Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 4 Complete Hausa Novel

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

Dedicated to my beloved sisters. 😍   

A wani madaidaicin table dake a bedroom ɗin nasa ta aza tray ɗin ta matsar dashi gabansa, yana zaune a gefen gadon yana daddana wayarsa, 

satar kallon wayarsa tayi ba kowa ya faɗo mata a rai ba fa ce husanna da jahad tabbas tana bukatar tayi waya da su, amma babu hali cos bata da waya, kuma ba yadda za’ai ta ce zata ari wayar sa, hauka ma take yi ashe?

Muryarsa taji a kunnanta “Thank you zuwa nan da 30 mins ka dawo ka dauki tray ɗin,”

Ta amsa masa sannan ta fi ce, acikin ranta tana faɗin’ tabbas ya kamata nakira naji wani hali husanna da jahad suke ciki wayyo Allah na gashi na lura kamar aunty azmi bata da waya a hannunta, 

A ɗakinsu twins ta tsaya domin gyarawa masu shi, a hargitse ta samu ɗakin sun tarwatsa komai, haka ta kama aikin gyara masu shi, bed ɗin ta soma gyarawa bed sheet din takai hannu zata cire, tsayawa tayi tana kallon wani abu a jikinsa, wani irin ruwa ne mai kitib kitib kamar kokko mai yawan gaske a jikin zanin gadon, tunani ta soma yi’ shin wannan menene ajikin zanin gadon a iya sani na gidan nan basa shan kokko to kodai madara ce ta zube a wurin gsky i na tunanin haka, 

kasancewar zanin gadon maroon colour ne hakan yasa abun ya fito sosai raɗau, cike da jin kyankyami ta tattare bedsheet ɗin ta zuba a laundry basket ɗinsu, 

Kammala gyaran gadon tayi sannan tayi mopping ɗin dakin tsaf ta gyara komai, gaban dressing mirror ɗinsu taje, mayuka tagani tsadaddun gaske iri iri, karaf idonta suka sauka akan wani kwalban magani, hoton dake a jikin kwalbar kawai take kwallo namiji da namiji ne zir babu kaya a jikinsu ɗaya yayi holding penis ɗin ɗayan,

Gabanta ne taji yayi mugun bugawa duk da batasan ma’anar hakan ba sai ranta ya bata cewa kawai magani ne na wani ciwon nasu na maza, 

Kammala gyarawa tayi afterwards ta koma bathroom ɗinsu, anan ne fa kwalwarta ta ƙara rikice wa ganin wannan farin abun da tagani a bedsheets ɗinsu, gashi nan a har jikin bathtube ɗin ko’ina sun hargitsa shi, haka ta daure ta wawwanke ko’ina tass, 

Bayan ta fito sai da ta sake duba kwalbar maganin nan a jiki taga an rubuta (Homosexual) shi kaɗai ta iya ganewa amma ita kanta bata san ma’anar kalmar ba don ba komai ta sani ba.

Sam ta manta da sakon junaid na ta koma after 30mins ta kwashi tray din abincin sa takai masa.

Sai da ta kammala gyarawa ɗakunan kowannansu ba ƙaramin gajiya ta kwasa ba, sauƙin ma ɗakunan sauran ba hargitsi ba kamar nasu Jahan da Ayaan ba, 

Har yanzu sehrish ta gaza mantawa da wannan abun da tagani ɗakin su twins, akwai wani abu da ya tsaya mata a rai wanda take tuna shi da jima wa daya faru dasu tana kokwanton cewa kodai wannan abun ne, bakomai bane fa ce Sperm !!!

Tafiya take yi jikin ta a kasalance wata irin kasala ce ta dabaibaye ta, labari mara daɗin ji, abunda take kokarin yi musu shine (Kyakkyawan Zato)

Dakyar take taka matattalar benen, idonta a cike taf da hawaye ‘Ya Allah kada kasa abunda nake zargi ya tabbata Ya Allah kasa nayi aiki na ba tare da na fuskanci wata matsala ba cikin salama na tafi nabar masu gidansu, ni kuɗi kawai nazo nema domin na taimaki ƴan uwana dake kwance asibiti bayan wannna bana bukatar wani abu,

Tura kofan room ɗin junaid ta yi, samun shi tayi ya gama cin breakfast bacci ya kwashe sa, sai sharar baccinsa yake cikin kwanciyar hankali da natsuwa, 

ɗan murmushi ta saki tare da cewa” Ya Allah ka tsare wannan bawan naka bansan halinsa ba amma ina yi masa kyakkyawan zato”

Hannu takai zata ɗauki tray din karaf idonta suka sauka akan wayarsa dake ajiye saman nightstand, ba komai ya fado mata a rai ba fa ce ta saci wayarsa ta kira goggonsu taji ya lafiyarsu Jahad, murmushi tasaki a hankali ta soma tafiya cikin sanɗa, saɗaf saɗaf ta tafi, 

Sai da tasha wahalar daukar wayar tasa sannan taga ashe thumbpring gare ta, dole sai da yatsansa sannan za ta 6uɗe, ɗafe kanta tayi tare da faɗin “wayyo Allah na” dama sarar ta ce, 

Juyawa tayi tana kallonsa yadda ya ke kwance yana baccinsa a natse, sama ya ke fuskanta ya wawware hannayensa, murmushi tasaki tare da fadin ‘abun zai zo mun da sauƙi,’

Hawa saman bed ɗin ta yi a hankali cikin sanɗa kamar mage, rarrafe a hankali tayi ta isa inda hannun damansa yake, yatsun hannunsa a buɗe suke gasu nan tsirara masu kyan gaske, bayan wayar ta juya inda thumbprint din ya ke, kwafa wa tayi a yatsansa na tsakiya, yasa mata wrong, matsar da wayar tayi ana gabansa cikin sa’a wayar ta bude, tsananin farin ciki ne ya bayyana a fuskarta, cikin sauri ta sauka ta lalla6a tafita ta tsaya a bakin kofan room din nasa, jikinta har kerma yake yi karta ya farka, tuni zufa ta soma tsastsafo mata a hancinta, 

Time ɗin da ta aza idonta akan wayar, Hoton da tagani a wellpepper ɗinsa ne yasa jin zuciyarta wani irin bugu, 

Zuba ma hoton ido tayi wato ainihin wani haɗaɗɗen matashin saurayi ne, ko a mafarki bata ta6a ganin mutun mai irin kyansa ba, kwayar idonsa ce tafi ɗaukar hankalinta, blue eyes ne da shi, wannan wani irin zazzafan kyau ne! irin wannan kyan shine mutane ke neman tsari da shi, jikinsa na sanye da kakin sojoji ba ƙaramin daukarsa su kayi ba, yayi hoton ne kamar a shirin film a saman mota yayi irin wannan zukunnawar da suke yi in zasu yi harbi da bindiga,  hannunsa riƙe da bindigar yayi hoton, doguwar sumar kansa wanda ya ɗaure ta tsayin ta har bayan wuyansa baka wulik, 

Kyawawan lips ɗinsa tabi da kallo dark pink kamar ya shafa janbaki, ga wani dogon hanci tubarkalla masha Allah, 

Tayi nisa cikin ƙurewa hoton kallon, sam ta manta da abunda take kokarin yi sai da wayar hannunta tayi ƙarar shigowar sako sannan ta dawo hayyacin ta, 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Please Share and drop your comments

Da sauri ta shiga wurin contacts, numbar goggo ta rubuta ta danna mata ƙira, ba tayi tunanin ko akwai recharge card a phone din nasa ba, amma ranta ya bata cewa ba zama a rasa ba, su da kullum cikin kuɗi suke, 

A jiyar zuciya ta saki jin numbern ya fara ringing, sai Allah Allah take suyi sauri su ɗaga before he get up,

Jin muryar goggo yasa sehrish sakin murmushin jin dadi 

“Assalamu alaikum goggo sehrish ce! Ina jahad don Allah inason magana da ita cikin sauri,” ta karasa maganar tana waige waige kar wani ya ganta, 

On the other hand goggo ta miƙa wa jahaad wayar, cikin dauƙi ta ƙarba tare da fadin”yar uwa ! dagaske ke ce ! Wayyo Allah na farin ciki,”

Dariya sehrish tasaki jin abunda jahadar ta ce, kamar zatayi kuka itama ta ce”I really missed you my sisters, so much, dana ji voice ɗinki i just felt like to cry,” ta karasa maganar idonta cike taf da hawaye,

“sister dama akwai abunda nake na fada miki amma narasa taya zanyi magana dake,” 

Sehrish ta ce “yanzu ina jinki pls kiyi sauri ba wayata ba ce ta yaron gidan ce baisan ma na dauka ba,” 

Cikin fargaba take sauraron jahaad ɗin”sister doctor ya ce ƙarshen month ɗin nan indai ba ayiwa husanna aiki ba, to ciwon nata zai habbaka sai dai a fidda ita ƙasar waje in ba haka ba mutuwa zata yi, sun sa mana ranar aiki 5 ga watan da zamu shiga….” kuka ne ya ci ƙarfin ta, itama sehrish ɗin kukan take yi haka suka dinga kuka ta wayar, babu mai lallashin wani,

“Idan kin gama wayar ina jira!!!

