Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 19 Book 2 Complete Novel

  

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

Around 12 Abban su ya dawo cikin gidan time ɗin duk sunyi bacci, bai wuce ɗakinsa ba sai da ya fara zuwa part ɗin Marshal Omar domin yaga ɗansa kafin ya wuce nasa ɗakin, lokacin daya tura kopan part ɗinsa shima nashi sak irin na Sgr ne, akwai hamshaƙin ƙayataccen palor aciki sai bedroom aciki,

 Wuce wa bedroom ɗinsa yayi ya shiga Ciki samun shi yayi saman shimfiɗeɗen gadonsa ya lullu6e da lallausan blanket ɗinsa,

   Murmushi Abbansu yayi tare da cewa “Yawwa haka nakeso my son asha bacci lafiya,” juyawa yayi zai fita Muryar Omar ta ratsa shi da cewa “Abbana idona biyu fa, i ave told u that i wll be waiting to ave ur hug, that’s why i stayed awake,’ 

    Omar ne yayi maganar a yayin da yasanya hannunsa yana janye Bargonsa ya miƙe zaune da murmushi a face ɗinsa,” 

   Ƙarasawa Abban yayi Omar ya tashi tsaye suka rungume juna ssae,

“Nayi missing ɗin Tiger ɗina ssae, ” ya faɗi yana bubbuga bayansa, Omar yace “Abbana nima haka, ina fata nasame ka lpy,” 

   “Lpy lou Alhamdulillah Omar,” ya yi maganar tare da janye jikinsa daga na Omar yana cewa “Ka koma ka kwanta Omar nima zan wuce ɗaki ynx,” 

     “Shikenan Abba, Mu tashi lpy,” 

Sallama su kayi abban ya fice,  kwanciya Omar yayi amma yana jin there’s something missing a heart ɗinsa tabbas akwai wanda baisa a idonsa ba, tun da ya dawo cikin gidan ba kowa bane face “Junaid,” ya bari ne kawai sae gobe ya neme shi su gaisa cos yyi missing ɗinshi,” 

Sehrish fa sam ta gaza runtse eyes ɗinta tayi bacci, duk ta takure kanta ta tsani jikin ta, ta6awar da haroon yayi mata ji take tamkar raping ɗinta yayi, tana saman gadon daga kwance ta tashi zaune tsakiyar gadon, ta matse kanta baiwar Allah,

___________________________/___/

Time ɗin da Abban su ya shiga ɗakinsa, yayi tunanin zai ga junaid a kwance yana sharar bacci, amma sai yaga wayam daga blanket sai pillow asaman gadon, abun ya ɗaure masa kansa, aransa ya ce “meyasa Junaid bai zo ya kwanta bane wai, ko dae yana a bedroom ɗinsa bara dae na canza kaya naje na duba sa,” 

   Shaf shaf ya cire kakin dake jikinsa, ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito ya zura jallabiya fara, sannan ya fice daga room ɗinsa izuwa na junaid dake a upstairs,

   Yana isa ya tura kopan ɗakinsa abun mamaki babu junaid babu alamarsa, har toilet ɗinsa ya duba babu Shi saboda tsabar ruɗu har cikin Laundry basket ɗinsa ya duba da cikin Wardrobe ɗinsa don yaga ko ya 6uya aciki 😂

   Amma babu shi, aikuwa hankali atashe abban su ya fito ya wuce part ɗin sgr, ya shiga har ɗakinsa ya bubbuga masa jikin ƙoparsa, 

  Sgr dake kwance natse saman gadonsa yaji knocing ɗin da abban ke masa, 

       Janye bargon jikinsa yayi, sannan ya tashi zaune yana kallon Abban nasu daker yake buɗe Eyes ɗinsa saboda bacci,

      A sanyaye yace “Abba me ya faru ne? Kai ne da kanka?

