Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 2 Hot Romantic Hausa Novel

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

                   By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

Page 5,6,7,8,9&10

Jin wannan bayanin daga bakin hajajju yasa jikin Sehrish yin sanyi , bata ce mata komai ba sai ma ta ci gaba da wasa da yatsun hannunta. Ci gaba da magana hajajju tayi “abunda za’ae tunda dai naga sisters din naki kuma munyi magana da gwaggo da take kula daku , ynx ki koma ki ci gaba da kula dasu saboda suna bukatarki kafin Allah yasa asamu aikin ,” 

Kamar an dasa ta haka tazauna idonta suka ciko da kwalla, kiris take jira ta fashe da kuka , dama bata jima da gama wancan kukan ba  

Wayar dake hannun hajajju ce ta soma ringing , picking tayi tare da karawa a kunnan ta tana fadin ” Manyan manyan gari ! Abban sojoji ashe kana nan ba’a neman mu , koda yake dama ku hamshakan masu kudinnan ganin ku sai an cike file.”

Natsuwa sehrish tayi tana sauraranta , ta lura da yadda hajjaju ke washe baki da alama koma wanene take wayan dashi Babban mutum ne ,

tuna damuwar da take ciki yasa ta daina sauraron wayar tasu ta shiga tunani kala kala a cikin zuciyarta , har hajjajun ta kammala wayar bata sani ba sai da taji tace “Ga samu ga rashi !!” dagowa tayi da idonta tayi tana kallon , hannu hajjaju tasa ta dafe kanta alamar takaici.

Sehrish tace “Hajiya meya faru?” Hajajju tace “Aiki ya samu mai tsoka , jin hka yasa sehrish ta soma murmushi “amma sai dai kash Namiji suke so mai aiki ba mace ce ba !” lokacin da hajajju ta idasa maganar tuni sehrish ta gumtse fuska hankalinta ya tashi.

Hajjaju ta ci gaba da cewa “ina tayaki bakin ciki gsky, sbd kinga mutumin nan daya kira ni ba karamin mai arziki bane , cos they can pay u 50k as your salary after that zasu dauki dukkan responsibilities din ! Ci  da shan ki wurin kwana lafiyayye sannan har school zasu iya saka ki ga sutura ya kike gani “?

Takaici ya hana tace komai ga samu ga rashi , ji take kamar ta cire takalmanta ta watsa da gudu saman titi kota rage radadin da take ji a zuciyanta  , 

“Sehrish kinyi shiru baki ce komai ba “? ta jima ba tare da ta ce wani abu ba sai da tayi zurfin tunani kafin tace “ZanJe ! Zan yi aikin a matsayin NAMIJIN akan y’an uwana babu abunda bazan iya yi ba don nayi basaja a matsayin namiji wannan abune mai sauki a wurina ,” 

In serious matter take mgnan ba tare da jin wani dar a zciyarta ba dagaske take dai , murmushi hajjaju tasaki don ba karamin burgeta tayi ba saboda tana da confidence akan komai da take so , ” hmmm sehrish kenan how can u change ur creator frm a girl to a boy i dont think u can act like a male zasu gane ki ne , ” 

Matsawa tayi kusa da hajiyar tare da rike kafarta tace “Don Allah hajiya ki taimake ni wlh zan iya , indai za’a samu makeup artist din da zai tsara ni ya mayar dani kamar namiji this is a simple thing , kawai amincewarki nake bukata,” 

hannu hajjaju tasa ta cirewa Sehrish hannunta data rike mata leg dinta dashi sannan tace “Babbar magana ! tun da nake bantaba yin wannan kasadar ba , natura house maid mace a matsayin namiji , sannan wannan mutumin da kika ji ina magana akan sa wato Abban Sojoji , y’ay’ansa maza goma sha takwas kuma dukkansu sojoji ne masu rike da manyan mukamai , dalilin dayasa yace namiji suke so a matsayin d’an aiki saboda ba yadda za’ai mace ta iya , bai ma dace ba , balle ma yaransa da kwata kwata basa da sauki , zafin rai ga ji da isa , ” 

Kamar zata yi kuka ji take in har hajajju bata amince mata ba zata iya rasa ranta , cikin kasalalliyar murya tace “Hajiya ki amince mun kawai ae ni nace zan iya wlh idan baki amince ba shinkafar bera zanci kawai na mutu kowa ya huta don bazansu naga mutuwar y’an uwana ba , ”  zaro ido hajajju tayi jin ta anbaci zata je taci shinkafr bera , kuma dagaske take ba alamar wasa a mgnrta , 

ruko hannunta tayi saboda harta mike zumbur zata figi hanya , “Meya yi zafi haka dawo ki zauna kinji , ni bazanso nayi sanadiyar mutuwar wannan innocent face din ba ,” komawa tayi ta zauna tana sauke ajiyar zuciya , 

Shiru suka yi na wani lokaci daga ita har hajajju , jin shirun yayi yawa yasa tace “Hajiya baki ce komai ba am so eargerly to hear frm u ,”  ta karasa maganan tana kallon ta , 

Wan nan shirun da hajajju tayi sake sake takeyi a cikin zuciyarta “taya zan kai yarinyar nan gidan soldiers a matsayin namiji ! duk ranar da asiri mun  ya tonu daga ni har ita kashin mu ya bushe ,  maganar da sehrish tayi ce ta dawo da ita ,  ” Sehrish i dont know what to do am just comfused ina tsoron hakan fa ,” 