A firgice ta juya idanuwanta azare jin muryar junaid, rufe idonta tayi tare da buɗe su ashe kunnanta ne suka jiyo mata hakan sam bashi bane , 

Ganin ya fara yi mata gizau yasa ta ce da jahad ta ajiye waya, zasuyi magana next time in ta samu chance irin wannan,

Cikin sauri ta goge numbar goggo da ta sanya, a wayarsa da duk wata shaida da zata tona cewa tayi amfani da wayarsa, 

Cikin sanɗa ta lalla6a ta mayar masa da wayar, har time din bacci yake yi, 

Haka ta koma ɗakin ta tana sharar kwalla,  safa da marwa ta shiga yi tana zagaye ɗakin, tunanin ta yadda zatayi ta samun kuɗin nan, 

“Yanzu yaya zanyi! kada husanna ta rasa rayuwarta! sam bata cancanci haka ba, tazo duniya a wahalce kuma ta koma! Ya ilahi i dont ave any other choice fa ce kai Ya Allah, nayi imani dakai, kai kaɗai ne gatan mu, Ya Allah ka kawo mana mafita Albarkacin manzon Allah (SAW) ❤

Dakyar ta samu ta shiga toilet don wanke jikinta, ganin cewa basu da wani aiki a kitchen saboda guys ɗin gidan in suka fita sai da marece suke dawo wa, hakan yasa basa making lunch da wuri, 

Don haka tana kammala wankan ta, da alwalarta tafito domin time ɗin azhar ya yi, har ta kammala sallah bata tuna cewa tabar gashin bakinta a cikin toilet ba, 

A saman sallayar ta kwanta tun tana shesshekar kuka tana rokon Allah har bacci ya ɗauke ta, 

Sehrish ta manta bata rufe kofan ɗakinta ba kamar yadda ta saba, shin na tuna mata ko kuma na kyale ta? tuna wa da cewa ba’a so a tashi mutun in yana bacci indai ba abu mai mahimmanci bane kamar sallah yasa na ƙyale ta, me zai biyo ba?

“Babu amfanin zama da mutun fasiƙi irin ka ! Ka saida mun ƴaƴa ! Saboda son abun duniya da son siyasa kai mutunne ko dabba! hakan baiyi maka ba sai da kabi ƴaƴana ka lalata musu rayuwa wannan wace irin masifab ce? 

“Wayyo Allah abba kadaina dukan oumman mu, jini ke zuba a jikinta, oumma ki daina kada ya kashe ki ! Oumma! Oummahhhh!

Da ƙarfi ta ambaci sunan a firgice lokaci ɗaya ta farka, kukan da take a mafarkin har a fili sharkaf haka tayi da zufa, zaune ta tashi a fujajen tana kuka bil haƙƙi, 

Dafe kanta tayi saboda wani matsanancin ciwo da yake yi mata, cikin shesshekar kuka take ambaton “umman mu,’ fuskarta duk ta jagule dama dama da hawaye, da alama wani mummunan abune daya taba faruwa a rayuwarta ta tuna, 

Haka ta dinga maimaita “Innalallahi wa inna ilaihirraji’un, 

Cike da jimami ta tashi daga saman sallayar, agogon dake manne jikin bango ta kalla ƙarfe 4:00 dai dai time ɗin la’asar yayi har yana kan wuce wa, 

dole ne ta canza sabuwar alwala saboda tayi bacci mai nauyi, 

Cire hijab ɗin dake jikinta tayi ta aza asaman gadon, ta jiƙe sharkaf da zufa, shiga toilet ɗin tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, hannun na dafe da chest ɗinta, cire kayan jikinta tayi , ta sakarwa kanta shower , yadda sassanyar ruwan ke sauka a jikinta haka zuciyarta ma ke sauka daga hawan da tayi, (ruwa rahama Ne!) duk yadda kake cikin kunar rai indai zaka shiga ka watsa ruwa a jikinka to tabbas zaka samu natsuwa, 

Bayan ta kammala bath ɗin ta karasa gaban mirror ɗin dake cikin toilet ɗin, tana bin jikinta da kallo, tana da tsayi ba laifi , sam bata da ƙiba amma ƙirjinta cike suke da boobs, sannan daga kasa akwai hips sosai faffadan gaske, launin fatarta choculate colour ce, expensive skin colour, tana da sexy eyes masu lumshe wa sometimes kamar na mai jin bacci wani lokacin kuma sai kayi tunanin tana shaye shaye ne, kwayar idonta fara ce tass mai launi brown colour, hancin ta ba dogo bane ƙarami ba ƙaramin kyau yayi mata ba, a bangaren lips kuwa tamakar shape ɗin love ❤ red colour masu tafshin gaske (macen novel ke nan komai nata is 100% 😂

Hannu tasa tare da shafa gefen wuyanta inda ke akwai wani rubutu a jikin fatar wurin da bakin rubutu kamar na tattoo aka rubuta (Sb) murmushi ta ɗan saki tuna wanda yayi mata rubutun, mayar da hannunta tayi akan sumar kanta wadda tayi tsayi yanzu ta sauko mata har kafaɗar ta , asalin gashin kanta har ƙugunta ya dira, amma silar hajjaju da ma’reeya suka datse mata shi saboda gudanar da aikin ta a matsayin namiji, 

Tunawa da sallah yasa tayi gaggawar mayar da kayanta, ta dauki gashin bakinta da ta bari a gaban mirror, ta fita 

Cikin sauri tayi sallar , bayan ta gama ta nufi kitchen wurin azmi taga in akwai aiki, samun ta tayi tana a ciki tana shirye shiryen fara aiki, 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Please Share and drop your comments

“Barka da aiki aunty azmi ” sehrish ta faɗi hakan tana kallonta, ɗagowa tayi da fara a fuskarta tace “ke ke da sannu saboda naganki kina ta sharar bacci,” 

Ras! Sehrish taji gabanta ya faɗi hankali a tashe take kallon azumi, itama kallon ta take tana sakin wani bazawarin murmushi, lokaci guda sehrish tabi ta susuce murya na rawa tace “dagaske kin ganni ina bacci !” dariya azmi tasaki tare da cewa “kwarai malam tukur ɗan basaja naganka kona ce naganki, ” 

Kallon kallo suka shiga yiwa junansu sehrish na tunanin tabbas ƙaryarta ta ƙare saboda azmi ta kira ta da ke amaimakon kai sannan taganta tana bacci da hijabi kuma ba gashin bakin nan nata da take sawa ya ilahi, 

Yayin da azmi ke mamakin wayau irin na wannan yarinyar, har tasan tayi shigar namiji tazo gidan sojoji aikatau ko tsoro bata ji, gskya ba ƙaramar ƙuruwa ba ce,

     

Sai faman wurga ido sehrish take yi,hannu tashiga tafawa tana faɗin “nashiga uku shikenan komai ya ƙare”

 sai faman wurga ido sehrish take yi,hannu tashiga tafawa tana faɗin “nashiga uku shikenan komai ya ƙare” 

Kana kallonta ka ga tsananin tsoro a fuskarta, lokaci guda tabi ta rikice ganin bata da wani mafita fa ce ta roƙi azmi ta rufa mata asiri, don haka jiki na rawa takarasa gaban azmi ta zube saman kneel ɗinta tana roƙonta “nasan nayi laifi amma bani da wata mafita ne don Allah ki rufamin asiri aunty azmi kamar yarda Allah ya rufa miki,” 

   Hmmm ja da baya azmi ayi tare da cewa”am sorry to say bazan iya rufa miki asiri ba ! laifin zai shafe mu mu biyu, wannan babbar qarya ce a girma na bai kamata na goyi bayan hakan ba, sannan bugu da ƙari sojojin gidan nan suka gane cewa ke maca ce ba namiji ba to tabbas ƙasusuwanki za’a fidda daga cikin gidan nan! kinsan matsalarki ? Cikin sauri ta ce “a’a ” 

“matsalarki shine kin aikata laifi biyu, na farko namiji suke so a matsayin ɗan aiki ba mace ba, ke kuma kinyi shigar mace kinzo, duk sunyi tsammanin ke namiji ce hakan yasa suka amince da ke rinka shiga har ɗakunansu kina gyara musu da sauransu, nabiyu laifin ƙarya! sun tsani maƙaryaci, kinyi karya baiwar Allah idan har suka son da wannan zancen ko ! Ba ma ke ba ni kaina ta shafa! don haka cikin salama ki tattara kayanki ki bar gidannan kafin su ankara” 

   Azmi na kaiwa nan ta juya mata baya ta ci gaba da abunda take yi, 

Jiki a mace sehrish ta miƙe, hawaye na gangarowa daga idonta kamar an kunna fanfo, cikin sanyin murya ta ce “shikenan…bakomai naji daɗin hakan zan tafi insha Allah,”

  Fi ce wa tayi a guje tana shessheƙar kuka, fadawa tayi ɗakinta ta datse kofar ta faɗa saman gadon ( kamar a indian film 😂)

Tasha kuka kamar ba gobe lokaci guda fuskarta ta kumbura tayi suntum, idonta suka yi jawur suka ƙankance kamar na ƴan chaina, 

Haka ta taso daga saman bed ɗin tana bin bedroom ɗin da kallo “ko a mafarki ban taba tunanin haka zata kasance dani ba, yanzu zan tafi nabar wannan daular, ni bama wannan bane damuwata ba ya rayuwar su husanna zata kasance su da suke cikin wani hali a asibiti, gashi bansamu kuɗin ba, wayyo Allah na, bansan wane irin zunubi muka aikata ba da rayuwarmu bata tafiya adai dai ba, tun kafin mu mallaki hankalinmu mu ke fuskantar ƙaddara iri iri meyasa !?

       Zube wa kasan tiles ɗin tayi tana kuka jikinta har jijjiga yake yi, 

Sam bata ji shigowar azmi ba sai dai mutyarta taji ta dirar mata a kunne” Ya sunanki ? ta jefa mata tambaya ,

     yunkurawa tayi ta tashi tsaye tana matse hanci ta ce “SEHRISH” 

Jinjina kai azmi tayi tare da ƙarasawa inda take, tafin hannunta ta sa tana share mata hawaye, sam sehrish bata yi tunanin hakan ba, 

sannan cikin natsuwa ta ce” nayi takaici dana sa wannan kyakkyawar fuskar zubda hawaye am so sad,” cike da mamaki sehrish ke kallonta, azmi ta ci gaba da cewa “kiyi hakuri ko kusa bazanso na raba ki da aikin ba! duk da ina tsoran abunda zai biyo baya, amma zan iya jurewa don ganin na taimaka miki,” jin wannan bayani yasa sehrish sauke nannauyiyar ajiyar zuciya,

mayar da hannunta tayi a saman shoulders ɗinta taci gaba da cewa” da farko ina so ki fadamun dalilin dayasa ki kayi basaja a matsayin namiji”?