    “Ina fa lafiya babu junaid fa acikin gidan nan”! Jin hakan yasa sgr yin saurin haurowa ya sauko daga saman gadon, jikinsa na sanye da night dress riga ce dai dai guiwarsa ta tsaya babu dogon wando sai dai shorts acan ciki, 

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

    Cikin ruɗu yace “Abba kamarya? How za’ace junaid baya cikin gidan nan!!!? ya tmby yana kallon abban nasu dake a tsaye,

    “Nima bansani ba, dawowa ta kenan, gsky akwai matsala,’ 

    Fito wa su kayi atare shida abban suka bi sauran bedrooms ɗin sauran saboda su duba su gani ko ya kwana a ɗakin sauran saboda yana yin haka in rigimarshi ta tashi sai ya za6i inda yake so ya kwana ko ɗakin waye kuma dole abarsa ya kwanta,

   Duk wanda akayi wa knocing ya buɗe daga yaji cewa Junaid ake nema sai kaga ya wartsake daga baccin da yake yi, hankalin kowa ya tashi matuƙa, 

   Gaba ɗayansu duk suka hallara a babban falon in ka cire Marshal saboda basu tashe shi ba tunda shi ranar ya dawo baisan wainar da ake toyawa ba Sai haroon, 

   Duk sukayi tsaye cirko cirko sai faman hammar bacci suke yi, 

   “A cikin ku wayasan inda Junaid yaje !!? Abban su ne ya tambaye su,

Kowa sai faman murxa ido yake yana hammar bacci, 

   Haɗa baki su kayi wurin cewa “Abban bamu San inda yake ba wlh,” 

   Tsawa sgr ya daka musu har sai da suka ɗan firgita yace “wannan wane irin shashanci ne ace junaid yabar gidan nan batare da kun sani ba har yakai wannan time ɗin a waje baku lura ba,!”?

 Murya na rawa Su twins suka haɗa baki wurin cewa “Junaid fa baya zuwa ko’ina kowa yasani yana cikin gida kullum sai dae wani abun daban,” 

    “Nima a iya sani na kenan gsky akwai matsala* acewar fawan 

Jabeer da Irfan suka ce “mun fa lura baya cikin gidan nan, amma gaba ɗayanmu munyi tunanin yana ɗakin Abba yana bacci shiyasa mukayi shiru,” 

 Bin su da kallo kawai sgr yake yi suma kallon shi suke yi suna kora bayani, 

    “Yakamata ajaraba kiran layinsa mana aji inda yake” acewar Khaleed, cikin sauri kanal yusif ya zaro wayarsa dake cikin aljihun wandon baccinsa, 

    Contact ya shiga ya dubo numbar junaid wadda yayi saving da *Last Born* Ya danna masa kira ta soma ringing,

    Gaba ɗaya koya ya saurara yana jiran amsa kira daga junaid, 3 times tana ringing junaid bai ɗaga ba,

    Hakan yasa kanal yusif yin amfani da wayarsa wurin duba location ɗin Inda wayar take,

    Gaba ɗaya kowa na jiran tsammani, kanal yusif yace “kai ! Location ɗin fa ya nuna cewa wayar tana acikin gidan nan that means junaid yana acikin gidan kenan ko yabar wayar tashi a bedroom ɗinsa ne,  

cikin hanzari su fawan suka haye upstars shi da su twins domin su duba ɗakin junaid koyana nan,

   A tsiyace suka tura ƙopan ɗakin suka shiga cike da tsammanin ganinsa amma sai suka ga wayam, sae wayarsa dake ajiye saman Pillow bisa gadonsa, hakan na nufin gida yabarta, 

   Duk basu ji daɗin hakan ba, jiki amace suka sauko down ɗin har haɗa baki suke keyi wurin tambayar Su ina junaid ɗin ? Suka amsa musu da cewa basu ganshi ba sai dae wayar shi kawai,

    “I know u will not see him cos i ave checked his bedroom already ya Ilahi,” acewar Abbansu ya faɗi cikin tsananin damuwa, 

 Hankalin kowa fa ya tashi, bazaman lpy ba Romeo ba junaid ba last born, ba shagwa6a boy Ba dole kowa ya rasa natsuwa,   

  “nasan inda yake ni,” 

Atare suka ɗago don suga wanene haroon ne wanda fitowarsa kenan daga shi sai gajeran wando ajikinsa,

   Har haɗa baki suke yi wurin cewa “Yana Ina!?

“Abada cin hanci a ɗauko muku shi,” kai kana ganinsa kasan yasha ya bugu idon nan sunyi jawur kamar na mujiya sai tangyaɗi yake yi,

    Tsoki suka ja atare,

Abbansu ya daka mishi tsawa “Haroon kadaina mun wannan wasan kasan inda yake ne ko baka Sani ba _”!!!

