irin shiga ta fitsara abun babu kyan gani, ga wasu manyan karti  maza suna shiga suna fita daka gansu kaga manyan yan duniya, dan basu da maraba da yan daba. Jalila takira zahra a waya “ke ya akeciki kunyi waya yatahone?” “Eh ya taho, yacemin yana hanya, yanzu su Saleema suka kirani, wai ina inane, nace musu nakusa zuwa” Jalila tace “good kice masa ya hanzarta inbahakaba zaki fita” “to shikenan” 

Ba’ayi minti goma ba da waya dasukayi da Zahra sega Motar Alhaji kabiru a layin gidan yayi parking dai2 kofar gidan da su  Saleema suke ciki, yana zaune a cikin mota be fitoba, zahra takira Jalila, “Jalila yacemin waigashi a kofar gidan” “kice masa yashiga kansa tsaye” Jalila ta katse wayar tanata addu’a Allah yakawo yan hisaban nan da gaggawa, tana kallo Alhaji Kabiru yafito daga mota ya doshi gidan nan, Jalila tana ganin ya shiga gidan, takira gidan radio ta sanardasu cewar hisaba sunzo kame a  unguwar dan bare kuma akwai wani gagarumin abun kunya dake shirin faruwa,

“Innalillahi wa inna ilaihi raji un” shine abunda Alhaji ya dinga maimaitawa ganin yarsa ta cikinsa Saleema da shiga rabin tsirara akan cinyar wani kato, suna shan shisha, gefe ga wasu sunata aikata badala ciki hada Sameera, a takaice dai gidane na manyan karuwai da yandaudu.

Koda Saleema ta dago tai ido hudu da mahaifinta a gigice ta mike daga cinyar wanda take zaune, tana zazzare ido, gaba daya sukayi cirko2 suna kallonsa, koda ya duba yaga waye Saleema take kan cinyarsa ba kowabane illa Jeje, a gigice Alhaji Kabir yace “Saleema abunda kike aikatawa kenan, kin cuceni kin cuci kanki Allah ya isa tsakanina da ke” ya maida idonsa kan Jeje “nizaka ciwa amana, karasa da wadda zakayi lalata se yar cikina, duk halaccin danayi maka a rayuwa wallahi seka ga karshenka sekaga abunda zanyi maka, sena dau mummunan mataki akanka” Jeje rasa mezece yayi gaba daya ya rude, daga gefe wani tsageran matashi yace “wai dan Allah meyakawo ka nan gurin, kake wannan maganganun ne, nina dauka harka kazo, kaima fa ana kaimaka matan nan guest house dinka to meye dan anyiwa yarka, abunda kakewa yayan wasu nefa” seda Alhaji Kabiru ya duba sosai sannan ya gane matashin, tabass suna kaimasa karuwai yana biyansu kudi. A fusace Alhaji Kabiru ya dau wata kwalba ya nufi inda matashin yake, Saleema se kuka takeyi, jin ance itama ga abunda mahaifinta yakeyi, yana zuwa ya bugawa matashin a ka, sauran matasan sukayo kansa, duk wanda yazo seya kaimasa suka da fashashiyar kwalba. 

Itako Jalila koda taga Alhaji Kabiru ya shiga cikin gidan nan ta kuma kiran yan jarida, tana gama wayar sega motar “yan hisba, tareda yan sanda, sukayiwa gidan dirar mikiya, suka kewaye shi, sannan wasu suka shiga cikin gidan, babban abun kunya da asara shine kama uba da ‘ya a gidan karuwai, nan aka tarkata kansu tsaf, Alhaji Kabiru se rantse2 yake, ga wadanda yajiwa ciwo da kwalba, Saleema banda aikin kuka ba abunda takeyi, kan Jeje se zubarda jini yakeyi,’yan sanda suka caje gidan inda akasamu miyagun kwayoyi, da kayan shaye2 kala2, kafin a tafi dasu yan jarida suma suka karaso, suka rufawa motar yansanda baya dan zuwa daukar rahoto, ba karamin farinciki Jalila tayiba, rasa inda zatasa kanta tayi dan murna, batasan lokacin dataji hawaye farinciki nabin fuskarta ba “Allah kai kabani wannan dama, Allah kaikabani nasara ba dabarata da wayona ba, Allah nagode maka, nagode da ni’imarka da kariyarka, Allah kasa sanadiyar shiryuwar bawanka ce tazo” hanyar titi ta nufo tana sauri, yamma tayi sosai, ta tafi gida gida cike da murna da farinciki. 

Takoma gida tanata murna, tana zuwa ta tarar da sa’ada tazo itada Naja wai a gidan zasu kwana biyu, Jalila ko takansu bata biba, murnarta kawai takeyi, 

Nana tace “Baby meye sirrin wannan fara’ar da murmushinne haka?” 

