Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 18 Book 2 Complete Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

~~~~~~~~SEHRISH

Jin knocking yasa ta tayin saurin miƙewa daga zaunan da take saman gadonta , ƙarasawa tayi jikin ƙopan tare da cewa “Wanene”?

“Aunty azmee ce” ta bata amsa daga waje, 

Ajiyar zuciya sehrish tasaki tare da buɗe mata ƙopan, shigowa azmee tayi jikinta na sanye da Doguwar riga sai babban mayafin da ta yafa,

“Ƙanwata me kke yi yanzu ne? halan kina nan zaune cikin damuwa ko? ko irin kiyi tunanin kin gaji da zaman kaɗaici ki kawomin Ziyara a bedroom ɗina bakya yi ko?

 

tayi maganar tana kallonta, cikin jin kunya sehrish tace “Aunty azmee bana so na taƙura maki ne, shiyasa bana zuwa ɗakin ki,” 

Murmushi Azmee tasaki tare da cewa ” babu wani batun takura anan, kawai bakya son zuwane, nima kaina gajiye nake da zama wani sa’in duk atukure mutun kamar maye shikaɗai a ɗaki haba,” 

azmee tayi maganar tare da shigewa cikin ɗakin sehrish tasamu wuri ta zauna gefen gadon, itama sehrish ɗin wuri tasamu gefen azmee tana fuskantarta,

Kallon juna su kayi lokaci guda suka sakarwa kansu murmushi, Azmee tace “Naji shiru baki tambaye ni game da sabuwar wayar da nace an baki ba”? 

Sehrish tace “jira kawai nake, in kin bani in kar6a,” 

Jinjina kai azmee tayi tare da cewa ” kiyi hkr sai zuwa gobe wayar zata iso,” 

“Babu komai aunty azmee zanjira ni da za’a taimaka mawa abani kyauta, amma aunty azmee wanene ya siyamun wayar”?

ta tambaya tana kallonta,

“Ba abani iznin in faɗa ba, sai nan gaba zaki ji koma wanene,’ 

  Murmushu sehrish tayi tare da cewa “Allah yakaimu time ɗin da rai da lpy

“Ameen” azmee ta amsa mata sun ɗan yi shiru na ɗan wani lokaci, kafin sehrish ta ce “Aunty azmee wai su Babban yaya Ina mahaifiyarsu take ko ta rasu ne? ta tambaya tana kallonta ,

“tana nan mana, tana zaune a sydney ƙasar Australlia,’ 

Jinjina kai sehrish tayi kafin ta kuma cewa “Amma mommynsu ita ba ƴar nigeria bace ko?

“Kin ga hotanta ne”? Azmee ta tambaya 

Murmushi sehrish tayi tare da cewa “ban shaida ba, amma naga hoton wata mata Mai kyau baturiya mai sanye da kakin Soja a bedroom ɗin Babban yaya saman bedside drawer aka ajiye hoton,

Azmeee tace “dawa tayi miki kama acikin su”?

Sehrish tace “Babban yaya sunyi kama ssae hada blue eyes ɗinsu ma, sai kuma su twins da fawan, amma dae aunty Azmee dukansu ba uwarsu ɗaya ba ko? Ta ƙarasa maganar tata da tambaya, 

Azmee tace “eh su Twins da fawan da Babban yayansu da junaid uwarsu ɗaya, suma su Kanal Yusif mahaifiyarsu daban’

Jinjina kai Sehrish tayi tare da cewa “Su mommynsu ƴar wata ƙasa ce aunty azmeee?

Cikin zolaya Azmee tace “Kice yau kin shirya son sanin wacece surikarki da alama naga kina ta jefamun tambayoyi akanta ko ba haka ba”?

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Sunnar da kai sehrish tayi tana kallon yatsun hannunta cikin jin kunya 

Azmee taci gaba da cewa “Sunan ta *Fatima ita ƴar America ce amma tana zaune a Australlia,” 

ɗan shiru tayi na wani lokaci kafin ta sake cewa “Aunty azmee Yaushe zata zo nigeria ne? ita bazata zauna nan ba ko Abba ya sake ta ne?