     Haroon yace “Billahil Azeemu na tsarance da rabbus sama’wati wal’ard nasan inda junaid yake, in ku kayi haƙuri kuka sa salama azuciyarku yanzun nan zan ɗauko muku shi,” 

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

 

gaba ɗaya mamaki ne ya kamasu su kace shikenan “Muna jira,” 

    Juyawa haroon yayi ya nufi hanyar ɗakinsa yana faɗin “saboda wannan ɗan shilan duk kun bi kun tashe mutane Fil laili……….

   Shigewa bedroom ɗinsa yayi yana ƙunƙuni,

Su kuwa zama su kayi suna ta faman jiran haroon ya fito musu da junaid,” 

     Jimmm kaɗan sai gashi ya fito hannun shi ruƙe da Pillow yana tangal tangal, 

 Zuba ido su kayi suna kallon ikon Allah, haroon na ƙarasowa ya shiga ƙoƙarin tu6e rigar pillown yana cewa “Yawwwa ynx zaku ga shegen ya faɗo daga cikin pillown ae nan cikin ya 6uya ja’irin,’ 

    Rai a6ace har haɗa hannu suka yi  Babban yaya da Abbansu suka sharara mashi zafafan maruka , daga shi har filon kowa yayi ƙasa baje,

   Ihu haroon yasaki tare da cewa “Eeeeeeee !!!huuu!!!huuuu !!! waman ƙadarallahu haƙƙa ƙadrihi yanzu abba daga abun arxiki zan nuna muku inda junaid ya 6oye sai kawai naji saukar maruka? Yaron nan fa akan idona ya shige cikin rigar filon nan ya 6uya amma shikenan bakomai,’

   Abun haushi abun takaici, banza kowa yayi dashi suka shiga tattauna yarda za’a yi a nemo junaid, 

    Kanal yusif yace “ina ga bari naje na sanarwa Azmee wata’ƙil tasan inda yake,

    “A’a bana tunanin hakan, kwarama wannan mai aikin tukur raina yana bani cewa suna shiri sosai da junaid wata’ƙil shi yasan inda yake tunda kusan shine tsaransa,” acewar Abban su

 yace hakan ne saboda abunda yagani wato da Junaid yyai ma sehrish magana ƙasa ƙasa lokacin da suna Cin abinci dama abbansu shine ya lura da hakan,

    Cikin sauri Fawan yace “Bari naje na tambayesa,’ 

    Yakama hanya da sauri ya nufi wurin ɗakin azmee don yana da tabbacin ɗakin tukur yana kusa dana Azmeee

    Sehrish na zaune idanu duk sun kumbura, taji bugun ƙopa da ƙarfi jiki na rawa tace “Wanene,” a tsorace ta tambaya, 

    Muryar fawan taji yana faɗin “Fawan ne, Fito maza ina son magana da kai,” 

 Cikin sauri sehrish ta kimtsa ta mayar da gashin bakinta, ta gyara ɗaurin kanta, 

     Sannan ta taso ta buɗe ƙopan cike da mamakin ganin fawan tabbas kam akwai matsala,

      “Gani,” ta faɗi a raunane,

Fawan yace “Kana da masaniyar inda JUNAID ! Yaje !?

      Zaro ido tayi gabanta na faɗuwa aranta tace “Ina junaid yaje har daren ne bai dawo ba ake nemansa,’

  Cikin sauri tace “a’a gsky ban da masaniya akan hakan,” 

     “Ka tabbata’?

“Eh wlh,” ta bashi amsa

 jiki a mace fawan ya wuce izuwa falon,

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

   

Shigewa cikin ɗakin tayi gabanta na faɗuwa sai lokacin ta tuno da cewa ɗazu junaid ya sanar mata da cewa su haɗu a garden After magrib,

.   “to kodai yana can ? May be ya jira ni ne yaji shiru banzo ba bacci ya kwashe shi Acan, kai anya kuwa !? taya ma zai zauna tun bayan magrib zaman jira na har yanzu kusan ƙarfe 1:00 na dare bai shigo ba, gsky bana tunanin hakan,