“Nana nima ban saniba ina murna ne kawai” “Hmm kyama fadi gaskiya” “gaskiyar kenan Nana” sukayi dariya gaba daya. Kan kace me Labari yafara yada duniya cewar an kai sumame gidan karuwai, inda aka kamo hada wani uba da ‘yarsa tareda yaronsa a gidan” nan da nan zance yafara zaga social media, da sauran kafafan watsa labarai, inda ake ta tir da Allah wadaran akan Alhaji Kabiru. 

Nana takira Jalila a waya “Jalila Allah yasaki a Aljannah, kinceci rayuwata da sauran rayukan dasu Saleema sukaso lalatawa, Allah yabiyaki da mafificin Alkhairi, Allah yabaki miji nagari me kaunarki” “ba komai Zahra, Nagode sosai nima Allah ya amsa mana bukatunmu” 

Alhaji Kabiru yashiga cikin matsanancin bakin ciki, yarasa msyake masa dadi, wai yarsa yakama da wanda ya amincewa wato jeje, abun bakincikin ankamoshi da yarsa a gidan karuwai, gashi ba’asan ainihin me yafaru ba amma zance yanata yada duniya, nan yashiga tunanin waima wacece wadda takirashi tace yaje gidanta ne, in akajima ya tuna yadda yaga yarsa da jeje, se ransa yakara baci, ya kalli Jeje yace “Jabir (shine ainihin sunan jeje) Allah ya isa tsakanina da kai, duk halaccin danayi maka a rayuwa amma ka lalata min yarinya” “dama can lalatacciyace, kuma halaccin dakayimin aiba kyauta kaimin ba aiki nake maka, shekaru nawa nayi inamaka bauta” “Au hakama zakace ko, zamu fita ai zakaga abunda zanyi maka, kasanni kasan halina” Jeje ya kalleshi “kabari kaga munfita lafiya tukuna, aisena bari munfita lafiya zaka samu damar yimin wani abu, dan haka sena fadi komai” zazzaro ido Alhaji Kabiru yayi, “me kake nufine wai?” inbaka ganeba seka bari sena aiwatar zaka gane”. 

   Duk yadda su Sa’ada sukaso bakantawa Jalila rai bata kulasu ba dan karma su bata mata farincikinta, tabar musu dakin takoma na halima ta kwana a can, tun sassafe tai salla, sukayi aikace2 dazasuyi itada halima a cikin gidan, sannan ta tafi gidansu Jalal itada Halima, tunda Ilham tai arba da Jalila takejin kaman ta dau wuka ta kasheta, suka gaisa da Mummy ta nuna mata kitchen Jalila suka shiga suka fara abunda yakamata, aka jima Nana itama tabaro wasu sa’ada gidan ta tabiyosu Jalila a ranar suka hada snacks din dayakamata, sukabar aikin dabasu gama ba zuwa gobe, kafin bakin suzo sesu karasa, Nana da halima suka koma gida, Jalila ta tsaya tana jarasa gyara kitchen din, Jalal ya shigo da katon kwando cike da fruit ya ajiye yai waje abunsa, ta zauna ta shiryasu a fridge sannan ta tafi. Wahsegari da safe Jalila ta dawo, bata tashi halima ba daga bacci saboda taga alamar tagaji sosai jiya, ta dama kunun gyada, ta dibi nata a dan karamin flask ta tafi dashi. 

Jalila tayi busy sosai a kitchen, dan bata samu ko karyawa tayi ba, dogon wandone a jikinta da rigarta har gwiwa me dogon hannu, ta daure kanta da dankwali, amma karshen gashin ta yafito, taji alamun ana kallonta, bata waigaba ta basar tacigaba da abunda take, cikin kitchen din ya karaso ba sallama ba komai yakama dube2, bata kulashiba tacigaba da aikinta ya jijjiga tea flask bakomai a ciki, tsaki yayi ya bude fridge yana kallon arrangement din datayiwa fruits din, still ya rufe fridge din, Jalila ta fuskanci yunwa yakeji, ta kalleshi “wai meyene?” “bansaniba” 

“karka sani din” yaje ya duba kettle yaga akwai ruwan zafi a ciki, ya dakko ya zuba bako lipton, ya dakko madara da sugar yana kokarin antayawa, ita Jalila ma dariya yabata, ta dakko flask ta zuba masa kunun gyada a cup, ta zubamasa samosa, ta mika masa, bako kunya ya karbe, yanemi guri kan kujera a kitchen din yai zamansa yafara ci, itakuma tacigaba da aikinta, wayarta tafara ringing, sunan sweet hanny shine akan screen din wayar, tadaga wayar tasa a kunnenta “Hello sisyna ya kike” hanan tace “Hmm ba fada meyakawo gaba Baby, kin yadani, kin manta dani ko?” “A’a hanan ban manta dake ba, ko zan manta komai bazan manta da yar uwata ba” 