Muryar na rawa ta soma magana cikin sheashekar kuka” ƴan uwana ne basu da lafiya rai hannun Allah an kwantar dasu asibiti, kuma doctor ya ce aiki za’a yi musu, shine nake kokari naga nasamu ƙudi na biya musu, ɗayar ma dr yace in har ya wuce 5 ga watan da zamu shiga sai dai a fidda ita Qasar waje ko tarasa ranta…..’ kukan ne yaci ƙarfin ta, 

Cikin lallashi azmi ta ce “daina kuka ya isa haka, na fuskanci matsalarki, duk da ina buƙatar bayani amma bani da enough time, riƙe wannan zamuyi magana an jima yanzu dai taimakon da zan miki shine, zaki ci gaba da aiki a matsayin Namiji kamar yadda kike yi, ko da gigin wasa karki bari su gane cewa ke maca ce ! sannan maganar kuɗi kuma nawa ne ake bukata ?

 Azmi ta tambaya tana kallon ta, sehrish ta ce “dubu ɗari tara ne” a tunanin ta azmi zatayi shock in taji kuɗin amma sai taji tace”zan iya ansar miki albashinki na wata na shekara ɗaya da rabi ! a baki a ɗunkule amma inaso ki sani ! duk runtsi duk wuya duk kuma duk irin wahalar da zaki fuskarta da wulaƙanci a wurin masu gidan nan, dole kiyi haƙuri ki jure! kiyi musu biyayya sau da ƙafa, ba maganar barin aiki , in kuma har kika ce zaki bari toh sai fa kin biya sauran kuɗin da kika ƙarba kin amince!!? 😰

taji ma tana nazari kafin tace”Eh na amince !!! zuciyarta na wani irin bugawa ba kowa ya faɗo mata a rai ba face Ayaan da jahaan , ynx ana nufin ta ɗaura aure da kaddararta na zama cikin gidan nan! ya ilahi,

“Yanzu account number zaki bani na wanda za’a turawa kuɗin aikin nasu,” azmi ta faɗa tana kallon cikin idonta, tsananin farin ciki ta gani a fuskar sehrish 😇

cikin jin daɗi tace “babu a wuri na amma zuwa anjima ko gobe zan samu na kawo miki,” azmi ta amsa da toh sannan ta kama hanyar fita har takai bakin kofa xata buɗe ta juya ta kalli sehrish dake ta faman sakin murmushi tace “kada ki manta ynx kina ƙarƙashin Iko na! komai zakiyi saida umarnina, idan har kika saba hakan, hmmmm,

 bata ida ba ta fi ce, 

sam sehrish bata damu da hakan ba, ita dai indai akan sisters ɗinta ne toh ko fiye da hakan ma zata iya jurewa, 

Jiki na rawa baiwar Allah ta shige toilet ta dauro alwala taci gaba da zabga nafilfilin miƙa godiya wa ubangijin mu Allah subhanahu wata’ala, 

   Matsalar su husanna tazo ƙarshe, sauran damuwa ta kau, shin yaya kke tunanin rayuwar sehrish zata kasance a gidan ABBAN SOJOJI ? 😢

  yinin ranar da fara’a a fuskarta hakoranta a washe kamar mai tallar maclean, cikin jin daɗi suka gudanar da aiki a kitchen tare da azmi don shirya dinner,

tunanin yadda zata sake ɗaukar wayar junaid takira husanna ta ce su turo mata account number, har zuciyarta take jin ƙaunar azmi saboda tayi mata rana ! Har abada kuwa ji take bazata taba sa6a mata ba! tayiwa kanta alkwarin zatayi mata biyayya bazata taba bijire mata ba ko taci amanarta ba,

A 6angaren junaid kuwa, bayan ya tashi daga bacci da jimawa ya wuce masallaci daya dawo ya tsaya a filin da suke buga ball na gidan tare da wasu daga cikin sojojin dake tsaron gidan,

  yunwa ce tasa shi shigo wa ciki after magrin prayer, muryasa suka dinga ji yana kiran “tukur ! ,

Wani irin farin ciki ne ya lullu6e sehrish, cikin ɗauki ta ajiye wanke wanken da take yi agaban fanfo, na kayan da suka yi amfani dasu,

Karasawa tayi wurinsa yana zaune saman 3 seater, yana daddana wayarsa, cikin girmamawa tace”gani ya ya junaid”  ta kirasa da hakanne saboda ya hana ta ce masa yalla6ai, girman jiki ne kawai dashi da kuma tsawo fuskarsa ce kawai zata nuna maka cewa yaro ne sharkaf,

 ta6e baki yayi tare da ɗan jefa mata kallo ya ce” ƴunwa nake ji, ” ya faɗa a shagwa6e, yana kallon ta 

cikin zumuɗi ta ce ” a shirya ma abinci a dining ko nan zan kawo maka,?

ta tambaya tana kallon wayar hannunsa kamar ta fisge ta saboda ita take bukata,

ɗan yatsina fuska yayi kafin ya ce” No a tsarin gidan nan bama iya cin abinci in ba tare da junan mu ba, duk yunwar da mutun ke ji dole sai an tattara an haɗu a table aci a tare, don haka kawo min coffee kawai, zan jira brothers ɗina su dawo sai mu ci dinner a tare,” 

 Wannan haɗin kan nasu ya burge sehrish sosai, suna son junansu, juya wa tayi, taje da tadawo hannunta dauke da cup din saman ɗan plate ɗin da ake aza sa, miƙa masa tayi tana kallon fine face ɗinta, 

Ƙarba yayi tare da faɗin”thanks”

komawa dining room ɗin tayi, tana goggoge chairs ɗin dake kewaye dashi, daga inda take tana satar kallonsa shi da yake zaune a falo,

Bayan ta kammala ta koma kitchen ɗin, azmi ta samu tana a ciki tana ganin ta ta ce “yawwa mlm tukur ayi maza a fara jera abincin a dining ko,” sunnar da kai ƙasa sehrish tayi cikin jin kunya, azmi tace “gsky hajjaju yar daru ce! da ita duk aka shirya wannan ƙaryar,” murmushi kawai sehrish take yi tana wasa da yatsun ta,

Ba tare da bata lokaci ba, suka soma shirya abincin, tana kaiwa tana jera masu, 

Ƙiris ya rage a fara kiran sallar magrib, bayan sun girma shiryawa azmi ta wuce ɗakin ta , sehrish kuwa falo ta wuce, anan ta samu Junaid yana sharar bacci, ya mimmiƙe kafafuwansa a saman doguwar kujerar,  Alhamdulillah thanks to Allah ta fadi hakan, ƙyalle ido tayi ta ga inda ya ajiye wayarsa saman chest ɗinsa, 

Cikin sanɗa ta soma tafiya a hankali a hankali take takawa, har ta idasa isa gabansa, leƙa fuskansa tayi kyakkyawa mai annuri, dimples ɗin nan nasa a lotse, kamar ba bacci yake yi ba,

Hannu takai a hankali ta ɗauki wayar tasa cikin rashin sa’a ta zame daga hannunta ta faɗi kasa ta daki haɗaɗɗen tiles ɗin dake kasa, har cikin zuciyarta taji faɗuwarnan, tsadaddiyar waya irin wannan, dafe ƙirjin ta tayi tana kallon wayon, ƙarar faɗuwar wayar tasa junaid yunkurin buɗe idonsa daga baccin da yake, cikin sauri ta boye bayan hannun kujerar tana sauke ajiyar zuciya, gyara kwanciyarsa yayi ya ci gaba da bacci, jin sakin ajiyar zuciyarsa yasa ta gane ce ya koma baccin nasa, hannu ta zura ta janyo wayar tana kallon screen ɗinta, Alhamdulillah ta fada ganin ba abunda ya same shi,

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Yunƙurawa tayi ta tashi tsaye, tana kallon sa, ya aza hannunsa ɗaya a saman stomach ɗinsa, ɗayan kuma a saman kansa, abun yazo mata da sauƙi, don haka cikin sauri ta jona wayar a yatsarsa, nan take wayar ta buɗe, 

murmushin jin daɗi ta saki, wannan hoton ta sake gani a wallpaper ɗinsa na wannan haɗaɗɗen matashin saurayin, har ranta so take tasan wanene wannan sarkin kyawun nan,

Ja da baya tayi a hankali tayi nesa dashi, izuwa gefen stair ta tsaya, contacts dinsa ta shiga ta rubutu numbar goggo, bugu ɗaya wayar ta shiga kuma aka ɗaga, cikin sa’a muryar jahaad taji tana kwaɗa sallama, da farin ciki ta ce”Jahaad ni ce Sehrish! banda isasshen lokaci pls listen to me,” a can 6angaren jahad ta natsu tana sauraron abunda sehrish zata ce mata”Nasamu kuɗin aikin account number zaki turomin cikin gaggawa saboda na fadamiki wayar ta yaron gidan ce nake dauka shi kansa baisani ba,” 

tsananin farin ciki ne yasa jahad yin ihu da fadin Alhamdulillah a cikin wayar tasu, ta ce “narasa inda zansa kaina don farin ciki ƴar uwa kice mun kusa barin asibitin nan dama wlh nagaji da zamansa….” sehrish ce ta katse ta ganin zata ja masu lokaci ga tsoran kar junaid ya farka “ke ba surutu zakiyi mun ba ki anso acct number ɗin likitan yanzu yanzun nan ki turamin kada fa ki 6ata lokaci asiri na zai tonu,” 

Tana gama faɗan hakan ta yi rejecting kiran, ta tsaya nan tana jiran shigowar saƙon jahaad, jikinta har rawa yake gudun kar junaid ya farka, har leƙen sa take yi taga ko yana motsi, 

Safa da marwa tashiga yi kamar mai ɗawafi, Allah Allah take jahaad ta turo saƙon tayi sauri ta kwafa ta mayar masa wayarsa,

tana nan tana jira, tajiyo ƙarar shigowar motarsu Ayaan,da wata irin jiniya motocin nasu ke shigowa, aiko nan take junaid ya soma motsi , saboda tsabagen ruɗu 😳, maimakon taje ta ajiye masa wayar ta ruga , sai ta haɗa da wayar duka ta watsa aguje sai bedroom ɗinta. 