Dariya azmee tayi tare da cewa “Wasa wasa sehrish kema fa kin iya surutu na lura wurine baki samu ba shiyasa kike noƙewa kamar bakyason magana,” tayi magana tana ɗan kallonta, 

“In har aka tashi aurenki da babban yayansu ae dole tazo asha biki da ita,”

Jin wannan maganar ta aunty azmee yasa Sehrish ɗan zaro ido hada dafe ƙirji aranta tana cewa “tab ! Wannan matar ta cikin hoto anya xata barni in zama surukarta daga gani zatayi zafi Allah,

Murmushi kawai azmee takeyi tana kallon Sehrish dake faman sake sake aranta, 

Ita kanta Azmeen  zolaya take mata amma tasan cewa sarai Alexandra bazata ta6a bari Sgr ya auri bakar fata ba, 

Sun jima suna fira har wurin sallar la’asar sannan azmee tayi mata sallama ta fuce izuwa nata ɗakin,

 

tashi tayi itama ta shiga ta ɗauro alwala tayi sallah, bayan tagama ta shirya zuwa kitchen don tasan da wuri zasu fara preparing dinner,” 

  time ɗin da tafito babu kowa wayam falon kai tsaye kitchen ta wuce, azmee bata iso ba don haka tafara fiddo abubuwan da zasu yi amfani dashi, tafara aikin kafin ita tazo,  Aiki take amma hankalinta natashe tarasa dalilin dayasa take jin wani irin ɗaci aranta, wanda hakan alama ce dake nuna cewa waninsu nacikin matsala, Ita ko suna hosana 

   Har azmee ta shiga sam sehrish bata ankara ba har sai da tace “Good girl haka nakeso kina aiki da azama,” murmushi sehrish tasaki tare da kallonta tace “Aunty azmee ae dama baki fito ba ni namiki aikin duka,’ 

   ɗan harararta Azmee tayi tare da cewa “Ki zubamin detergent aciki a matsayin gishiri?  

  Dariya sehrish tayi jin abunda tace “No aunty azmee bazan sake wannan mistakes ɗim ba,’ 

    Azmee tace “Hmmmm zamu gani ae,’ 

Shiga ciki tayi suka kama aiki cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala, basu jera abincin a dining ba sun bari sai after magriba prayer,”

  Cike da zumuɗi ta shiga tayo wanka, ta kimtsa kamar kullum, hada alwalarta jira kawai take Yi a kira sallar magrib taje su haɗu da junaid cos she’s so eager to see him,’ 

  _________________________________

Fitowa daga wanka junaid yayi fuskarnan a washe zai haɗu da sehrish ɗinsa, daga shi sai shorts ajikinsa, shaf shaf ya shirya cikin shirt ash colour mai dogon hannu sai dogon wando black colour, wow baƙaramin kyau kayan su kayi mashi ba, ya feshe jikin shi da turaren spice bomb sannan ya zura shoes a ƙafansa launin wandonsa, 

 Hannun nan nasa na manne da wrist watch ta diamond mai kyan gaske,  ya fito fess abunshi, 

   Time ɗin da ya fito ana cikin kiran sallar ne, don haka yayi deciding zuwa yayi sallah in ya dawo direct zai wuce garden, 

Sehrish

Bayan tayi sallah ta fito don ta wuce wurin haɗuwar tasu a hanyar fita kwatsam suka ci karo da Haroon wanda shigowarsa kenan, 

  Ji tayi gabanta ya faɗi rass, murmushi yasakar mata tare da cewa “ta kwana gidan sauƙi, dama don ke nashigo ciki don haka ki haɗomon Tea ki kawomin yanzu a bedroom ɗina i wll be waiting,” yana faɗin hakan ya wuce part ɗinsu, 

   Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, ga junaid tasan already now he is waiting for her and now ga haroon na jiran takai masa Tea, kuma batasan me yake son ce mata ba, 

   Addu’a kawai takeyi acikin zuciyarta, juyawa tayi ta shiga kitchen ɗin, ta haɗo masa tea ɗin sannan ta fito ɗauke da cup ɗin a ɗan plate ɗinsa,’ 

     Tsayawa tayi a bakin door room ɗin nasa ta yi masa sallama muryarsa taji ta ciki yana cewa”Antayo kawai,” 

   Wato bama sai ya amsa sallamar ba, zuciyarta na ɗar ɗar ta shiga, yanayin da taganshi yasa hankalin ta tashi matuƙa, ya cire kayan jikin shi daga shi sai shorts, jikin nan nashi duk hairs fitowarsa kenan daga bathroom yana ganin ta ya tsaya yana bin ta da kallo, ” 

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng


    Murya na rawa tace “Ga tea ɗin,” da buɗar bakinsa sai cewa yayi “Ni ba tea nake buƙata ba wadda takawomin tea ɗin nake buƙata,’ 

     Baki asake sehrish ta tsaya tana kallonsa, bi yayi ta gefenta ya isa izuwa kopan ɗakin ya datse shi don kar wani ya faɗo ciki,” 

   Hankalin sehrish fa ba ƙaramin tashi yayi ba kallonsa kawai take yi jikinta na kerma, 

   Dawowa yayi inda take yasanya hannun shi ya kar6i kayan tea ɗin ya ajiye su asaman bedside table ɗinshi, 

  Sannan ya ɗago yana sakar mata wani irin shu’umin murmushi, matsawa yayi kusa da ita cikin tsananin tsoro sehrish ke ja da baya har sai da ya ƙure ta, 

   Cikin tsananin tashin hankali tace “Wai me kake so ne !? Why u closed the door pls ‘? tamkar zatayi kuka tayi maganar, 

      “So nake ki shayar dani that’s what i want,” 

     Zaro ido sehrish tayi tana girgiza mishi kai tace “bangane ba nashiga uku !!!,” 

    dariya haroon yayi kafin ya ɗaure fuska yace ” Feeding ɗina zakiyi kamar yarda uwa take shayar da jaririnta nono, shine abunda nakeso in kuma kika bijire mun, Hmmm kin shiga Uku !!! don kuwa zan tona miki asirine kowa yaji cewa ke maca ce, da zarar hakan ta faru kin mutu yarinya, 

  Fashewa da kuka sehrish tayi lokaci guda, tsawa haroon ya daka mata tare da cewa “Ke!! Yi mun shiru, ko da yake ci gaba da kukan idan wani yaji ya tambayi jin ba’asi zan sanar mishi cewa ke macace !!.    