“Nima ina goyon bayan yarinyar nan” larai ce tayi maganar shigowarta kenan taji suna tattauna wa , bin ta su kayi da kallo , wuri ta samu ta zauna kafin taci gaba da magana “Wurin samun biyan bukata rai ba abakin komai ya ke ba , tun da har tace zata iya kawai ki amince mata ! saboda ni na taba kallon wani korean film irin haka actress din ciki ta yi shigar namiji ba tare da wani ya gane ta ba kuma tacimma nasara ,”  jinjina kai hajajju tayi tare da watsa hannayen ta tace “Shikenan Finally i agree tunda har larai ta Jefa miki kuri’a kun rinjaye ni ,” dariya sukayi su duka ba karamin dadi sehrish taji ba , ynx hajajju ta yarje mata sauran shirin yarda abun zai kasance , 

Mayar da idon ta kan larai tayi tace “To ynx ta ina zamu fara “? Larai tace “ae magana ta kare kawai mu da muke da Professional makeup artist a hannu ko kin manta da Mariiiya ? murmushi hajajju tasaki tare da cewa ” ae Mareeya karshe ce ! Indai wurin canzawa mutun kamanni ne insha Allah gobe zan yi inviting din ta kuma a gobe za’a kammala komai don ya ce mun Jibi suke son mai aikin ta je ,” 

Har larai ta bude baki zatayi magana ta jiyo muryar yaran nan dake cikin Kitchen wadanda take koyama aiki , suna kokoyi muryar d’aya daga cikinsu taji tana cewa “Aunty larai gatanan xata wanke gas cooker da ruwa ,” da sauri ta mike ta nufi hanyar kitchen din tana cewa “Allah ya wadaran naka ya lalace har waning nayi muku kada ku taba komai amma saboda kan kifi gare ku baku gane komai salon kujama mutane ko !?

Hajajju tace “ke ma da laifinki akan me zaki baro min su a kitchen salon suyi mun barna ,”  mayar da idon ta tayi kan Sehrish “ki je ki huta time din sallah ma yayi nima bari na tashi ,”  

Ta shi tayi ta shiga ciki , wanka tayi ta dauro alwala , ta fito ta shimfida prayer mat tayi sallah , kamar yarda ta sama kullum sai ta daga hannayenta tayi sama da 30mins tana rokon Allah cikin harshen larabci take jero addu’oin ta da bukatanta da damuwarta tana neman Allah ya yaye mata su , 

Bayan tagama ta tube hijabin ta ajiye , sannan ta hau saman bed ta kwanta dama jiya bata samu isasshen bacci ba , don haka lokaci guda bacci ya kwashe ta , tana cikin bacci y’an matan nan suka shigo , sai faman fadin wash Allah suke , koda sukayi arba da ita kwance ta baje gashi ta cire hijabin kan ba head tie, nan fa suka fara santin gashin kanta , ita dae bata son meke wakana ba tadai ji sama sama ana ja mata gashin kai , 

Zama sukayi kamar sun sami television sukai ta kallonta , ba karamin lalata sukayi ma kanta ba duk sun cukuikuye mata gashi yar kalaban nan sun warware mata ita , sun mai da karamar mahaukaciya ,

Nauyin bacci ne ya hana ta farka amma tabbas taji ana shafa mata kai kasa kasa ,

Sai da ana kiran sallan isha sannan ta farka , mika tayi tare da yin hamma , time din sun fita daga cikin bedroom zuciya sauko da legs dinta tayi kasan tiles din tana sauke ajiyar zuciya , kafin ta mike ta shiga toilet , tana cikin yin alwala tayi shafuwan kai ta shafo gashin kan ta mamaki ne ya kamata jin ba kitson dake kanta da sauri ta idasa alwalar ta je gaban mirror ita kanta sai da ta firgita da ganin yadda suka susuce mata gashinta , amma ba wannan bace damuwarta , zullumin kada husanna ta mutu da kuma aikin da zata fara ,

Karanta Littafin>>> Matar Hariji Page 1-10 Hausa Novel


Zama taci gaba da yi a bedroom din , tana tunene tunane , ga yunwa tana ji amma takasa fita ta nema , 

Turo kofan sukayi suka shigo hannunsu dauke da tray abincin aka zuba musu shinkafa da miya ne sun cinye sun rage mata d’an kadan, ajiye mata sukayi suna dariya suka fice , abunda basu sani ba ita kallon Shashashu take masu ,

Bin a bincin tayi da kallon ba don tana jin yunwa ba da bazata ci Ba don sun jagula shi, haka ta zauna ta dinga turawa a baki kamar zatayi kuka , har dare yayi tana zullum abu daya kuma dashi ta kwana,

In the morning

Around 10:30am makeup artist dinan ta iso gidan a time din duk sun hallara a falon hajjaju , bayan sun gama gaisawa , ma’reea ta bukaci ganin Sehrish , kwala mata kira hajajju tayi fitow tayi da sauri ta iso inda suke , bin ta da kallo mareeya tayi frm head to toe , sannan tace “Wannan ae mai sauki ne , naga tana da tsayi jiki ne dai babu sosai , abunda za’ae kayan maza za’a samo riga da wando oversize saboda su kara mata girma , sannan wadannan abubuwan , tayi magana tana nuna kirjinta da hannunta ” dole a matse su don naga suna da girma ssae tubarkalla , ” cikin jin kunya rishi ta dukar da kanta kasa ,  murmushi larai da hajajju sukayi , su kuwa y’an matan nan dake baje a kasan carpet dama  basu da burki washe baki suka shiga yi wato anzo dai dai inda suke so ,  

Hajajju tace “ynx me za’a sa a yi tighting dinsu “? Ma’reeya tace “mai sauki ne akwai wani abu da muke amfani dashi na matse tumbi shima zai iya yi ,”  hankalin rishi ba karamin tashi yayi ba har bata son lokacin da tayi subul da baka ba tace “in suka bace fa ya zanyi ,”? gaba dayansu suka kwashe da dariya mareeya tace “wato kada su bace a rasa nayiwa miji gayu ko ,” cikin jin kunya ta dukar da kai ,  larai tace ” dagaskiyar ta fa nono ae yana daya dagacin abunda ke kayatarda maza in suka bace ae ba magana ,”   ta karasa magana tana dariya , duk kunya ta gama kamata,