Ana dara ga dare yayi ?😳

tashi zaune yayi tare da yin miƙe, da hamma lokaci guda hannu yasa ya rufe bakin nasa, wayarsa ya soma lalube yaga bata nan bai kawo komai aransa ba sai yayi tunanin ko ya barta a room dinsa ne, 

   Shigowarsu brothers ɗin nasa ne yasa shi, sakin fara’a , a jere suka shigo su 7, ƙarasa wa kanal yusif yayi ya russuna tare da rungumesa yace”barka da hutawa my bro ina fata kana cikin koshin lafiya,” da fara’a ya amsa masa da cewa “am fine bro kun dawo lpy,” kanal ya masa masa da eh, kafin ya wuce, shima khaleed karasawa yayi inda junaid ɗin ke zaune ya rungume sa tare da cewa”My sweet bro ya enjoyment,” bai basa amsa ba sai murmushin da yayi masa, haka irfan da jabeer duk suka rungumesa kafin suka wuce ɗakunansu,

 Ya rage saura twins da fawan, harara fawan ya sakar masa tare da wuce wa ta gabansa yana rera waka cikin zolaya yake cewa”Lalatacce lalatacce ne ko a gidansu wannan haka yake,” ɗaure fuska junaid yayi don ya tsani tsokanarsa da fawan ya ke yi, 

A tare Ayaan da Jahan (Masoya 😂) suka ƙarasa kowanne ya manna masa kiss a cheeks ɗinsa kafin suma suka wuce ciki,

Shima junaid ɗin tashi yayi ya shiga ciki domin ɗauro Alwala saboda liman na ta kwaɗa kiran sallah, 

A bangaren sehrish kuwa, tana nan maƙale da wayar junaid a hannunta, zuciyarta na harbawa, sai zagaye ɗakin take tana faɗin, nashiga ukuna ynx ya zanyi in junaid ya nemi wayarsa ya rasa, in kuma ya ganta a hannuna nasan dukan tsiya zan sha, kuma su kore ki daga aiki ace mun 6arauniya, yanzu ya zanyi ni nasamu na mayar masa da wayarsa wayyo Allah na,

Ƙarar shigowar message ne taji ƙirrrr! da sauri ta duba, account number ne jahad ta turo mata, cikin sauri ta laluba cikin drawer chest, inda ta ajiye diary din da take rubutu acikinsa Wanda tazo dashi , biron da ta saka a tsakiyar littafin ta dauko ta bude page tayi copying numbers ɗin, tana gama wa , ta mayar ciki ta ajiye, 

Sannan ta yi hanzarin deleting sakon daga wayar tasa, fitowa tayi daga ɗakin tana leken ko akwai mutun, duk basu kai da fito wa, 

har tasa hannu zata koma ciki taji alamun mutun, junaid ɗin ne ya fito yana naɗe hannun rigarsa, da alama masallaci zai wuce, 

Ba karamin dadi taji ba, yana fi ce wa, ta lallabawa cikin sauri ta shiga ɗakinsa ta ajye masa wayar a saman nightstand,

Fito wa tayi tana sauke ajiyar zuciya, yanzu abunda ya rage mata takai ma azmi acct number ɗin,

ɗaki ta koma, ta ɗauki diary ɗin ta yago papern data rubuta numbar, ta fito ta tunkari ɗakin azmi, dayake ba nisa yana kusa da nata, wannan ne karo na farko da ta fara shiga ɗakin ta,

Sallama tayi, azmi dake zaune saman sallaya ta amsa da “wa’alaikum salam shigo ciki,” 

Cikin natsuwa sehrish ta shiga ciki, wuri ta samu ta zauna kusa da ita ta lankwashe kafarta tayi zaman cin tuwo,

Cazbaha take ja, a hannunta ɗan murmushi tayi tace”wai malam tukur ne yau a ɗakin namu kodai mafarki nake ne? Cikin jin kunyarta sehrish ta ɗukadda kai tana murmushi,

“tabbas kuwa shine to mara ba lale marhaban daga ganin wannan gashin bakin naka akwai magana,” dariya ce ta kubce ma sehrish, ta shiga 6a66aka ta,

daga bisa ni ta tsagaita tare da cewa “aunty azmi dama acct number ɗin ne na kawo miki,” ta karasa maganar tana miƙa mata paper ɗin, karba azmi tayi tare da fadin”kin tabbata ta likitance? Sehrish ta ɗaga kai tare da cewa “Eh tashi ce,” 

“Toh shikenan kije kawai insha Allah zuwa gobe za’a tura masu kudin,” 

Azmi ta fada tana adana takardar a saman carpet din.

After isha prayer, kowannan su ya hallara domin gudanar da dinner ɗinsu, amma banda mutun biyu, Ayaan da Jahaan wato twins,

duk sunyi dressing cikin pyjamas ɗinsu gwanin kyau, abunka ga mazajen novel ga haske ga tsari ga kwantacciyar suma 😉. (Allahumma arzukni 😂)

 Kowannansu yaja kujera ya zauna suna fuskantar junansu, a tsaye dogon dining table ɗin ya ke, mai 12 seats ne

 “Abinci ya riga masu cin shi hallara ikon Allah,” acewar jabeer, fawan ya ce “gasu aci ci mala’ikun tauna suma sun hallara ” ya ƙare maganar cikin zolaya yana kallon junaid fuskarsa da murmushi, tsoki junaid ya ja baice masa komai ba don bayasan hayaniya wani lokacin, 

Khaleed ya ce “zaku fara disturbing ɗin mutane ko”? ya ambaci hakan yana kallonsu, kanal yusif ya ce “barsu su fara mai rabon shan duka baya jin bari sai ya sha sa,” 

dariya irfan yayi tare da cewa”Zanso naga ana dukan junaid wai waya ga shagwa6a haka zai dinga ihu yana buga ƙafa a ƙasa kamar ƙaramin yaro yana cewa mommy daddy babban yaya ,” 

jin wannan maganar ta irfan yasa sauran tuntsirewa da dariya, hakan ba ƙaramin ƙulesa yayi ba, 

 “Ae naga yaron ya girma ! Jin ya ke we’re equal wit him, wuyansa ya isa yanka, bansan dalili ba, ” acewar jabeer

 Fawan ya ƙarbe da cewa “ah ba dole ba tunda Ak47 ɗinsa ta yi girman tamu,”

gaba ɗayansu suka tuntsire da dariya, adai~dai lokacin sehrish ta karaso domin yin serving dinsu abincin taji suna wannan maganar ba abunda ya dira a kunnanta sai kalmar (Ak47),  sam batasan mai hakan yake nufi ba,

iya ƙuluwa junaid ya yi shiru kawai ya yi bai tanka musu ba, ya rasa maiyasa suke masa haka, 

Shi kansa kanal yusif saida ya murmusa amma bai bari sun gani ba, gudun kar raini ya fara shiga tsakaninsa da younger brothers ɗinsa, 

   Jin jina kai fawan ya yi ya ce “haba no wonder ! no wonder! thats y naga y’an mata sun fara bin layi, kai ka ga followers ɗinsa a insta da tiktok, ka ce ashe Ak47 ce ke ruɗarsu …..” 

dariya ce ta ci ƙarfinsa ya kasa idasa maganar, haka sauran ma dariya suke yi, ran junaid ba karamin 6aci yayi ba, kiris yake jira ya fara kuka,

   duk wannan firar da suke a kunnan sehrish wadda ke zuzzuba musu abinci a plates da abin sha, sam batasan inda suka dosa ba, 

  Kanal yusif ne ya yi gyaran murya tare da cewa “Is enough ! Stop teasing him, kuna bata wa bro ɗina rai, ” dakatawa yayi da maganar yana kallon junaid wanda ya ci ka ya batse, tuni ruwan hawaye sun kwanta a idonsa, cikin sauri kanal yusif yace “karka kuskura ka bari wannan expensive tears ɗin naka su zuba, kai in banda abunka ae yabonka su kayi, AK47 abun so ce ynx mata sun fi son namiji mai wannan size ɗin, kuma wannan alama ce da ke nuna cewa ƙanin namu ya ƙosa aure yake so,” 

   wata irin dariya ce ta 6alle wa sehrish ita kanta batasan ta sake ta ba, gaba ɗaya suka dago suna kallon ɗan aikin nasu a matsayin shashasha, cikin jin kunya sehrish tasa hannu ta toshe bakin ta tana sunnar da kai kasa, 

  Harara khaleed ya wurga mata tare da cewa “ƙaramin ɗan iska nifa nasan wannan mai aikin namu kwarto ne, ƙurun ɗan duniya ne, rikakken ɗan tasha, in ba haka ba menene abun dariya a nan? ya tamabaya yana hararar ta, ita dai shiru tayi bata ce komai ba, a tare sauran suka ja tsoki,

Har sun soma cin abincin kanal yusif ya lura cewa babu twins a wurin don haka ya ɗago ya kalli tukur tare da cewa “jira kake sai an baka umarnin ka kira twins?wai kai wane irin sullu6iyo ne am just doubting abt u,” 

  Jiki na rawa sehrish ta ce “am sorry sir,”  sannan ta kama hanayr bedroom din nasu, 

 “wai ku baku lura da wani abu ba”? jabeer ya tambaya yana kallonsu, fawan ya ce “me kenan,” jabeer ya ce gaba da cewa “wlh wannan ɗan aikin namu tukur sam ni banga abunsa ba babu alamarsa,” bin shi sukayi da kallo a yayin da suke ƙoƙarin fahimtar me yake so yace musu, 

   Junaida ya ce “which thing are u talking abt”? yayi maganar ne a lokacin da yake ƙoƙarin tura dambun nama a bakinsa, jabeer ya ce “hmm kada ku ce naci ka sa ido amma Allah ku lura da gaban wandonsa sam babu alamar abun namiji a wurin,”  sakin baki su kayi suna kallonsa , kafin fawan ya ce “maganarka gsky wlh, nima najima ina tunanin hakan, cos duk yadda namiji yasa trouser sai ka alamun abun nan amma shi shafe ko dai ba mutun bane”?

