Uncategorized

Abban Sojoji Chapter 14 Book 1 Complete Hausa Novel

 

“`The father Of Soldiers“`

        

Story 

     &  

       Written 

       By 

      Hafsat Bature

          (Boss Lady)

   Murmushi hosana tayi daga kwancen da take tana kallonta, miƙa mata hannunta tayi tare da cewa “pls taimakamin na tashi kasala nake ji ajiki,” 

  Ruƙo hannunta jahad tayi daker ta miƙar da ita tsaye, tana faɗin “wash Allah ba dole ki ji kasala ba, kinci uban abinci kin kuma zo kin kwanta,” acewar Jahada,

       Wuce wa hosana tayi tare da shigewa toilet ɗin, tana jiyo muryar jahad tana cewa “Hosana akwai shampoo ciki pls ki wanke wannan mahaukacin gashin kan naki, mara tsari nasan ki da taurin kai, bakisan wanke sumar kan ki, ko nazo na taya ki wanke wa..”? ta tambaya tana jiran amsa, 

“Banso,’ ta cikin toilet ɗin tabata amsa, dafe kai jahad tayi tare da cewa “Oh God!!”  saboda tasan hosana bazata ta6a yarda ta wanke sumar kanta ba, kuma bata so wani ya wanke mata, shiyasa kullum gashin kanta a cukurkuɗe yake, gashi duk tafisu yawan gashi da cukowa, duk da kowa da yawan nasa, 

jahad na zaune saman stool gaban mirror tana shafa cream ajikinta, sai ga saude tashigo da sallama, da fara’a a face ɗinta tace “wow masha Allah, tubarkallah wannan dogon gashin fa kamar na larabawa,” tayi maganar tana kallon sumar kan jahad wadda ta zubo mata har wurin waist ɗinta, 

   Cikin jin kunya jahad ta sunnar dakai, saude taci gaba da cewa “duk da nake bafullatana, nima ina da gashi amma bai kai ko rabin naki ba, ke wata ƙabila ce ? Jahad tace “BUXUWA,” 

Saude tace “No wonder, shiyasan ya, hakan na nufin cewa ku ƴan niger ne ko? 

  “Mahaifiyar mu buzuwa ce ƴar niger, amma mahaifin mu bafullatani ne ɗan nan,” 

saude tace “Wow wow!, haba ! ae dole kyau ya haɗu a wurin nan, dole kuyi kyau yara,” murmushi kawai jahad ke saki, ganin yadda saude ke zuzuta su duk da itama ɗin kyakkyawa ce, 

Wuce wa ciki saude tayi ta buɗe wardrobe ɗinta, riguna ta ɗauko musu dogaye sun sha guga ninkakku, ta ajiye musu asaman gadon sannan tace “Gashi nan kusanya rigunana ne, duk da nasan sunyi muku tsayi sosai,” 

Download>>> Ingarman Namiji Complete Document

“Mungode sosai aunty, Allah yasaka da alkairi,” saude tace “mention not pls,” sannan tafice don tabasu damar wataya wa, 

    “Jahad kinji yadda iska ke shiga jikina, ga wani ƙamshi dake fitowa sako da lungu na hammata ta,” hosana ce tayi maganar wadda fitowarta kenan daga toilet ɗin, 

   A lokacin jahad ta kammala sanya doguwar rigar da saude ta fiddo masu, na materials ne pink colour masu kyalkyali, ba karamin kyau su kayi mata ba,  cikin 6acin rai take kallon hosana 

“Meyasa wai baki da hankali ne, ke shashashar ina ce? Ba sai da nace miki ki wanke sumar kanki ba,”? ta tambaya a ƙule tana kallon hosanar, 

     Da buɗar bakinta sai cewa tayi “Gashina ne ko Gashin ki”? Shiru jahad tayi don tasan ynx zata tada rigima har ajisu, 

“Gashin ki ne hosana, zo kisanya kaya gashi nan aunty ta fiddo mana mu sanya,”  wuto wa tayi daure itama da towel ajikinta, ta zura rigar materials ɗin, tayi kyau amma gashin kanta sai uban wari ya ke yi, babu yadda jahad ta iya da ita, bayan sun kammala shiryawa, atare suka haye saman gadon suna facing ceilling, “what are u thinking about jahad”? Hosana ce ta tambaye ta, cikin sanyin murya jahad tace “SEHRISH, ke fa me kike tunani? Murmushi hosana tayi kafin tace “Wannan kyakkyawan mutumin, mai ƙarfi wanda ya ceto rayuwarmu daga shiga haɗari, daga na rufe eyes ɗina shi nake gani, lokacin da na faɗa jikinsa, bakiji ƙamshi ba wlh ya haɗu” 😇

Jahad tace “shegiya ashe kina cikin hayyacin,” 😂 dariya su kayi gaba ɗayansu

………………….SEHRISH…………………

Ta gyara komai tsaf na bedroom ɗinsa, tsayawa tayi tana kallon hoton dake jingine saman side drawer ɗinsa bayan bedside lamp, hannu takai ta ɗauki hoton tana kallo, wata mata ce acikin hoton fara tas baturiya, mai kyan gaske kai kace itace tayi kanta don kyau, jikinta sanye da uniform ɗin na sojoji, kakin ba ƙaramin kyau su kayi mata ba, tsaye take tayi saluting a cikin hoton, bin sumar kanta sehrish tayi da kallo, launin gashin matar yayi yellow mai tsayin gaske, kwayar idonta kuma blue colour ce, wannan ba kowa bace face*Alexandra* Ummu Rafayet, ummun Ayan da jahan kuma ummun micheal(makel) da ROMEO 💞

Murmushi sehrish tasaki matar ta burgeta, duk da batasan kowacece ba amma kamannin fuskarta sak irin na Babban yayansu, akwai kyau, daga ganinta wayayyiya ce ajin farko,” 

Hannu sehrish tasanya tare da shafa hoton a fili tace “kowacece wannan matar amma ta haɗu kuma ta burge ni, gashi tana kama da Babban yaya sosae,” ta karasa maganar tare da mayar da hoton inda yake ta ajiyesa, 

Sannan ta tura kopar toilet ɗinsa ta shige 😯 uhmmm hmmmmmm, tsayawa sehrish tayi tana tunanin anya ba kuskure tayi ba, wannan ae ba toilet bane, jimmmm tayi tana ƙarewa toilet ɗin kallo, lokaci guda ta dabarbace saboda haɗuwarsa, an raba shi biyu 6angaren toilet da kuma na bathroom wurin wanka kenan, ba ƙaramin girmane dashi ba, kamar a mafarki take bin komai da kallo, shiga ciki tayi ƙamshin wurin na dakar hancinta, 

ba komai yaja hankalinta ba face wurin wankansa, wato irin standing jacuzzi ɗin nan ne (kwamin wanka), wande ke zagaye cikin glass, sakin baki  sehrish tayi galala tana kallon ikon Allah, mayar da eyes ɗinta tayi kan bathroom cabinet ɗinsa, jerun wasu matsiyatan Shampoo ne, mayuka iri iri masu kyau da tsadar gaske, duk na gyaran jiki ko mace albarka wannan, 