“Dan Allah ka yi hkr ka kyaleni in tafi, bazan iya aikata abunda kake so ba, meyasa zaka neme ni da fasikanci kaifa musulmi ne kaji tsoran Allah………..

  Tsawar da haroon ya daka mata ne yasata yin shiru, matsawa yayi ya matse ta jikin bango har numfashinsu na harhaɗuwa,

Wata irin Zufa ce ke wanko mata mai zafin gaske ta jikinta, haroon ya matseta daker take numfashi, 

       Cikin shesshekar kuka tace “dan Allah  …….’ bata ƙarasa ba taji shigar harshen shi acikin bakinta duk yadda taso ta kwace kanta ta buge haroon ta gudu amma hakan ya faskara, yadda yasa dukan hannayensa yana shafa jikinta, ƙoƙarin cire mata rigar jikinta yake yi ma, har time ɗin bai janye tongue ɗinshi daga nata ba sai faman sucking lips ɗinta yake yi, 

Kuka takeyi kamar ranta zai fita wani irin raɗaɗi mai ɗacin gaske take ji aranta, 😥

Ayayin da sehrish ke cikin wannan tashin hankalin, shi kuma junaid bawan Allah yana a garden yana jiran zuwanta, sai faman dube dube yake yi yana tunanin kota ina Sehrish ɗinsa xata 6ullo, amma shiru ga yunwa yana ji ssae, amma yayi alƙwarin bazai ta6a barin garden ɗin ba har sae sehrish tazo sun ga juna , 😥 

Ringing ɗin wayarsa ne ya shigo da ƙarfin gaske hakan yasa yasaki sehrish da sauri domin dama there’s important call da yake jira wanda baxae bari yayi missing ɗinshi ba,

Cikin sauri ya isa inda wayar take saman gadonsa, hakan yaba sehrish damar watsa wa da gudun gaske daker tasamu ta buɗe kopan room ɗin nasa ta fuce tana shesshekar kuka,

 In da Allah yasota babu kowa a main palor ɗin , da gudun gaske ta wuce bedroom ɗinta kai tsaye ta faɗa saman gadonta, jikinta na wani irin kerma ga uwar zufa, wani irin ƙyanƙyamin tadinga ji wanda hakan ya haifar mata da jin amai, nan take tafara yunƙurin aman jiki na rawa ta miƙe daga kan gadon ta faɗa toilet haka ta rinƙa kwarara aman kamar kamar me, bayan ta kammala tasanya ruwa sosai ta korasa, sannan ta shiga wanke mouth ɗinta, ji take haroon najasa ya goga mata, 

Sai da tayi brush ta gurje bakinta har sae da le6enta ya fashe sannan tasamu salama azuciyarta, 

    Tasha kuka kamar kamar me, taji tsananin tsanar Haroon a zuciyarta, domin duk namijin dayayi attempting touching some part of her body, tsanar shi take yi gaba ɗaya, 

    Fitowa tayi jiki asanyaye ta haye saman gadon tayi covering jikinta da bargo tana ci gaba da kuka kamar ranta zai fita, sam ta manta da maganar gaɗuwarsu da Junaid,

Haroon ko baiso kiran nan yayi interrupting ɗinsa ba, yaso ace ya idasa nufinsa ga yarinyar, sae faman huci yakeyi gaba ɗaya ya kwaɗaituwa da son kasancewa da yarinyar domin bai ta6a jin macen da lokaci ɗaya ta tayar mishi da sha’awarsa gaba ɗayaba ba irin yarinyar, yaci alwashin sai ya ci gaba da yi mata barazanar zai tona mata asiri in ba tayi masa abunda yake so ba , 