     Haka sehrish ta rinƙa tunane tunane aranta, har ta samu wuri gefen gadon ta tazauna zuciyarta ta saƙa mata cewa “Junaid fa rigimamme ne zai iya yiyuwa yana can ya dage akan in banzo ba ba zai bar garden ɗin ba, kai gsky fa haka nake tunani hankali na bazae kwanta ba har sai naje na duba garden ɗin can, tana faɗin hakan ta miƙe.

a hankali ta buɗe kopan ta fito cikin sanɗa, gabanta ne ya faɗi da ta hango su gaba ɗaya sun hallara a babban palorn cikin tashin hankalin rashin junaid, har sun fara yanke sha’warar fara kiran friends ɗinsa da sauran ƴan uwa aji koya je can,

   Dafe zuciya sehrish tayi tabbas kuwa in tabi ta entry ɗin main palor zasu tambaye ta jin ba’asin ina xataje, don haka tayi deciding ta canza hanya cos there’s many doors acikin gidan da zaka iya fita compound ɗin gidan,

     Ja da baya tayi a hankali dama slippers ne a ƙafarta marasa sauti, cikin sanɗa ta lallaba, ta miƙi doguwar hanyar da zata sada ta da backyard ɗin gidan,

    Taci sa’a akwai Key ajikin ƙopan jikinta na kerma tasanya hannu ta murɗa key ɗin kopan ta buɗe, ahankali ta zura ƙafa ta fuce,

   tsoranta kada security guard ɗin dake strolling acikin gidan su ganta a daren nan tana shawagi tabbas sai sun tuhume ta, gashi ko’ina na gidan Haske ne 6ayau kamar rana saboda fitilun kwan da aka ƙawata shi dasu masu hasken da kyan gaske kamar rana,

   A hankali sehrish ke tafiya kamar 6arauniya, har Allah ya shigar da ita cikin garden ɗin kai tsaye wurin da garden chairs ɗin suke ta tunkara,

     tunkan ta ƙarasa ta Hango mutun a ƙanƙame saman kujera ya kifa kansa saman table ɗin gabansa, gaba ɗaya jikinsa sai kermar sanyi yake na tashin hankali,

    Zaro ido sehrish tayi cikin tsananin tashin hankali ta watsa aguje inda yake gabanta na faɗuwa, tabbas kuwa Junaid ne, dafe kanta tayi tare da cewa “Innalallahi wa’inna ilaihirraji’un !!! Nashiga Ukuna ! Junaid meyasa !!!!!

      Cikin tashin hankali tayi maganar tuni hawaye sunzo mata shar a face ɗinta,

      Matsawa tayi dab dashi tasa hannu ta bubbuga table ɗin dake gabansa murya a mace take ambaton sunan shi “Junaid…junaid…,’

    Wani irin dogon numfashi yaja hatta yatsun hannayansa kerma suke yi, ko eyes ɗinsa bai iya buɗewa tabbas yaji Muryar sehrish amma sam yagaza bata amsa, so yake yayi mata magana taje ta sanar da wani daga cikin gidan yazo ya taimaka mishi ya tashi amma ya gaza, saboda sautin muryarsa baya fita, Lips ɗin ma nasa rawa suke yi kaf kaf,

    Bin ziraran yatsun hannun shi tayi da kallo ganin suna kerma kaf ! kaf !! Hakan ya tabbatar mata da cewa Junaid idonshi biyu, sanyi ne yakamashi ssae,. 

        Cikin sauri sehrish ta cire mayafin da take naɗe gashin kanta dashi ta rufa ma junaid abayansa, duk da mayafin bai da wani kaurin da zai masa magani,

         Zubewa tayi saman guiwarta agaban table ɗin, saitin fuskarshi dake kwance saman table ɗin tace “Junaid meyasa? Why pls? meyasa zaka cutar da kanka har haka? dan Allah ka buɗe idonka junaid, ka tashi mu tafi,’ 

         Daker numfashinsa ke fita sam sehrish batayi tunanin tana 6ata lokaci ba wurin agaza masa,

       So yake ya buɗe idonsa ya kalle ta amma sam ya gaza, sai kerma eye lids ɗinsa suke yi,  

     Hawaye ne kawae ke fita a idon Reesh, tana cikin wannan zuƙunnan karaf idonta suka sauka akan Hancinsa da Jini ke ɗigo wa,

   Waro ido tayi waje a firgice ta fashe da kuka tare da faɗin “Junaidd…!!! innalallahi wa’inna ilaihirraji’un nashiga ukuna Wayyo Allah !!!