“Anya kuwa Jalila? Kina guduna saboda inason Jawwad ko? Karki damu hakan baze shafi zumuncinmu ba, amma yakamata kikawomin ziyara, in duni6da gaskiya bekamata ace tunda kikabar kaduna baki kuma zuwa ba” 

Kwalla ce ta taru a idon Jalila, cikin muryar kuka Jalila tace “Hanan bazan iya zuwa kaduna, bazan iya zuwa anguwarmu ba, Hanan hakan ze tayarmin da hankali, inzo unguwarmu ummi bata nan, bansan inda take ba, kiyi hakuri Hanan, amma kina raina daks da sauran mutane masu mahimmanci danake dasu a garin” takarasa maganar hawaye nabin idonta, “Jalila na fuskanci abunda yake damunki, inajin damuwarki a zuciyata, kiyi hakuri mucigaba da addu’a kinji, kidena kuka” gyada kai Jalila tayi kaman tana gaban Hanan, sannan tace “Nagode Hanan, kigaida kowa da kowa mussaman babana” “zasuji Insha Allah yar baba” ta kashe wayar, duk kokarin da Jalila tayi ta cigaba da aikinta amma takasa, tanata kokarin daurewa ta hadiye kukanta amma takasa hawaye ketabin idanunta, sosai Jalal yaji tausayinta ya kamashi, yaji inama ace shima zeji wannan kaunar da shaukin da y’aya sukeji game da iyayensu mata, har fuskar Jalila tayi ja. Tasowa yayi yazo bayanta ya tsaya yana kallon ta, dagowa tayi ta kalleshi suka hada ido, “Meyasa bazaki karbi kaddara a duk yadda tazo miki ba, memakon kiyi addu’a amma kike kuka, hakan bekamata ba, kizama jaruma mana” dauke kai tayi takuma fashewa da kuka wannaan karon hada sheshsheka, sunkuyowa yayi daf da ita a hankali yace, “Ummi tana raye, kuma zaki ganta very soon, jikina yana bani” da sauri ta kalleshi ya jinjina mata kai, yai mata alama  tasa hannu ta goge hawayenta, “da mutum yana da ikon sauya kaddararsa, kokuma kuka yana canza wani abu, da mutane dayawa sun fita daga matsalolin dasuke ciki, wani lokacin mukanyi kuka ne don samun sassauci a cikin damuwar da take damunmu, amma ta wata fuskar kukan yana karamana matsala ne da damuwa, ummi tayi rayuwa me tsayi ba tareda yan uwanta ba, kuma hakan besa wani abu yafaru da itaba, dan haka kema addu’a zakiyi kicigaba da hakuri ” yana gama fadin hakan ya mike ya kai hannu ya juye sauran kunun gyadan nan ya juya ya fice, Jalila tabi bayansa da kallo, tai ajiyar zuciya tacigaba da aikinta jikinta a sanyaye. 

Wajen karfe shadaya na rana mummy ta shigo tanayiwa Jalila sannu da aiki, Jalila tace yawwa” Mummy barka da safiya”

“Yawwa barka ya aikin?” “lafiya kalau Mummy nakusa kammalawa ma” “to masha Allah” Bayan Mummy tafita ba dadewa Jalila taje gida ta dakko wasu spices ta dawo, ta windowa kitchen dake harabar gidan taga Ilham tana zukar wani abu a kwalba da syringe tana tsirawa ruwan a jikin wani jan Apple, Jalila ta tsaya tana kallonta, tana gamawa ta maida shi cikin fridge ta rufe ta fita ba tareda ta lura Jalila ta ganta ba.  Se wajen karfen daya Jalila ta karasa girkin Abincin tareda taimakon Nana data biyota daga baya. Sun kammala komai sun gyara kitchen din kaman ba’ayi amfani dashi ba, suka fito itada Nana, daddy yana palour “Sannu da aiki yaran kirki, nasaku wahala ko?” Jalila tai murmushi “ba wani wahala daddy mun kammala komai ma” “Masha Allah, Allah yayi Albarka” Nana tace “Ameen daddy, amma ni gaskiya nagaji” “Aidama ke lazy ce Nana” sukayi dariya, daddy yace “Jalila amma in sunzo aizakizo kiga yan uwan yayanki ko?” murmushi tayi ta jinjina kai, daga nan suka fita suka tafi gida. Jalila ta gaji dan haka wanka tayi, Naja tana kan gadon ta baje, Jalila ta haye gadon ta kwanta itama, Naja ta kalli Jalila “malama meye haka? Bakiga nice a kwance agurin ba” “Eh banganiba, babu a house ko?” 

A fusace Naja tace “amma kinsan karyane kicemin babau a house ko” “in akwai a house ai dabakiyi wannan shirmen ba, kodayake aiba mamaki a sha rashin hankalin nono” “kut me kike nufi?” 

