Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 17 Book 2 Complete Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

Wuce azmee tayi dakinta agajiye saboda ta samu ta huta, yayin da tabar sehrish tana faman kwashe dishes ɗin izuwa kitchen, bayan ta kammala wanke komai ta mayar dasu inda suke ta jera, 

Sannan ta kama hanyar futowa daga kitchen ɗin, sam bata lura dashi ba sai dae taganshi agabanta kamar Aljani, 

Tsorone ya kamata jikinta ya shiga kerma, dariya haroon yayi tare da cewa “Ina son ganinki baby da yaushe zamu haɗu ne,”? Ya tambaya yana kashe mata ido, 

Murya na rawa sehrish tace ” Zuwa anjima yanzu agajiye nake, inaso na huta,” 

Jinjina kai yayi tare da cewa “Okey, ki tabbatar kin kawomin kanki ɗakina, zan jira ki anjiman,” 

“Insha Allah,” ta faɗi tare da bi ta gefenshi ta wuce hankali atashe, tuni hawaye sun soma zarya a kuncin ta ,

tana shiga bedroom ɗinta ta shiga yarfa hannu tana safa da marwa, damuwa iri iri daga nan sai wancan, babban tashin hankalinta a yanzu batasan da wata manufa haroon ke nemanta ba, runtse ido tayi tare da faɗin “Ya Allah ka tsare ni daga sharrin wannan bawan naka, Ya ilahi ni ynx bansan ya zanyi ba, gashi yace nakai mashi kaina ɗakinsa,” ta ƙare maganar tana mai jin bugun zuciya da fargabansa, 

Daker ta tsagaita da zagaye zagayen da take yi a ɗakin nata, 

      gefen bed ɗinta ta hau ta ɗan kwanta eyes ɗinta na facing ceilling thinking abt many things, a haka har bacci 6arawo yayi awon gaba da ita, tasha bacci Ssae, dama ga weather ɗin is so comport,

Ba ita tafarka ba sai around ƙarfe 2 da mintuna har time ɗin sallah ya haura, tashi tayi tana dafe ƙirji domin kuwa har mafarkin haroon sai da tayi wai yace zai tona mata asiri wurin babban yayansu, da ta tabbatar da cewa mafarkine sai ta sauke ajiye zuciya tare da furta “Thank God it was a dream,” 

  Da hanzari ta shiga toilet tayi wanka ta ɗauro alwala, sannan ta fito ta nufi wardrobe tayi dressing kanta cikin riga da wando, sannan ta ɗauki hijab ta sanya, ta janyo sallaya ɗinta dake a saman murfin wardrobe ɗin dama nan take hanging ɗinta sometimes hada hijabin sallanta, 

     Shimfiɗawa tayi sannan ta kabbara sallah, a natse take yin ibadarta ta, bayan ta kammala  sallar ta zauna saman carpet ɗin ta lankwashe ƙafarta, ta ɗaga hannayenta  ta shiga jero addu’a, ta jima hada hawayenta domin tabbas tana ji aranta akwai wasu ƙalubalen da zata fuskanta acikin watan nan, tana roƙon Allah ya bata ikon cinye koma wata irin jarabawace sannan yabata damar tsallake duk wani ƙalubalen da zata fuskanta,” 😥

Bayan ta kammala ta miƙe tare da naɗe sallayar ta ninke ta sannan ta cire hijabin ta ninke ta itama ta tura su cikin wardrobe dukansu, 

Hayaniya taji daga harabar gidan alamar ana buga ball daga wajen murmushi tasaki tabbas tasan su junaid ne ke wannan,  wasan,  

Ji tayi tana marmarin itama ta kalli wasan ball ɗin nasu wataƙil ta rage ƙuncin da take ji a zuciyarta, 

   Da azama ta ƙarasa jikin window ɗinta ta naɗe curtains ɗin sannan ta zuge glass ɗin ta tsaya tana leƙensu, 

  Su 6 ne acikin ragar filin ball ɗin dake acikin gidan , shi da wasu daga cikin soldiers ɗin dake tsaren gidan, 

 time ɗin da ta aza idonta akan  junaid sai da taji zuciyar ta ta buga, sanye yake cikin kayan kallonsa riga da gajeran wando dai dai guiwarsa kana ganin waɗannan fararen ƙafafun nasa na rainon madara abun ba’ace wa komai,

 launin kayan nasa red colour ne, wayyo ruwan kyau white in red dress na pyjamas, abayan rigar tashi an rubuta (ROMEO) No 10,

  gaba ɗaya yazama tamkar tauraro acikin su sai faman tsalle tsalle yake ga kwantacciyar sumarnan tashi sai faman yarfo masa take saboda akwai Iska sosai a wurin,  hakan ba ƙaramin kyau ta ƙara mashi ba, 