   Jinjina kai kawai sehrish ke yi, haɗaɗɗen mirror ɗin dake cikin toilet ɗin mai girman gaske, ga wash basin agabansa, mai ɗauke da taps biyu na ruwa,  daga gefe kuwa soap dispenser ce,  gashi an ƙawata shi da vase a ajiye ƙasa, (Tukunyar flowers)

     Zuƙunnawa sehrish tayi ƙasan hadaɗɗen tiles ɗim mai walkiya, ta zabga tagumi, aranta tana mamakin cewa wai nan toilet ne ? Idan har nan toilet ne to mukuma irin namu toilet ɗin ya sunan shi ? (Nace ba kewaye ko ki ce banɗaki) 😂 

Download>>> Kwarata Complete Document

ta jima tana shirita, domin ba abun da ke buƙatar gyara a toilet ɗinsa, komai tsaf, kallo kawai ta tsaya yi daga bisani ta ɗanyi goge goge kawae , 

       Fitowa sehrish tayi ta sauko down tana ko zata ganshi, basa nan ba kowa duk sun fita, 

         Wuce wa nata room ɗin tayi, tayo wanka, ta fito ta zura riga ta maza dai dai guiwa, ta zauna gefen gadon tana tunanin duniya, kallon sama tayi tana cewa “Oh ni yanzu wata rana nima zanyi saurayi, har nayi aure na haifi ƴa’ƴa,? When ? Ina so nima nayi shiga irin ta mata, na wataya nayi rayuwar ƴanci yaushen hakan zata faru ? 😥

Ajiyar xuciya tasaki tana tunane tunane, 

Kwankwasa kopan akayi, cikin sauri tace” wanene? Azmee tace “wa kika sani yake zuwa ɗakin ki in ba ni ba,”? 

Murmushi Sehrish ta saki tare da miƙewa ta buɗe mata kopan, sanye take da hijabi milk colour hannunta riƙe da Cazbaha, da murmushi a fuskarta tace “ƙanwata ina fata dae ba zaune kike hakanan ba kina tunane tunanen duniya? karfa ace bakiyin zikri? Ba istigfari da sauransu? 

   Sunnar da kai sehrish tayi, don kuwa batayi, ae tun ran da tasanya SGR a idonta, ta rage duk wani abu da take yi, 

“Hmmm dama raina ya bani, gsky zamuyi faɗa dake muddin baxaki, daina zama hakannan ba kina sa damuwa aranki ba, 

“Insha Allah aunty azmee zan rinƙa ƴi,” jinjina kai azmee tayi kafin tace “Albishirin ki,”? 

Cikin mamaki sehrish tace “Goro,” 

Azmee tace ” an bani sabuwar waya nabaki,” 

Ɗan zaro ido sehrish tayi cikin mamaki tace “Who”? Murmushi azmee tayi tare da cewa, ” i will let u know but not now, yanzu dae da anjima bayan magrib kina da baƙo,” 

    Waro ido sehrish tayi tare da cewa “baƙo kuma aunty azmee ? wurin wa zai zo? Tayi maganar cikin ruɗu, 

   Azmee ta dafa kafadarta tare da cewa “bakowa bane , fa ce wanda nace miki, yasan cewa ke maca ce !! yau zaku haɗu, na shirya muku haɗuwa a Garden, ki same shi immediately after magrib prayer,” 

    Murmushi sehrish tasaki tana jujjuya ido, ta ɗan jinjina kai kafin tace “shikenan aunty azmee Allah yasa naga alkairi,” yanayin yarda tayi maganar taba azmee dariya, 

   “Ni zan wuce, maganar wayarki kuma, sai zuwa gobe zan baki ita, salon kuma in ga yarinya ta buɗe tiktok ko insta don na lura kan ƙanwar tawa rawa yake yi,” ta ƙarasa maganar cikin zolaya da dariya a face ɗinta, 

Itama sehrish dariyar take yi, duk da batasan menene tiktok da insta ɗinba, sunan kawai ta ta6a ji ana faɗa,” .

Bayan azmee ta fita, sehrish ta daka wani uban tsalle sai saman gadonta, tsananin murna ne ya bayyana a fuskarta, rawa ta dinga yi tana tsalle tsalle asaman gadon jin an mallaka mata waya, gashi kuma zata haɗu da wanda yasan cewa ita maca ce acikin gidan, addu’a take yi Allah yasa koma wanene acikinsu yakasance mai sauƙin kai kamar hafsat bature,

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Yini tayi tana zullumi acikin ranta,wanene wannan dayasan cewa ita maca ce ba namiji ba, wayyo Allah yasa junaid ne don yafi su sauƙin kai, ko ba komai wannan wani mataki ne nasara arayuwata, ga kyautar waya kuma an bani, wayyo daɗi bisa daɗi yanzu ya’azayi na rinƙa waya da ƴan uwana? ta faɗi jiki a mace,.

Zama tayi saman gadon ta janyo pillow tare da rungumesa jiki amace, taso ace lokacin da zata riƙe  waya, ta rinƙa samun su Hosana da jahad, amma kash tun time ɗin da junaid ke ara mata wayarsa, ta daina jin ɗuriyarsu kullum switch off, sehrish ta jima tana tunanin menene yasa ba’a samun wayar tsohuwa ne ? What’s happening wit them?

 

💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞

…………..AMANI……………………

tunda taji dirar motoci acikin gidanta, kuma dama Cg abbas ya sanar da ita cewa, Rafayet yace masa zai zo gidansa ya kawo masa ziyara, hakan yasa sai faman rawar kai take yi, shiri na musamman tayi, ta ɗauki wankar less maroon colour wanda akayiwa ado da stones doguwar riga ce tabi shape ɗin jikinta, ko mayafi bata sanya ba, ta zubo da gashin kanta har gadon bayanta, dama fa akwai kyau abun saiya bada Citta, kai kace ba matar aure ba, ƙanin miji zai zo an dage ana ta zabga uwar kwalliya,” 

   fitow tayi daga bedroom ɗinta, tana saukowa daga saman stair, cikin tafiyar rangwaɗa da yanga, dama legs ɗinta nasanye cikin highheels launin kayanta, ta fito fess abunta Balarabiya 

      Ƙamshin turarenta ya gama gauraye falon, tunkan ta idasa isowa ta zuba mishi ido yana a zaune saman 3 seater, ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana daddana wayar hannunsa cikin natsuwa,

gaba ɗaya ya tafi da imanin Amani, saboda tagaza janye eyes ɗinta daga nashi, daker ta iya samun natsuwa har tace mashi “sannu da zuwa Babban yaya, ashe kaine nayi mamaki wlh, ban ta6a tunanin zan ganka ba agidan namu,” tayi maganar tare da samun wuri itama tazauna suna facing ɗin juna,

   Ya jima bai bata amsa ba, kusan 5 minutes sannan yace “Yawwa ya nasame ku,”? 