“inkika bari, nakuma bude baki da nufin mayar miki da martani sekinyi kuka, dan haka kiyi abunda ya dameki bacci zanyi” Jalila ta kwanta abunta, tabar Naja tana kallonta, can cikin bacci Jalila taji Nana tana cewa “Ke Jalila ki tashi, bakinku sunzo fa?” A hankali Jalila ta bude ido “wane bakin kuma?” 

“Bakinsu Jalal mana, ki tashi yau zakiga yan uwansu, masu irin hancinsa” 

Jalila takuma juyawa akan gadon tace “ni dan Allah ki kyaleni mana” “Ke Jalila kinada matsala wallahi, dan Allah ki tashi muje, akwai wanda nakeson gani a cikinsu, inajin kunya inje ni kadai” Jalila ta bude ido ta kalli Nana, “ikon Allah, Nana kinda damuwa, wallahi nikam ki kyaleni” 

Nana tace “kar Allah yasa kije” “eh bazaniba” har Jalila tafara bacci, ta tuno Apple din nan, kartaje Ilham takuma zuba wani abu, zumbur ta mike, ta bude drower tasaka kayanta, tafito da sauri ta tafi gidansu Jalal, harabar gidan duk motoci, tundaga varrender take jiyo hayaniyar mutane, ta bude kofar palour a hankali, dayawansu kamansu daya da Daddy Jalal, duk haka suke da dogon hanci sosai aranta tace “tab wannan ko bata sukayi da wannan hancin nasu za’a ganesu” se yare sukeyi, ga Jawwad ma a cikinsu, shima se yaren ake dashi, tanaji daya yana tsokanar Nana, da wata irin hausarsa yace “gaskiya Nana kin girma kin ganki kuwa, waike yan mata tunoki nake lokacin kina dan karamarki” Nana ta dan zumbura baki “kajika Kaima ai da bahaka kake ba, ji yadda ka wani tara gemu, waikai dole ka girma” dariya sukayi gaba daya, daddy yai murmushi yace “Nana yaushe zaki dena surutu ne, bakinki baya mutuwa” kallo daya zakayiwa Jalal kasan yana cikin farinciki, fara’a yake sosai, ‘yan uwansa duk nutsatstsu, amma shi yafita daban a cikinsu dan gashin kansa ba kyan gani, ga kallo daya zakayi masa kasan lips dinsa yana shaye2, setaji hakan ba dadi, a hankali ta sulale ta shiga kitchen ba wanda ya ganta, Tana tsaye a kitchen din Ilham ta shigo taci kwalliya sosai, gashi tasa wani turare me karfi, wanda sam bashida dadi, wani banzan kallo taiwa Jalila sama da kasa a wulakance, “Aikin banza jaraba da maita, tunda kingama abunda akasaki aisekikoma inda kika fito ko, ko yanzunma wani munafuncin zakiyi, shine kika dawo” 

“Aini bana munafunci kaina tsaye nake abunda nakeso, Aikinne ban gama ba, nazo nakarasa wanda aikin da nakarasa yafi kowanne mahimmanci, na bata aikin wasu dan gyara nawa, kamar yadda nasha fada muddin aikin wani yashigo nawa, sena bata shi” kallon Jalila tayi cike da mamaki wannan karon kuma me take nufine, kwafa Ilham tayi tawuce ta  fara daukar kayan Abinci tana fita dasu, alhalin lokacin da Jalila take aikinta ko dauraye spoon Ilham bata tayata ba, Jalila ta tsaya tana kallonta tagama fita da kayam Abincin, ta dawo ta bude fridge tafara jera fruit a tray, tana kallon Ilham ta dakko Apple din nan tai masa guri na musamman akan tray din, tayi waje, Jalila tabiyo bayanta ta tsaya a window tana kallonsu, Ilham sewani iyayi take tana kwarkwasa, Jalila tayi mamaki da bataga Mummy ta fito ba, bakin su biyar ne maza hudu se mata uku, duk daka gansu kasan yan uwan daddy ne, 

Ilham cikin iyayi tace 

“bari kufara da fruits kafin kuci Abincin ko” cikin bakin daya shima me matukar kama da Jalal yace “Eh hakane gaskiyanki Ilham” tafara binsu daya bayan daya tana basu Apple, Jalila tana kallonta ta dauki Apple din nan ta mikawa Jalal, ya mika hannu ya karba shima kamar kowa dayake Apple yana daga cikin favorite fruit din Jalal. Jalila tana ganin irin kallon da Ilham kewa Jalal, Ilham na ganin Jalal yaci Apple din nan tafara murmushi. dawowa Ilham tayi da tray din ta ajiye a kitchen, har zata fita Jalila tace “bar murna karenki yakama zaki kinyi mantuwa” waigowa Ilham tayi tana kallonta, kawai taga Jalila tana jefa Apple sama tana cafewa