Natsuwa sehrish tayi tana kallonshi daga inda take tsananin tausayin shi take ji ganin sai faman cin shi suke, in yasha wahalar cafke ball ɗin su kwace, ji take kamar tayi fiffike taje ta shigar mishi duk da bata ta6a jaraba buga ball ba, 

  Ransa ne ya basa cewa Sehrish na kallonsa saboda abun a  jininsa yake muddin reeesh na a wurin sai yaji a heart ɗinsa sometimes heart beat ɗinsa ke canzawa,

daga inda yake ya shiga waiwayon ta ina zai ganta aikuwa cikin sa’a ya hange ta jikin window ta leƙensu, murmushi ya saki na jin daɗi aransa yana cewa ashe sehrish tana kallonsa kenan may be ma ba yau ta fara ganinsu suna buga ball ba aiko dole ya ƙara himma wurin wasan nasa yasamu yaci don ya burgeta sosai, 

    Bata lura da cewa junaid ya ganta ba saboda akwai tazara sosai a tsakaninsu, 

   Da gudu junaid ya shige cikin su yasamu nasarar kwace ball ɗin cikin sa’a sai gashi yaci, aiko gaba ɗayansu suka sanya sowa suna jinjina mashi, yau yayi abun arziƙi, 

  Ita kanta sehrish dake leƙensu kamar ta diro ta window ɗin taje inda suke ball ɗin don murnar junaid ɗinta yaci ball,.

   Abun ya matuƙar basu mamaki ganin yadda junaid ke ta cinsu ball har 5 times, alhalin bai ta6a cim nasara akansu ba even one time, yau kam kamar ansa masa battery haka yake abun nasa, fuskar nan tashi ɗauke da murmushin nasara don yasan dole sehrish taji daɗi ssae, 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

A hankali motocin SGR suka shigo cikin gidan a jere dawowarsa kenan shi da wani abokinsu,

  Bayan motocin sun dakata da sauri wani black american army mafi kusanci dashi mai suna Armstrong ya buɗe masu mota, A natse ya zuro ƙafarsa masu sanye cikin haɗaɗɗun takalma na maza, yana sanye da Army trouser, sai t shirt fara, kyau kam ba’a magana, sun bi shape ɗin jikin shi ta ko’ina ya bada ma’ana kuma ya bada Citta, 

Sumar kannan kamar kullum tasha gyara ya daureta ta zubo mishi har gadon bayan shi,

Sai faman lumshe shining blue eyes ɗinshi yake alamar agajiye yake da bacci a idonsa,

 Abokin nashi da suka zo tare shima yana sanye cikin army trouser da shirt, akwai kyau natsattse dashi ɗan giant ba fari bane yana da duhun fata amma ya haɗu, 

 Murmushi kawai sehrish ke saki ganin shi, wani irin sanyi taji azuciyarta, sam batayi tsammanin zasu dawo yanzu ba, murna a wurinta ba’a magana, har tafara tunanin ta hanzarta taje kitchen ta shirya mishi abunda zai sama cikin shi,” 

    Murmushi adams yayi tare da cewa “Kamar junaid nake gani fa, dama junaid na wasan ball ne har haka”? ya tambaya yana kallon Sgr ayayin da suke ɗan tattakawa suna tafiya atare, 

     “Shine mana,” ya bashi amsa a takaice, 

Adams yace “kai gsky fa yaron nan yayi girma sosai zanyi wa daughter ɗina kamu,”

   Sgr yace “So u get ready to pay for the price? 

  Dariya adams yayi tare da cewa “In dae za’a mallaka mana Junaid ae ko nawa ne farashinsa zamu biya,” 

   Jinjina kai sgr yayi batare da yace komai ba, 

Junaid kam dake buga ball tun da ya hango babban yayan nasu yabar musu filin kwallon ya fito a guje kamar ƙaramin yaro bai tsaya ko’ina ba sai a bayan babban yayan nasu ya rungumeshi ƙam, 

tsayawa da tafiya sgr yayi jin yadda junaid ya rumgumoshi ta baya, 

    “oh junaid ni baka ganni bane wato babban yayan naku kawai ka sani ko”? adams ya faɗi yana kallon shi,

   Janye jikin shi yayi daga na Sgr, cikin jin kunya yace “a’a yaya adams ba haka bane,” ya faɗi tare da matsawa yayi hugging ɗinsa “ko kaifa yanzu naji bayani, nayi tunanin wariyar launin fata za’a nuna mini,” dariya su kayi atare jin abunda yace, shi kanshi sgr sai da ya ɗan so yayi murmushi, 

    “Yaya adams wane ni na isama, kafi ƙarfin wannan Allah, tukunna ma meyasa baka zuwa kawomun ziyara, ko dan Babban yaya baya ƙasar ne? Dama kullum ba’a ganin ka sai in Babban yayan mu yazo sannan kke zuwa ko? Ya tambaya yana kallon shi irin kallon na kama mai laifi ɗinnan, 