    Cikin kashe murya tace “lfy lou Alhamdulillah,’ .

     shiru su kayi ba magana aranta tace “tabɗijan can ! Wai dama haka yake da miskilanci? Ko kallo babu balle magana,’? ta tambayi kanta acikin zuciyarta, 

Miƙewa tayi tare da cewa”Bari na kawo maka snacks da abunsha,” 
  dakatar da ita yayi da hannunsa yace”No need thanks” 
Murmushi ta ɗan yi tare da komawa ta zauna, tana ci gaba da kallon fuskarshi, kafin ta mayar da idonta kan surar jikinsa tana haɗiyar yawu, 
  “Banason Kallo,” ya faɗi yana ci gaba da dannar wayarsa, cikin jin kunya Amani ta janye idonta, tana mai mamakin taya akai haryasan tana kallonsa, 
   Cikin kashe murya tace ” Babban yaya ae dole na kalle ka, kai fa abun kallo ne, kuma ni ban ta6a ganinka ba ido da ido, shiyasan ya,’ ta ƙare maganar tana cizon pink lips ɗinta alamar ya cije ta, 
    shi kuwa ba ta ita yake ba, burinsa yayansa Abbas ya ƙaraso, su ga juna, yayi kewarsu sosai, 
Muryarta ce ta ƙara ratsa shi “Babban yaya, ko dae baka farin ciki dani ne amatsayina na matar yayanku ishaq,’? ta yi maganar tana kallonsa,
“Why’? ya tambaya har time ɗin bai ɗago ya kalleta ba, gyara zama tayi tare da cewa “to naga u don’t even want to look at me, atlease u should put ur eyes inside mine,” 
  Amani ba ƙaramin takura masa tayi ba, ji yake tamkar ya tashi yabar gidan, don baisan nacin magana, 
    “Plsss babban yaya,” 
dogon tsoki yaja tare da cewa “becareful with me,” gabanta ne taji ya faɗi jin gargaɗin da yayi mata, tabbas mace bata gabansa, 
Jiki a mace Amani tabar falon, cikin bedroom ɗinta ta koma, jiki na rawa ta ɗauki phone ɗinta dake ajiye asaman pillow ta dannawa AUNTY BABBA kira, 
 Ringing 3 ta ɗaga kiran bayan sun gama gaisawa cikin zumuɗi Amani tace “Aunty ko kinsa cewa SGR na cikin gidan nan yanzu haka? tayi maganar da murmushi a face ɗinta, 
A can 6angaren kuwa cike da mamaki aunty babba tace “Are you serious? shi da kansa kuma”? 
dariya Amani tayi tare da cewa “wlh kam,baki ji yadda naji ba dana gansa duk da rashin maganarsa, yaci ka ji dakai wlh,” 
Aunty babba ta fashe da dariya ta cikin wayar tare da cewa “ki barshi zai zo hannu ne yanzu dai ya maganar Ziyartar wurin bokan nan baba ibliss? kin sama mana kuɗin? 
 Ajiyar zuciya amani tasaki tare da cewa “tukunna dae auntyna, ina nan ina tarairayarsa, ina so nabi komai a sannu, insha Allah nan ba da jimawa ba, zaki ji daga gare ni, da kaina ma zanzo kd na kawo miki ziyara,” 
Aunty babba tace “To shikenan, Allah ya kaimu lpy, shiri na musamman zamuyi, domin ganin munci nasara akan waɗannan zafafan guda biyu,” 
sun jima suna waya a tsakaninsu, agame da yarda zasu ziyarcin wurin hatsabibin bokan nan Baba iblisssss 👹
A can ciki kuwa, dirar Abbas kenan fuskar nan dauke da fara’a kamar gonar auduga jin cewa Sgr ya kawo masa ziyara da kansa, sanye yake cikin kakinsa na sojoji daga headquater yake, 
yana shiga falon Rafayet ya miƙe fuska a sake suka rungume juna sosae, kamar karya sake shi haka Abbas ya ji, 
“Am really glad to see u bros, nayi kewarku sosae kamar kamar me,” abbas ya faɗi hakan cikin tsananin farin ciki, ruƙo hannunsa yayi suka zauna a mazauni ɗaya, suna kallon juna cike da kewa, 
Cikin sanyin murya babban yaya yace”Nayi kewarku sosae, har ma bazan iya faɗa ba,” 
ƴar dariya abbas yayi tare da cewa “Wake koya maka hausa ne? nayi mamakin jinta raɗau abakin ka duk da har yanzu da sauranka, last time da kazo daker kake fahimta in anyi magana,” 
  Jinjina kai Babban yayan yayi tare da cewa ” bana so nazo ƙasar nan ne arinƙa gulmata bana ji, that’s why na dage na koya saboda su Ammi,” 
Dariya abbas yayi sosae jin abunda Rafayet yace, a wasa wasa shima ya iya zolaya in yaso , bayan abbas ya tsagaita da dariyar ne yace “Am wai baku gaisa da Amani ba? naga ko abunsha ma bata kawo maka ba,” 
  “No tazo mun gaisa, ni nace bana son komai shiyasa,” 
Jinjina kai Abbas yayi tare da cewa “meyasa baka son shan abu ko cin abu in kazo gidan mutanene nifa ɗan uwanka ne jinin ka, shikenan  nima duk ranar da kayi aure nazo gidan ka, matarka tayi mun tayin abinci  bazan ci ba,” 
      wani kallo babban yayan yayi masa tare da ɗan ta6e baki kafin yace “NEVER,”  wato bashi ba aure har abada, 
   Murmushi abbas yayi yana kallonsa yace “hmmm haka dayawa irinka suke cewa but at the end sai ga lamarin ya sauya, irin ku ma mace tafi juya ku, sannan maza irinku da basa ra’ayin mata ko aure wlh basu iya faɗawa tarkon so ba, haukace wa suke yi idonsu ya makance lokaci guda,” .
   Abbas ya ƙare maganar da zolaya yana kallon fuskar Sgr, wanda ya tamke fuska yana sauraran bayanin yayan nasa,” .
Miƙe wa yayi tare da cewa “Ni zan wuce,” 
   “Haba Babban yayansu, nasan magana tace tayi hurting ɗinka am sorry 4 that, it was a joke,” 
Abbas ya faɗi tare da miƙewa shima ya ruko hannunsa cikin lallami,’ 
  “Ba abunda kake tunani bane yaya abbas, time ɗin tafiyana ne yayi, saboda ko wane lokaci na rayuwata yana da amfani, kuma a ƙirge yake” 
Murmushi abbas ya saki yana jinjina kai yace “kuma fa hakane, na tuna da wannan, ae nama gode ssae da ziyarar da ka kawomin, Allah yabar zumunci,” ya faɗi hakan a yayin da ya matsa suka sake hugging junansu, sannan su kayi sallama,