  Ya tambaya cikin mamaki, dariya junaid ya yi tare da cewa “may be it is small like atom,” gaba daya suka dara

  Kafin kanal yusif ya dakatar dasu da cewa “shame on u guys, kuna maza , mazan ma sojoji kuna gulma, u have to stop it bana so mai aikin nan ya ji wannan maganar a barta anan, kowa ya mayar da hankalinsa ya ci abincin sa,” 

  A bangaren sehrish kuwa time ɗin da ta isa dakin su twins, gabanta faduwa kawai yake yi gudun abunda zata taras,

tana sa hannu a ƙofar ta 6uɗe, sun mata da kofar a buɗe, sallama ta kwaɗa musu jin ba amsa ya sa ta tura kai, 

   Gabanta ne yayi mugun faɗuwa rass !! tuni zuciyarta ta hau bugawa da ƙarfi, ta gaza believing da abunda idonta ke nuna mata, kwance suke zir haihuwar uwarsu babu kaya ajikinsu, sun harɗe da junansu suna shan jikin junansu , wannan wane irin tashin hankali ne ! 

   dukkan ilahirin jikinta rawa ya ke yi, a tsora ce taja da baya ta juya ta fi ce cikin sauri, wannan fitar da tayi ne ƙarar kofar da ta daka yasa su, dawo wa hayyacinsu suka ɗago a tare suna kallon kofar da ta mayar da kanta ta rufe, alamar wani ya shigo, cikin sauri Jahan ya zame jikinsa daga na Ayaan, 

  shima ayaan ɗin ya tashi zaune cikin wata irin kasala ya ce “meya faru sweetheart wani ya gan mu ko? ya tambaya yana lumshe idanunsa da alama bai gamsu ba, cikin damuwa jahan ya ce “i think so ! mun shiga uku duk laifin ka ne ayaan why u didnt close the door bfr we start doing it,” 

 hararar sa ayaan din yayi ” komai sai ka ce its my faults you’re also a guilty, cos you too why u didnt close it !,” 

  ya tamabaya yana kallon cikin idonsa cike da sha’awarsa,  

      hannu yasa tare da dakatar dashi ya ce” its ok ynx ka tashi mu shiga ciki, mu wanke jikin mu ya 6aci sosai, 

ruko hannunsa yayi kamar mata da miji suka shiga cikin toilet a tare, 

 duk wannan maganar da suka yi akan kunnan sehrish wanda ke zukunne a kopan ɗakin nasu tana kuka ƙasa ƙasa, abunda yasa bata tafi ba saboda tsoran abunda kanal yusif xaice mata, ya zama wajibi ta sanar dasu su fito su halarci teburin cin abincin, 

   cikin kuka take faɗin “ya Allah ka shiryi waɗannan bayin naka ! su gane gaskiya su daina aikata wannan mummunan zunubin da suke yi, ina jin su har cikin raina, ina ji musu tsoran su mutu suna aikata wannan babban zunubin, wa’iyazu billah ! 

   Alamun motsi taji wanda ke nuni da cewa suna kan hanyar fito wa ne, a guje ta tashi ta samu wuri ta 6oye, 

   ruƙe da hannun junansu suka fito, sunyi fess da su, kai ka ce bazasu iya aikata wannan zunubin ba, 

  Lokacin da suka ƙarasa dining ɗin suka ga ƴan uwan nasu duk suna a wurin sai hankalinsu ya kwanta, hakan na nufin ba wanda ya gansu, 

      wata irin soyayya ce mai ƙarfi tsakanin Ayaan da jahaan, ga tsananin sha’awar junansu da suke kamar hauka, kullum cikin saduwa da junansu suke basa gajiya, abun har ya wuce na hankali, su yi a bedroom wani sa’in suyi a toilet, 

   Allah yana rufa musu asiri domin babu wanda yasan suna aikata hakan, sai sehrish ! wata irin rayuwa suke yi a gidan, yasu yasu ba mai shigar ma wani ɗaki, sai fa in wani kwakkwaran dalili ne, 

Lalacewarsu har ta kai ga sun ɗaurawa junansu aure, da kansu ba tare da wani ya sani ba, 

Shi kuma Fawan jarabar bin mata gare sa, duk da matan ne ke binsa, shi kuma yana basu haɗin kai, yayin da irfan da jabeer suke gogaggun ƴan shaye shaye, duk wani abun shaye shaye da kasani to suna dashi, mugayen kwayoyi suke sha ba tare da sanin kowa ba, ga wata ɗabi’ar fita ƙarfe shabiyun dare da suke yi , sai ƙirfan2 suke dawo wa in suka tafi night club ukun nan, fawan jabeer da irfan,

   tun da azmi ta sanar da ita cewa ta tura masu ƙudin, nan fa hankalinta yaƙi kwanciya, burin ta taji ya ake ciki can asibitin, kullum ita ce kamar kusu wurin satar wa junaid waya ko tsoro ba taji,

  Kamar kullum haka yau ma ta saci hanya ta lalla6a taje daukar wayarsa, yana bacci, wyar na ajiye a saman ƙirjinsa, jikin sa na sanye da nightwear, 

  hawa saman gadon tayi cikin sanɗa kamar munafuka, ɗaukar wayar tayi cikin sa’a, sai da tagama duk wannan wahalar ashe ya canza password ɗinsa, yanzu dole sai da fuskar shi sannan wayar zata bude wato face security ya sanya, haka ta zaune dirshen tana saman gadon tana kallonsa, tunani take yi meyasa ya canza security ɗin wayarsa to kodai ya gane ana ɗaukar masa wayarsa ne, a’a bana tunanin haka kawai ra’ayi ya yi ya canza, tae wannan maganar a zuciyarta,

   Lalla6awa tayi ta matsa dai dai face 6insa, ɗaga wayar tayi wadda ke riƙe a right hand ɗinta, ta saita fuskar screen ɗin wayar a fuskarsa, amma taƙi buɗe sai ya rubuta mata not recognized,

ran ta ne ya ba ta cewa tabbas sai idonsa na 6uɗe sannan security ɗin wayar zata 6uɗe, cike da takaici takai hannu zata ajiye masa wayar a ƙirjinsa kamar yadda ya ajiye ta, tana ƙoƙarin lalla6a ta sauka, bata yi wani aune ba taji yayi wani irin ƙwaƙƙwaran juyi ya haɗa da ita duka ya rungume ajikinsa kuma ruƙo bana wasa ba, 😳

Allah kaɗai yasan tashin hankalin da sehrish ta shiga, zuru zuru tayi da ido, hancin ta na shaƙar ƙamshin turarensa, lokaci guda ta shiga cikin yanayi, ganin bata da wata hanyar tashi yasa ido ya raina fata, bin wuyansa tayi da kallo gwanin kyau, ji take kamar ta gartsa masa cizo a wannan lallausar fatar tasa ko ta samu ta tsere,

tashin hankalin da ba’a sa masa rana, ga azmi na jiran ta a kitchen saboda safiya ce akwai aikin haɗa breakfast, da sauran aikace aikace, ga junaid ya maƙale ta a jikinsa ta rasa yadda za’ae ta fita, 

tana cikin wannan tunanin na yadda za’ae ta raba jikinsa da nata, ya ƙarayin wani kwakkwaran juyi, atare suka mirgina ƙiris ya rage su faɗo ƙasa, saboda tsabagen ƙiɗima tuni taji fitsari ya zo mata, komai ya tsaya mata cak, bugun zuciyarsa kawai take saurara, 

Sun ɗau 30 mins a haka, ta ƙura masa ido yayin da shi baisan meke wakana ba, 

Wayarsa ce ta soma ringing da ƙarar gaske, wannan sautin ne ya dirar masa a tsakiyar kunnansa, nan ya soma nuƙu nuƙu buɗe ido,

tsananin tsoro ne suka bayya na a fuskar sehrish, yana ƙoƙarin buɗe idonsa, cikin sauri ta janye hannayensa daga jikin ta, ita kanta batasan ta iya wannan ƙarfin halin ba sai yau, juyi tayi da ƙarfi ta sulale a ƙasan bed ɗin ta  durkushe a ƙasan, hankali a tashe 

kamar mafarki haka junaid ke kallon lamarin, tabbas ya ga gifcin mutun daga jikinsa, amma sai ransa ya basa cewa duk cikin bacci ne abunda ya gani, 

hannunsa ya kai tare da ɗaukar wayar tasa dake ta faman buga ringing, tare da karawa a kunnan sa cikin shagwa6a ya ce “Assalamu alaikum babban yaya na, am angry wit u cos i ave been waiting for your call since yesterday night, ” ya yi maganar tamkar yana a gabansa, 

Sehrish da ke zuƙunne kasa cikin tashin hankali, tabaza kunne tana sauraron wayar da junaid ya ke yi, jin ya ambaci sunan babban yaya yasa ƴan cikin ta ƙadawa, sam tarasa dalilin daya sa in aka ambaci sunan nan take jin faɗuwar gaba,

ganin yayi nisa a wayar tasa ne yasa tayi tunanin ta rarrrafe ta fi ce daga ɗakin, don haka ta soma tafiya a ɗurkeshe a ɗurkushe, cikin sanɗa take rarrafa wa, 

Ko waiwayen bayanta bata yi burin ta ta fice daga ɗakin before ya ankara, junaid kuwa dake maƙale da waya yana zabga wa yayan nasa shagwaba sam bai lura sai da yayi wani kwakkwarn juyi yana faɗin “just come back home i wanna see you serious…” bai ida maganar ba karaf idonsa suka sauka akan ɗan aikin nasu wanda ke tafiya cikin sanɗa yana rarrafawa zai fi ce,