   Adams yace “junaid ba haka bane aiyuka ne sun min yawa, nima ae bana ƙasar ban jima da dawo daga Norway ba,” 

  Junaid yace “tom shikenan ina tsarabata “?

   yayi maganar hada riqe ƙugunshi, hakan ba ƙaramin dariya ya ba Adams ba, hatta shi babban yayan nasu dake kallonsu abun ba ƙaramin nishaɗartar dashi yayi ba, especially yadda junaid ke magana, komai nasa burgeshi yake yi, junaid young bro ɗinshi ne kuma crush ɗinsa ne,

  “In dae kana son tsaraba to kazo gidana ka amsa da anjima,” 

   ɗan zaro ido junaid yayi tare da cewa “tab !!” sannan Ya kalli babban yayan nasu tare da cewa “zaka barni inje ?” 

    Fashewa da dariya adams yayi yana kallon ikon Allah, wato sgr shine ke sarrafa shi, 

     Sgr yace   “Why not but not today zuwa tomorrow ko jibi zan sa akawo maka shi har gida,” 

   Ya ƙare maganar tare da cewa “am tired of standing, Lets go in,” 

    Atare suka jera junaid na tsakiyarsu ya ruƙo hannun kowannansu fuskar nan ɗauke da murmushi a haka suka shiga ciki,

  Wuce wa upstairs su kayi, a part ɗinsa adams ya zauna saman 3 seater, shi kuma sgr ya wuce bedroom ɗinsa don ya rage kayan jikinsa, 

    “Bari nazo yaya adams,”  junaid ne ya faɗi tare da tashi ya fice cikin sauri don yaje ya shirya masu abunda zasu sha, 

  Fitowa yayi sanye da shorts a jikinsa sai ƴar singlet fara, hannunsa ɗauke da phone ɗinsa ya ƙaraso ya zauna On royal sofa ɗin da Adams ke zaune amma akwai tazara a tsakaninsu saboda mai zaman mutun ukuce,” 

   Kallonshi adam yayi tare da cewa “Surgeon ka fa tara abubuwa da dama, ina so na tattauna wani abu dakai mana,” 

    Sgr yace “ina sauraron ka,” 

Adams ya gyara zama tare da cewa “yanzu fisabilillahi kalli kanka da kyau,” 

    Cikin mamaki sgr yabi jikinshi da kallo kamar yadda Adams yace sannan ya ɗago ya kallesa yace “what u mean”? 

   Murmushi adams yayi kafin yace “Haba sgr ka mallaki kowane abu da ake buƙata ajikin ɗa Namiji harma ka wuce, kalli fa in kyau ne da anzo gunka anzo ƙarshe kai kankat ne, in arziki ne da anzo gunka anzo ƙarshe, in Ilmi ne na addini dana zamani da anzo gun ka anzo ƙarshe, baiwa iri iri Allah ya baka to maiya rage maka a yanzu “?

   Tun da Adams yaso ma bayanin Sgr ya ke bin shi da wani irin kallo saboda ya gano inda ya dosa, 

    Duk cikin friends ɗinshi babu mai mishi katsalandan irin adams, saboda kusan halinsu ɗaya, adams ne kawai ya ware daban acikinsu, 

    Ci gaba da magana adams yayi ” da ace ni na mallaki waɗannan abubuwan daka tara, wlh da yanzu na ajiye mata har 4 Cuf, yadda kke da farin jinin nan ta ko’ina binka ake don asamu shiga, Amma sam ka haramta ma kanka mace duk wannan Hadaɗɗiyar Surar taka sai dae suyi ta kallo suna haɗiye yawu’ 

     Shiru sgr yayi yana kallon fuskan adams daya daddage yana kora masa bayani, 

   Jinjina kai adams yayi tare da cewa “ae dama nasani, u wll not say anything kabarni ina ta zuba kamar radion da bata da saiti,” 

     Lumshe ido sgr yayi tare da cewe “me kke so nace”?

    ta6e baki adams yayi tare da cewa “abunda ka iya kenan, nasha wahalar koro maka bayani amma u ar asking me me nakeso kace,” yayi maganar hada ɗaure fuska yana kallonshi, 

     hakan yasa sgr saki wani ɗan kayataccen murmushi batare da lips ɗinshi sun motsa ba, dimples ɗinsa ne kawai suka bayyana alamar murmushi yyi,’ 

       adams yace ” ka ga wannan murmushin naka, wanda ko namiji ya kalla sai gabansa ya faɗi, duk in kayi shi nasan da wata manufa,” 

      sai lokacin sgr yace “ka kammala bayanin naka”?