……………………SEHRISH……………………….
Bayan sallar La’asar wuraren ƙarfe 5 na yamma, suna kitchen ana ta faman girke girken abincin dinner, ƙamshi ya gauraye ko’ina, 
      tana tsaye tana yayyanka kayan lambu a saman chopping board, fuskar nan a washe abubuwa biyu na mata yawo aranta, na farko shine wanene wannan wanda xata haɗu dashi yau a garden wanda yasan cewa ita maca ce, na biyu kuma shine new phone ɗin da aunty azmee tace an bata kyauta, bakomai take ɗauki da wayarnan ba fa ce shegen son kallon fina finai dake gare ta, ga son sauraron music gata mayyar selfy kamar hafsat bature 😇
     “Ji mana, ki dubamin girkin nan , ynx zanje na dawo,” azmee ce tayi maganar a yayin da take fi ce daga kitchen, ..
       Cikin sauri sehrish tace “To aunty azmee,” 
Ajiyar zuciya tasaki tare da cewa “ko ƙarfe nawa yanzu i ave to check the time, ina da baƙo fa,” ta faɗi cikin zumuɗi tana kallon agogon dake manna a bagon kitchen ɗin,  shida saura murmushi tasaki tana faɗin “lokacin haɗuwa ya kusa Ya Allah ka bani ƙwarin guiwar tunkarar koma wanene wanna,” 
   ta faɗi tana nuni da knife ɗin da ke hannunta, 
Azmee kuma da ta fice bedroom ɗin junaid ta wuce,  domin ta ƙara tunasar dani haɗuwar da ta shirya musu da sehrish,” 
    Sai faman knocking take yi, amma sam baiji ta ba, yana tsaye riƙe da ƙugu gaban closet ɗinsa ya buɗe yana kallon jerin kayansa, yama rasa wanne zai sanya domin haɗuwa da sehrish ɗinsa for the first time, sai zabga murmushi yake yi ba magana, tun da azmee ta sanar mishi da haɗuwarsa da sehrish yarasa tsaye ya rasa zaune, sai rawar kai da zumuɗi yake, kamar sabon ango 😌
  daga shi sai short ajikinsa, sai da azmee ta ɗaga murya da cewa “Junaid ka buɗe aunty azmee ce inason magana da kai,” 
  Ae yana shaida muryarta a kunnansa jiki na rawa, yayi hanzari zuwa ya buɗe mata kopan, yana sakar mata murmushi, 
   “Ango kasha ƙamshi,” azmee ta faɗi cikin zolaya,
   “Ka ce ka shirya haɗuwa da amaryar taka kenan,”? 
Cikin ɗan jin kunya yace “Kai aunty azmee, nifa kunya nake ji,” 
  yadda yayi maganar da shagwa6a yasa ta yin ƴar dariya tace “uhm junaid kenan Romeo shugaban ƴan soyayya yau zai haɗu da juliet ɗinsa akaro na farko, yakama ka rubuta wannan a diary ɗinka saboda tarihi,” .
   ɗagowa yayi da dariya a fuskarsa yana kallon azmee jin abunda yace, 
     “Insha Allah aunty azmee, dole na rubuta wannan, saboda rana ce ta farin ciki da bazan ta6a mantawa da ita ba arayuwata,”  cikin sanyin murya junaid yayi maganar, alamar yana jin abun aransa sosae, 
Azmee tace “hakan yayi kyau, ynx dae ni zuwa nayi na ƙara karfafa maka guiwa kasan kai mutumina ne, inaso ka saki jiki sosae, sbd rishi yarinya ce mai shegen tsoro, tana da wani hali dana lura dashi yanayin yadda mutun ya tarbe ta itama haka xata kar6esa, i mean yadda kasakar mata fuska haka itama zata sakar maka tata, kuma zata saki jiki da kai sosai kamar ɗan uwanta, Junaid nasan baka da ƙanwa mace, gaba ɗayanku maza ne, to inaso ka ɗauki sehrish amatsayin ƙanwarka, kai kuma ka zama tamkar yayanta mai share mata hawayenta, kuma abokin shawararta,”  natsuwa junaid yayi yana sauraran maganar azmee har cikin ransa bayaninta ya kwanta masa aransa, 
Bayan ta kammala maganarta ta tace “Junaid ni zan koma kitchen, nasan gobe akwai labari mai daɗi daga wurinka, zanji ya haɗuwarka da juliat ta kasance,” 
  Dariya kawai junaid yake yi, yana faɗin “insha Allah aunty azmee, ngde ssae ke ce silar farin ciki na,” 
  Murmushi azmee tasaki tare da juyawa ta fice tana cewa “Karka manta kaifa ɗane a wurina junaid, cikina ne kawai baka zauna ba, amma ni na shayar dakai ina alfahari da hakan,” 
Rufe door ɗin yayi, tare da daka uban tsalle na murna, runtse idonsa yayi tare da dunkule hannunsa yana faɗin “Can’t wait to seeeeeee you Sehrish My dreamy Girl…………. 
     koma wa kitchen ɗin azmee rayi suka ci gaba da aiki, tana lura da sehrish cikin sauri take yin aikinta fuska ƙumshe da murmushi, ba don komai ba sai don tayi saurin taje tayi wanka ta kimtsa bayan sallar magriba ta wuce garden wurin wanda aka ce zata haɗu dashi 😘
💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕💕
  …………..Twins………………………………
kwance su ke rungume da juna a katafaren ɗakin da suka ɗauka na hotel ya haɗu iya haɗu, da alama sun gama biyan buƙatar junansu ne bacci ya kwashe su, sam babu sutura ajikinsu zir suke manne da juna kamar tip da tyre, 
      Wayar Jahan ce dake saman bedside table ta soma ringing taken waƙar Shape of you ta Ed shareed,” 
  Almost 3 times tana ringing an rasa wanda zai ɗauka cikinsu saboda daɗin bacci,  har calling ɗin yayi rejecting, wani ya sake shigo wa da ƙarar gaske, 
    Ayaan ne yafarka cikin kasalalliyar murya ta wanda ke cikin shauƙi da jin bacci yace,”babe ur phone is ringing pls get up and pick the call, its disturbing my ears,” ya ƙare maganar yana bubbuga ƙafadar Jahan da hannunsa, 
        daker jahan ya buɗe idonsa da su kayi jawur ya kallesa da su kallon so da ƙauna yace “Honey bazaka gane bane, ko yatsana bana ji zan iya motsawa, wata irin kasala nake ji kasan fa mun jima muna yi,”   