“Ilham kinsaba lamba, saboda na canza Apple din” a razane ta kalli Jalila, Jalila ta karaso gaban Ilham, ta kamo hannunta ta doramata Apple din, duba da kyau wannan shine Apple din dakika zubawa magani ba wanda yaci ba, ko baki gayamin ba nasan abunda kika zubawa Apple din nan na asiri ne akan Jalal, Ilham shi so ba’asiyan sa kuma sihiri be isa yabaki soyayya ba koya soki na lokaci kadanne, in abun ya barshi shikenan, yanzu meye ribarki a cikin cutar da dan uwanki? “

Koda Saleema ta dago tai ido hudu da mahaifinta a gigice ta mike daga cinyar wanda take zaune, tana zazzare ido, gaba daya sukayi cirko2 suna kallonsa, koda ya duba yaga waye Saleema take kan cinyarsa ba kowabane illa Jeje, a gigice Alhaji Kabir yace “Saleema abunda kike aikatawa kenan, kin cuceni kin cuci kanki Allah ya isa tsakanina da ke” ya maida idonsa kan Jeje “nizaka ciwa amana, karasa da wadda zakayi lalata se yar cikina, duk halaccin danayi maka a rayuwa wallahi seka ga karshenka sekaga abunda zanyi maka, sena dau mummunan mataki akanka” Jeje rasa mezece yayi gaba daya ya rude, daga gefe wani tsageran matashi yace “wai dan Allah meyakawo ka nan gurin, kake wannan maganganun ne, nina dauka harka kazo, kaima fa ana kaimaka matan nan guest house dinka to meye dan anyiwa yarka, abunda kakewa yayan wasu nefa” seda Alhaji Kabiru ya duba sosai sannan ya gane matashin, tabass suna kaimasa karuwai yana biyansu kudi. A fusace Alhaji Kabiru ya dau wata kwalba ya nufi inda matashin yake, Saleema se kuka takeyi, jin ance itama ga abunda mahaifinta yakeyi, yana zuwa ya bugawa matashin a ka, sauran matasan sukayo kansa, duk wanda yazo seya kaimasa suka da fashashiyar kwalba. 

Itako Jalila koda taga Alhaji Kabiru ya shiga cikin gidan nan ta kuma kiran yan jarida, tana gama wayar sega motar “yan hisba, tareda yan sanda, sukayiwa gidan dirar mikiya, suka kewaye shi, sannan wasu suka shiga cikin gidan, babban abun kunya da asara shine kama uba da ‘ya a gidan karuwai, nan aka tarkata kansu tsaf, Alhaji Kabiru se rantse2 yake, ga wadanda yajiwa ciwo da kwalba, Saleema banda aikin kuka ba abunda takeyi, kan Jeje se zubarda jini yakeyi,’yan sanda suka caje gidan inda akasamu miyagun kwayoyi, da kayan shaye2 kala2, kafin a tafi dasu yan jarida suma suka karaso, suka rufawa motar yansanda baya dan zuwa daukar rahoto, ba karamin farinciki Jalila tayiba, rasa inda zatasa kanta tayi dan murna, batasan lokacin dataji hawaye farinciki nabin fuskarta ba “Allah kai kabani wannan dama, Allah kaikabani nasara ba dabarata da wayona ba, Allah nagode maka, nagode da ni’imarka da kariyarka, Allah kasa sanadiyar shiryuwar bawanka ce tazo” hanyar titi ta nufo tana sauri, yamma tayi sosai, ta tafi gida gida cike da murna da farinciki. 

Takoma gida tanata murna, tana zuwa ta tarar da sa’ada tazo itada Naja wai a gidan zasu kwana biyu, Jalila ko takansu bata biba, murnarta kawai takeyi, 

Nana tace “Baby meye sirrin wannan fara’ar da murmushinne haka?” 

“Nana nima ban saniba ina murna ne kawai” “Hmm kyama fadi gaskiya” “gaskiyar kenan Nana” sukayi dariya gaba daya. Kan kace me Labari yafara yada duniya cewar an kai sumame gidan karuwai, inda aka kamo hada wani uba da ‘yarsa tareda yaronsa a gidan” nan da nan zance yafara zaga social media, da sauran kafafan watsa labarai, inda ake ta tir da Allah wadaran akan Alhaji Kabiru. 