   Adams yace “a’a ban idasa b

a, i just start it now,” yayi maganar yana tsuke fuska

    “Ok Go ahead in ka kammala zan baka amsa a dunƙule,” sgr ya faɗi tare da ci gaba da dannar wayarsa kunnansa na akan Adams,” 

       Adams yace “haba jama’a kaga ƙato har ƙato amma ba zancen mace a ransa, zuciyarsa kaman ta dutse,’ 

   Aransa kuma yace “kwarama da ba macen aransa, tab yadda yake da ƙirar nan da kyawun nan da ace ɗan iskane shi da Allah kaɗai yasan matan da zaiyi disvirgin ɗinsu, mata fa zasu sallawanta sosai yadda suke haukanshi suna kawo mashi kansu, tun ranar da matata tayi arba dashi shegiyar har yau kullum sai tace mun ina friend ɗin nan naka mai blue eyes shi bazai kawo mana ziyara ba,

     Sam ya tafi tunani har sai da muryar sgr ta katse shi da cewa “are u gossiping me in your heart”? 

     Dariya adams yayi tare da cewa “ya akai kasan ina gulmarka bayan acikin zuciyata nake magana,” 

    “Naji araina” ya faɗi yana ɗan harararsa,

murmushi kawai adams yayi masa tare da cewa “nima bari na danni wayata, da na zauna naita zuba nikaɗae,’  yana maganar yana sa hannunsa cikin aljihunsa ya zaro wayarsa yaci gaba da danna shima, falon yazama shiru,

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

___________________________________

Time ɗin da junaid yaje ƙopan kitchen ɗin domin ya shirya musu abunda zasu sha, Sehrish yasamu aciki ta kammala jera Fancy cups masu ɗauke da Coffee aciki sai plate mai ɗauke da snacks acikin tray, sam bata lura da junaid ba, shima tun da yazo ya tsaya yana ta faman kallonta fuskarnan ɗauke da murmushi har kullum ƙara burge shi tayi, 

     Gyaran murya yayi, hakan yasanya Reesh ɗagowa a ɗan firgice a tunaninta Haroon ne ashe junaid ne, tana ganin sa ta sauke ajiyar zuciya tare da faɗin “junaid sannunka,” 

     “Yawwa sehrish na jima a tsaye ina kallon ki, wa kika shiryama wannan ne,’ yayi maganar tare da idasa shiga ciki yana nuna tray ɗin dake saman table, 

        Sehrish tace “babban yaya nagama hada abokinsa suka zo”

      Junaid yace “yawwa Good girl kin hutasshe ni, dama nima zuwa nayi na shirya musu sai naganki,” 

     Murmushi tasaki tana faman sunnar dakai, 

     “Bari naje ciki inaso na yi wanka, sannan pls in kina da free time mu haɗu a garden mana”? ya tambaya yana kallonta, 

              Cike da zumuɗi sehrish tace “Shikenan wurin ƙarfe nawa”?

    “After magrib prayer yyi maki”?

   “Eh” ta amsa mashi kafin yasa kai ya fice daga kitchen ɗin Izuwa br ɗinsa, dama a ƙagare yake daya cire kayan ball ɗinsa,

bakomai yasa ta ɗoki ba fa ce tana tsananin son garden ɗin gidan ya haɗu sosai dama ita ma’abociyar son kayataccen wuri ce mai shufke shufken flowers da ruwa mai gudana, 

A hannu ta ɗauki tray ɗin ta fuce dashi izuwa upstairs part ɗin babban yaya, sai da ta ɗan jinkirta da ta iso ƙopan shiga, tasama ma kanta Calmness, Sannan tayi sallama a natse “Assalamu Alaikum,” 

Ta jira aka amsa mata sannan ta shiga A hankali take tafiya kamar wadda ta ɗauko  Kwai a hannunta, 

    Kowannansu wayace a hands ɗinshi, sai da taje gabansu tace “ina wunin ku,” sannan adams ya ɗago yana kallonta yace “yawwa fine boy, drinks ne aka kawo mana,” yayi maganar tare da sa hannu ya ɗauki one cup, matsawa tayi ta miƙawa sgr tana kallon shi sam bai ɗago ba har sai da tace “ga shi,” sannan yasa hannu ya ɗauka, ta ajiye musu tray ɗin a saman table, 

     kamar karta fuce haka take ji, wani irin sanyi take ji in tana kallonsa, yayi wani fresh abunsa cikin singlet da shorts, 

     “Ji mana,” adams ne yayi mata magana cikin sauri ta juya ta kallesa tare da cewa “Na’am”

“Amma kai sabon mai aiki ne ko? Ina aunty azmee ne?

  ya tambaya yana neman jin ƙarin bayani

Sehrish tace “Eh sabone, aunty azmee tana nan,” 

Jinjina kansa yayi kafin ya kuma cewa “Suna fa”?