___________________________________

Sam ya gaza manta fuskar twins ɗin, tsananin kewarsu ce ke ɗawainiya dashi, bakomai yake tunawa ba face yadda hosana ta faɗo mishi ajikinsa a asibitin nan, haƙiƙi wannan wani yanayi ne da bazai ta6a mantawa arayuwarshi ba, 

Bakowa bane yake wannan tunanin ba fa ce marshal omar, wanda ke a hakimce cikin haɗaɗɗiyar motarsa mai lumfashi ana driving ɗinsa, ya jima da shigowa abuja batare da yasanar da kowa ba, ya fara biya wa guest house ɗinshi ya huta ssae sannan ya shirya shigowa cikin gidan nasu, 

A dai dai time ɗin da motocin shi ke shiga cikin gidan, suka haɗe dana su Sgr, da su kanal yusif duka a lokaci ɗaya suka jero izuwa cikin gidan kowa ya dawon kenan, 

   Kusan tare duk su kayi parking ɗin motocin nasu, fitowa Omar yayi fuskarshi ɗauke da murmushi ganin mutuminsa ɗan uwansa rabin ransa wato Rafayet, wanda shima fitowarshi kenan daga motarsa, 

gaba ɗaya su kanal yusif suka firfito shi da sauran dukansu fawan twins, Jabeer irfan da khaleed farin cikine ƙarara A fuskansu ganin Yayan nasu yadawo sunyi missing ɗinshi sosai,

    Ƙarasawa su kayi inda yake suka shiga rungumarsa ɗaya bayan ɗaya,

Har haɗa baki suke yi wurin cewa “yaya Omar munyi kewarka ssai, bamusan yau zaka dawo ba kayi mana zuwan bazata,” 

   Murmushi Omar yasaki tare da cewa “I miss u 2 guys hope nasame ku lpy ? 

   Suka amsa mishi da ” muna lfy Alhamdulillah,” 

 “Good” ya faɗi tare da matsawa inda Sgr yake jikin mota jingine yana kallonsa, fushi yake dashi dama bada son ranshi ba ya tafi,

     ganin ya tunkaro shi yasa shi dakatar dashi tare da cewa “kada ka kuskura kace zaka zomin nan, i don’t wanna see u bansan ka ba,” 

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng


    Da dariya a fuskar Omar ya ƙarasa yana faɗin “haba lion in nazo ka kashe ni, amma nikam sai na rungumi sanyin idaniyata,” 

  Yana faɗin hakan yasanya hannu zaiyi hugging ɗinsa, sgr yajanye jikinsa tare da kai masa punch a ƙirjinsa, aikuwa omar ya daddage shima yakai mashi naushi,

 Zuba ido su kanal yusif su kayi suna kallon ikon Allah dama haka suke da wasa da wasa su jibgi junansu abun ajininsu yake sun saba, 

    kamar afilin dambe suka shiga kaiwa juna naushi a ƙarshe kuwa sgr ya janyoshi tare da rungume shi ajikinshi ssae yace “Tiger I missed u so much, ka tafi kabarni,”

     dariya Omar yayi tare da cewa “Wato shiyasanya ka nannaushe ni saboda ka huce haushinka ko? 

   “Eh mana,” ya bashi amsa ayayin da Omar ke janye jikinshi daga na sgr yace “mu shiga ciki Har ynx akwai gajiya atare da ni, ” 

.. Jerewa sukayi suna tafiya yayin da su yusif ke bayansu,

    “Abubuwa dayawa sun faru a tafiyar danayi, omar yafaɗi a lokacin da suke shugewa palor ɗin,

   “Haba kamar me”? Sgr ya tambaya,

Omar yace “Idan na huta zuwa gobe zaka sha story bro,” . 