Nana takira Jalila a waya “Jalila Allah yasaki a Aljannah, kinceci rayuwata da sauran rayukan dasu Saleema sukaso lalatawa, Allah yabiyaki da mafificin Alkhairi, Allah yabaki miji nagari me kaunarki” “ba komai Zahra, Nagode sosai nima Allah ya amsa mana bukatunmu” 

Alhaji Kabiru yashiga cikin matsanancin bakin ciki, yarasa msyake masa dadi, wai yarsa yakama da wanda ya amincewa wato jeje, abun bakincikin ankamoshi da yarsa a gidan karuwai, gashi ba’asan ainihin me yafaru ba amma zance yanata yada duniya, nan yashiga tunanin waima wacece wadda takirashi tace yaje gidanta ne, in akajima ya tuna yadda yaga yarsa da jeje, se ransa yakara baci, ya kalli Jeje yace “Jabir (shine ainihin sunan jeje) Allah ya isa tsakanina da kai, duk halaccin danayi maka a rayuwa amma ka lalata min yarinya” “dama can lalatacciyace, kuma halaccin dakayimin aiba kyauta kaimin ba aiki nake maka, shekaru nawa nayi inamaka bauta” “Au hakama zakace ko, zamu fita ai zakaga abunda zanyi maka, kasanni kasan halina” Jeje ya kalleshi “kabari kaga munfita lafiya tukuna, aisena bari munfita lafiya zaka samu damar yimin wani abu, dan haka sena fadi komai” zazzaro ido Alhaji Kabiru yayi, “me kake nufine wai?” inbaka ganeba seka bari sena aiwatar zaka gane”. 

   Duk yadda su Sa’ada sukaso bakantawa Jalila rai bata kulasu ba dan karma su bata mata farincikinta, tabar musu dakin takoma na halima ta kwana a can, tun sassafe tai salla, sukayi aikace2 dazasuyi itada halima a cikin gidan, sannan ta tafi gidansu Jalal itada Halima, tunda Ilham tai arba da Jalila takejin kaman ta dau wuka ta kasheta, suka gaisa da Mummy ta nuna mata kitchen Jalila suka shiga suka fara abunda yakamata, aka jima Nana itama tabaro wasu sa’ada gidan ta tabiyosu Jalila a ranar suka hada snacks din dayakamata, sukabar aikin dabasu gama ba zuwa gobe, kafin bakin suzo sesu karasa, Nana da halima suka koma gida, Jalila ta tsaya tana jarasa gyara kitchen din, Jalal ya shigo da katon kwando cike da fruit ya ajiye yai waje abunsa, ta zauna ta shiryasu a fridge sannan ta tafi. Wahsegari da safe Jalila ta dawo, bata tashi halima ba daga bacci saboda taga alamar tagaji sosai jiya, ta dama kunun gyada, ta dibi nata a dan karamin flask ta tafi dashi. 

Jalila tayi busy sosai a kitchen, dan bata samu ko karyawa tayi ba, dogon wandone a jikinta da rigarta har gwiwa me dogon hannu, ta daure kanta da dankwali, amma karshen gashin ta yafito, taji alamun ana kallonta, bata waigaba ta basar tacigaba da abunda take, cikin kitchen din ya karaso ba sallama ba komai yakama dube2, bata kulashiba tacigaba da aikinta ya jijjiga tea flask bakomai a ciki, tsaki yayi ya bude fridge yana kallon arrangement din datayiwa fruits din, still ya rufe fridge din, Jalila ta fuskanci yunwa yakeji, ta kalleshi “wai meyene?” “bansaniba” 

“karka sani din” yaje ya duba kettle yaga akwai ruwan zafi a ciki, ya dakko ya zuba bako lipton, ya dakko madara da sugar yana kokarin antayawa, ita Jalila ma dariya yabata, ta dakko flask ta zuba masa kunun gyada a cup, ta zubamasa samosa, ta mika masa, bako kunya ya karbe, yanemi guri kan kujera a kitchen din yai zamansa yafara ci, itakuma tacigaba da aikinta, wayarta tafara ringing, sunan sweet hanny shine akan screen din wayar, tadaga wayar tasa a kunnenta “Hello sisyna ya kike” hanan tace “Hmm ba fada meyakawo gaba Baby, kin yadani, kin manta dani ko?” “A’a hanan ban manta dake ba, ko zan manta komai bazan manta da yar uwata ba” 

“Anya kuwa Jalila? Kina guduna saboda inason Jawwad ko? Karki damu hakan baze shafi zumuncinmu ba, amma yakamata kikawomin ziyara, in duni6da gaskiya bekamata ace tunda kikabar kaduna baki kuma zuwa ba” 