Rishi tace”Tukur,” 

Abun mamaki sai taga yana mata dariya gashi kuma yana bin ƙafafunta da kallo abun ya ɗan bata tsoro,

 Tsagaitawa da dariyar yayi tare da cewa “Wow good wasan kwaikwayon fa yayi kyau sosai,” sam Bata gane me yake nufi ba duk ta dabarbace, duk wannan maganganun nasu a kunnan sgr, 

  “u can go mr Tukur,” adams ya umarce ta yana mai ci gaba da ɗan murmusawa, 

   Jiki asanyaye sehrish ta fuce tana mai mamakin wannan abokin na Sgr, komai yake nufi da dariyarsa Oho, ta faɗi tana yarfa hannayenta, 

       Kurbar coffee ɗin yayi yana cewa “Sgr ina kuka samu ɗan aiki ne? 

     “Don’t know,” ya bashi amsa,

Adams yace “Wannan fa maca ce tayi shigar maza wlh, amma fa ta iya shiririta,” 

    ɗan kallonsa sgr yayi tare da cewa “Wa kenan? 

  “House boy ɗin nan mana, daya kawo mana drinks yanzun nan,” 

  Sgr yace “Are u serious ? 

Adams yace “Of course baka ta6a lura bane?

   Sgr yace “taya zan lura, bayan ko face ɗin mai aikin bansani ba,’ 

Adams yace “No wonder that’s y baka lura da hakan ba, amma fa maca ce wannan hada sa gashin baki, ‘ ya ƙare maganar yana dariya don kam ba ƙaramin nishaɗi abun ya bashi ba, shigar yarinyar amatsayin namiji kamar ɗan chali chali, 

   “Amma ko meyasa tayi hakan”? Adams ya tambaya yana kallonshi,” 

  Ajiye cup ɗin dake hannunsa yayi tare da cewa “Zan bincika, koma  wa ya turo ta, zan sani ne, zasuyi bayani,” Acewar sgr, 

   “Gsky kam, u ave to investigate about it, kasan mugun mutun bakasan da wata siga zai shigo rayuwarka ba, especially yadda kke da suna haka ba’a rasa enemies masu son kawo muku hari ta bayan fage, ya kamata ka miƙe tsaye akan lamarin wannan mai aikin tukur, kasan da wata manufa yazo domin kuwa wlh maca ce ba namiji ba,” 

    Adams ne yake kora masa bayani yana ƙara jaddada masa akan mai aikin Don ayi saurin dakatar da shi daga abunda yake ƙoƙarin aikatawa, 😳

Sehrish fa batasan wainar da ake toyawa ba, Ashe watan cin uban wata yayi acikin gidan nan 😂

   bedroom ɗinta ta koma tana safa da marwa, cike da tunanin dariyar da taga abokin sgr nayi mata aranta tace wata’ƙil shigar mazan da nayice ta bashi dariya Allah saki, 

__________________________________

A hankali motocin marshal Omar suke shiga cikin katafaren gidan General Ishaq wanda ke a Unguwar rimi, 

 Hamshaƙin gidan wanda sojoji ke tsare dashi ta ko’ina, jahad sai faman bin gidan take da kallo ganin haɗuwarsa ta cikin glass ɗin motar, jinjina kanta tayi aranta tace “Aljannar duniya,” 

  Juyawa tayi ta kalli hosana wadda ta kwantar da kanta a kafaɗar Jahad ɗin sai faman bacci take shararawa murmushi jahad tasaki tare da cewa “Nasan hosana in taga wannan haɗaɗɗen gidan dole ta susuce,’

 Mayar da idonta tayi kan glass ɗin tana ƙarewa gidan kallo aranta tace “Allah yasa kamar yadda gidan nan yake da kyau mutanen gidan ma zuciyarsu ta kasance mai kyau ce kamar haka, Ya Allah kasa kasancewar mu acikin gidan nan yasa ƙarshen wahalar mu kenan, Allah yasa  mutanen gidan suyi marhaban da zuwan mu kuma su tarbemu hannu bibbiyu kamar yadda goggon katsina tayi mana,” ta ƙare maganar tana mai jin wani sabon yanayi atattare da ita, 

A jere motocin suka tsaya, sajan ɗin dake driving ɗinsu ya fito ya buɗe musu mota, 

fitow jahad tayi tana faɗin “Hosana ki tashi mun iso fa,” 

daker hosana ta buɗe idonta da sukayi luhu luhu tana bin jahad dake mata magana da ido, daker ta iya sa ƙafa ta futo daga motar tana murje idanunta don taƙara tabbatarwa kanta cewa dagaske ne hamshaƙin gidan da take ganinsu aciki ba mafarki ba, aiko ta shaida hakan, 

    Fitowa Marshal Omar yayi daga tashi motar, yana sauke ajiyar zuciya kafin ya juya ya kalli su hosana yace ” ku biyo ni,” 

  Bin bayansa su kayi atare suka shiga hadaɗɗen jigunannan babban falon Aunty babba, wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa ta cikinsa abunka ga ƴan maiduguri dama an shaidasu akan hakan, 

Wasu irin haɗaɗɗun Sofas ne masu Numfashi sets guda, launinsu Maroon colour, ga sofa tables ɗinsu launinsu, 