   Jinjina kai Sgr yayi tare da cewa “Okey,”

Sai da sgr yakai Omar har izuwa bedroom ɗinsa dake a upstairs sannan ya wuce nashi,

Rage kayan jikinsa yayi sannan ya shiga towel yayi wanka ya fito ɗaure da towel a waist ɗinshi, gaba ɗaya jinsa yake cikin nishaɗi musamman da yaji shi acikin gidansu cikin ƴan uwansa, duk da tunanin twins ɗin nan na ɗawainiya dashi, yaso ya kira yaji ya suke bayan daya barsu amma yyi deciding ya bari sai da safe ya kira Aunty babba ta basu wayar, 

    Dressing kan shi yyi cikin sleeping dress riga da wando masu kyan gaske milk colour zo kaga ruwan kyau, Omar fa na musamman ne, feshe jikinsa yayi da turare sannan yasa hannu ya ɗauki wayarsa da ya ajiye a gaban mirror, 

    Missed call ya gani na Abban su murmushi yasaki tare da cewa “Abbana kenan baka mantawa da ƴaƴanka duk yawanmu,” 

    Zama yayi a bedside sannan ya danna wa Abban nasu kira bugu ɗaya yyi picking thats means jiransa yake ya kira dama,

   tunkan yayi sallama Abban yasoma magana “Omar ka shigo Abujan ne? nayi trying number ɗinka baka ɗaga ba why ‘

    Cikin natsuwa yace “Abbana nasanya wayata silent so bansan ka kira ba am sorry for that, ynx haka ina a cikin gida,

     “Alhamdulillah Omar naji daɗi sosai, da Allah ya mai domin kai lafiya, kayi wanka ka ci abinci ko”?

     wannan magnar tasa Omar jin tsananin ƙaunar Abban tasu haka yake duk da girmansu in ya kirasu a phone sai ya tambayesu sun ci abinci sunyi wanka, Soyayyar mahaifi kenan 

     “Abbana nayi abinci ne kawai zan nema yanzu, yaushe zaka shigo gida ne “? Omar ya tambaya,

       “Akwai abunda ya tsaida ni ne, amma insha Allah wurin ƙarfe 12 zan shigo,”

    Omar yace “Allah ya shigo dakai lpy, my dad i will be waiting to ave ur hug,” 

  Sun jima suna waya, daga bisani omar ya ajiye wayar gefensa, da murmushi a face ɗinsa, kulawar da abbansu yake basu na matuƙar ƙara musu jinshi azuciyarsu 

( Allah sarki yayin da wasu basu da Uban wasu kuma akwai uban amma baisan ya kula dasu koya damu dasu haka ba)

Azmee ce kaɗai ta fito ta wuce kitchen domin shirya abincin, ita kanta tayi late wurin zuwa shirya musu dinner ɗin, hakan yasa bata tsaya neman sehrish ba, ta wuce kitchen ta shiga kwaso warmers ɗin acikin tray tana kaiwa saman dining table, 

 tunkan ta idasa jerawa ma, suka fara fitowa kowa sae hamma yake a yunwace suke da alama, 

  “Aunty azmee 2 times kenan ina leƙowa daga bedroom ɗina in ga in an shirya dinner amma ina ganin ba komai,”  fawan ne yayi maganar yana shafa ciki, 

   Murmushi azmee tasaki tare da cewa “kuyi hkr dan Allah, wlh bacci ne ya ɗan kwashe ni,” 

   “Ai kina ma ƙoƙari Allah, girka wa ƙattai abinci, ɗawainiya da tazurai ae is not a simple ɗin wlh,’    ɗagowa su kayi gaba ɗaya dan suka wanene me maganar haroon ne wanda shima fitowarsa kenan, 

   kawar dakai kowa yyi cike da jin haushin maganarsa, zama kowannansu yayi, twins na kusa da junansu sai fawan, su irfan da jabeer da khaleed suna facing ɗinsu,

   Sai haroon daya iso shima yasamu wuri ya zauna yana faɗin “don ƙaniyarku bazaku gaishe ni ba? wai me kka maidani ne sai kace ba yayanku ba, yayi maganar yana kallonsu,

     banza su kayi dashi sai fawan ne yace “babu kyau ana cin abinci ana surutu,” 

“To fitsararre iya magana dama ae ammi ta faɗi cewa bakujin magana kamar uwaku,” 

 Rai a6ace suke kallo shi abunda suka tsana kuma basa so, ganin sun ji haushi yasa shi ci gaba da cewa “Ƙarya nayi ne? Ammi tace ƴa’ƴan fatima fitsararru ne masu jan kunne ƙarya tayi ne”? ya tambaya yana kallonsu,

    Rai a6ace khaleed yace “yaya Haroon ka daina menene haka wai? taya zaka rinƙa cin mutuncin ƴan uwanmu agaban mu?