Ƙura ido 👀 junaid yayi yana kallon ikon Allah, acikin ransa yana cewa” lallaima wannan ɗan rainin hankalin wato raini ya fara shiga tsakanin mu, bari in tsara in ga ƙarshen game ɗin, 

sam batasan ya ganta ba,lokacin da ta isa ƙofan ɗakin ta saki wata irin ajiyar zuciya, maimakon ta fice ba tare da ta waiwaya ta kallesa ba, amma ina ranta ne ya bata ɗan juya mana ta kalle sa tun da ta tsira, juyawa tayi a hankali tana sauke ajiyar zuciya, karaf idonsu ya shiga na juna, ganin dagaske ita yake kallo ido cikin ido ya ganta asiri ya tonu, hannu ta shiga tafawa da yake ta kware wurin iya fauzewa sai kawai ta 6a66ake da dariya hhhhhhhh kamar mahaukaciya, 

Tsananin mamaki ne yasa junaid yin kasaƙai yana kallon ikon Allah,

bata dakata da dariyarba cikin salon wayau da dabara ta fice tana tikar dariya, hada janyo masa kopa da rufe wa, 

tana ganin ta fito ta tsagaita da dariyar tare da aza hannunta a saitin zuciyarta tace”wai Allah na tsira” da gudu ta sauka kasa ta wuce kitchen,

     har ynx junaid bai dawo daga duniyar mamakin da ya tafi ba, tunda ya ke a rayuwarsa ba’a ta6a raina masa wayau irin na yau ba, ya ma rasa mai zaiyiwa ɗan aikin nan nasu, wane hukunci zaiyi masa, 

   “Zamu haɗu” ya fada a fili, kafin ya tashi ya shiga cikin toilet, 

  gaban wash basin ya tsaya, yakai hannu ya ɗauko toothbrush ɗinsa, ya matsa maclean a jikinsa, ya shiga goge hakoransa,a hankali yake komai saboda tunanin mai aikin nan nasu daya tsaya masa aransa,

  Bayan ya kammala ya kunna mixer tap ɗin ruwa ya soma zubo wa wanke mouth ɗinsa yayi sannan shima brush ɗin ya wanke sa ya mayar dashi cikin holder dinsa, 

       wanka yayi shaf shaf ya dauro towel a west ɗinsa, ya fito yana matse sauran ruwan dake ɗiɗɗiga a sumar kansa da hand towel, 

a gabn mirror ya tsaya yana kallon zunzurutun kyansa, a nan ne idonsa yakai saman fatar wuyansa, wani dogon gashi ya gani siriri mai tsayin gaske, tsananin mamaki ne ya kamasa, a cikin ransa ya ke faɗin “ynx duk wankan danayi amma wannan gashin bai bar jikina ba kodai har yanzu ban iya wanka bane haba junaid be a big man mana kana abu sai ka ce na ƴara,”

hannunsa yasa a hankali ya tsafko gashin, ya ɗago sa izuwa saitin eyes ɗinsa yana kallo, sai lokacin ya lura cewa tabbas wannan gashin mai tsayi bana sa bane to na wanene !!!! 😱

Sannu da zuwa mlm tukr, acewar azmi wadda ke magana tana kallon sehrish dake shigowa cikin kitchen, ɗan murmushi tayi tare da cewa ……………………

Kin riga da kin gane cewa ni maca ce,” ta faɗi hakan da ƴar shagwaba

Azmi ta ce “Oh kin shirya asirinki ya tonu ko? muddin nakira ki da sunanki na ƴan gayunnan to zasu gane cewa mai aikinsa fa maca ce ba namiji ba, daganan zasu ɗauke shi izuwa barrack ɗinsu na sojoji a acanza masa halitta,” 

azmi tayi maganar ne da zolaya, yayin da tsoro ya bayyana a fuskar sehrish hannu tasa tare da rufe baki alamar ta shiga uku,

dariya azmi tayi tare da cewa” idasa shigowa mana, ina so zaki yanka mun wasu fruits nan zan hada fruit salad ne, ki duba cikin fridge ki dauko kayan marmarin kizo ki fara,” 

karasa wa tayi inda refrigerator ɗin ya ke sai da ta fara daukar bowl ɗin da zata zuba su ciki sannan ta buɗe sa, kaya ne iri iri shaƙe acikinsa, dangin kayan marmari dasu vegitables, ga ɗanyen nama iri iri na dabbobi daban daban, 

Zubo su tayi da yawa ta fara wanko su sannan ta dawo ta aza saman table, ta dauko knife ta shiga gyarasu, yayin da azmi ke ta faman ƴan soye soye,

Jin shirun yayi yawa yasa sehrish cewa” aunty azmi wai inaso in san wanene wannan babban yayan dasu junaid suke yawan faɗansa, wai shine babba a gidan nan ne,”?

da ta ambaci sunan shi sai da azmi ta ɗan girgiza, tajima bata yi mata magana ba, sai da tasamu natsuwa ta kana  face ” idan na fara baki labarinsa to tabbas zamu kwana muna yi, bashi bane babba ba amma shakkarsa da suke ji yasa yazama babba, wani irin mutun ne mai zazzzafan zuciya, bai da sauki in dai akan aikinsa ne, baya ragawa kowa, baya sauraron kowa, yana da matukar karfi tun daga kan surar jikinsa zai tabbatar maki da cewa mugun karfi gare sa, idan yaga Mara gaskiya kuwa idonsa makancewa yake yi, in fara hukuntasa har sai ya ɗanɗani kuɗarsa, ko ni agabana kwanakin baya daya zo sai da ya kashe mutun 4 acikin gidan nan, ko kai ɗan ubanwaye kayi laifi, haka zaisa a kawo masa kai har cikin gidan nan ya yanke ma hukunci kuma ba uban da ya isa ya tanka, to wama ya isa? Jikan soja,ɗan shugaban sojoji mahaifiyarsa soja, yayyensa sojoji ƙannensa sojoji, shima kuma soja a bangaren kyau kuwa sai dai mu ce Tabarakallahu ahsanul khaliqin, wlh tunda nake a duniya ban taba ganin mutun mai zazzafan kyau irin nasa ba! irin kyan da sai Allah kawai ke tsare mutun saboda bakin mutane da masu kawo masa hari, wani irin miskilin mutun ne ke zan iya ce miki akwai lokacin daya jera kwana uku baiwa kowa magana ba hatta abbansu sai dai kawai yayi nuni da hannunsa ayi masa abu kaza, Isarsa da jin kansa ga izza dayake takama da abun sai addu’a, 

Jinjin kai sehrish tayi kafin ta ce “amma meyasa shi bazai dawo gida bane ya zauna cikin ƴan uwansa,” 

Azmi tace “ya za’ae ya dawo nan bayan a can us ya taso tun yana yaro  a can kuma yake aikinsa a matsayin surgeon general,” maimata sunan sehrish tayi “Surgeon general meke nan,” murmushi azmi tayi saboda ta lura sehrish so take su ƙare firar tasu akan babban yaya , 

“Matsayinsa ne na aiki na faɗa miki bari nayi miki a ware yadda zaki fahimta, he’s a professional surgeon doctor kuma general ne na sojoji,”

Sakin baki sehrish tayi don mamaki wannan matsayi har haka ! surgeon general, tabɗijan can ta ambata tana jinjinawa lamarin ashe mutun inya karanci military surgery zai iya kuma zama general ɗin sojoji lallai iko sai ubangiji matsayi biyu,

murmushi tasaki Cikin zumuɗi ta ce “zanso naganshi ga kyau ga class ga matsayi biyu gsky ba ƙaramin jarumi bane,” a tunanin ta acikin zuciya tayi maganar sai ji tayi azmi tace”Insha Allah muna sa ran zuwansa nan kusa, amma kafin yazo ina tunanin Abbansu zai riga sa dawo wa domin shi ma yayi tafiya zuwa Qasar chaina, wani muhimmin taro ne yakaisu nasu na sojoji,” 

wani irin daɗi ne ya rufe sehrish, saboda ta ƙosa tagansa, acikin zuciyarta tace “naso naga ranar da zanyi tozali dashi nagadai wanene wannan babban yayan wayyo daɗi….

Muryar azmi ce ta tsaida ta daga tunanin “meyasa baki tambaye ni sauran matansa da baki taba ganinsu ba sai babban yaya,”? tayi tambayar tare da juyowa tana kallonta,

Sukuyar da kai sehrish tayi tace “saboda tun ranar da hajjaju ta kawo ni gidan nan da sunan sa na fara cin karo,shiyasa na kosa nasan wanene shi,” 

Hmmmm azmi tace ” akwai sauran zafafan ma irin su Captain duk wani matsayi da kika sani na soja agidan nan akwaishi, mutum goma ne sauran matasan da baki sani ba, ynx bamu da lokaci amma duk lokacin dana samu natsuwa sosai, zamu shiga garden ko muje swimming pool area akwai kujeru na shan iska awurin saina zauna na baki labarin gidan Abban sojoji,” 

Cikin jin daɗi sehrish ta ce “zanji daɗin hakan sosai kinga saina san ta yadda zan zauna da kowa,” 

Shiru su ka ɗanyi na wani lokaci kowa naci gaba da aikinsa, can da jimawa sehrish ta sake cewa “last question about babban yaya aunty azmi,” dariya azmi tayi tace “ina sauraron ki,” sehrish ta ce “wai bayan babban yaya menene sunansa ne na gaskiya,”?