lumshe ido Ayaan yayi tare da ƴunƙurawa ya tashi shi, yakai hannu ya ɗauki wayar, jahan na cewa “Yawwa honey duba ka ga wane ɗan takurar ne, ke kira na, 
   natsuwa yayi yana dubawa, cikin tsananin tashin hankali yace “Jahan!!!! wlh Babban yaya ne ke kira !!!” yayi maganar da ƙarfin, 
   Ae tuni Jahan ya miƙe garas jin an ambaci sunan Babban yaya, jiki na rawa yasanya hannu ya karbe wayar dake hannun Ayaan yana kallon sunan da ya bayyana akan screen ɗin wayar,” 
  Wani irin kallo jahan ke bin Ayaan dashi cikin kashe murya ta masoya yace “Ayaan ka daina mun irin wannan abun Allah! kamin kowane irin wasa amma banda wannan,’ 
   Tuntsirewa da dariya Ayaan yayi yana masa gwalo tare da cewa “Ni zaka cema wae kasala kake ji  ko yatsa ba ka iya motsawa, shiyasa namaka wannan wasan,”   
Pillow Jahan ya wawura dake gefensa ya kifa masa a fuska, nan suka shiga wasa da junansu, 
A ƙarshe suka koma suka kwanta, ba tare da sun bibiyi kiran da ake masu ba, Jahan ne ya kwanta yayin da Ayaan ya kwantar da kansa a ƙirjinsa, shi kuma jahan ɗin yana shafa masa sumar kansa, cikin sanyin murya Ayaan yace “Jahan! anya kana tunanin ranar da asirin mu zai to nu? wane hukunci za’a mana,” 
  “Kisa,” kaitsaye Jahan ya bashi amsa, cikin tsananin tsoro Ayaan ya janye jikinsa daga na jahan ya tashi zaune saman gadon yana kallonsa a tsorace yace “Jahan dagaske kisa ne? Kashe mu za’ayi,”? 
Tashi zaune shima Jahan yayi tare da cewa “Am serious Ayaan kai fa mai ilimi ne ! Sarai kasan hukuncin waɗanda ke aikata homo a addinin musulunci,! munsan da hakan kuma muke aikatawa tabbas duk ranar da Babban yaya yasani wlh kashe mu zaiyi bazae ƙyale mu ba, duk son da yake mana hakan bazae hana yaƙiyi mana hukuncin daya dace damuba domin nema mana sauƙi wurin Allah,” 
Wasu irin hawaye ne ke zuba a fuskar Ayaan cikin tsananin tsoro yace “Jahan ni banso na mutu yanzu, banso na mutu ina aikata wannan mummunan zunubin wlh banso, Jahan kullum babban yayanmu yana ja mana kunne akan mu riƙe mutuncin mu, mu ji tsoran Allah mu guji sa6a mashi domin muyi kyakkyawan ƙarshe kuma mu tsira ranar gobe ƙiyama amma meyasa zamu zama na farko da zamu karya masa zuciya duk irin soyayyar da yake nuna mana”?  cikin ƙunar rai Ayaan ke maganar yayin da idonsa ke zubar da hawaye masu raɗaɗi, 
   Jikin Jahan ya gama mutuwa shima idon nasa cike tab da hawaye yace “Ayaan yaya zamuyi? bamu da za6i, kaima kasan bada san ranmu muke aikatawa ba, Ayaan….kafi kowa sanin azaba da raɗaɗin da muke sha in har mu ka wuce 24 hours bamu sadu da junanmu ba,’  
Cikin shesshekar kuka Jahan ke kora masa bayani, cikin sanyin murya ayaan yace “Babban yayan mu yazame mana komai arayuwa, ya sama mana rayuwar farin ciki, kullum yana ja mana kunne akan kar muja masa abun magana a family roƙonsa kenan amma mun gaza cika masa hakan, ko da yaushe dangin abbanmu suna cewa ƴa,ƴan momyn mu basu da kunya fitsararru ne, tabbas sunyi gaskiya tunda gashi nan, bamu tsoron Allah muna aikata zunubi irin wannan,…….” .
“Ya isa haka !!! Nace ya isa Ayaan , kadaina cewa bamu tsoran Allah, mu bayin Allah ne kuma masu tsananin tsoransa, Allah yana sane damu kuma asannu zai kawo mana ƙarshen matsalarmu, zai warware mana duk wata masifa dake damun mu,” 
Jahan ne yayi wannan bayanin a yayin da ya komar da jikinsa ya kwanta tare da jan bedsheets a lullube jikinsa yana sharar kuka, .
Shima ayaan ya kifa kansa jikin pillow yana matsar kwalla, suna masu danasanin rayuwarsu da tazo musu a haka,” 😥
‘Shin meke damun su TWINS ne ? da son ransu suke aikata hakan ko kuwa akwai wani abu a ƙasa ne? Nifa na rikice ina buƙatar ƙarin haske game da waɗannan bayin Allah,’ . 😥
……………Sehrish…………………
Bayan sun kammala dinner ɗin, azmee tace 
“Sehrish ki je ki yi sallah, bari na idasa jera dinner ɗina, sannan karki manta ki isa a lokaci dan Allah,” 
Azmee ce tayi maganar a yayin da take fice wa daga kitchen hannunta riƙe da warmers cikin tray , 
“To aunty azmee ynx kam zan kimtsa,” tana gama faɗan hakan ta wuce bedroom ɗinta, bayan tayi sallar magrib tayo wanka shaf shaf tayi ta kimtsa, cikin dogon wando Jeans da riga ƴar ta maza, ta naɗe gashin kanta taturasa cikin hularta sannan ta laga mayafi daga sama, ta gyara gashin bakinta ya zauna daram, 
Tsayawa tayi tana kallon kanta cikin mirror ɗin, murmushi ta ɗanyi kafin tasa kai ta fice, tana Allah Allah acikin ranta,
   Babu kowa a babban falon, bi tayi ta wuce time din da  tazo harabar gidan adai dai time ɗin motocin su suka soma shigowa hada ta sgr duk ba’a tare da suke ba, amma atare suka iso gidan hadasu kanal yusif dasu irfan fawan da sauransu,
tsayawa tayi tana kallon motocinsu, firfitowa su kayi atare, kowanne cikin kakinsa, sai bayan sun fito sannan wani soja narkeke ya fito daga cikin motar Sgr ya buɗe masa ita, shima ya fito dama jeans ne da t-shirt ajikinsa, ganin sa yasa su kanal yusif ƙarasawa suna gaishe shi, 
Gwanin burgewa sehrish tabisu da kallo especially mutumin ta, sai da duk suka shige ciki sannan ta wuce cikin garden ɗin gidan cike da fargabar wa zata tarass, 