  Azmee dake a tsaye hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, gashi bata da ikon dakatar dasu ƙa’idar aikinta kenan,

       “Ta ina suka zama ƴan uwanku? uba kawai kuka haɗa dasu bayan nan sai me? uwa kowa da tashi, kun manta irin tsanar da Uwarsu take yi maku ? Ita batasan baƙar fata,

     A zafafe Jahan yace “Kai ya isa wlh, kabar ganinka yayanmu wlh zanci maka mutunci a wurin nan,

     “Dama ae baku da mutunci gashi ka faɗa da bakin ka, ae gadonsa kayi wurin uwarku,”

   Ruƙe hannun jahan Ayaan yayi ganin yana ƙoƙarin tashi yakaiwa haroon bugu, shima fawan ƴunƙurin yayi amma irfan ya dakatar dashi,

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

   duk wannan maganganun na Haroon a kunnan Marshal Omar wanda ke tsaye saman stairs yana sauraronsu, babu wanda yasan cewa ya fito, 

    Haroon yaci gaba da cewa “Ae da kunbarsu Allah jiki magayi in ma yara……..’

   Shaƙar da Marshal yayi masa ce ta bayansa yasan shi dakatawa, da karfin gaske ya ruƙo kwalar rigar haroon gaba ɗaya ya wuntsilo dashi ta bayan daga saman kujerar sai gashi ƙasa baje

Wani irin sanyi suka Ji aransu, dama ya hanasu sakat ya hanasu cin abincin ga yunwa suna ji,

    Wani irin biji biji haroon ya rinƙa gani murya na rawa yace “Ya Allah ka nuna min annabi kamar yadda naga wannan bawan naka zahiran a idona,” 

        Damƙoso Omar yayi tare da ɗagosa ya buga shi ƙasa da karfi sai ga haroon asusuce kamar wanda aka zarewa lakar jikinsa sam ya fita hayyacinsa agigice yake faɗin ” Innalallahi wa’inna ilahirraji’un akashe ni kawai a huta,” 

  su fawan sai faman murmushi suka saki ita kanta azmee ba ƙaramin daɗi taji ba, ci gaba da saving ɗinsu tayi, ta zuzzubama kowannansu, cikin nishaɗi suke cin abincin nasu suna kallon yadda Yaya Omar ke jibgar haroon,’

         “Bazaka min shiru ba don ubanka,” marshal ya faɗi a fusace

      “Ae wlh sai dae akashe ni,” agalabaice haroon yayi maganar,

      Miƙar dashi tsaye Marshal yayi a lokacin so yayi ko hannunsa ne ya gota masa wata’ƙil yashiga taitayinsa,  cikin sauri kanal yusif ya iso yana faɗin “Yaya Omar ae masa afwa ya jibgu ae,”

      Tsoki Omar yaja tare da yin wurgi da haroon kamar kayan wanki haka ya gangara saman tiles ɗin yana faɗin ” sakayya na wurin ubangiji, sai mun haɗe a ƙiyama kowa zaiyi bayani,” 

   Fashewa da dariya su fawan su kayi, shikansa marshal abun yaso ya bashi dariya, wato shi bakinsa bai ta6a mutuwa sai dae akashe shi kamar yadda ya faɗa, 

    Wuce wa Omar yayi shida Kanal yusif suka zauna,

    Cikin girmamawa ya gaishe da azmeee, murmushi tasaki tare da cewa “Omar saukar yaushe? ashe ka dawo,

  “Ban jima da shigowa ba,” ya bata amsa,

“Ya gajiyar tafiya “? ta tambaya tana kallonsa,

  “Alhamdulillah gajiya tabi jiki,” ya faɗi ayayin da yake kai kofin Tea ɗin da azmee ta zuba mishi abakinsa yana sha,

   Muryar haroon suka ji yana cewa “ae dole gajiya tabi jiki yaya omar tun da anjibgi ƙato kamata agaban ƙanne na,’  Yyi mgnr tare da miƙewa  yana harararsu Su twins da fawan saboda jin haushinsu da yake yi, yana baƙin ciki dasu, kullum gani yake yi Abbansu yafi son su ƴa’ƴan Mommy alexandra akansu, kullum da wannan baƙin cikin yake kwana, kuma yaci alwashin in bai yi sanadiyar Mutuwarsu ba saiya naƙasa su !!!!!!!!!!!

Fasa cin abincin yayi ya wuce bedroom ɗinsa yana huci,

Natsuwa su kayi suna cin abinci kowannansu ya lura babu junaid amma sai ransu yabasu cewa yana a bedroom ɗinsa yana bacci, hakan yasa basu damu ba,

Bayan sun kammala kowa ya wuce ɗakinsa domin baccin da suke ji ssae, 

Junaid fa har time ɗin yana a garden ƙanƙame da jikinsa saboda sanyi, ko’ Ina  Na jikinsa rawa yake yi  amma yagaza tashi yabar garden ɗin saboda sunyi da sehrish zata same shi acan, bawan Allah gashi athmatic, That’s the secrets Of true Love

Sehrish kuwa kamar matatta haka take kwance idonta luhu luhu, wasu siraran hawaye ne masu xafi ke saukar mata daga eyes ɗinta, haroon ya ƙuntata mata yasa ta tsani jikinta, ko’ina ƙyanƙyaminsa take ji,

Ga wani matsanancin ciwon kai da take fama dashi saboda kukan da tasha, ga zazza6i duk ita ɗaya, duk wannan bai hanata tunanin Sgr ba, shin yaci dinner ɗinsa kuwa, so take ta tashi taje ta dubasa amma tsoran karta haɗuwa da haroon ya hana ta fita, 

Aunty azmee itace takai masa dinner ɗinsa a part ɗinsa, har ɗagowa yayi ya kalleta a tunaninsa mai aikin nan ne da akace masa maca ne, wanda yake so yakama hannu dumu dumu.