Ma’reeya ta ci gaba da magana “Sannan naga kamar tana da tsayin gashi ko,”? hajajju tace “Sehrish cire hijabin mana tagani , hannu tasa ta cire hijabin ta rungume a kirjinta ,

Hada baki sukayi wurin cewa “Tubarkalla masha Allah ,” ma’reeya tace ” yarinyar kamar balarabiya wurin tsawan gashi, gsky ni kishi nake da wannan gashin naki don haka dama dole indai zakiyi acting a matsayin namiji sai an datse miki shi ya koma guntu kamar nawa dai”,  nan fa hankalin ta ya tashi saboda tana bala’en son gashin nan nata , kamar zatayi kuka tace “don Allah hajajju karki bari ayimun aski ni inason gashi na ,” takarasa maganar tana kallon hajjaju , 

Murmushi hajajju tayi tace ” Sehrish ba Aski zata miki ba rage miki shi za’ae , ke da zaki neman kudi wake ta wani gashi , ” 

Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta , larai tace “Gsky yarinyar nan da ace a matsayin mace zata je aikin nan tsaf zata auren mai gidan,”  hannu hajiya tasa abaki tace “ke ! tab y’ay’an sa kuwa da sun yi farfesu da namanta sojoji fa akace hmmm !! ”  dariya sukayi su duka , mareeya ta cigaba da bada bayani “Sannan dole a canza mata suna daga SEHRISH  zuwa TUKUR ,” a tare suka hada baki wirin cewa “Tukur kuma !”? murmushi ma’reeya tayi tare da jaddada masu maganarta ta  ” kawai kuwa ! sannan zan sa mata gashin baki irin na maza wanda ake fixing dinsa tare da eyebrows na kanti.

Hajajju ta ce “Gashin baki dai. wannan dana nasani ? amma me amfanin hakan “? ma’reeya tace “Wannan wani salo ne kuma ina tabbatar miki da zaiyi aiki , duk da sehrish yarinya ce har a fuskarta amma indai nasa mata gashin baki dana jagira , zata kara suffanta da namiji zata koma kamar d’an daudu kuma dama in kin lura yanayin jikin y’an daudu basa da kiba sai tsayi ,”   

Gaba daya sun amince da maganar ma’reeya , shiri na musamman akayi ma Sehrish a washe garin ranar cikin riga ta maza milk colour mai maballai a gaban rigar , sai wani burgujejan wando falazu da aka sama ta kamar kafar agwagwa haka yake pink colour , sun matse mata kirjinta , shafe ta koma kamar babu su , an datse dogon gashin kanta an barmata guntu irin nawa sai suka samu kallabi irin launin  trouser din suka nannade mata shi akai kamar rawani , kallabin nada tsayi sai da yar jela ta zubo ta gefe , sai ta koma kamar d’an chali chali , ga gashin bakin da suka sanya mata , ya hau radau ya zauna , haka jagirar da suka samata , ta zauna cuf  , duk wani abu na ado na jikin y’a mace babu shi a tattare da ita yanzu ,

Karanta Littafin>>> Macijine Shi Complete

Shin koya wannan wasan kwaikwayon zai kasance ? mezai faru ranar da suka gane cewa sehrish macace ba namiji ba ? Kowa yasan ya sojoji suke  👊.

Tunda a sussuba suka kama hanyar zuwa abuja , ita da hajjaju , zuciyarta sai dar dar take yi mata , a natse hajjaju ke driving dinsu , yayin da sehrish ke gefenta , idonta nakan glass din motar , tana kallon yadda suke wuce wurare daban daban , zahiri tana kallon bishiyoyin da suke giftawa na cikin dajijjikan da ke a side road  kamar suna gudu da kafafuwansune , a hankali zuciyarta ta sauya mata akalar tunaninta izuwa rayuwarsu ta baya , nan take taji wasu zafafan hawaye na sintiri a idonta , zuciyarta ce ta soma yi mata magana “Sehrish kowane d’an adam yana da irin tasa kaddarar, Allah yana jarabtar bayinsa ne domin ya gwada imaninsu , kiyi kokari ki cinye wannan jarabawar , ki rungumi kaddara a duk yadda tazo miki dama can rutacce ne daga Allah dukkan tsanani yana tare da sauki ! Allah yana sane daku kuma shine gatanku ,”

Hannu tasa tana clearing face dinta saboda bata so hajjaju tagani , tunanin y’an uwanta shine yafi komai tayar mata da hankali , bata san wani gidan mahaukata bane zasu juri daukar nauyin haukan ta ba idan akace yau husanna tarasa ranta , haka abubuwa suka dinga zuwa mata aranta har suka isa garin abuja,  wuraren karfe 2:30 na rana  ,

Wannan ne karo na farko da ta fara yin tafiya mai nisa irin wannan , 

tunda suka shiga take kallon manya manyen gine gine , har suka iso gidan da zasu wato gidan Abban sojoji , sehrish ta razana da ganin katafaren ginin mai matukar girman gaske da daukar hankali , irin gidan da ta saba gani a cikin  mafarki, 

Lokaci da idonta suka sauka kan Narka narkan sojojin  dake tsare da babban gate din gidan sai da taji gabanta ya fadi rass , bakake ne wulik dasu sanye cikin uniform dinsu , ga bindigu rike a hannunsu , ga wasu guns din soke a west dinsu , 

Wani irin miyau ta hadiye ganin an tsaida motarsu , nan take taji zufa na gangaro mata ta cikin sumar kanta ,  guda biyu ne suka karaso inda motar tasu take , d’aya ne yasa hannu yayi knocking  , hajjaju ta zuge glass din , ita kanta a tsorace take cikin en ena tace “barka dai sannu ku da aiki ,”  amsa yayi da “yawwa muna bukatar sanin daga ina kke kuma wurin wa kka zo “? 