“Zan faɗa maki amma da sharaɗi daga wannan tambayar mun rufe babin babban yaya,” acewar azmi a yayin da take sauke kasko daga saman gas, 

“Na yarda toh,” sehrish ta ce tana ƴar dariya, azmi tace “Sunan shi……” shiru tayi ba ta ida ba, 

Sehrish data ƙosa ta ƙagara taji sunan cikin zumuɗi tace “pls aunty azmi ki ƙarasa mana,” 

murmushi azmi tayi dama ita take jira don ta ga yadda take son taji sunan, 

gyaran murya azmi tayi sannan tace “Sunan shi RAFAYET!,” 💋

kamar yadda sunan ya diro mata a kunnanta haka zuciyarta ma ta bata wani sauti na musamman, cikin sanyi murya ta maimaita sunan “RAFAYET suna mai daɗin gaske,” 

daga nan firar tasu nasamata aya.

suka shiga shirya breakfast ɗin sehrish ce ke kaiwa kamar kullum tana jerawa a dining, har lokacin maimaita sunan take acikin zuciyarta “rafayet,rafayet, tarasa dalilin hakan (dama in mutun ya kasance ƙaddarar ka hakan ce take faruwa) 😉

Sun kammala shirya komai tsaf, one by one suka soma fitowa, duk sun shirya tsaf cikin kakinsu, banda junaid wanda jallabiya ce milk colour a jikinsa, abun ba’a magana, 

Ynx sehrish ta daina bin ɗakinsu, tana tashe su, saboda sunce basa buƙatan hakan, taji dadin wannan saukin da ta samu, mutun ɗaya ne wani sa’in dole sai taje, wato junaid don nauyin bacci gare sa, bai cika tashi dakansa ba sai an tashe shi, gyaran ɗakunan su kawai ke kaita, sai kuma wani abun inya taso, 

Kowa yasamu wuri ya zauna ana jefa wa juna kallo, kafin su soma gaishe da junansu cikin so da ƙauna, 

Kowanne sai ya faɗi abunda yake so ya ci sannan saita zaro plate ta zuba masa, haka abun ke tafiya,

cikin natsuwa suke cin abincin nasu, fawan ne yayi gyaran murya tare da cewa “Uhm AK47 yau ba magana,”?

tuntsire wa suka yi da dariya su duka hatta shi kansa sai da ya yi murmushi, Ayaan yace “she’s eating food thats why,” nan ma wata dariyar ta tashi, ɗagowa jahan yayi ya saci kallon Ayaan tare da kashe mishi ido, dama suna facing ɗin juna, murmushi ayaan ya yi, 

Jabeer daya lura da su ya ce “toh ƴan iska kashe kashen idon me naga ana yi ne,” dariya su kayi su biyun, khaleed yace “there’s something behind they’re trying to hide it,” 

ganin za’ayi babu shi yasa shi tsoma baki “abun sirri ne atsakaninsu,” acewar Irfan wanda ke ƙoƙarin ajiye spoon ɗin dake hannunsa saman plate ɗin gabansa, 

junaid ya ce “what ever it is, idan kero na yawo zabo na yawo wataran za’a haɗu,” cikin sauri Ayaan yace “ubanka mai bakin ja6a insha Allah baza’a taba haɗuwa ba,” 

wannan maganar tasa su fashewa da dariya, ita kanta sehrish dake tsaye akansu daurewa kawai take yi amma bakinta na ƙumshe da dariya ,

kanal yusif dai baice komai ba yau baya jin ƴ’an maganar sai dai in sunyi shiriritar tasu ya ɗan murmusa 😊

kallonsa khaleed yayi ganin yau yaƙi cewa komai don haka ya ɗanyi gyaran murya cikin zolaya ya ce “su yaya yusif ciki yana ta ɗauka ko magana babu,” 

ɗagowa yayi tare da ɗan jefamar harara cikin sanyayyiyar muryarnan tasa yace”bana son shashanci fa, kar na sake jin wani yayi magana acikin ku” 

Shiru su kayi tsit kowa ya natsu yana zubawa cikinsa, 

   Karar faɗuwar cokalin junaid ne yasa su dagowa suka kallesa, cikin sauri sehrish ta duka domin ta ɗauko masa, 

   Zuƙunna wa tayi kasan table ɗin takai hannu zata ɗauko cokalin kenan !

Idonunta suka hango mata abunda su Twins ke yi, dayake suna facing ɗin juna shida jahaan, ƙafafunsu na maƙale dana juna sun harɗe su , 

  girgiza kai tayi aranta tace”jaraba” ɗagowa tayi ta miƙa masa cokalin hararar ta yayi tare da cewa”change another spoon for me i can’t use this one,” 

mamaki ne ya kamata ganin inda cokalin ya faɗa a tsaftace yake, don ita ji take ko abinci za’a zuba mata a ƙasan wurin to tabbas zata sa harshe taci don ta shaida tsaftar wurin, 

giɗa kai kawai tayi, ta ɗauko wani a inda suke jere ta miƙa masa, yasa hannu ya karba, 

 Sam ta gaza tsaida idanunta a kan wanda zata kalla cikinsu, kowa ta kalla kyau, shi dai kanal yusif wani irin sanyin kyau ne dashi ba fari bane tass wankan tarwaɗa ne, shi kuma khaleed tamkar ɗan kasar Ethiopia, launin fatarsa yayi irin choculate ɗin nan, da jabeer da irfan duk kalar fatarsu daya da yusif,

Amma in akazo wurin junaid, Ayaan da jahan da fawan farare ne tass kamar ka ta6a jini ya fito, natural white ne a tattare da junaid su twins kuma sunyi jawur, fawan kuma bai kaisu haske ba nasa mai yellow ne, dukkansu masha Allah suna da dogon hanci, ga kyawawan idanu ga kuma launin lips ɗinsu ga dimples ga kwantacciyar suma, duka dai 😇

  Idonta yafi tsayawa akan junaid kallonsa take amma zahiri tunanin wayarsa take yi, har ranta bata ji daɗi daya canza security code ɗinsa ba, yanzu yaya zatayi ta kira su tsohuwa ?

 ɗaya bayan ɗaya suka fara tashi kowa ya fi ce, wato wata irin motace jibgegiya ta sojoji idan suka hau ta, kowa sai yasan cewa ƴan gidan Abban sojoji ne suka fito Saboda da wata irin jiniya suke janta,

 Sehrish

gyara wurin ta shiga yi, ta tattara komai da sukayi amfani dashi ta wuce dasu kitchen, sai da ta wawwanke komai tsaf ta mayar dasu cikin kitchen shelves,

 Sannan ta koma tana gyaggara dining table area ɗin, ta tsaftace wurin sosai,

   komawa tayi tana gyara babban falourn, ƴan goge-goge ƴan kakkabe kakkabe, da sauransu nan take wurin yayi tsaf, bakomai yake ƙara burgeta ba face komai nasu zaka ga launin sojoji ne (army colour) hatta teburin cin abincin da chairs ɗin dake zagaye dashi duk kafafunsu launin army ne, daga saman teble ɗin ne kawai glass,

Hatta 2 sets na royal sofa ɗin dake a katafaren palourn suma army colour ne, haka sofa tables ɗin duk launi ɗaya, da sauran abubuwan, lallai wannan yaci ka gidan Abban sojoji.

Ita kaɗai take ta faman wannan aika ce aikacen saboda azmi bata jin daɗi headache ke damunta dama ta sanar da ita, zata sha magani ta ɗan kwanta,

tunanin ta ynx yadda za ta goge waɗannan long stairs ɗin kullum wahalar su take ji, bin wurin tayi da kallo, wasu irin tagwayen bene ne masu double starcase ɗin nan, a zagaye suke, left & right , in kabi na hannun haggun zaka iya zagayo wa ka sauko ta hannun daman ka, a tsakanin su akwai space, a space ɗin nan zaka iya shiga ta tsakankanin benayen ka miƙi hanya anan zai kai ka bedrooms ɗin su Ayaan waɗan da ke a down kenan,

In kuma ka hau saman ɗaya daga cikin stairs ɗin zai kai ka , upstair in da ke akwai hanyoyin da zasu sada ka da jerin ɗakunansu junaid, a kalla bedrooms ɗin dake a gidan totally da wanda ke akwai mutane da wanda babu zasu kai 30, 

  Falo kuwa akwai manyan manya sunkai 9, kuma kowanne an ƙawata shi da attractive & expensive furnitures, 

Amma babban cikinsu shine wanda kana shigowa ciki zaka fara cin karo dashi, main palour ɗinsu kenan 

Ni nasan duk yadda zan kwatanta haɗuwar gidan nan ba kowa bane zai gane ba saini dana shirya kuma na gabatar 

don hka just imagine it like the one u used to see in your dream, 🙅

  tasha wahala sosai wurin gyara gyatan ɗakunansu don ma ba ɗauda kawai iya bedsheet ne zaka samu an yamutsa, sai kaya in an cire kaga anyi wurgi dasu ƙasa, wani ma don iyayi kayan nasa a saman mirror ta same su,

 Bayan ta kammala dukan aiyukan, gajiya ta saukar mata bagatatan, ɗaki ta koma cike da jin ƙyanƙyamin jikinta, 

Maballin rigar ta ciccire ta zame ta duka ta ajiye ƙasa, cire wandon tayi shima, sannan tasa hannu ta cire naɗin mayafin kanta, kafin tasa hannu ta 6an6are abunda take matse ƙirjinta dashi, tana ciresa taji wata irin iska na shigarta, gaba ɗaya boobs ɗinta a mugun taƙure suke, ba abunda ya same su, amma ƙan nipples ɗinta ba ƙaramin hurting ɗinta ya ke ba,  

   Ita kanta tausayin kanta taje ji, yadda ƙiri~ƙiri ta canza kanta daga mace zuwa namiji, duk tabi ta takure halittarta, hannu tasa ta cire ɗan gashin bakin da take mannawa, ɗago dashi tayi tana kallonsa tana matuƙar son ainihin halittarta ta mace, 

   gaban dressing mirror taje ta ajiye shi, toilet ta shiga tasakarwa ƙanta shower, ta haɗa hada hairs ɗinta ta wanke saboda ya fara tashi, gashi tana buƙatar tayi shaving, batasan ya zata yi, sauƙin bata da gashin armpit amma can under ɗinta kuwa akwai sosai,

   ta gama yanke shawarar zata ɗebo shaving cream ɗin junaid taga hada set na shaver gare sa, dama shine marainin wayan ta, 

ganin cewa babu kowa gidan daga ita sai azmi wadda ke can kwance tana sharar bacci, hakan yasa ta yanke shawarar cewa yau zata sakata ta wala, don haka ta shirya tsaf cikin riga t-shirt white colour da black trouser, sai da ta tabbatar ta matse ƙirjinta kamar yadda ta saba, sannan ta aza gashin bakin da take sawa, lalubawa tayi cikin jakar kayanta dayake ba duka kayan ta zuba cikin wardrobe ɗinba, anan tasamu hular da hajjaju ta siya mata, irin wannan hular da ake kira da tashi da kwakwa,

  sai da ta tabbatar ta naɗe gashinta cikin ta cunkushe ta matse shi sannan ta kifa hular a saman kanta, sai gashi ta fito fes kamar ɗan saurayi, 