A 6angaren su Hosana kuwa, tun da suka samu su kayi wanka suka yi alwala da sallah, basu yi kuskuren fitowa daga ɗakin ba, tsoransu kar wannan matar ta shigo basu son dame zata fara musu ba, 

Yinin ranar cikin fargaba su kayi shi, suna ta faman zagaye zagaye a ɗakin, sallah ce kawai ke tsaida su,

Daga bisa ni  bayan sallar Magrib ne bacci ya kwashe su a saman shimfiɗeɗen gadon dake ɗakin, sun sha gajiyar tafiya hakan yasa sukai ta sharar bacci kamar matattu, 

A tsiyace Ta shigo da motarta acikin gidan, tayi parking ɗinta a wurin ajiye motocinsu, sannan ta harba murfin motar da ƙafarta don bala’i ta bude sannan ta fito,

Jikinta na sanye da less tsadadden gaske blue colour yasha adon duwatsu, less mai tsada amma an wulakanta shi wurin ɗinkinsa, 

Riga da skirt ne rigar ta matse ta ƙam kamar zata tsage, wuyan rigar yayi girma sosai tamkar boob ɗinta zasu fito dukansu, 

Skirt ɗin kuwa ya ɗameta over, ga wata uwar tsaga da akayi mashi tun daga guiwarta tsagar ta fara har ƙasan ƙafarta, kuma daga ciki batasa komai ba,

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Hannunta na sanye da knuckle rings, mai kyan gaske Hancinta ma nasanye da Nose ring, 

tana riƙe da  purse A hannunta launin kayanta, 

fuskarnan na sanye da Makeup hada eye lashes tasa na kanti tayi fixing,

 bakin nan nata yasha uban jan baki red colour  Sai faman taunar cingam take yi a tsiyace, 

ɗaurin ɗan kwalin kanta kadae ya isa ya tabbatar maka da cewa bata da sauƙi,

Cike da yauƙi tashiga tafiya kwas kwas saboda ƙafarta na sanye da wasu matsiyatan high heels masu tsinin gaske, 

Kai tsaye ta wuce bedroom ɗinta, hannu tasa ta turo kopan tana faɗin “am so tired ina buƙatar watsa ruwa naci abinci nayi wan……..’ 

Bata idasa ba saboda abunda tagani kamar a mafarki Yan mata saman gadonta suna bacci, 

Hannunta tasa ta murza idonta donta tabbatarwa kanta abunda take gani aikuwa ta sheda hakan

  A fili tace “Bura’ubancan !!! Yau akeyin ta wlh,” 

  Wurga purse ɗinta tayi saman gadon sannan ta fuce waje a tsiyace take kwalawa Aunty Babba kira 

“Mom!! Mom!! Mommyyyyyy !!

A razane aunty babba ta fito daga bedroom ɗinta ta sauko down tana faɗin “Hafsat meya faru haka kke kwalamun kira haka ? yaushe kika shigo ne?

ta tambaya tana kallonta,

Uban tsoki taja tare da cewa “Mom duk ba wannan ba! Suwanene waɗancan yaran isassu dana gani kwance asaman bed ɗina? a faɗace tayi maganar tana riƙe qugu,

Aunty babba ta yatsina fuska tare da cewa “ni wlh sam nama manta dasu, wlh Omar ne ya kawomana tsintattun yara tagwaye wai su zauna tare damu acikin gidan nan na wani lokaci……….’ 

Zaro ido hafsat tayi tare da cewa “Jakar uban can kayyasa !!  sai kika amince ke kuma !?

Babu respect hafsat take magana da mahaifiyarta koda yake dama ance magaji mafiyi,

Yarfa hannu aunty babba tayi tare da cewa “To ya kike so nayi !? Omar fa ne ! Na isa na hana shi yin iko da gidan yayansa ?

Jinjina kai hafsat tayi tare da cewa “aiko zasu ci ubansu wlh ! they’ll regret being here in this home !