Da sauri hajjau ta dauko wayarta cikin yar purse dinta ta shiga neman number abban,  yatsun hannunta sai kakarwa suke , kira d’aya tayi masa ya daga , bayan sun gaisa ta sanar masa da abunda ke faruwa, ya umarce ta da ta basu wayar , mika musu tayi daya daga cikinsu yasa hannu  ya karba tare da karawa a kunnansa ,   juyawa hajjaju tayi tana kallon sehrish wadda tuni ta ta gama tsuma , ta nannade wuri d’aya ta matse jikinta , idon nan sunyi furi furi kamar wadda tayima sarki karya ,  muryar sojan taji yana cewa “take your phone , u got permission to go in , but firstly we must check the car ,”  kallon sehrish tayi tare da cewa ” mu fita zasu bincika motar ,” bude mota sehrish tayi ta fita , itama hajjajun ta fito , suka tsaya suna jiran su gama binciken nasu , 

Matsawa Sehrish tayi kusa da hajiyar tayi kasa kasa da murya tace “hajiya amma nan barrack din sojoji ne ko “? cikin rashin natsuwa hajjaju tace ”  A’a gida ne na sojoji dae not a barrack ni bana cikin kwanciyar hankalin wadannan sojojin sun firgitani , sai kace wasu masu safarar miyagun kwayoyi za’a tsare mu ! that’s why ban cika son zuwa gidannan ba ! ,” takarasa maganar tana yatsina fuska , 

Jikin sehrish ya gama yin sanyi , bin jikinta tayi da kallo tasha kayan maza , ga uban burgujejan wandon da tasa kamar zata tashi sama, kara kankame jakar dake hannunta tayi wacce ke kumshe da y’an kayan  da hajjaju ta bata kyauta , 

Hatta purse din hajjaju sai da suka bincika , zuciyar sehrish sai bugawa takeyi tunanin ta masu gadi sun kasance haka da ban tsoro ina ga y’ay’an gidan da taji ance they’re all soldiers 😒

Download >>> Yar Harka Romantic Novel 

Muryar sojancce ta ratsa kunnanta “lemme see your bag “! cikin sauri ta mika mar jakan , zazzago kayan ciki yayi kasa yana duddubawa , trousers ne da riguna na maza , da hijabai da ta kudundunesu saboda sallah  ,  bayan ya gama checking dinsu ya dago ya zuba mata ido yana kallonta , nan take taji fitsari ya cika mata mararta , sunnar da kanta tayi kasa , jikinta na rawa , Ji tayi yasa hannunsa ya dankwashi kanta yana cewa “mara kunya kana namiji baka iyasa Cap akan ka , kai ga d’an daudu ko ? sai dai kasa abu na mata ka nannade kai kamar wani limamin masallaci “,

Karasa maganar yyi tare da wurga mata jakar , sannan ya juya ya tafi , hannu tasa ta dafe wurin don taji zafin rankwashinta da yayi mata wannan gabjejan hannun nasa , dole ita ta zukunna ta kwashe kayanta daya zubar a kasa ,

A karshe dai Sun sami shiga ciki , a jiyar zuciya Sehrish tasaki , time dinda motar tasu ta wuce babban gate din ta shantalelen titin da zai kai ka can cikin gidan , 

A hankali take bin ko ina da kallo ta cikin glass din motan , tana kara jaddada haduwar ginin , taga wurare daban daban  masu ban sha’awa , sai ta dinga tunanin cewa kodai tabar nigeria ne domin daga inda kasa kafarka cikin gidan kamar ka fita daga 9ja ne 😔

ihu da sowar da taji ne  yasa takai idonta wurin , y’an matasan samari ne kyawawan gaske suke wasan football , acikin playing field n gdn , gwanin burgewa tabisu da kallo har sai da suka wuce su , 

A wurin da aka ware na parking space , hajjaju ta tsaida motarsu , wurin cike yake da motocinsu Na gayu ga kuma jibjibgan motocin irin na sojojin man 

Waigawa hajjau tayi ta kalle ta tace  “sehrish ki natsu dan Allah in mun shiga kada ki jamun , kuma kada ki manta sunan ki tukur daga ynx ,” cike da gamsuwa ta masa mata da “Toh”

Fitowa sukayi daga motan suka miki hanyar data zata sada ka da babban falon gidan , tuni sehrish ta raina kanta , tamkar karta taka kasan tiles din take ji saboda wani irin design ne mai daukar ido , duk yadda ka taka saiya bada sauti kwas kwas , 

Komai na cikin living room din mai tsadar gske ne , kana gani kasan bana nan bane , an kawata shi da expensive furnitures , wasu hamshan royal sofa ne aciki  , set shida ne a jere , ko da ido ka kallesu kasan zasuyi laushi da dadin zama  , duk yawansu basu cike falon ba saboda girmansa ya isa a gina madai madaici gida acikinsa, 

Komai da ake bukata acikin falo akwaisa sai da ba tarkacen nan na hauka komai a natse ,

Bin ceiling din tayi da kallo ba irin rufin da tasaba gani bane , wannan na glass ,  acikinsa akwai light bulbs masu haske wurin 

Hankalin hajjaju ba karamin kwanciya yayi ba ganin falon tsit ba kowai sai sanyin a.c dake ratsa sassan jikin mutun, dama zullumin ta ace wadannan sojojin na nan , 

Ruko hannun sehrish tayi wadda hankalinta ke kan twin stairs din da tagani wato tagwayen bene guda biyu wadanda zasu kai ka upstairs, tsantsararrun gaske  , 

Sehrish tace “hajiya naji tsit ko ba kowa ne ? hajjaju tace “ina ga duk suna wurin aiki , mu samu wuri mu zauna mu jira wata’kil mai aikinsu na nan ,” 