Falon yasha ado da decorative object ga vase ajiye (tukunyar flower) ga wata irin faskekiyar plasma manne a wall ɗin kai komai fa yaji ya haɗu, 

 Babu kowa a falon sai sanyin A.c dake ratsa sassan jikin mutun, 

  “Have a seat,” umar ya umarce su sai faman bin ko’ina suke da kallo , a tare suka zauna saman 2 seater suka takure junansu tsoransu dawa zasu fara cin karo, 

Shima yasamu wuri saman 3 seater ya zauna yana facing ɗinsu idon shi nakan hosana wadda ke ta faman lumshe ido saboda baccin da takeji ga yunwa, 

 Phone ɗinsa ya zaro daga trouser pocket ɗinshi ya danna numbar aunty Babba ya buga mata Calling, 

      Da ƙarfi wayarta ƙirar Iphone 13 pro max ta soma ringing tana ajiye saman bedside drawer gefen lamp, 

  Hajiyar na hakimce tana sharar bacci Saman haɗadɗen gadon nata, jikinta na sanye da riga da wando masu kyan gaske ga laushi kamar sleeping dress haka suke, 

    takurar da ringing ɗin yayi mata ne yasa ta buga uban tsoki a ƙule cikin bacci take cewa “Mtsww Wai wanene ne yake son takuramin ina tsaka da jin daɗin baccina,” ta ƙarasa maganar tana buga Uban tsoki rai a bace ta tashi zaune fuskarnan kamar Alkubus a kumbure take don ma Allah yasa akwai kyau da haske ssae da ba ƙaramin muni zatayi ba, 

     Hannu tasa ta fisgi wayar ta duba ta ga wanene, sunan (Marshal Omar ) ne ya bayyana akan screen ɗin wayar, ae tuni ta wartsake daga baccin da take yi, jiki na rawa ta ɗaga tare da karawa a kunnanta tace “salamun Alaikum,” bai amsa mata ba sai cewa yayi “Muna a palor muna jira,” 

  Cikin sauri tace “oh to gani nan zuwa,” 

  Ta ajiye wayar tare da miƙewa tasa hannu ta ɗauki mayafin kayan jikinta dake ajiye saman gadon, ɗaure shi tayi akanta maimakon tayafa shi a jikinta, sumar kannan nata tasha ƙananun kitson kalaba, 

    

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

     A hankali take tattaka steps ɗin benen tana saukowa down, tun da suka ji takon takalmi suka ɗago suna kallonta haƙiƙa sun tsorata da kyawun matar ga yanayinta na  marasa son mutane da hayaniya haka,

Jinjina kai su kayi tare da kallon juna lokaci guda suka mayar dakansu ƙasa, 

  A second to the last steps na stairs ɗin ta tsaya Curus ! tana kallon tagwayen matan da tagani zaune saman kujerunta sai taga abun kamar a mafarki gadai marshal omar zaune to su waɗannan isassun da suka zauna matan saman kujerunta su wanene ta tambayi kanta, har hannu take sawa tana murza idanunta don ta tabbatar cewa ba mafarki take yi ba, 

  Idasa saukowa tayi har time ɗin bata sauke idonta ba daga nasu Hosana wani irin kallo take binsu dashi kallon neman ƙarin bayani,

   Muryar Omar ce ta katse ta da cewa “barka da fitowa aunty, fatan na same ku lafiya,” 

Lokaci guda ta saki fuskarta ta ƙarasa ta zauna saman 1 seater tana cewa ” Yawwa Omar saukar yaushe? wlh bacci ne ya kwashe ni nasan dae ka ce mun zaka zo nan bfr ka wuce abuja,” 

  Omar yace “Eh hakane, ina yaya ishaq ne?

“Ae bayan kabar nan, shima yayi tafiya,” 

   Ta faɗi tana kallonsu hosana da jahad, wadanda suka sha jinin jikinsu tuntuni musamman da suka gaisheta sai tayi kamar batagansu ba,

    Miƙewa tayi tare da cewa “bari na kawo muku abun ta6awa,” 

    tayi mgnr tare da wuce wa kitchen, tana shiga ta tsaya riƙe da qugu tana sake sake iri iri aranta.

“Su wanene waɗancan twins ɗin da Omar ya kawomin a gida? hankali na fa bazai kwantaba har Sai nasan su wanene da kuma matsayinsu a wurinsa,” 

   ta ƙarasa tunanin nata tare da shigewa ciki tana shirya musu  Abunsha dana ci,” 

  

   Su hosana da jahad kam sunfa shiga taitayinsu tundaga irin kallon da Aunty Babba tayi musu, 

  “Bacci kike ji ne har yanzu”?