Ko da ta isa cikin hadaɗɗen garden ɗin sai ta boye bayan bishiya tana leƙensa
Tsaye yake cikin dress na pakistani masu kyan gaske riga dogowa ta wuce guiwarsa sai wano burgujeje irin nasu, 
Rigar mai dogon hannu ce purple tasha adon sparking stones, wandon kuma light pink ne zallah ba kwalliya jikinsa , daga gefen kafaɗarsa scarf ne (mayafin da mazan pakstan ke yarfawa a shoulders ɗinsu) 
Zuba mishi ido sehrish tayi tana tunanin wanene wannan ? Saboda ya juya mata baya, bazata iya shaidasa ba, 
Launin fatarsa da tagani fari tass da kuma kwantacciyar sumar kansa smooth black ya tabbatar mata da cewa bazai wuce Junaid ba ko Fawan ko cikin su twins saboda sune ke da wannan hasken 6ayau, 
Shiru tayi tana ƙoƙarin gano kowanene da kanta, amma sam ta kasa canka har sai da muryarsa ta ratsa kunnanta mai sanyin gaske “Sannu da zuwa,” 
Murmushi sehrish ta saki tare da cewa “Yawwa sannun ka,” 
Shima yace “yawwa meyasa ki ka 6oye a bayan bishiya, kina shakkar ganin kowanene ya kamata ki fito,” 
ƴar dariya sehrish tayi sannan ta fito daga bayan bishiyar ta tsaya daga bayansa tace “Wanene kai,’ meyasa bazaka juyo ba mu fuskanci juna ba? 
  “Zan juyo amma firstly saikin fara faɗamin wanene Ni ki canka kawae,” 
Wani irin daɗi ne ya rufe sehrish, natsuwa tayi tana kallon bayansa ciki da son gano ko wanene shi, 
Shima shiru yayi yana jin duk wani motsinta, burinsa sehrish ta shaida shi kafin ya juyo mata da face ɗinsa, 
  “Am waiting 4 u Sehrish,” ya faɗi da murmushi a face ɗinsa, 
   Shiru sehrish tayi tana tunanin wani abu aranta, 
“Idan har zanyi zurfin tunani zan iya gano wanene, na farko wannan hasken shi fari ne sol, fawan kuma hasken fatarsa mai yellow yellow ne, Ayaan da jahaan kuma nasu yayi ja haka launin fatarsu, kai wannan fa kamar junaid ne,”  
Tayi maganar acikin zuciyarta, wani tunani ne ya sake zuwa mata, 
Junaid shagwa6a66e ne duk yadda yayi magana ana gane wa, yanzu bari na gwada wani abu a sanina da junaid baida jumuri in ya gaji sosai yaji naƙi bashi amsa dole yayi magana da shagwa6a, 
Murmushi sehrish tasaki ta tsaya riƙe da waist ɗinta tana jiransa ya hasala yayi mata magana, 
Aikuwa maganar sehrish ta tabbata, da yaji shiru shiru bata bashi amsa ba kuma tayi masa shiru, 
Cikin shagwa6a ya buga ƙafarsa tare da cewa” wai ba zaiki yi magana ba, so ki ke ki wahalar dani koooo.. .’  yayi maganar tamkar zaiyi kuka, 
  Fashewa da dariya sehrish tayi cikin tsantsar murna da farin ciki tace ” *JUNAID*!!! Wlh kaine na gano ka ,” tayi maganar da ƙarfi, 
  Wani irin farin ciki ne ya rufe junaid juyowa yayi fuskarnan tasa ɗauke da kyakkyawan murmushi , 
*Zubawa juna ido su kayi suna ta faman sakarwa juna murmushi, don ita sehrish hada dariya sosae Sam farin cikin ta ya gaza 6oyuwa* 😁😁😁
daker suka dakata daga yiwa junansu dariya, junaid yace “bismillah sister tukur ga wuri ki zuna,” yayi da maganar yana nuna garden chairs ɗin, 
  Murmushi sehrish tasaki cikin jin kunyar abunda junaid yace wato Sister tukur, cikin natsuwa suka zauna suna fuskantar junansu haɗaɗɗun kujeru ne irin french bishro design ɗin nan, gabansu akwai table launinsu coffee color, 
   Sai faman sunnar da kai sehrish take yi tana wasa da yatsun hannunta,
   Yayin da junaid ya zuba mata ido,bayan masu ƴan mintina yace “Can we talk”? 
  “Yeah” sehrish ta bashi amsa
Junaid yace “First of all, naji daɗin ganinki as a woman, ina fata ke ma haka? 
Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa “Sosae ma,” murmushi junaid yayi kafin yace “in da gaske ne, to inaso ki ɗago da idonki ki kalli cikin nawa muyi magana, sannan ki cire wannan gashin bakin da cap ɗin nan inaso na ganki da kyau,” 
ɗan waro ido sehrish tayi tare da cewa “In wani ya ganni fa”? 
Junaid yace “ae babu wanda zai zo nan, duk ynx suka dawo agajiye so karki ji komai, 
Ajiyar zuciya tasaki tare da sa hannunta ta cire gashin bakinta, ta ajiye shi asaman table ɗin gabansu, sannan a hankali tasanya hannu, ta zame mayafin da ta naɗe hular dashi, sannan ta zame hular gaba ɗaya, ta ajiye su asaman table ɗin duka, 
Lumshe ido junaid yayi yana kallonta, a yayin da sumar kanta ta soma warwarowa da kanta ta zubo mata har ƙugunta, tayi mata tamkar hijabi, kwantacciyar suma dark black very smooth, 
Cikin sanyin murya ta wanda ya gama kamuwa yace “Masha Allah yanzu nan tukur ɗinmu ne ya koma haka? Ƴar kyakkyawar budurwa,” 
  Yayi maganar da zolaya, fashe wa da dariya sehrish tayi, sai da ta tsagaita sannan ta samun ƙwarin guiwar cewa “I want to ask you something pls,” 
Junaid yace “Ina sauraron ki,” 
ɗan gyara murya tayi sannan tace ” yaushe ne ka gane cewa ni maca ce? kuma sannan ya kaji aranka,” 
   murmushi junaid yasaki kafin yace “Na jima  da sanin hakan, but am sorry to say bazan iya faɗa miki ranar da nagane cewa ke maca ce ba, sai nan gaba, sannan maganar ya naji araina dana gane hakan, seriously i felt so happy bansan ma yanda zan misalta ba,” 
Wani irin daɗi ne ya rufe sehrish sai faman satar kallonsa take tana sunnar da kai,
“I ave a question too,” junaid ya tambaya, 
Cikin sauri sehrish tace “What”?
“It’s just a question pls, don’t feel anything, am… Kece ki ke mun amfani da wayata ko?  Ya tambaya yana kallonta, 