Suna kokarin zama suka ji takon takalmi daga left dinsu , karfaffar maca ce irin giantess dinnan , tana da hasken fata , jikinta na sanye da doguwar riga ta atampa har kasa ta kashe daurin d’an kwalinta , tana ganin hajjaju ce ta saki fara’a tana fadin “me nake gani kamar hajjaju makkatin “?  murmushi hajjaju  tasaki tare da cewa “kwarai kuwa nice AZUMI ashe kina ciki , nayi tunanin ba kowa ciki ne ,” 

Karaso wa tayi inda hajjaju take tayi hugging dinta tana cewa ” I really missed u alot hajjaju  kin boye mana nayi expecting din bakya kasar ne ,” sakin juna sukayi hajjaju tana dariya tace “Ina nan mana ina zani an gaya miki ynx barin kasar nan sauki ne yadda komai ke kara farashi , yar dubai dinnan danake zuwa kamar hauka ynx nadaina saboda rashin kudi ,” 

Murmushi azmi tasaki , tare da nuna masu wurin zama tace “bismillah ku zauna bari na shiga na kawo muku abin sha , firar zata fi dadi idan kuka jika makoshinku , 

tana gama fadan hakan tajuya ta nufi hanyar da zata kai ka kitchen dinsu , zama sukayi a tare saman 3 seater , har lokacin sehrish na makale da yar jakarta a kirjinta , sai karewa falon kallo takeyi tana jinjina kyansa , wai itace zata rayu a cikin katafaren gidannan , wayyo dadi boye farin cikinta kawai take yi , ta wani bangaren kuwa hankalinta a tashe yake , saboda batasan ya rayuwarta zata kasance ba a matsayinta na yar basaja , matsayin namiji a gidan sojoji , 

Dawowa azumi tayi hannunta dauke da tray , plate ne mai dauke da snacks , sai 2 cups da jug , a jiye su tayi a sman table sannan ta janyo shi izuwa gabansu ta ajiye ,

 Koma tayi tazauna tana murmushi , Sehrish kuwa sai kallon matar take yi har taji ta burgeta saboda tana son mutum mai fara’a ,

Lemu ne a cikin jug din zuba musu hajjaju tayi ta mika ma sehrish , cikin sauri ta karba dama kishi take ji , kurbarsa tayi wani irin sanyi ya ratsa ta ga dadin gaske , 

Azumi ta bi ta da kallo cikin mamaki tace “in ce ko wannan ne d’an aikin da akace za’a kawo mana”? hajjaju ta danyi guntun murmushi tace “eh shine sunan shi tukur kwararre ne wurin iya sarrafa abinci ,” saboda jin karyar da hajjaju ta shirgo akanta yasa ta kusa fetsar da lemun da takurba a bakinta , abunda ya kusa sata ta shake shine da ta ce kwararrene wurin iya sarrafa abincin shin yaushe ta son da wannan ? 

Sauraron hajjaju ta ci gaba dayi jin  tana introducing dinta a wurin azumi ” yaro ne mai matukar basira ga wayau , zakiji dadin yin aiki dashi ,” takarsa maganar tare da ajiye cup din dake a hannunta saman table din gabanta , sannan ta kalli sehrish tace “tukur wannan itace azumi , itama y’ar aiki ce a gidannan amma taji ssae tana kula da yaran gidan hakan yasa ta zama tamkar uwa agaresu , ina fata zakuji dadin yin aiki da juna ,” 

Dakyar sehrish ta kakaro murmushin dole tace “Insha Allah hajiya ,” 

Ita kadai tasan halin da ta shiga , wannan zaman da tayi  ji ta , kamar ta dosa na ass dinta  a saman wuta , saboda tsabagen tsoro , A ranta sai maimaita kalmar ‘yaya goma sha takwas kuma duk sojoji  take yi , 

Azumi ta janye idonta daga kan sehrish (tukur) ta mayar da idonta kan hajjaju tare da cewa “am inaso na tambaye ki tundazu maganar ke shigemin meyasa kika daina leko mu bayan ina da tabbacin cewa kina zuwa abuja zuwane kawae ke baki yi ,”

Murmushi hajjaju tayi tare da yin yar dariya tace “ai dole zuwa gidannan ko jaraba ! oh kin manta Abunda ya faru last time dana zo ko ? Ina wannan BABBAN YAYAN nan nasu wani mai shegen kyau tubarkalla kamar d’an sarkin aljanu mai kirar zakunan nan ,” dariya azumi tayi tare da cewa “wai wa kike nufi cikinsu , kinsan suna dayawa , akwai major , akwai Captain ga janar , akwai Marshall ga kuma Canal da sauransu , kowa da sunan da ake kiransa  ” takarasa maganar tana kallonta 

Sarai tasan wa take nufi amma tafiso taci gaba da zuzutashi don hajjaju ta iya bada labari , 

taci gaba da cewa “oho nidai nasan shi kadai suke ce ma babban yaya , ina gaya miki last dana zo , lokacin nazo dubiyar wannan younger bro dinnasu mai asthma wanda  aka fidda kasar waje akayi masa aikin a kirjinsa , ” azmi tace “oh nagane junaid kike nufi ae suna waje suna buga ball ynx yaji sauki Alhmdllh ,”

Hajjajun ta ci gaba da cewa “ina fadamiki daga zuwa abun arziki , wlh ina shigowa falon nan ni bansan meya faru ba , nasame shi da y’an uwannan nasa sae faman rirrike shi sukeyi sai huci yake yi just like a hungry lion from the bush gaba daya yayi watsi dasu  kasa , ya daga dining table yayi wurgi dashi , gabana ya fadi  rass banyi aune ba naji yace “don ubanki kama hanya ki fice, ashe ya ganni ” 