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng


        A zabure ta miƙe ta juya da gudu don taje ta sanarwa Aunty azmee wata’ƙil ta taimaka wurin sanar dasu halin da Romeo yake ciki don azo ataimake shi karya mutu,

      Har  Tayi nisa da gudun nata muryar shi ta ratsa kunnan ta “Sehrishhhhhhhh,” cikin wata irin matacciyar murya wadda ta galabaita yyi maganar,

      A razane ta dakata tare da juyo tana kallon shi, samun shi tayi ya buɗe idonshi waɗanda suka rune jawur daker yake ƴunƙurin tayar da jikinsa da dukkan sauran ƙarfinsa,

     Cikin tsananin tausayi sehrish ta koma da gudu wurinsa tana faɗin “junaid,’  tashi yayi zaune yana fidda numfashi a hargitse muryarsa na rawa yace “ki taimaka mun numfashi na zai iya ɗauke wa, ki goyani ki kaini wurin Abbana,’ 

    ɗan zaro ido tayi tana kallonsa can kuma tayi tunanin ae junaid bazaiyi nauyi ba, ba wani girman jiki gare shi ba, duka nawa yake 

     daddagewa sehrish tayi ta tsugunna masa tare da cewa “hau muje,” daker junaid ya sauko ya faɗo bayanta tare da ƙanƙameta yana numfashi a sama sama, 

      Jigumm sehrish tayi saboda wani abu da taji ya yi mata yawo ajikinta, 

       “Ki tashi mana so kike na mutu ko,” junaid ne yayi maganar daker cikin shagwa6a, bawan Allah,

         Da iya ƙarfinta na ƙarshe, daker sehrish ta miƙe tana tangal tangal zata faɗi amma ta hana hakan, ta dake ta cije ta miƙi hanyar fita daga garden ɗin da junaid goye abayanta kamar wani ƙaramin yaro, ya lafe abayan sehrish ɗinsa, tana jin numfashinsa a gefen wuyanta saboda nan hancinsa yake, tana jin yarda junaid ya ƙanƙame mata stomach ɗinta saboda ta nan ya zagayo da hannayensa, 

   Cikin sa’a ta fuce dashi daga garden ɗin kuma ba wanda ya ganta har ta shige dashi cikin ƙopan da ta fito, yanzu tunaninta shine yarda za’ae ta haɗa junaid da ƴan uwansa batare da wani ya ganta ba, tsayawa tayi tana wannan tunanin aikuwa junaid ya fashe mata da kuka mai sautin gaske yana cewa “wai bazaki shiga dani ba so kike na mutu ko,’ duk yarda sehrish taso ta hana junaid magana abun ya faskara sai ma ya ƙara sautin kukan wanda hakan ya janyo hankalin Mutanen gidan dake a falo,

.    gaba ɗayansu sunji kukan junaid da muryarsa, har haɗa baki suke yi wurin cewa “Kai wannan ae kukan junaid ne !!,’ 

     gaba ɗayansu suka nufi hanyar da suka jiyo muryar junaid yana kuka yana yima sehrish faɗa akan taƙi ta motsa takai shi ɗakinsu,

     Jin takon takalmansu alaman sun tunkaro wurin yasa sehrish shiga tashin hankalin, gashi ta cire mayafinta, hular kanta ta karkace dogon gashin kanta duk ya barbazo waje, ae kuwa a firgice ta saki Junaid ya faɗi ƙasa tumm !tayi saurin zame mayafinta dake jikinsa, kamar aljana tayi Wuff ta boye a wani saƙo hannunta dafe da saitin zuciyarta,

    Junaid kuwa ganin sehrish ta jefar dashi ƙasa ta gudu yasa shi ƙara sautin kukan nashi ya karaɗe ko’ina yadinga burgima a ƙasa yana faɗin “wayyo Allah na, ta jefar ni !! bazaki zo ki goyani ba ki maida ni wurin Abbana ba, Wlh saina tona miki asiri tunda kikai mun hakan…….’ sam junaid fa baya cikin hayyacinsa yake waɗannan maganganun, sehrish kuwa saboda ruɗin abunda junaid yace, tuni futsari ya kufce mata ta cikin wandonta ya soma zuba zirrrrrrrrrr ! Mai zafin gaske cije le6enta tayi tare da runtse idanunta,