Kwalla ce ta taru a idon Jalila, cikin muryar kuka Jalila tace “Hanan bazan iya zuwa kaduna, bazan iya zuwa anguwarmu ba, Hanan hakan ze tayarmin da hankali, inzo unguwarmu ummi bata nan, bansan inda take ba, kiyi hakuri Hanan, amma kina raina daks da sauran mutane masu mahimmanci danake dasu a garin” takarasa maganar hawaye nabin idonta, “Jalila na fuskanci abunda yake damunki, inajin damuwarki a zuciyata, kiyi hakuri mucigaba da addu’a kinji, kidena kuka” gyada kai Jalila tayi kaman tana gaban Hanan, sannan tace “Nagode Hanan, kigaida kowa da kowa mussaman babana” “zasuji Insha Allah yar baba” ta kashe wayar, duk kokarin da Jalila tayi ta cigaba da aikinta amma takasa, tanata kokarin daurewa ta hadiye kukanta amma takasa hawaye ketabin idanunta, sosai Jalal yaji tausayinta ya kamashi, yaji inama ace shima zeji wannan kaunar da shaukin da y’aya sukeji game da iyayensu mata, har fuskar Jalila tayi ja. Tasowa yayi yazo bayanta ya tsaya yana kallon ta, dagowa tayi ta kalleshi suka hada ido, “Meyasa bazaki karbi kaddara a duk yadda tazo miki ba, memakon kiyi addu’a amma kike kuka, hakan bekamata ba, kizama jaruma mana” dauke kai tayi takuma fashewa da kuka wannaan karon hada sheshsheka, sunkuyowa yayi daf da ita a hankali yace, “Ummi tana raye, kuma zaki ganta very soon, jikina yana bani” da sauri ta kalleshi ya jinjina mata kai, yai mata alama  tasa hannu ta goge hawayenta, “da mutum yana da ikon sauya kaddararsa, kokuma kuka yana canza wani abu, da mutane dayawa sun fita daga matsalolin dasuke ciki, wani lokacin mukanyi kuka ne don samun sassauci a cikin damuwar da take damunmu, amma ta wata fuskar kukan yana karamana matsala ne da damuwa, ummi tayi rayuwa me tsayi ba tareda yan uwanta ba, kuma hakan besa wani abu yafaru da itaba, dan haka kema addu’a zakiyi kicigaba da hakuri ” yana gama fadin hakan ya mike ya kai hannu ya juye sauran kunun gyadan nan ya juya ya fice, Jalila tabi bayansa da kallo, tai ajiyar zuciya tacigaba da aikinta jikinta a sanyaye. 

Wajen karfe shadaya na rana mummy ta shigo tanayiwa Jalila sannu da aiki, Jalila tace yawwa” Mummy barka da safiya”

“Yawwa barka ya aikin?” “lafiya kalau Mummy nakusa kammalawa ma” “to masha Allah” Bayan Mummy tafita ba dadewa Jalila taje gida ta dakko wasu spices ta dawo, ta windowa kitchen dake harabar gidan taga Ilham tana zukar wani abu a kwalba da syringe tana tsirawa ruwan a jikin wani jan Apple, Jalila ta tsaya tana kallonta, tana gamawa ta maida shi cikin fridge ta rufe ta fita ba tareda ta lura Jalila ta ganta ba.  Se wajen karfen daya Jalila ta karasa girkin Abincin tareda taimakon Nana data biyota daga baya. Sun kammala komai sun gyara kitchen din kaman ba’ayi amfani dashi ba, suka fito itada Nana, daddy yana palour “Sannu da aiki yaran kirki, nasaku wahala ko?” Jalila tai murmushi “ba wani wahala daddy mun kammala komai ma” “Masha Allah, Allah yayi Albarka” Nana tace “Ameen daddy, amma ni gaskiya nagaji” “Aidama ke lazy ce Nana” sukayi dariya, daddy yace “Jalila amma in sunzo aizakizo kiga yan uwan yayanki ko?” murmushi tayi ta jinjina kai, daga nan suka fita suka tafi gida. Jalila ta gaji dan haka wanka tayi, Naja tana kan gadon ta baje, Jalila ta haye gadon ta kwanta itama, Naja ta kalli Jalila “malama meye haka? Bakiga nice a kwance agurin ba” “Eh banganiba, babu a house ko?” 

A fusace Naja tace “amma kinsan karyane kicemin babau a house ko” “in akwai a house ai dabakiyi wannan shirmen ba, kodayake aiba mamaki a sha rashin hankalin nono” “kut me kike nufi?” 

“inkika bari, nakuma bude baki da nufin mayar miki da martani sekinyi kuka, dan haka kiyi abunda ya dameki bacci zanyi” Jalila ta kwanta abunta, tabar Naja tana kallonta, can cikin bacci Jalila taji Nana tana cewa “Ke Jalila ki tashi, bakinku sunzo fa?” A hankali Jalila ta bude ido “wane bakin kuma?” 