Wallahi a tsorace  a fujajen nabar gidan don tsabagen rudi , da kafa nakama hanyar fita babban gate din saida wani soja cikin security din gidan nan yace mun hajiya kin manta motarki , sannan fa natuna jiki na rawa nakoma nadauko,” 

Tun kafin ta idasa labarin azumi da sehrish suke ta faman tikar dariya , kamar cikinsu zai kulle , ita kanta hajjajun dariyar take yi , 

dakyar azumi ta tsaida dariyarta tace 

“Hmmm sai ynx nagane wa kike nufi , ai da kinsani ba ki daina kawo mana ziyara ba domin shi ba sojan nigeria bane , US ARMY ne ba a kasar nan yake ba yna dai zuwa sometimes in yasamu hutun aiki ,” 

Hajjaju tace “bazaki gane ba ne , yadda na tsorata , ai ko ba don shi ba , wadannan tantiran na gidannan marasa jin magana…” Azumi ta katse mata maganarta ta da cewa “twins kike nufi , tom & jerry suna nan haryanzu basu canza ba sai ma abunda yayi gaba “,

Hajjaju tace “ehen su nake nufi”, 

Ci gaba da fira sukayi , yayin da hankalin sehrish ke atashe , tunda taji sun ambaci babban yaya sai taji tsoransa har ya shiga ranta , sam ta nemi natsuwarta ta rasa , 

Sun jima suna fira har time din ba wanda yashigo daga cikin soldiers din ,  har hajjaju tayi shirin tafiya , bayan ta yiwa azumi bayanin akan nemawa tukur wato sehrish alfarmar in tayi one month da fara aiki ta taimaka a ansar mata kudin wata uku a dunkule , 

A tare suka fita har bakin motar ta , sannan suka tsaya suna idasa takarkare zancen 

“meyasa bazaki jira abban ba yazo? koya yi miki sallamarki ne “? hajjaju tace “ae indai abba ne bani da matsala dashi nasan zanji alert kinsan hannunsa a bude yake , kuma Abunda yasa nake sauri zan shiga gwarinpa ne gidan wata goggo na ” 

Murmushi azumi tayi tana kallonta,

Ita ma murmushin tayi mata , harta bude mota zata shiga tasake juyo wa ta kalli azmi tace “pls game da tukur na baki amanarsa , ki kula da duk wani motsi nasa pls ,” 

Azmi tace “in dai nice u don’t ave to worry about it I will look after him insha Allah ,” sallama sukayi hajjaju ta shige cikin motarta ta ja ta , 

Bayan fitarsu sehrish ta zabga uban tagumi tana jin kewar kasancewarta ita kadai a wannan hamshakin gidan da batasan kowa a cikinsa ba , gashi tazo a matsayin namiji , duk in ta tuna wannan hankalinta tashi yake , abu dayane ke kara mata karfin guiwa , y’an uwanta in ta tuna su sai taji ba irin kasadar da bazata iya shiga ba ,

Dawowa ciki azumi tayi fuskarta a sake tace da sehrish ” tashi mu shiga ciki na nuna mka bedroom din ka , in ka huta zuwa anjima  before magrib zamu shiga kitchen”,

Sehrish ta amsa da toh tare da mike wa tabi bayan azmi , suka shiga ciki tayi mamakin bedroom din da azmi ta nuna mata a matsayin nata na yar aiki , wannan koda amayarce tasamu wannan falillahil hamdu , ba tarkace a ciki , single bed ne , ga beside drawer mai dauke da bedside lamp a samanta  ga wardrobe madai-daiciya ta manne jikin bango ,  ga wadatattun curtains a kowane window , komai na cikin bedroom din brown color be banda labulayen da suka kasance milk colour , da zanen gadon , 

Ba abunda ya kara burgeta sai dressing mirriow din da tagani , duk da ba cosmetics a samansa , madubin yayi mata da yar chair din dake gabansa ,

Murmushi azumi tayi ganin yadda yaron yake ta farin ciki don haka tace “komai yayi ko “? da sauri ta amsa da “eh hajiya harma yayi yawa ” 

Dariya azumi tayi jin yace harma yayi yawa , 

“Ynx dai ni zan shiga ciki , ka zauna ka huta , sannan akwai bedsheets a cikin wardrobe din nan , in zaka canza saika dauka ,” tana gama fadan hakan ta fice , 

Kamar jira takeyi azumi ta fita tahau ihu tana tsalle , kafin ta tsagaita da haukan nata ta shiga bathroom din dake ciki , 

Nan fa ta soma wani sabon kallon , ko a mafarki bata taba tunanin zata mallaki irin wannan tsantsararren bathroom dinba mai kama da bedroom saboda haduwarsa , 

Dakyar ta samu natsuwa , ta dauro alwala tafito , a cikin wardrobe din ta samu prayer mat (sallaya) ta dauko ta shimfida , ta kabbara sallah , duka ta hada tayi zuhr da isha saboda batasamu damar yi ba a kan hanya , gashi ynx ankira isha’e shiyasa ta hadesu duka tayi ,

Bayan ta idasa sallar , ta daga hannayenta sama tana addu’ei at the end ta fashe da kuka , Sbd tuna wa da halin da y’an uwanta ke ciki , magana ta soma yi cikin kuka ” har ynx na gaza yarda cewa nice zan yi rayuwa a cikin wannan daular ba tare da y’an uwana ba , taya zanji ddin rayuwata batare dasu ba , ni ina nan sukuma suna asibiti cikin wani hali , Allah sarki rayuwa ! bazan taba yafe ma wanda yayi silar shigarmu cikin wannan tashin hankalin ba , Ya Allah ka hana sa jin dadin duniyar nan gaba daya , Ya Allah ka kaskantar da rayuwarsa kamar yarda yayima ta mu…..” kuka ne yaci karfinta har ta kifa kanta saman sallayar tana cewa “I will never forgive u in my life and I will neva forgt u ! i must take revenge koda ace nikadai ce na rageda zan yafe maka ka shiga aljanna to tabbas bazaka taba shigar ta ba.