  

Isowa su kayi gaba ɗayansu sunyi mamakin ganin junaid baje a ƙasa yana burgima sai faman sambatu yakeyi yana faɗin “wlh saina tona miki asiri kowa ma yasani Allah,’ cikin kuka da shagwa6a yake maganar,

      Atare suka haɗa baki suna cewa “Junaid ! ina ka shiga muna ta nemanka? Kai da wanene ? Ta ina ka shigo,’ 

      Jin muryoyinsu yasa shi dakatawa yana kallonsu idonshi biji biji sam bai gane su wanene akanshi,

   Murya na kerma yace “ita ce ta shigo dani, ta goyani kuma ta jefar dani ƙasa ta boye acan wurin,’ yayi maganar yana nuna inda sehrish ta 6oye, 

   Tuni temperature ɗin jikin sehrish ya ɗau wani irin mahaukacin zafi, nan take wani futsarin ya sake zubo mata na tashin hankali, tuni zufa ta gama wanko mata sharkaf wandon jikinta kuwa ya jiƙe sharr,

   Babu abunda take furtawa Acikin zuciyarta fa ce “La’ila ha illah anta subhanaka inni kuntu minal Zalimin,’ 

Gaba ɗaya idonsu ya kai inda junaid ya nuna musu, 

    “Ah Wannan Fa aikin shaiɗanun aljanu ne kubarmin kawai A ya neh nayi maganin ƴan Iskan,” acewar haroon

   Yana maganar ya nufin wurin,

Sgr bai tsaya jin bayanansu ba, hannu kawai yasa ya ɗago junaid dake kwance, ya ɗauke sa kamar wani ƙaramin yaro ya aza shi a ƙafaɗarsa, ya juya batare da ce musu komai ba ya wuce dashi part ɗinsa, 

   Shi dae abbansu ajiyar zuciya kawai yake saki tunda Allah ya dawo masa da Baby junaid ɗinsa lafiya, kallon sauran yayi tare da cewa “Kowa yaje ya kwanta, koma mekenan gobe zamu duba,”

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

   Juyawa su kayi gaba ɗayansu kowa na faman sauke ajiyar zuciya suka wuce rooms ɗinsu, ban da haroon wanda ke faman sakin murmushin mugunta, domin kuwa ya hango ƙafafun sehrish masu sanye da wannan slippers ɗin nata na ƴan gado, 

   Bayan kowa ya bar wurin, sehrish tayi tunanin ta lalla6a ta wuce ɗakinta, dama idonta na runtse a hankali ta buɗesu gaf taga fuskar haroon a kusa da tata, wage baki tayi zatayi Ihu yayi saurin sanya hannunsa ya toshe mata baki yana faɗin “Ƴar shila, ae dama nasan kece ja’ira, na hango waɗan nan ƙafafuwan naki masu kama dana Zabbi,’

    Tsananin bakin ciki ne ya cika sehrish ganin mutumin da ta tsana,

   A faɗace tasanya hannunta tare da Buge nasa, da gudun gaske ta wuce shi ta faɗa bedroom ɗinta tana shessheƙar kuka, datse ƙopan tayi gudun kada haroon yasamu damar faɗo mata,

      Jingina jikinta tayi jikin ƙopan bayan ta rufe, tana kuka mai cin rai, ta ƙara jin tsanar haroon a ranta hada shine yaja mata barin junaid yayi ta faman jiran ta a garden gashi hakan yayi masa Illah ssae, duk inta tuna ɗigon jinin junaid da tagani daga hancinsa, sai taji wani irin ba daɗi aranta, 

   Ta jima jikin kopan kafin daga bisani ta wuce toilet ta tu6e wandon daya jiƙe sharkaf da futsari tasa shi a bucket ta wanke sa, sannan ta shanya shi a siririyar rigiyar dake a toilet ɗin, wadda akayi ta domin shanya panties, da hanging ɗin kaya, bayan ta kammala tayo wanka sannan ta fito ta canza wasu kayan riga da wando

daga bisani ta haye saman gadonta tana sauke ajiyar zuciya, shigewa tayi cikin bargo tana dariya lokaci guda da ta tuna abunda junaid yaso yayi mata a yau da ta shiga uku kuwa, daker bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,