  Wurga ido sehrish tayi ta ɗan kalli ruwan dake gudana wurin, taƙi yarda su hada ido saboda jin kunyarsa,
ƴar dariya junaid yayi kafin yace “tun da bazaki ban amsa ba, bari ni na baki, kece ki ke mun amfani da wayata kina kiran ƴan uwanki, da farko Nasanya security ɗin wayata finger print, wato sai kika rinƙa lalla6owa while i was sleeping kina using da yatsana kina buɗe wa, afterwards dana gane ana mun using  da phone ɗinsa saina maida shi face security nan ma ki kayi kokarin ki sa a face dina don ki bude ko ? Anyi hakan ? 
Ya tambaya da murmushi a face ɗinsa yana kallonta, sai faman sunnar da kai take yi tana dariya, 
Junaid yaci gaba da cewa “ranar dana kama ki a bedroom ɗina, kina rarrafe zaki kin lalla6a zaki gudu, time ɗin na tashi daga bacci, muka haɗa ido dake zaki fice, kawai sai kika fashe mun da dariya ko ba haka akayi ba,’? Ya ƙare maganar tasa da tambaya, 
Hannu sehrish tasanya a bakinta, tana ta faman tiƙar dariya shima kansa dariyar yake yi, 
Bayan sun tsagaita da dariyar tasu junaid yace “bayan nan akwai time ɗin da kina saving ɗinmu abincin dinner, phone ɗina yayi ringing, nayi picking call ɗin kwatsam sai ki kaji muryar Sister ɗinki, wanda hakan yasanya arazane ki ka saki cup ɗin dake hannunki har ki ka 6arawa Ayaan ruwan coffee mai zafi, Anyi hakan? 
Ya sake jefa mata tambayar yana yi mata kallon MAGE TA KAMA 6ERA, 
Cikin jin kunya sehrish tace “Am so sorry pls,” 
  “why are u saying sorry to me sehrish? Ni baki mun laifin komai ba, abun ma sai ya zamar mun kamar drama, naji daɗin hakan,”  ya faɗi yana ci gaba da kallonta,
      After some minutes duk sunyi shiru sai da arinƙa jefa wa juna murmushi ana satar kallon juna, rishi jin abun take tamkar a mafarki wai yau itace tare da ɗaya daga cikin ƴa’ƴan abban sojoji mai sauƙin kai haka, addu’arta shine Allah yasa sauran ma su kasance masu sauƙin kai a duk lokacin da Allah zai sa su gane cewa ita maca ce,” 
     Jin tayi masa shiru yasanya shi sake cewa “a matsayin me zaki ɗauke ni yanzu Aboki ko ɗan uwa”? 
           Sehrish tace “Da so samune duka biyun, I need both,’ 
  Wani irin daɗi ne ya rufe junaid kamar kamar me, ji yake kamar ya rungume sehrish ajikinsa, farin cikinsa sam yagaza 6oyuwa, 
Sun sha fira har wurin sallar magrib sannan suka tsagaita, sehrish ta maida gashin bakinta da hularta duka yadda suke sannan suka kama hanya atare suna ƙara tattaunawa kamar karsu rabu da juna, sai da rishi ta fara shiga ciki da jimawa, sannan junaid ya shiga saboda kar a gansu atare, 
(Guys nima fa sun burgeni wlh, haɗuwarnan ta rishi da junaid ta tafi dani)💋
________________________________
*Dama nace akwai annoucement to gashi, Littafin nan littafi ne mai yawan gaske Kuma idan nace zan datse shi to tabbas zan lalata littafin daɗinshi zai ragu sosae bama zai yi tsari ba don haka Part 3 of this Novel will be paid Book, abubuwa da dama waɗanda basai na faɗa ba Ina fata zaku goyi bayana, Nasan duk ranar dana ce na dakata da rubutun littafin nan babu wanda zaiji daɗi acikin readers ɗinshi don haka muyiwa juna Adalci, Sorry 4 the late annoucement* 😔🙏
Ci gaba
_________________________
Zuba musu ido goggon katsina tayi tana kallonsu ko kyaftawa babu, kamar wadda tayi gamo da aljanu, 
Zaune suke suna facing ɗinta sun matse juna cike da tsoran abunda tsohuwar zata ce musu, 
 Ta jima da farka wa daga bacci amma batasan dasu acikin gidan ba, saboda suna can cikin ɗakin saude suna bacci, ita kuma sauden bata sanar da ita cewa Omar ya sa an kawo wasu ƴara ba sai yanzu bayan sallar magrib ta ke sanar da ita, shine tasa ta kira mata yaran tagansu,” 
“Jahad me yasa take kallon mu? bata son mu ko? Korar mu zatayi ko”? Hosana ce tayi ƙasa ƙasa da murya tana raɗawa Jahad a kunne, 
Jahad tace “nima bansani ba, amma ina tsoran kartace bata son mu, in ta kore mu, ina zamu sa rayuwarmu?   Cikin raɗa suke maganar tasu, duk sai da suka gama raɗe-raɗen sannan su kaji goggon katsina ta fashe da dariya tare da cewa
 “kun ta6a jin inda uwa ta guji ƴa’ƴanta !? Ku fa jinina ne, ƴa’ƴan abusufyan ae ƴa’ƴana ne halak malak,” 
Kallon juna su kayi jin abunda tsohuwartace, atare suka hada baki tare da cewa “ABUSUFYAN kuma wanene shi ? mu bamu son shi ba,’ 
ɗaure fuska goggon katsina tayi tare da cewa “Bansan shashanci in ma zolayata ku keyi to ku daina, ni ba amun irin wannan wasan yanzu na burkice,  ku faɗamin gaskiya ku ba ƴa’ƴan abusufyan bane,? 
 Babu wasa a fuskarta tayi tambayar, 
hankali atashe suka ce “wlh bamu son shi ba, bamu son wa kike magana akai ba, mu yau muka zo gidan nan,” 
Sassauta murya goggon katsina tayi tare da cewa”kuna nufin ku ba ƴa’ƴan abusufyan bane ? Ni zaku raina wa hankali ko? Kubar ganin nafara tsufa da hankali na wlh Wannan furfurar da kuke gani akaina, bata tsufa bace ta arziƙi ce,” 😡 
ta yi maganar tana hararansu, cikin tsananin tashin hankali jahad tace “wlh goggo gaskiya muke faɗa miki, bamu son shi ba, mu ba ƴa’ƴansa bane,”  