Jahad ce tayiwa hosana tambayar, a kasalance hosana tace “sosai ma ga yunwa ina ji,” 

   “Wacece ke jin bacci”? Marshal Omar ya tambaya don yaji firar tasu,

Hosama tace “Ni ce, kuma hada yunwa nake ji ma,” tayi maganar tana ɗan turo baki, 

    Murmushi gefen fuska yasaki yana ɗan kallonta yanayin yadda tayi maganar ba ƙaramin tafiya tayi dashi ba, 

    ” ok ki bari ki fara cin abincin sai ki yi wanka inyaso daga baya sai kiyi baccin ko? ya faɗi yana kallonta, hosana tace “to shikenan,”

  Ya jinjina kansa 

Shigowa Aunty Babba tayi hannunta ɗauke da tray tinkis tinkis take tafiya, har ta ƙaraso ta ajiye musu shi a saman table ɗin dake kusa da Marshal Omar, 

      “ki miƙa musu, ni bana buƙatar komai ynx,” ya faɗi yana kallon wayar dake hannunsa dayake dannawa, 

     daurewa kawai aunty babba takeyi, matsar musu da table ɗin tayi gabansu tace “gashi nan ƴan mata,” 

Har haɗa baki sukeyi wurin cewa “mungode,” 

Jiki na rawa hosana ta ɗauki coke mai sanyi ta buɗe tashiga ɗaɗɗakar lemun har ta kusa shanyewa duka,  jahad kuwa jiki asanyaye ta ɗauki robar swan tana sha, 

Jinjina kai aunty Babba tayi ganin yadda yarinyar take ta faman kerma jikinta na rawa taga abunci aranta tace “To fa !

   Bayan ta koma ta zauna ta kalli marshal Omar tare da cewa “har yanzu bakayimun bayanin waɗannan twins ɗin ba dana ganku atare,”?

    gyara zama Omar yayi cikin natsuwa yasoma magana “Babu buƙatar dogon bayani, na kawosu ne zasu zauna nan atare daku na wani lokaci…….’

     Yadda aunty babba ta zabura tsaye yasa shi dakatawa da bayanin yana kallonta yace “lafiya”?

 A susuce ta koma tazauna tana cewa “babu komai ci gaba da bayani,” 

Ajiyar zuciya yasaku tare da cewa ” zasu zauna anan, kamar yadda nace bana buƙatar kowa ya kashe ko sisin shi akansu, komai suke buƙata lissafi kawai za’a yimun na turo,’ 

   Murmushin yaƙe aunty babba tayi tare da cewa “wannan ae mai sauƙi ne Omar, zasu samu kulawa sosai amma abunda nakeso nasani shin su wanene su? 

      “Ba buƙatar sani Aunty Laila, kawai a kulamun dasu yadda ya dace,” ya faɗi yana kallonta,

    Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa “shikenan za’ayi kamar yadda kace insha Allah,” 

  Ya amsa da “Okey ynx zan wuce masallaci kafin nadawo pls abasu bedroom ɗin da zasu zauna su huta,” 

Ya faɗi tare da miƙewa yasa kai ya fice, 

Maida idonta tayi kansu Hosana da jahad fuskarnan a murtuke, 

Hosana sai faman cin fried rice ɗin da ta shaƙe a plate takeyi tana korawa da lemu a cup, ko lura da kallon da Aunty babba keyi musu batayi ba, 

    Sai jahad ce ta ankara da hakan har tayi saurin ajiye spoon ɗin dake hannunta cikin plate gabanta na faɗuwa, 

    Muryarta ce ta katse su da cewa “kai !! Su wanene ku? ƴa’ƴan waye ku a dangin Su Omar?

   dakatawa da cin abincin hosana tayi tana kallonta, murya na rawa jahad tace ” Mu bamusan kowa a dangin shi ba, taimakon mu yayi saboda ya tsince mu cikin wani hali,’ 

Fashewa da dariya aunty babba tayi har saida suka razana, hannu tashiga tafawa tare da cewa “Wlh kun shiga uku !! meyasa baku bashi shawarar yakai ku Orphanage Home ba? Sai gidana za’a kawomin tsintattu, to bari kuji in faɗa muku Omar yayi gangancin jefa rayuwarku cikin haɗari domin ni bani da Imani wlh,’ ta faɗi a faɗace tana kallonsu 

  Gabansu ne yayi mugun faɗuwa just now suka zo gidan amma gashi matar gidan ta bayyana musu halinta tabbas akwai matsala, 

  Shewa tayi “Ahayyye !!! wai ni za’a kawo wa tsintattu na riƙe ae wlh kun shiga uku kuna cikin masifa domin Laila bata da mutunci , 

    Sam sun gaza ci gaba da cin abincin jikinsu sai kerma yake yi saboda tsoran wannan matar da ta kira kanta da Mara imani, mara mutunci, 

         jinkirtawa tayi tana kallonsu tana yatsina fuska kafin tace “me kuka tsaya kuna kallone? Kuci gaba da cin abincin ku domin daga inda Omar yasa ƙafa yabar gidan nan kuda ganin Abinci sai dae kuji ƙamshin sa Wlh,”  ta faɗi tare da miƙewa ta wuce room ɗinta dake asaman upstairs, 