A hankali Babban yaya ya kwantar da junaid saman shimfiɗeɗan gadonsa, har lokacin junaid fa bai dae na sambatu ba akan abunda sehrish tayi masa, sai da yaji yatsun sgr a bakinsa, sannan ya ware idonsa da kyau yana kallonsa, yayi tsit daga maganar da yake yi,

   Tashi yayi ya kashe a.c ɗin ɗakin gaba ɗaya, sannan ya kunna masa Room heater (na’urar dake ɗumama ɗaki ta zafi) nan take bedroom ɗin ya ɗumama da wani irin ɗumi mai daɗin gaske, hakan yasanya junaid fara dawowa cikin hayyacinsa, sanyin jikinsa ya soma ragewa ssae, 

      Bayan ya kunna masa, ya fice daga ɗakin izuwa medication room ɗinsu, inda suke ajiyar magunguna,

      Abunka ga professional surgeon doctor within minutes sai ga junaid yadawo cikin sense ɗinshi, bayan babban yayan nasu ya bashi medicine ɗinshi yasha,

  Sannan yace “Bazan ƙyale ka Ba junaid, u must explain to me where did u go in this night, ka tanadi amsar da zaka bani before tomorrow, Kana mun wasa da lafiyarka ko?” sgr ya faɗi yana kallonsa A yayin da suke daga zaune saman gadon,’ 

        narai narai junaid yayi da ido yana kallonsa, aiko hakan ya fusata sgr rai a6ace yace “zaka kwanta kayi bacci ko saina murƙusaka a wurin nan”?   Koma wa  junaid yayi tare da jan bargo ya lullu6e hada fuskarshi duka, bawan Allah yana so yace ma Babban yayan nasu Yunwa yake ji, amma ya gaza saboda ganin yadda ya fusata dashi,

    Kwanciya shima sgr ɗin yayi yaja bargon ya lulu6e jikinsa har wurin neck ɗinsa sannan bacci ya kwashe su, su duka,

  (Bacci da Yunwa😥)

________________________________________________________________

A 6angaren su hosana kuwa, tun da suka shiga cikin wannan tsohon store ɗin da Aunty babba ta turasu, Sam sun gaza samun sukuni, daker numfashin su ke fita saboda ƙura ga ko ina a tsohe ba windows, 

   Sun jima a tsaye cikin tashin hankali ga wani yin bacci da suke ji,

   Jiki a mace hosana tace “nidae bacci nake ji, zan kwanta ko,a ƙasan ne,” ta faɗi tare da tattarewa zata kwanta ƙasa, ruƙo hannunta jahad tayi tare da cewa “A’a hosana in ki ka kwanta ƙasan nan wlh ƙwarin nan shigar miki cikin kunne zasuyi suyi miki illah,’ ta faɗi tana kallonta cikin karayar zuciya,

      Muryar tamkar zatayi kuka hosana tace “to ya kike so nayi jahad ! A tsaye zamuyi baccin ne !!,

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

 

  Jahad tace “a’a bari ki ga dabaran da zanyi mana mu kwanta,” tayi maganar tare da sakin hannun hosana ta wuce inda jarkokin nan suke burjiki, tasa hannu tashiga ɗauko su tana kwantar dasu ƙasa a jere, kusan jarka Goma sha biyu ne, ta rabasu shida shida biyu na jikin biyu su ka ɗanyi faɗi, sannan ta ta ɗauki tsumman dake a ƙasan ledar ɗakin tashiga kakka6esu saboda sunyi ƙura ssae ga matattun girgizo asaman su, daker tasamu suka ɗanyi haske sannan ta wurgar da tsumman, ta cire mayafin jikinta wanda saude tabata, ta shimfiɗa musu asaman jarkokin, 

  murmushi hosana tayi na jin daɗi ganin irin dabarar jahad, gashi ta mayar da Jarkoki sun zama kamar single bed,

     Itama jahad ɗin murmushi tasaki tare da juyawa ta kalli hosana tace “To ya kika gani yanzu? 