Ita kanta ba ƙaramin daɗin jikinta taji ba, fitowa tayi ƙafarta sanye da takalmi roba na maza, 

Kama hanyar ɗakin junaid tayi, cikin sauri take tattaka matattakalar stair ɗin, a gajiye ta iso ɗakin tura sa tayi ta buɗe ta shige, 

Komai tsaf a tsanake dama ita ce tayi gyaransa, cikin jin daɗi ta wuce cikin toilet ɗinsa, agaban bathroom cabinet ta tsaya, anan taga jerin tsaddun mayukansa, duk wani abu na gyaran jiki akwashi kai kace na macene ba na namiji ba, 

Tsawa tayi tana tunanin me yakamata ta ɗauka, tunani ta shiga yi ” kodai kawai na tsaya anan nayi shaving ɗin inyaso in na gama in tsaftace masa wurin yadda bazai gane ba sai in samu in lalla6a in fi ce, saboda in na ɗaukar masa zai iya gane wa, ƙarshe ya kamani a matsayin 6arauniya, ya zanyi ni,” ta fada tana ƙarewa wurin kallo

hannu tasa ta ɗauko roban shaving cream ɗin ganin yana da kusan guda uku yasa ta yanke shawarar ta ɗauki ɗaya bazai gane ba, sai ta haɗa da shaver guda biyu, tun da taga yana dasu dayawa a cikin ledarsu,

ruƙo su tayi a hannun ta saboda haɗama irin tamu ta bil’adama zuciyarta ta raya mata cewa mai zai hana ki haɗa da shampoo saboda wanke kai ga kuma sabulai masu ƙamshi sannan kina buƙatar turare na fesawa a jiki, 

Murmushi tasaki jin wannan zancen na zuciyarta, 

A fili tace “abun sai na samo wurin da zan zuba su baxan iya ɗauka ba a hannu na, 

Fitowa daga bathroom ɗin tayi ta shiga neman wurin da zata sa kayan, a nan tasamu wata shopping bag, ƴar jakar nan ta siyayya, komai cikin sauƙi take ganin sa, 

Komawa cikin toilet ɗin tayi ta shiga jidar kaya tana zurawa aciki, Sam bata tunanin cewa sata take yi ita ina gani take kamar ta zama ƴar gida in ta ɗauka halal ne.

A gajiye ya shigo cikin gidan jikinsa sanye da kayan kwallo riga da gajeran wando, yellow colour ba ƙaramin kyau sukayi masa ba, hannunsa riƙe da kwallo yana ɗan bugata a hannunsa, kafin ya rungumo ta a ƙirjinsa, cikin sauri ya haye upstair yana isa kofan ɗakinsa, yasa ƙafarsa ya harba door ɗin ta buɗe,

Saboda tsananin firgice sai da tasaki kayan dake rungume a ƙirjinta, zo kaga tashin hankali, daga cikin toilet ɗin take jin shigowarsa, tuni ido ido ya raina fata musamman da taji tabbas shine ɗin dai ya shigo, ana dara ga dare yayi 🙉

“Nashiga ukuna junaid ya dawo tafaru ta ƙare ” ta faɗa ido luhu-luhu, tuni jikinta ya fara rawa, matsawa tayi jikin kofan tana leƙansa,

samun shi tayi yana cire takalmansa, ganin he’s trying to takeoff his clothes, 

Hakan yasa ta fargaba, koma wa tayi ciki tasa tafin hannunta tana bugun goshin ta, tuni ƴan matan hawaye sun bayyana, sintiri hawayen suka soma yi suna sauka a kumatunta, tashin hankalinta kada junaid ya ce zai cire kayansa saboda shi baisan da human being aciki ba, 

Kuma tana da tabbacin cewa yadda ya dawo a gajiyen nan, wanka zai buƙaci ya fara yi, cikin tsananin tsoro ta furta “ae shikenan waman ƙadarallahu hakka ƙadrihi,”

wayyo Allah na there’s no way out, ya Allah ka kawo min mafita, ni nasan alhakin satar dana zo yi masa ne Allah ya kamani, hannu ta ɗaga sama tana addu’a tana cewa Ya Allah bazan ƙara ba ya Allah kafi kowa sanin cewa ni ba 6arauniya bace wlh sharrin shaɗain ne da kuma zuciya 😥

Ashhhh ! a wani irin yanayi yayi wannan sautin yayin da yake cire rigarsa da alama something is hurting him may be he gets wound, 

Wurgi yayi da rigar saman bedmatress ɗinsa, hannu yasa yana shafa gefen cikinsa wurin yayi jawur abunka da kalar madara, ciwo ne wurin amma is not much, 

A gefen gadon ya zauna yana sauke ajiyar zuciya,

Leƙo shi sehrish ta ƙarayi ganin sa zaune yasa taji sanyi aranta, zuba mishi na mazurin ta tayi tana kallonsa

A wani irin yanayi yake lumshe kyawawan idanuwnsa, teeth ɗinsa ya ɗansa yayi biting red lips ɗinsa, kai ka ce wanda ke cikin shauƙi ne,

hakan ba ƙaramin feelings ya sa sehrish ba, ita da ke leƙensa ta cikin toilet, 

Mayar da kanta ciki tayi tana tunanin dabarar da zata yi masa ta samu ta fice, ranta ne ya bata cewa kawai ta fauze tayi kamar wanke toilet ɗin take yi tunda ita house maid ce tana da damar shiga ko’ina, 

Murmushi tasaki tuna wannan dabarar, acikin zuciyarta ta ce ashe hakanan nake wahalar da kaina gaskiya kan kifi ne dani, bana gane komai cikin sauƙi 

wurga idonta rayi kan kayan da ta zubar, ji tayi bazata iya barin shaving cream ɗin nan ba, koda zata mayar masa da sauran, matsawa tayi wurinsu da ta zubar da kayan, ta zuƙunna ta kwashi robar shaving cream ɗin da shaver guda ɗaya,

Cikin aljihunan wandon jikinta ta sanya su, amma robar tayi ɗan zumbuɗi tayi tayi amma taƙi idasa shiga haka tabarta, 

Sauran ta tattara su ta mayar masa a cikin bathroom cabinet ɗin, 

cikin sanɗa ta tura kofan ta fara zuwa kai tana leƙansa, ganin idonsa rufe ya tabbatar mata da cewa junaid fa bacci yayi awon gaba dashi don haka ta soma tafiya cikin sanɗa maimakon ta wuce ta fice cikin salama, 

Amma hango jerin turarurrukansa da tayi agaban mirror yasa ta tsayawa, koma wa tayi a hankali ta cafko kwalbar turare ɗaya, ƙiris ya rage kwalbar ta faɗi kasa saboda ta kusa ta zame daga hannunta, 

Wani irin bugun zuciya taji amma ganin ta same ta raɗau a hannunta ysa ta sauke ajiyar zuciya, 

“na tsira” ta faɗa alokacin da ta samu ta fice cikin sa’a ,

Sam sehrish batayi tunanin cewa yaya Qarfin ƙamshin turaren yake ajikin mutun ba ! Kunsan turaren maza da ƙamshi, 

cikin jin daɗi ta wuce bedroom ɗinta, jera su tayi agaban mirror ɗinsa, ran ta fal da farin ciki ganin itama yau ta fara jera abu a gaban mirror, 

junaid

Bacci yayi na ɗan wani lokacin sai wuraren asr prayer ya farka, ƙarar shigowar message a wayarsa ne ya tayar da shi, a ɗan firgice ya tashi hannu yasa tare da shafa face ɗinsa yana sauke ajiyr zuciya, 

 Idonsa yakai kan well clock ɗin dake manne, hadaddiyar gaske ƙarfe 3:59 dai dai time haryaso ya goce masa, 

  Cikin kasala ya tashi kamar wanda ke shirin yin kuka, faɗawa cikin toilet yayi ya jagwalgwala wanka ya fito, 

  Closet ɗinsa ya bude riga da wando ya dauko, t-shirt ɗin ja wandon black colour, 

Hannu ya kai ya dauki wayarsa dake gefen fillow ɗinsa, buɗe wayar ya yi tare da karawa a fuskarsa nan take security ɗin wayar ya buɗe, 

   buɗewa yayi ya fito daga room nasa, a natse yake tafiya yana daddana wayarsa message ɗin ya buɗe ya soma karantawa kamar haka

  “Sister kwana biyu naji baki kira kin tambayi ya ya jikin mu ba, anyi mana aiki cikin nasara, naji sauƙi sosai husanna ma taji sauƙi sai dai hanyarzu akwai sauran mentel illness akanta, sunanki kawai take kira sehrish sehrish dan Allah ki kira mu muji voice ɗinki,”

  tsayawa ya yi cike da tsananin mamakin ganin wannan saƙon a wayarsa a fili yace wacece kuma sehrish da husanna ! A wayata kuma !! me hakan yake nufi, wani namin amfani da wayata ne shin wai ma wanene wannan sehrish ɗin !!! 

   Kansa ya gama ɗaure wa, a hankalin ya idasa saukowa daga saman stair ɗin, ransa ne ya basa cewa kawai wasu ne sukayi kuskuren hada numbarsa, don haka ya share lamarin da cewa in ya samu lokaci zai kira number ɗin ya sanar dasu cewa its a wrong number, tunda yaji maganar rashin lafiya ce tana da mahimmanci kwara su son cewa basu sa number dai dai ba. 😳

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Please Share and drop your comments

•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•

Back to top button