Bata tashi daga saman sallayar ba har aka kira Magriba tana tunanin abu daya, sai da ta kammala sallar sannan ta nad’e carpet din ta turasa cikin wardrobe , tare da hijab din duka.

tsayawa tayi gaban dressing mirror tana kallon kanta a cikinsa , sak namiji ba wanda zai gane mace ce sai yanayinta ya koma kamar d’an daudu , hannu tasa tare da shafa gashin bakin da ma’reeya ta sanya mata , murmushi ta d’an saki a ranta ta ce “Sehrish ke nan dramatic girl.” 

Kara kimtsa kanta tayi saboda azmi tace mata akwai aiki a kitchen da zasuyi, sai da ta fara rufe kofar dakin gudun kada Azumi ta same ta tana canza kaya , ta gane cewa maca ce ita , 

Cire kayan jikinta ta yi , ta maida su cikin bag dinta , sannan ta dauko wasu riga da wandon , ta rige a hands sinta gaban mirror din ta koma ta tsaya tana kallon jikinta , ziririn pant ne a ajikinta , takai hannu tasha fa flat tommy dinta , wanda yake a dam’e kaman bata cin abinci saboda shafewarsa , 

Mayar da hannun tayi saman boobs dinta wadanda ta matse su gam , da abun matse belly , har cikin ranta ba taso hakan ba tana son abunta ssae , amma ba yadda zatayi duk cikin aiki ne ,

ga hairs dinta da aka maida mata shi guntu , amma hakan bai dame ta saboda a iya sanin ta in aka aske mata gashi irin hakan cikin one month zai koma yadda ya ke tsayinsa ma harya karu , 

Jin alamar tafiyar mutun kamar bedroom ta ake nufowa shine ysa ta yin saurin , zura dogon wandon tare da rigar sa , tayi gaggawa gyara daurin da m’reeya ta yi mata , mai kamar rawani , 

Kwan ! kwan !kwan taji an knocking , cikin sauri ta karasa ta bude kopan azmi ce tsaye fuskanta da murmushi tace “tukur ina fata ka shirya sbd ynx zamuje na nuna maka yarda abun aikin yake  ,” 

Cikin girmamawa sehrish tace “toh hajiya ,”  

Azmi tayi mata wani irin kallo har gaban sehrish ya tashi a tunaninta ta gano lagwanta , amma sai taji tace “stop calling me hajiya , my name is azmi call me by my name , cos we re d same , am a house maid just like u ,” 

taka rasa mgnr tare da fice wa tana cewa “follow me” rishi ta bi bayanta tana d’an murmushi , 

Kitchen suka shiga amma sehrish ta gaza gane a ina suke , haduwar wurin ce ta rikitar da ita , an kawata komai na kitchen din da dukkannin abubuwan da akeso,

Sam ta manta aiki ya kawosu sai faman kalle-kalle take yi , sai da taji muryar azmi a kunnanta sannan ta dawo dai dai 

“tukur ynx bamu da enough time , we’ll make a dinner now in yaso zuwa tomorrow i will explain everything  to u ,  Especially zama da samarin gidan nan darasi ne me zaman kansa duk zan koya maka ,” 

sehrish sai take ganin maganar azmi kamar shiriri tace , ynx har akwai mutumin da za ace sai  an koyi darasin zama dashi ? 

haka suka fara aiki , azmi ce ke yin girkin , yayin da tabarma sehrish ferar dankalin turawa , ga yankan albasa , acewarta tafara da karamin aiki , 

Suna cikin aiki sehrish tafara jiyo karar shigowar motoci , rass taji gabanta ya fadi , da jiniya motocin ke shigowa , 

“Hmmmm wannan alama ce mai nuna cewa masu gidan sun dawo ” a cewar azmi ,

Zuciyar sehrish sai harbawa take yi saboda tsananin firgicin da wa zata fara cin karo ,

“Ka’ida ne daga sun shigo babban falo zasu fara kwalamin kIra ka saurara kaji  ,” azumi ta fada tana murmushi , 

Hannun sehrish sai  kakarwa suke yi , 

ita dai baza ta iya tantance muryar mutun nawa bace amma taji sauti iri iri 

“Azumi ! Azmi !! Azam zam !!!” da karfi suke kwala mata kiran without any respect ,  cikin sauri azmi ta fice tana ce ma sehrish “pls ka kula da girkin am coming back now ,” 

Sehrish ta amsa da toh , daga inda take tana iya hangosu saboda kitchen din irin model design dinnan ne wanda ba kopar shiga gare sa a bude yake bata iya identifying faces dinsu , 

Hankali a tashe azmi takarasa wurunsu tana fadin “welcome back Sirs ,”  ko arziki amsa bata samu ba sai complaining da suka soma yi mata, “Ina fata angyara min bedroom dina don bansan kazan ta ! in ma kinsan baki gyara ba let me know ,” daya daga cikinsu ne yayi wannan maganar , 

matsawa tayi kusa dana gefensa don taji shi mai zaice  , hannu ysa yana shafa ciknsa yace “Ni matsala ta abunda zansa ma cikina pls kafin na shiga ciki nayi bath na tarar da abinci jere saman dining table if not kinsan sauran ,” 

matsawa azmi ta sake yi kusa dana gefensa dayake duk suna a jere kusansu takwas, 

” Na fadamiki Injin wanki  na ya samu matsala dazu da safe ga shi na tara kayan dauda , gajerun wanduna na ma duk sunyi dirty dafatan kin wanke mun su ,” 