Jin yadda jahad ta karyatata yasa ta fashe wa da matsanancin kuka, zaro ido su kayi ganin tsohuwar na sharar kwalla, kuka fa sosai hada jan majina tana faɗin “saboda na fara tsufa kke gudu na ko? ban ta6a tunanin ƴa’ƴan abusufyan zasu guje ni ba, wlh sai na kirasa a waya nasanar masa tashin kunyar da kukayi wa goggonsa wlh baxai ƙyale ku ba…’ 
tayi maganar tana shesshekar kuka abun kamar a mafarki su hosana da jahad suke kallon lamarin, 
  Jin kukan goggo yasa saude fitowa daga kitchen hankali a tashe karaso wa tayi tana faɗin “Subhanallahi goggonmu me nake gani haka kamar kuka a idonki,’ 
  Ƙara fashe wa da kuka gaggon katsina tayi tare da cewa ” saudatu dan Allah waɗannan ba ƴa’ƴan abusufyan bane?  tayi maganar tana nuna su Hosana da hannunta, 
  Sakin baki Saude tayi galala cikin mamakin rigimar goggon katsina, girgixa kai tayi tare da cewa ” wlh narasa meke damunki goggo ! Sarai fa kinsan cewa Uncle abusufyan bai ta6a aure ba ko? wai yaushe ma yayi budurwar ballantana ma aure har akai ga ƴa’ƴa, anya goggo kina shan maganinki akai akai’? 
  Miƙewa tsaye goggon tayi idonta cike taf da kwalla fuskarta a damuje tasa idonta cikin na saude tace” saudatu hada ke za’a ƙaryatani ko? ke ma kallon zararriya kike mun ko? saudatu da hankali na wlh, waɗannan yaran ƴa’ƴan abunsufyan ne, Jini na ne ina ji ajiki na, dan Allah kudaina mun yawo da hankali wlh zuciyata zata iya bugawa in mutu a wurinnan,” 
   Goggo tayi maganar cikin ƙunar rai da jin ɗaci aranta saboda ita harga Allah ta tabbatarwa kanta cewa tagwayen nan ƴa’ƴan abusufyan ne, mutun da bai ta6a aure ba, hasalima ma ba a nigeria yake zaune ba gaba ɗaya, 
   Shiru saude tayi tana kallon goggo dake ta faman kuka kamar ƙaramar yarinya aranta tace “tabbas goggo fa hauka ya tashi gadan gadan, don haka a kunnan babban likita dole nasanar mishi a bincika kwakwalwarta in ba haka ba kawai daga ganin yara sai kice wai ƴa’ƴan Uncle sufyan ne, yau yau ɗinnan fa yaran nan suka fara zuwa gidan nan tab lallai akwai matsala awurin nan……..”, muryar goggonce ta katse ta da cewa 
   “Saudatu kinyi shuru baki ce komai ba? ƴa’ƴan abusufyan ne ko?
   Yarfa hannu saude tayi saboda tama rasa amsar da zata bata, 
Jinjina kai goggon katsina tayi tare da mayar da idonta kansu hosana da jahad waɗanda jikinsu keta faman kerma saboda tsoran tsohuwar don sun lura tana da ta6in hankali, 
Rai a6ace tace  “Wlh ku ƴa’ƴan abusufyan ne !! Ni zakuyiwa karya don kutmar ubanku !! Kunci buhun ubanku ƴan kan uba
 !!! , 
Hankali atashe su hosana ke kallonta, saude kuwa aza hannu tayi akai tana faɗin”goggo dan Allah kidaina !! Kidaina zaginsu mana akan abunda basu sani baaa……
  tunkan ta ida goggon tasa hannu ta buge mata baki, dafe baki sauden tayi don taji zafin bugun, 
 Ci gaba da magana goggon tayi a birkice tana kuka, ” Ae dama nasani ba wanda zai goyi bayana akan magana ta, amma ni nasani wlh ku ƴa’ƴan ZAINABU ne, dama haka uwarku take kamar ku ɗinnan, shegen taurin kai da kafiyar tsiya, kunnan ta kamar na zomo, fitinanniyar yarinya ƙiri-ƙiri ta guji jini na, dama sai da nace mata cikin jikinta na Abusufyan ne amma taƙi yarda ae dama nace mata jiki magayi amma taƙii ji, kunnan ƙashi ko ae ynx nasan taji jiki bawan Allah bai mata komai ba amma taƙisa, wlh cikinsa ne ku ƴa’ƴansa ne amma kunƙaryata ni, ga falo falon kunnuwanku nan irin na abusufyan shima dayake baijin maganata kangararre ne yaƙi jin magana ae gashi nan……
Zuba kawae goggon katsina  takeyi ba ƙaƙƙautawa kai kace radiyon da bata da saiti, notikan kanta sun kwance sai faman zazzaga musu bala’e take yi, tana yi musu magana akan mutanen da basu san da zamansu ba, 
   tashi su kayi atare su ka tsaya suna kallonta haƙika sun tsorata da tsohuwar tuni idonsu ya cicciko da kwalla, 
  Goggon katsina bata dakata da surutun ba har sai da Saude tace “goggon kiyi hakuri dan Allah, nima na yarda cewa su ƴa’ƴan Uncle sufyan ne, sai yanzu na ƙara lura da kamannin nasu dagaske ne abunda kika faɗa, 
  saude na gama faɗan maganar ta kalli su hosana tayi musu alamar su amince suma da maganarta don asamu ta lafa, 
Cikin sauri suka zube saman guiwowinsu agabanta tare da cewa “Dan Allah kiyi haƙuri goggonmu, munyi miki laifi, tabbas mu jininki ne mu ƴa’ƴan abusufyan ɗinki ne, ki yafe mana munsa kin zubda hawayenki,” 
Sanyi goggo taji aranta dama ita burinta kawai su amince cewa su ya’yansa ne, hannu tasa tana share hawayenta, bayan ta kammala ta miƙa hannayenta tare da ruko nasu ta tsayar dasu tsaye fuskarta da murmushi sai kace ba wadda tagama sharbar kuka tace ”  Alhamdulillah har hankali na ya kwanta ynx, amma fa kun wahalar da gaggonku sosae kun sani ina ta faman zubda hawaye na, da ace abusufyan na nan kuma yasan abunda ku kayi ma goggonsa tabbas sai ya muku dukan tsiya” , 
  Sunnar da kai su kayi tare da cewa “ayi mana afuwa goggonmu, bazamu ƙara ba insha Allah,” 
   Murmushi tasaki tare da cewa ” ku koma kuzauna ƴa’ƴana, yanzun nan zan kira mahaifinku a waya ku gaisa,”   🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️
BossLady❤️ Inaso naji ta bakin ku game da annoucement ɗina nasan kowa ya karanta, sannan comment akan page ɗin yau 

Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now!

Back to top button