     “Yayi kyau ssae jahad ,” ta bata amsa da murna a fuskarta,

    “Zoki kwanta to,”  jahad ta faɗi tana Yi mata alamar tazo ta kwanta,

Wuce wa hosana tayi tare da hayewa saman jarkokin ta kwanta, sannan itama jahad ta hau a hankali ta kwanta suna fuskantar junan su,

      tace “mu kuma haka rayuwarmu zata ƙare Ko jahad? ko munyi addu’a Allah baya kar6a……

  Cikin sauri jahad tace “Waya faɗa miki? Karna sake jin kince haka, Allah shi ya halicce mu, kuma yana sane damu, yana jarabtarmu ne ba don baya sonmu, face donya jaraba ƙarfin imanin mu, in har muka cinye jarabawar nan, zamu kasance masu nasara arayuwa,’ 

   Hosana tace “Yaushe jarabawar zata ƙare jahad? Ae anyi mana dayawa yakamata suma wasu a ɗandana musu jarabawar mukuma mu huta,’ 

    Murmushin takaici jahad tayi kafin tace “Allah shine mafi sani hosana, mu ci gaba da addu’a kawai kada mu daina, domin Allah yana fushi da duk wanda baya rokonsa,’ 

    Cikin sanyin murya hosana tace “Insha Allah bazamu fasa Yin addu’a ba, muna kai kukan mu wurin  Allah ba, har sai ranar da muka koma gare sa,

    Murmushi jahad tayi tare da cewa “Hakane hosana,”

    A haka har wani wahalallan bacci ya kwashe su, tsakar dare wani uban zafi ya fargar dasu, wata irin zufa ce ke zazzafowa daga jikinsu,

    Hosana duk ta razana sai kuka take ta faman yi saboda bata da juriya duba da halin da take ciki ga ciwo ga ta6in hankali,

      Daker jahad ta shawo kanta, da cewa ta kwanta ita zatayi mata fifita, cikin kuka tace “dame zakiyimun fifitar,”?

    Jahad tace “Hijab ɗin jikin ki, zaki bani,” hannu hosana tasanya ta cire guntun hijab ɗin dake ajikinta wanda saude tabata, ta miƙawa jahad, Sannan ta kwanta saman jarkokin,

     A haka Jahad ta shiga yi ma hosana fifita tana kore mata saurayen dake shawagi asama, nan take bacci ya ɗauki Hosana mai nauyin gaske,

     Baiwar Allah Jahad idonta sunyi jawur saboda jin bacci, amma sam tagaza runtsawa saboda fifitar da take yima Hosana, tana tsananin tausayinta ssae, tana jin son ƴar uwarta bazata so wani abu ya kuma cutar da ita ba,

    Tana Hamma tana yi mata fifita idonta na rurrufewa saboda bacci Amma haka ta jure ta tsayar da kanta don hosana tasamu isasshen bacci 😥 wani sa’in in tana gyangyaɗi har kusan faɗama Hosana take ta galabaita ssae, 

Rayuwa kenan wasu mutanen basu da ɗigon imani aransu, basa tuna dame aka haliccesu, basa tuna ta yadda suka zo duniya, Son zuciya kawai, Ynx duk girman gidan general ishaq a ƙalla ba’a rasa bedrooms sama da shida, ga palor Amma a rasa inda za’a ba rai ya kwanta don baƙar mugunta da zalunci sai Store ɗin ajiye tarkacen buhunhuna da jarkoki? Wasu mutanen dae ba tausayi aransu,😿

Masu gidan na can suna shan ra6ar a.c a haɗaɗɗun bedrooms ɗinsu yayin da sukuma suke nan suna fama da Uban zafi, haƙiƙa su hosana sunyi dana sanin zuwansu gidan nan , sai suka ji dama Yaya Omar ya barsu gidan Goggon katsina da aunty saude, Allah sarki ƙaddara ta riga fata 😖

 

**********************  ⬇ **************************

**********    Ai Hausa Novels  ****************

*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

 

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 08138873799

Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

**********************  ⬇ **************************

***************   Ai Hausa Novels   ****************

**********************  ⬆ **************************

_ku gyara zama domin kuwa yanzu hot pages suka fara, da zafi zafinsu hada hayaƙi ma🔥😅 Sannan kada maganar payment ta sagar muku da guiwa zanyi muku sauƙi ssae, kuma ku shaidane akan littafin nan in yayi daɗi ma kunsani ba asara zakuyi ba_ 🤝💋

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Back to top button