Haka ta dinga sauraransu ba wanda baiyi magana ba acikinsu , bayan ta gama sauraransu one by one tace ” Komai da kuka lissafamin na kammala sa , abinci ne kawai shima ynx zan idasa ,” 

Kama hanya suka yi kowa ya wuce bedroom dinsa , wasu na upstairs wasu na a downstairs, 

Babu abunda ya burge sehrish sai kakin sojojin dake jikinsu , abunka ga handsome guys ga tsawo ga hadaddiyar sura sai abun ya bada citta 😘

tunanin ta soma yi a ranta “oh ni ko wanene babban yaya acikinsu , koda yake naji azmi tace ba sojan nigeria bane U.S ARMY ne , zanso nagansa daga ji ya hadu yadda hajjaju ke zuzu tashi ,” 

takarasa tunanin tana murmushi ita kadai abunta , shigowa azumi tayi tana fadin “maza tukur a shirya abinci a dining before su fito, ai ina ji girkin ya isa ya kammalu ,” 

Wasu hadaddun kuloli ta dauko daga kitchen cabinet kamar ranar aka budesu daga kwalinsu tsantsar kyansu kamar ba abinci za’a zuba ciki ba , saboda yadda murfinsu ke glowing har face dinka zaka iya gani aciki just like mirror , 

A wani faffadan tray ta shirya komai ciki , ta mika wa sehrish azuwan taje ta fara shiryasu a dining , 

Gaban ta na faduwa ta karba tsoranta da wa zata fara cin karo a cikinsu ,  time din da ta isa dining room din , mutun d’aya ta samu zaune shi ya rigasu fitowa jikinsa na sanye da white tshirt da black  short  , bai lura da ita sai da yaji cool voice dinta ta sauka a kunnan sa ” sannu da hutawa ” a natse ya dago yana kallonta , 

lokacin da suka hada ido kara ware idonta tayi ganin irin kyawunsa , dan matashi ne ba zai wuce 18years ba , a tunaninsa zai ga mace amma sai ya ga namiji tabbas shi muryar mace ya ji mai dadin gaske a kunnan sa , 

Wani kayataccen murmushi ya sakar mata , wanda yasa ta shiga yanayi ,  cool voice dinsa ce ta ratsa ta “am nace ko sabon mai aikin da akace za’a kawo mana ne?daga masa kai tayi alamar eh , 

Jinjina kansa yayi tare da d’an tabe small lips dinsa  , 

Soma jera abincin tayi , bayan ta gama ta koma ta dauko sauran abubuwan da bata kawo ba ,

Allah Allah take ta kammala jera abincin kafin sauran su karaso , muryarsa ce ta kara katse ta ” chicken pepper soup din nan zaka zuba mun ka hadamin da irish cikin plate din ,” ta amsa toh kamar wata munafuka haka take sunnar dakai , Ji take kamr asirinta zai to nu ,  

Plate ta zaro daga cikin set na filattan da takawo , bude daya daga dana cikin kulolin tayi , nan da nan kamshi ya gauraye wurin , saving spoon ta dauko ta soma zuba kazar a cikin plate din , sai faman hadiye miyau take yi , ga hannun ta dake kakarwa ga wani gumi dake sauka daga gefen sajenta ,

Kammala zuba kazar tayi sannan ta bude kular da ke dauke da irish ta zuba masa k’adan  muryarsa ta sake ji “yayi mun k’adan ka take mun plate din ”  

cika masa plate din tayi dam sannan ta tura masa gabansa , cikin sauri ta kama hanya zata koma ciki  “spoon din fa ko so kake na dauka da kaina ne sannan a gidan ku haka ake ba mutun abinci ba tare da drinks ba ‘? har zuciyarta taji wannan maganar a tunanin zaiyi saukin kai ganin da farko yayi mata murmushi ,  

lallai ta jinjina wa izzarsa , ga cokulan kusa da shi ga kuma drinks din da ta jera amma yafi karfin yasa hannu ya dauka sai da ita ta mika masa , 

guntun murmushi tasaki koma tayi ta mika masa cokalin sannan ta zuba masa lemu a cikin glass cup ta mika masa , yamutsa fuska yayi tare da sa hannu ya karba yana cewa ” gsky kana bukatar training don da ace babban yaya ko captain kayima haka da ka gane barno gabas take don sai kayi tsallan kwad’i ,” 

Ya karasa maganar yana kurban lemun da ta mika masa , a wani irin yanayi sehrish ta juya wannan ne karo na biyu da taji an ambaci BABBAN YAYA , hakan nakara sa mata tsoransa a zuciyarsa , 

Komawa tayi kitchen ta samu azumi tana gyara wuraren da suka bata , jin shigowarta yasa ta dagowa tare da cewa “subhanallah meyasa ka dawo ka kammala saving dinsu ne “?   

“A’a naga basu fito bane shiyasa na tafo ,” tayi maganar fuska a yamutse  sbd rashin natsuwa da take ciki , azumi tace “maza ka koma karka ja mun bala’i , bakasan halin mazan gidannan ba ,” 

Ba haka sehrish taso ba , jiki a sanyaye ta kama hanyar komawa dining room din ,  hannu azumi tasa ta rike habarta alamun mamaki tace “lallai dole na mike tsaye akan yaron nan ! yana abu kamar mace anya wannan ba dan daudu bane ? ta tambayi kanta ,

Tunkan takarasa ta ke hangensu , a lokacin suke karasawa  saman dining din kowannen su yaja kujera yazauna , Kasancewar table din dogone mai mazaunin mutum goma sha 12,  

Tana jin dayansu na cewa “wai uban wa ake so ya zuba mana abincin ne? cikin sauri sehrish ta karasa tana cewa “ni ce yallabai ,” 

Gaba daya suka d’ago suna kallon ta sai ta tsorata tayi wuri wuri da ido.

Share and Comments

Back to top button