“Bakinsu Jalal mana, ki tashi yau zakiga yan uwansu, masu irin hancinsa” 

Jalila takuma juyawa akan gadon tace “ni dan Allah ki kyaleni mana” “Ke Jalila kinada matsala wallahi, dan Allah ki tashi muje, akwai wanda nakeson gani a cikinsu, inajin kunya inje ni kadai” Jalila ta bude ido ta kalli Nana, “ikon Allah, Nana kinda damuwa, wallahi nikam ki kyaleni” 

Nana tace “kar Allah yasa kije” “eh bazaniba” har Jalila tafara bacci, ta tuno Apple din nan, kartaje Ilham takuma zuba wani abu, zumbur ta mike, ta bude drower tasaka kayanta, tafito da sauri ta tafi gidansu Jalal, harabar gidan duk motoci, tundaga varrender take jiyo hayaniyar mutane, ta bude kofar palour a hankali, dayawansu kamansu daya da Daddy Jalal, duk haka suke da dogon hanci sosai aranta tace “tab wannan ko bata sukayi da wannan hancin nasu za’a ganesu” se yare sukeyi, ga Jawwad ma a cikinsu, shima se yaren ake dashi, tanaji daya yana tsokanar Nana, da wata irin hausarsa yace “gaskiya Nana kin girma kin ganki kuwa, waike yan mata tunoki nake lokacin kina dan karamarki” Nana ta dan zumbura baki “kajika Kaima ai da bahaka kake ba, ji yadda ka wani tara gemu, waikai dole ka girma” dariya sukayi gaba daya, daddy yai murmushi yace “Nana yaushe zaki dena surutu ne, bakinki baya mutuwa” kallo daya zakayiwa Jalal kasan yana cikin farinciki, fara’a yake sosai, ‘yan uwansa duk nutsatstsu, amma shi yafita daban a cikinsu dan gashin kansa ba kyan gani, ga kallo daya zakayi masa kasan lips dinsa yana shaye2, setaji hakan ba dadi, a hankali ta sulale ta shiga kitchen ba wanda ya ganta, Tana tsaye a kitchen din Ilham ta shigo taci kwalliya sosai, gashi tasa wani turare me karfi, wanda sam bashida dadi, wani banzan kallo taiwa Jalila sama da kasa a wulakance, “Aikin banza jaraba da maita, tunda kingama abunda akasaki aisekikoma inda kika fito ko, ko yanzunma wani munafuncin zakiyi, shine kika dawo” 

“Aini bana munafunci kaina tsaye nake abunda nakeso, Aikinne ban gama ba, nazo nakarasa wanda aikin da nakarasa yafi kowanne mahimmanci, na bata aikin wasu dan gyara nawa, kamar yadda nasha fada muddin aikin wani yashigo nawa, sena bata shi” kallon Jalila tayi cike da mamaki wannan karon kuma me take nufine, kwafa Ilham tayi tawuce ta  fara daukar kayan Abinci tana fita dasu, alhalin lokacin da Jalila take aikinta ko dauraye spoon Ilham bata tayata ba, Jalila ta tsaya tana kallonta tagama fita da kayam Abincin, ta dawo ta bude fridge tafara jera fruit a tray, tana kallon Ilham ta dakko Apple din nan tai masa guri na musamman akan tray din, tayi waje, Jalila tabiyo bayanta ta tsaya a window tana kallonsu, Ilham sewani iyayi take tana kwarkwasa, Jalila tayi mamaki da bataga Mummy ta fito ba, bakin su biyar ne maza hudu se mata uku, duk daka gansu kasan yan uwan daddy ne, 

Ilham cikin iyayi tace 

“bari kufara da fruits kafin kuci Abincin ko” cikin bakin daya shima me matukar kama da Jalal yace “Eh hakane gaskiyanki Ilham” tafara binsu daya bayan daya tana basu Apple, Jalila tana kallonta ta dauki Apple din nan ta mikawa Jalal, ya mika hannu ya karba shima kamar kowa dayake Apple yana daga cikin favorite fruit din Jalal. Jalila tana ganin irin kallon da Ilham kewa Jalal, Ilham na ganin Jalal yaci Apple din nan tafara murmushi. dawowa Ilham tayi da tray din ta ajiye a kitchen, har zata fita Jalila tace “bar murna karenki yakama zaki kinyi mantuwa” waigowa Ilham tayi tana kallonta, kawai taga Jalila tana jefa Apple sama tana cafewa

“Ilham kinsaba lamba, saboda na canza Apple din” a razane ta kalli Jalila, Jalila ta karaso gaban Ilham, ta kamo hannunta ta doramata Apple din, duba da kyau wannan shine Apple din dakika zubawa magani ba wanda yaci ba, ko baki gayamin ba nasan abunda kika zubawa Apple din nan na asiri ne akan Jalal, Ilham shi so ba’asiyan sa kuma sihiri be isa yabaki soyayya ba koya soki na lokaci kadanne, in abun ya barshi shikenan, yanzu meye ribarki a cikin cutar da dan uwanki? “

Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

.. 

I want comments not stickers or just thanks 

Daga alkalamin Aysher cool 

Back to top button