“Ae bama sai kin faɗa ba, ynx dai am sorry my daughter nakai miki su bedroom ɗinki, nayi hakan saboda Omar yana nan ne shiyasa nayi musu amma ynx wancan Tsohon Store ɗin zan maidasu da zama ciki,” 

Jinjina kai hafsat tayi tare dace “Can yafi dacewa dasu yanzu dae muje a fitar mun dasu daga bedroom ɗina, ni saina ma Canza bedsheet Allah, sannan ina jin yunwa hope kin shiryamin abinci na Mommy,” tayi maganar tana shafa ciki

Aunty babba tace “dolena ne wannan, yanzu muje ɗakin mu fitar dasu, kisamu kiyi wanka na shirya miki abinci kici,

Atare da aunty babba suka shiga cikin ɗakin, su hosana bayin Allah na kwance suna sharar bacci 

hafsat tace “Eyyehh !! Banza tasamu an haye mun gadona ana sharar bacci, wlh nasan maganinsu,’ 

 Tana faɗin hakan ta juya ta fita daga ɗakin izuwa parlor in da freezer take, 

Murmushi aunty babba tayi don tasan me hafsat zata ɗauko,

Aikuwa sai gata hannunta ɗauke da Cool water har yasoma ice acikinsa cikin ƙatuwar bottle, 

Dariya aunty babba ta fashe da ita, tana faɗin “Good my daughter hakan yayimun wlh,” 

Cire murfin robar tayi batare da tausayi ba ta zazzaga musu ruwan mai matuƙar sanyi a jikinsu, 

A firce jahad da hosana suka farka jin dirar ruwa mai sanyi ajikinsu, jahad na faɗin “innalallahi wa’inna ilahirrajin’un, muryarta tamkar zatayi kuka ita kuwa hosana fashe wa tayi da matsanancin kuka saboda bata son sanyi balle ita mai asthma, jikinta har wani irin kerma yake yi,

  Ido luhu luhu yayi jawur daker suke kallon Aunty Babba da hafsat dake tsaye suna kallonsu,. 

  Hafsat tayi mamakin kamannin su iri ɗaya sak aranta tace “Ashe har ynx ana yin twins masu kama da juna haka, ba laifi suna da kyau,” 

  A fili kuma ta daka musu tsawa har sai da suka firgita Hosana ta ƙanƙame jahad don batason sauti mai ƙarfi,

 “GET UP !!!! Maza a tasarmun daga gado na, ku sauko Mun haka nan ankawo mana mutane tsintattu cikin gida,’   tayi maganar tana yi musu alama da hannu na su sauko,

   Jiki na rawa suka miƙe tare da saukowa daga saman gadon jikinsu na rawar ɗari saboda sanyin A.c ne ya haɗu da sanyin ruwan da Hafsat ta watsa musu, 

    Tsayawa su kayi a tsananin tsorace suna faman shessheƙar kuka,

    Tsoki aunty babba tayi tare da cewa “ku biyo ni,” 

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

  Bin bayanta su kayi ta fuce dasu daga ɗakin, sunyi mamakin ganin suna ta faman tafiya acikin wata Corner na gidan,

Adai dai ƙopan wani Room ta tsayar dasu, hannu tasa ta riƙe handle ɗin kopar tare da buɗewa tace “To ƴan matan mama ga fa makwancin ku daga yau,’ 

    Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba domin kuwa, wani tsohon store ne na ajiyar kayan abinci, tarkace ne kamar hauka, jarkoki da galon aciki na manja dana mai da akai amfani dasu awargaje, Sun tsufa sunyi ƙura, ga buhun hunan Shinkafa dana gero dana fulawa duk gasunan, ƙasa kuwa sunkin doyoyoyi ne ajere da dankalin hausa dana turawa, da gunduwa gunduwar Albasa, babban tashin hankalin ɗakin ko fanka babu duk ƙura ga yanar girgizo har jikin bango, ga ƙwari kuma a ƙasan suna shawagi, Ga manyan drawers waɗan da ke a datse jikin bango da alama na ajiyar tarkace ne,’ 

  “Uban me kuka tsaya kuna kallo kushi ga mana! Ko saina shigar daku ne !?

    Basu yi mata musu ba jahad ta ruƙe hannun hosana suka shiga cikin store ɗin sannan aunty babba ta ƙara da cewa “daga yanzu nan ne wurin kwanan ku   Kuma wurin zamanku, saboda baku da gurbi acikin gidan nan,” 

   ta faɗi hakan tare da turo kopan kuma tasanya Key ɗin dake ajiki tayi Locking ɗinta, ba damar fita kenan, ko taya mutun zai iya kwakkwaran Numfashi a ɗakin nan !? 😰

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Back to top button