   Tuni hawaye sun soma zubo ma jahad masu zafin gaske har taji ta tsani abincin da take ci ma, ita kuwa hosana jikinta yagama mutuwa jin abunda matar tace wato su da ganin abinci sai dae su ji ƙamshinsa, tuna wannan yasa ta fashe wa da kuka, 

  Haƙiƙa suna cikin tashin hankali kuwa,

Cikin kuka hosana tace “jahad Mun shiga uku,dama yaya Omar yabarmu gidan goggon mu da aunty saude,’ tayi maganar tana lashe hannunta ga hawaye sha6a sha6a,

  Cikin shesshekar kuka jahad tace “hosana duk yadda za’ae karmu bari yaya Omar ya tafi yabarmu agidan nan, wlh kashe mu zatayi tace bata da Imani, kuma xata mana Horon yunwa innalallahi mun yi gudun gara mun faɗa gidan Zago 😭

Jikinsu duk ya gama mutuwa ga gajiyar tafiya gashi suna son suyi sallah su ɗan kishin giɗa amma ba halin hakan, 

Murya na rawa jahad tace “Hosana ki ci gaba da cin abincin, kwara muci ko na yau ne tunda tace daga yaya Omar yabar gidan sai dae muji ƙamshinsa, 

   Hannu suka sa Hannu suka ci gaba da cin abincin ba ƙaƙƙautawa, hannu baka hannu ƙurya suna ci suna matsar kwalla, 

   Sai da suka kammala da komai sannan suka jinkirta suka zauna jiki a mace, 

Jin ƙarar shigowar motocin Omar yasanya Aunty babban yin saurin fitowa daga room ɗinta ta sauko down jiki na rawa ta kallesu tare da cewa “Maza ku share hawayen nan dake a fuskarku, wlh muddin ku ga ja Omar ya gane cewa wani abu ya faru saina Murƙusaku a wurin nan, Dallah ni ku taso ku biyoni, 

   Jiki na kerma suka bi bayanta cikin hanzari takai su wani room ya hadu sosai ba hayani komai simple, 

   Shiga ciki su kayi rai a6ace tace “ku shiga toilet ku gyara jikin ku, ko da gigin wasa kar na kuskura naga wata ta leƙo d daga ɗakin nan balle ma ta fito!”

    Tana gama faɗin hakan ta fuce tana sakin murmushi mugunta, 

       Falon ta koma ta tattare kayan abincin da sukayi Amfani dashi ta wuce dasu kitchen, tana a cikin kitchen ɗin tajiyo shigowarsa, 

  Fitowa tayi tana faman sakin murmushi taƙarasa tana faɗin “harka dawo kenan,” 

 Ya amsa mata da cewa “Eh ina yaran suke,” ya faɗi a yayin da yake zama saman seater, 

     itama ta zauna tana faɗin “Ae tunda kasa kai ka fuce, bayan sun kammala cin abinci na nuna musu ɗaki ynx haka sun kammala wanka sunyi sallah ynx bacci ma suke yi,”

  lumshe ido Omar yayi alamar jin daɗi aransa sannan yace “naso ace na nasake gaisawa dasu don yanzu zan wuce abuja,” 

  cikin sauri tace “gsky kam, amma fa sunyi nisa a baccin nasu, bai kamata atashe su ba, 

   Omar yace “hakane kuma, Ni yanzu zan wuce,” ya faɗi tare da miƙewa 

Aunty babba tace “Toh Omar agaishe mana da mutanen gidan Allah ya tsare hanya,” 

    Su hosana dake cikin ɗaki suna faman safa da marwa duk maganar da Omar yake yi da aunty babba a kunnansu yake yi, bayin Allah suna so su fito suce mashi karya tafi yabarsu a hannun wannan matar amma ba hali don ta tsawatar musu akan karsu Kuskura Su fito, hawaye kawai ke zuba daga idanuwansu domin suna leƙen Omar ta Window ɗin ɗakin, a yayin da yajuya baya ya soma tafiya shi kanshi hakanan ya dinga jin babu daɗi jikinshi atlease yaso ya sanyasu acikin idonshi kafin ya tafi tunda baisan ranar dawowarshi ba, 

 Har yakai bakin kopan fita daga falon ya juyo ya kalli aunty babba dake tsaye yace “AMANATA ki kulamin pls,” 

Murmushi tasaki tare da cewa “Baka da matsala dani ƙanin Miji na, insha Allah zan kula maka dasu sosai,’ 

   Jinjina kansa yayi tare da juyawa yasa kai ya fice,” 

Su Hosana najin tashin Motocin shi, nan take suka fashe da wani irin matsananin kuka mai cin rai suka rungune junansu😭

 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

      

   *BossLady* 

Back to top button